Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

sbd ita, hakan yasa tace ‘’adda ai ya daina wallahi dama chan stress ne na school activities yayi min yawa yanxu kuwa da akayi hutu kinga na daina kwata kwata’’ jinjina kai kawai amra tayi sannan ta hau kan gadon su ta lulluba sai barci.



Washe gari Thursday ta matsanancin ciwo amra ta tashi wanda ya janyo mata sumewa har sau biyu, dama yawanci haka period dinta ke azabtar da ita, idan azabar tayi yawa sumewa kawai takeyi, salima ne kawai ke kula da ita sai mama rabi mai aiki wadda ke lekowa dubata jefi jefi, haka tayi spending ranar akwance washe gari Friday tadan samu sauki wanda yasa ta fara prepation din competition dinsu na school, dukda tanajin ciwon marar nata amma haka ta daure ta fara practising, sai wajen sha biyu na dare ta gama komai ta rufe books dinta sannan ta kwanta gefen yan uwanta.



Washe gari karfe bakwai na safe daidai ta gama shiryawa tsaf cikin uniform dinta wanda salima ta wanke kuma ta goge mata, saida ta dan shafa powder tayi kyau fess fess sannan ta goga lip gloss kada, tadan fesa turaren ta mai sanyin kamshi sannan sukayi sallama da salima ta wuce wajen haladu wanda ke jiranta, gaishe sa tayi bayan ya amsa aranshi yana yaba kyawawan halayyarta da kannenta ba kamar sauran yaran gidan ba.



Karfe bakwai da rabi ta iso school wanda daga yan class dinsu duka sai malamai biyar da principal din school din, shiga cikin school bus dukkansu sukayi sannan suka kama hanyar makarantar NTIC, agaban parking space dake cikin compound din school din daga gefe sukayi parking inda sukaga hadaddun school buses suma suna sauke student din makarantu aciki, anatse su amra suka fara saukowa suka jeru waje daya gwanin burgewa, saida suka jira head of school dinsu hajiya abida da mijinta suka iso tukunna suka kutsa kai cikin school hall din inda ake event.

