Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

sake kiran sunana sannan na juyo ina share hawaye

"Zinatu me kika zo yi a nan?" Ya tambayeni har yanzu da mamaki a fuskarsa.

Dabara ta zo min na ce "Aiki na zo nema".

Sai ya bud'e baki da mamaki ya ce" aiki kuma? To an d'auke ki?"

Na girgiza kai alamar a'a

Ya ce"banda shirme ki taho neman aiki ba tare da shawara ba? Kuma ba jiya na ji ana zancen kayan lefenki ba? Ko kuma shi Habib d'in ne ya ce ki nemi aikin yi kafin auren?"

Na cigaba da hawayena,ba tare da na ba shi amsa ba. Sai ya wuce ya barni tsaye ina goge hawayen

To bayan na fita daga wurin a maimakon na yi gida,sai na yi 7:30 restaurant,ina ta rarraba ido bayan na shiga wurin,sai na je wurin wani da nake kyautata zaton ma'aikaci ne,tunda ga shi da uniform me d'auke da sunan wurin,na yi masa sallama ya amsa

Sannan na ce"don Allah zan iya ganin manager?"

Ya ce"e ba matsala,ga office d'in shi can".

Na shiga k'ofar da ya nuna min da sallama,aka amsa ana yi min izinin shigowa,wani matashi na gani kwance akan doguwar kujerar dake office d'in

"Hajiya barka da zuwa" Ya fad'a ya na tashi zaune

"Barka" Na ce,ina zama a wata kujerar

Na ce"alfarma na zo nema"

Ya ce"to,ta mene?"

Na d'an cije baki kafin na ce"don Allah aiki nake nema a wurin nan".

Ya ce"tabb! Aikuwa baiwar Allah, ba mu jima da k'ara ma'aikata ba,yanzu dai sun wadata gaskiya ba ma buk'atar k'ari".

Na yi saurin