Tunda suka shiga school din suke ta faman kalle kalle, wato makarantar tayi mugun haduwa sosai, babu hayaniya kwata kwata sai sautin muryoyi da mic daga cikin hall din, anatse suka fara shiga ciki inda ake welcoming dinsu sannan aka basu sits da table wanda aka saka tag din school dinsu, zama sukayi na dan lokaci suna kora ruwa da juice da aka aje akan tables, karfe tara daidai kowa ya hallara, makarantu hudu cur, ko wacce school da garzo ko gwarzuwar su anan aka fara kiran sunayen participant, da yan NTIC aka fara, nan aka kira mutun uku sannan suka hau stage dinsu wanda shima da tag din school dinsu akai sai aka kira leader international school, bayan gabatarwa aka fara da first set of two schools din, tambayoyi akayi masu na wasa ‘qwaqwalwa sosai guda uku, daga bisani aka basu two minute each suyi solving,lokaci nayi aka karbi result din su, bayan yan mintuna judges sukayi announcing winners, tashin farko aka watsar da leaders school, bayan Yan mintuna kadan aka kira next set of schools, saida aka fara kiran aero school sannan aka kira makarantar su amra wato ar-rahman, anatse suka fara fitowa aka basu nasu questions din, after two minutes kuwa aka karbi results dinsu sannan aka mikama jugdes, result din da judges suka fada ya matuqar bama mutane mamaki sbd duk cikin schools din an dauka sune zasuzo ah karshen baya wato Yan ar-rahman school sai gashi sun samu point da yawa, sauka sukayi sannan aka kira yan NTIC da kuma Yan Ar-rahman wato school dinsu amra, anan take kuwa suka tapi stage, saida suka tsaya tukunna aka fara masu questions, first attempt kuwa dukkansu suka samu same points, ganin haka yasa aka kara basu mai zafi sosai, ganin haka yan NTIC suka fara cije hakora, time yana clicking kuwa aka karba result, kallon mamamki kowa yake ma yan Ar-rahman school sbd jin cewa sune winners, amra kuwa dadi kamar zai kashe ta because tayi contributing sosai, bayan an salami yan NTIC sannan aka dawo kan yan Ar-rahman nan aka shaida masu ana buqatar gwarzuwa daya acikin school din, wato zasuyi competing against each other, nan aka shiga bawa kowacce question dinta sannan aka umarcesu dasu rubuta ajikin paper, abinda basu sani ba shine same question aka basu kuma answer question din yana da wuya sai idan mutun ya kasance mai qwazo sosai very smart sannan zai iya ansa question din, ahankali presenter ya fara karban ta farko wadda ake kira da fadila,anan ya fadi ansa data rubuta anan take kuwa judges sukace wrong ansa, next student kuwa mai suna hamida itama aka fado nata,anan take judges sukace wrong, ahankali presenter ya karasa wajen amra wadda itace last, kallon paper dinta yayi sannan ya kalleta, ahankali ya fada ansa dinta ay kuwa nan take judges din sukace correct, tafi aka fara yan school dinsu amraa me zasuyi banda ihu don murna, kowa murna yake and kowa is so proud of her, ahankali aka umarci sauran da su koma anan kuma akace amra ta tsaya, nan shugabanni suka fara congratulating dinta murna ma ya hanata dago da kai ta kallesu, daya bayan daya aka dunga zuwa ana congratulating dinta, maza suna bata hannu mata kuma suna rungumeta, jinta ajikin wata mata wadda kamshin turaren oreal ya cika duk wajen sannan kuma wani connection me sanyi ya ratsa sakaninsu yasa amra dagowa ta kalleta, tana sanye da wani tsaddaden lace wanda akalla zaikai 300k anyi mata dinkin bubu, fuskarta fara sol tasha dan cute lipstick fuskarta dauke da murmushi, ‘’congratulation beautiful you’re re such a genius, I’m impressed, infact I am so surprised because this question is the hardest question that only a certified phd holder can answer it, weldone my dear Allah ya maki albarka,’… wanni irin nutsuwa da sanyi dadi ya sanya amra kasa daina kallonta, saitaji kamar ammin ta ce ta rugumeta, ahankali ta fara Magana ‘’Thank you so much ma,’’murmushi matar tayi mata.

Free page….





Chapter 33-34



Wucewa matar tayi sannan ta zauna a high chair domin tana daya daga cikin manyan guests, kiran presenter tasa akayi, bayan yazo da girmamawa ta mashi magana cikin sirri san nan ya wuce stage, anatse matar ta tashi ta futa daga hall din fuskarta dauke da murmushi, bayan futarta presenter ya fara bayani kamar haka ‘’muna farinciki zuwan kowa da makarantun da suka halarci wannan grand competition din sannan yanxu zamu fadi kyautar da makarantar da taci wannan competition zata samu hade da gwarzuwar data zo itace ta farko, each participant na school din ar-rahman yana da kyautar dubu dari biyu sannan school management din ar-rahman ta samu kyautar miliyan biyar domin bunqasa ilimi acikin makarantar daga karshe kuma mss amra ta samu kyautar scholarship a UAE (united arab emirates) sannan anyi sponsoring karatunta kona shekara nawa harta gama tare da accommodation, sannan tanada damar zabar duk makarantar da takeso ah uae, daga karshe kuma ta samu kyautar waya da check na miliyan biyu daga anonymous guest, mungode da zuwanku duka”.

Tunda amra taji wannan batu suman tsaye ne kawai tayi, she can’t believe it, wai ita aka yima wannan kyauta, hawaye ne suka gangaro afuskarta, daga bisani ta fuskaci alqibla tayi sujjada tare da godiya ga Allah, saida aka bama kowa kyautar sa sannan suka wuce school, anan ta samu haladu yazo yana jiran isowarta, ganin irin farin cikin da take yasashi tambayarta, murna ma kadai ta hanata fada mashi, saida suka iso gida kuma hankalinta ya tashi tunawa da yan uwanta, daga karshe dai ta kawar da baqin cikin ta karasa cikin dakinsu, koda ta isa ciki akwance ta samu salima tana barci abinta salim kuwa yana gefenta yana wasa da yar nokia amra wadda take bari agida, ganinta yasashi tasowa har gabanta yace ‘’ sannu da dawowa adda’’ kitchen ya nufa ya kawo mata ruwa lokacin ta shiga wanka saida ta fito ta nemi abinci tukunna ta tashi salima, ‘’albishirinki yar kanwata?” zumbur salima ta zauna sannan tace adda kicemin kinci kawai nama sani’’ girgiza mata kai amra tayi, ay kuwa aguje salima ta tashi tana rawar murna farinciki duk ya lullubeta, dakatawa tayi sannan tace adda fadamin kyautar da suka baku, aykuwa nan take fuskar amra ta chanza, tagumi tayi sannan tace scholarship aka bani, ganin abun farin ciki amma kuma amra ta bata rai yasata zama kusa da ita sannan tace ‘’adda scholarship fah kika samu kai alhamdulillah but why do you look so sad?’’ shuru amra tayi idonta na kawo ruwa, kollon salima tayi tace ‘’salima scholarship amma ba’a nan ba’’ jin haka yasa salima dariya sannan tace ‘’to sai me adda,inace idan kinje zaki dawo hutu ko and besides mu na tare mana tunda ba kasar zaki bari ba’’ kallonta amra tayi sannan tace ‘’ah Dubai ne fah salima’’ …zaro ido salima tayi sannan daga bisani kuma ta daka tsallen murna sannan tace wayyo allah na dadi kasheni, adda na dubai fa kikace wayyo Allah alhamdullih’’.. mamaki ya hana amra rufe baki ganin qanwarta na farin ciki, farin cikin abunda zai raba su wanda bazata taba yarda haka ta kasance ba, kallonta amra tay sannan tace ‘’salima kina tunanin zan karba schorlaship dinnan ne?, inaaa..ay bazan karba ba, bazan iya rabuwa dake da salim ba, zandai karbi wayarda aka bani sai cash din 200k din da aka bama kowa each sannan sai check din 2m din amma gaskia bazan karba schorlaship dinba,’’ tashi tayi kawai ta fuce salima kuwa dadi kamar ya kashe ta.



Washe gari Sunday amra bata cikin walwala kwata kwata salima kuwa sai tausasa ta take yi akan babu komi ta karba schorlaship din watakila shine zai zame masu alkhairi don idan ta gama karatun kamar sun tsallake baqar ukubar da suke ciki ne ayanxu, zama tayi kawai tana sauraron salima amma bata jin zata iya amincewa. Bangaren Yan gida kuwa babu wanda yasan maganar scholarship din sai daddy wanda yana kallon news da safe yaga program din da akayi na grand Competition din NTIC kuma ya ganta lokacin da ake bata grand kyaututuka daga karshe dai dariya yayi aranshi yana cewa ‘’this is the beginning’’.



Free page….



Chapter 35-36



Washe gari Monday da kyar salima tasa amra ta amince domin zuwa school ta karbo kyaututtukanta dukda tace bazata karba scholarship ba.

Futowa tayi haladu ya dauketa har school dinsu, ba laifi da akwai mutane a school din wanda rabi teachers ne, wucewa tayi wajen head office bayan tayi sallama, kallonta mrs abida tayi fuskarta dauke da murmushi sannan tace ‘’my beautiful student, I’m so proud of you my dear zoki zauna kinji’’… samun guri amra tayi sannan ta gaisheta sannan ta fara mata bayannin cewa bazata karba scholarship ba, tambayrta mrs abida tayi dalilinta, nan ta shaida mata cewa bazata iya tapiya tabar kanneneta ba, sanin irin rayuwar da su amra keyi ah gidan ruqonsu yasa mrs abida ta gane inda zancen amra ya nufa,



nunfasawa kawai tayi sannan ta fara Magana ‘’ amra inason kisan cewa karatunki yana da matukar amfani bake kadai bama harda kannenki, kece uwarsu kece ubansu yanxu idan baki nemi ilimi ba dame zaki taimaki kannenki harsu dogara dakai, shawara zan baki kamar yanda uwa zata bama yarta, idan har kinason cire kannenki daga rayuwar da kuke ciki to ya zama dole ki tattara courage dinki ki natsu ki kwantar da hankalinki, ki karba scholarship dinnan, dama ce kike samu don wallahi idan kika bari ta kufce maki bazaki kara samun kamarta ba, shawara ce na baki, sannan if you’re worried about siblings dinki, Allah yana tare dasu koda kina nan ko baki nan idan har abu zai samesu toh duk isarki duk karfinki bazaki iya hanawa ba, sannan nima zan taimaka maki wajen kula da kannenki da harkar iliminsu kinji ko’’

girgida mata kai tayi alamun gamsuwa sannan tace to shikenan ma’’..

sundan tattauna daga bisani ta bata check dinta na 2m da cash sai latest iphone xmax dinta, godiya amra tayi sosai, daga bisani mrs abida tace ‘’kije kiyi shawara sannan ki fada ma mai riqonku duk yanda kika yanke saiki dawo koki kirani awaya sai mu fara processing komai kinji ko’’ godiya amra tayi mata sannan ta wuce ta koma gida.



Wunin ranar da tunani batun scholarship dinta ta wuni daga karshe ta yanke shawarar tunkarar daddy tukunna idan ya amince fine idan ya hana babu yanda zatayi don shi ne wanda kawai zaiyi sponsoring upkeep dinta.



Dare nayi wajen karfe tara bayan ta daidaici lokacin hutawarsa sannan ta wuce sama domin ganin daddy, ahankali tayi sallama yana zaune sitting room dinshi shi kadai yana cin dambun nama yana kallon news, ahankali ta kutsa kai ciki, bayan ta gaisheshi sannan tadan nunfasa ta fara Magana ‘’ daddy daman munyi end of the year competition a school dinmu kuma nice na zo gwarzuwar shekara sannan na samu scholarship da kyaututuka’’… kallonta yayi sannan yace ‘’okay’’… shuru ta danyi sannan tace ‘’daddy daman naga tunda wannan opportunity ne mai kyau yasa nace bari naji ta bakinka ‘’… kallonta yayi sannan yace ‘’are you planning on accepting the schorlaship?”girzigiza mashi kai tayi sannan yace ‘’okay to naji harda accommodation ko? To shi kuma expenses dinki kuma fah da upkeep waye zai baki ko kudin da suka baki zai Isheki shekarun da zakiyi? Shuru tayi sannan tace ‘’daddy daman ina neman taimakon wannan awajen ka’’… kecewa yayi da dariya sannan yace zan iya taimakon ki yar badaru amma bashi zan baki,saboda dawainiya da nayi daku kawo yanxu nayi na Allah yanxu kuma lokacin biyan bashi yazo’’ shuru tayi hawaye na bulbulowa afuskarta wai wannan wan mahaifinta ne mafi soyuwar babanta’’ shuru tayi daga nan kuma wata jarumta tazo mata lokaci guda ta kalleshi har cikin idonshi tace ‘’na amince duk abinda kayi mana zan biyaka koda kuwa zai zama karshe nunfashina, saidai alfarma daya inason kannena su kasance kamar kowa agidan nan”. Tana kaiwa nan ta fuce, kwata dady yayi aranshi yana Kara jin tsanar yaran.



Amra kuwa Daki ta dawo inda ta samu salima nacin goruba anatse amra tayi mata bayanin amincewar ta wanda hakan ba karamin dadi yayima salima ba saidai bata gaya mata yanda sukai da daddy ba.

Free page….



Chapter 37-38



The next day,

Tana tashi ta kira mrs abida a yar wayarta ta shaida mata komai, mrs abida taji dadi sosai da amra ta yarda, nan mrs abida ta shaida mata cewa zasu fara processing passport dinta inda ta umarceta data zo school on Monday don ta kaita ayi mata passport, godiya tayi mata sannan sukayi sallama.



Komai dai yana tafiya daidai don har anyi ma amra passport yanxu visa ake jira saidai hankalinta atashe yake jin anytime visa ya fito za’a saya mata ticket daman already an shigo new year.



Yau visa amra ya fito sannan ayau ta fara processing komai na makarantar da zataje wato Middlesex university dubai inda zata karanta nursing, an shirya mata komai harda accommodation tana isa chan school kawai zataje tayi registrating sannan sai lectures.



Allah sarki amra za’a shiga sabuwar rayuwa……..😭



Something is waiting for amra, this is just the beginning, Amra is approaching her destiny…………………….✍️







Yau saura kwana biyu tafiyar amraa,tana kwance agadon su babu abinda take sai tunanin tafiya, yanxu shikenan haka zata tafi tabar kannenta, wazai tsaya masu, waye zai kula mata da su, kuka ne ya kufce mata, jin sallamar ishaq yasa ta saurin goge hawayen daya zubo mata,

kallonta yayi sannan ya shugo fuskarshi dauke da murmushi yace ‘’ sis nazo nayi congratulating dinki daxu nakejin salima da mama rabi suna hirar ah kitchen, yanxu sis ni baki daukeni dan uwanki bane banida darajar da za ah fada min wannan kyakkyawan labarin na tafiyar ki school, gaskia banji dadi ba sis’’, mumushin yaqe amra tayi sannan tace

‘’I’m so sorry bro, wallahi duk na shaáfa ne duk tafiyar ya fita kaina, ishaq bansan ya zanyi ba inajin tsoron barinsu salima su kadai, ishaq dan Allah ina neman alfarma awajen ka don Allah idan bana nan ka kula min da kanne na nasan kai kadai ka damu da walwalar mu’’



takai karshe hawaye na zubowa akan fuskarta, lallashinta ishaq yayi sannan yayi mata alqawarin zaiyi kokari wajen kula da kannenta, sallama yayi mata sannan ya fuce.



Shugowa dakin salima tayi da sallama sannan tace adda ki tashi mu shirya mu tafi domin ki samu ki bude account din sannan mu wuce kasuwan. Kasuwa sukaje inda anan amra ta sayama kanta kayan barci sabbi dasu bra da panties daidai kudin su masu arha sannan tayi ma su salima yan kananun sayayya wanda zaiyi masu amfani koda ace batanan, duk wannan hidimar da kudinda ta samu sukayi, wucewa sukayi wajen masu abayas, anan ta saya kala biyar masu kyau daidai kudinta, sannan suka wuce bank domin bude account, daganan suka tsaya shagon wayoyi na zamani anan ta bada karamar nokia ta cika da kudi suka musanya da android mai kyau domin tanason ta barma su salima domin jin lafiyar,wunin ranar awaje sukayi shi.



Bayan sun koma gida sai alokacin ta tuna da sabuwar wayarta wadda tundo tazo da ita ta aje while kudin da ta samu wanda aka bata cheque dinshi ta bama mrs abida ta aje mata

ko zata buqata nan gaba ko kuma idan kannenta zasu buqata dukda an diba kusan rabi wajen yi mata visa da flight ticket.



Yau thurday gobe Friday jirginsu zai daga wajen karfe uku na rana, kwata kwata bata cikin nutsuwarta lafewa tayi akan gado zazzabi yana neman lullubeta, salima kuma tana zaune tana shirya mata kayanta ah cikin akwati, saida ta hada mata komai duka yan kayayyakin ta sai yar jakar da ta saya mai chain guda biyu masu kyau da abayoyin da ta sayo, bata wani kwasa wasu kaya masu yawa ba.

Suna nan zaune taji shugowar daddy saida ta tabbatar ya huta sannan ta wuce sama part dinshi, kodata shiga yana nan zaune kamar kullum yana waya, karasawa tayi saida ta bari ya gama sannan suka gaisa nan ya miqa mata wasu papers yace tayi signing, karba tayi ya fara signing bayan ta gama ta miqa masa,

Karban papers din yayi yana murmushi ya bata wani envelop yace ‘’ first upkeep dinki ne wannan na rubutashi acikin contract da kikayi signing yanxu sannan duk sanda kika buqaci kudi zan baki idan har kika gama makaranta baki biyani ba acikin gadon ku Zan dauka wato gidan ubanku wanda yake Abuja a maitama’’



kallonshi amra tayi afurgice sannan tace ‘’amma daddy ba haka mukayi dakai ba, baka cemin zaka musanya yarjejeniya da gidan gadon mu ba shi kadai muka mallaka ni da qannena ,’’ baiko kalleta ba yace zaki iya tafiya



kuka ne ya kufce mata kawai ta fice daga dakin.

Koda ta koma daki saita fara dana sanin amincewa da batun biyan bashi da dady yace zatayi ashe tun farko manufarshi Kenan abinda yakeso, shiyasa yayi sauri ya amince da tayi mashi maganar school din, kuka kawai take yi koda salima ta shugo ta ganta saitayi tunanin kukan tafiyar da zatayi ne gobe, zama tayi gefenta tausayi yayarta ya gama lullubeta, rugume juna sukayi sai kuka, jin alamun shugowar salim yasa suka tsagaita don kar ya gane me suke ciki gudun karya shiga damuwa sbd ciwon zuciyar shi, Haka suka kwanta rungume da juna.

Cikin dare kuwa amra kamar an tsikareta ta fara jn wannan ciwon bayan nata dai alamun zata fara period dinta, tashi tayi ta nema Panadol kawai tasha, cikin ikon Allah barci ya dauketa.



Free page….



Chapter 39-40



Koda ta tashi da safe da ciwon ciki ta tashi kadan kadan kuma yau ta kasance ranar tafiya, anatse take yin komai don duk jikinta yayi sanyi, karfe bakwai daidai ta wuce toilet, tayi wanka sannan tazo ta zauna gefen su salima wanda bancin su kawai suke, zuba masu ido tayi sannan tace ‘’kannena banida kamar ku duk duniyar nan, zanyi kokari nayima kaina alkawari zan kula daku kuma insha Allahu zanyi ilimi na fitar daku daga qangin rayuwar nan insha Allah, salima wadda tashinta Kenan ta bude idununta ta kalli yayar ta wadda qwalla shar akan fuskarta tace ‘’adda dan Allah ya kamata ace kin daina koke koken nan saikace mutuwa zamuyi idan kika tafi, nayi maki alkwari wallahil azeem bazan taba yin abinda zaisa ki damu ba idan kika tafi, zan kula da salim zan zama uwa agaresa zan kula dashi kinji adda kidaina damuwa dan Allah”… dakyar salima ta lallashe ta sannan itama ta wuce don tayi wanka.



Bayan salima ta fito,kimtsawa itama tayi sannan suka wuce kitchen, a tare sukayi breakfast da mama rabi inda tayi ma amra fada akan ta kula da kanta da mutuncin ta sannan tayi Ma amra alkwari kula dasu salima.



Daki suka koma nan salima ta tashi salim ya shiga wanka ita kuma amra ta dauko sabuwar wayar ta sannan tayi exchanging number da sabon sim din data sayama su salima, ganin karfe sha daya saura yasa ta saka sabuwar abayar ta sannan ta wuce sama domin yima masu gidan sallama, koda taje part din haj kareema batama tsaya ta saurare ta ba ta koreta, fitowa tayi ta wuce part din Haj labiba, koda taje bangaren haj labiba kuwa, ba laifi tadan kulata hardasu Allah ya kiyaye,…direct kasa ta sakko abinta sannan ta koma wajen salima koda ta shiga dakin azaune ta ganta, hannunta dafe da cikinta, karasowa tayi tana tambayarta ko bata da lafiya, ganin hankalin yar uwarta zai tashi yasa salima saurin yin yaqen wahala tace ‘’laa adda dan period pain ne yama daina’’….magani amra ta bata tasha sannan itama ta shirya cikin atampa yellow doguwar riga. Wardrop dinsu amra ta bude nan taga envelop din da dady ya bata, daukar envelop din tayi sannan ta bude, kudi ne aciki dollars wanda akalla zaikai 5k dollars ajiyewa tayi aciki yar chain handbag dinta sannan ta dawo daki ta zauna, suna nan zaune ishaq yazo suka dan taba hira bayan kiran sallar zhuhr ya wuce masjid su kuma suka tada kabbarar sallah, saida suka idar sannan sukayi addua ita da kannenta, salim kuma ya fara kiciniyar fitar mata da akwatinta, lokacin it’s about 2pm batason tayi latti shiyasa ta shirya futa da wuri sbd flight din Karfe uku ne. Koda suka fito bayan sunyi sallama da mama rabi harda yan hawayenta sannan ta bata farar kasar data saya mata don kartayi kewa sannan suka karasa wajen haladu driver, shiga cikin napep din sukayi saiga ishq, shima shiga yayi domin yin rakiya.

Direct Aminu kano international airport suka wuce inda anan suka hadu da mrs abida wadda zata bata passpost dinta da visa dinta da komai na school, godiya tayima mrs abida sosai saboda tayi mata qoqari sosai sannan ta juya wajen kanneneta, salim wanda idonshi ya ciko da kwalla ya kalleta yace ‘’addana yanxu tafiya zakiyi ki barni ko’’ kallonsa tayi cike da kauna da kewarsa sannan tace ‘’ my salim karkayi kukakaji ko I promise to buy you a big army jet toy and I will come back soon so that I can bring you and salima kaji ko ‘’… dariya yayi jin tace zata dawo ta tafi dashi, kallon salima tayi sannan tace ‘’salima dan allah ki kula kinji, ku dinga kirana idan kuna buqatar wani abu sannan ga ishaq nan zai kula daku kinji sannan duk wani abu dake damunku ga mrs abida ga mama rabi ga ishq na tabbatar zasu kula daku’’… rungume kannenta tayi sannan ta sakesu ta wuce da sauri cikin airport din sbd hawayen dake shirin zubo mata don idan Har ta tsaya suka fara koke koken nan toh fa tafiyar nan bazata yiwu ba ganin kusan Karfe uku ta kusa yasa suma suka wuce gida kowannan su dauke da kewar ta,… ita kuwa amra kuka sosai takeyi harta iso counter din emirates, anatse ta gama komai ta wuce da luggage dinta, abinma yazo mata da sauqi sbd sun taba tafiya lokacin iyayensu na raye lokacin sunje morocco wajen uncle din mamansu. Koda ta wuce ciki wuri ta samu ta zauna domin jiran jirginsu, ko five minutes batayi ba da zama aka kira jirginsu nan kowa ya Tashi domin yin boarding saida suka gama tukunna suka wuce harabar jirgi, anatse take tafiya sanye da abayarta wadda suka sayo black, tayi mata tsam gata dama akwai diri sai tabi shape dinta tayi
DOWNLOAD
DOWNLOAD

7 Comments On AUREN KATIN KASA
avatar
salma-6

10 months ago

Reply

wonderful

avatar
salma-6

10 months ago

Reply

wonderful

avatar
fatima-7-2-5

9 months ago

Reply

I need complete one

avatar
fatima-7-2-5

9 months ago

Reply

I need complete one

avatar
aisha-2-9-6

6 months ago

Reply

I need complete pls

avatar
aisha-2-9-6

6 months ago

Reply

I need complete pls

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to aisha-2-9-6

You can only get the complete by purchasing it through the Author

Please Login or Register in order to submit comment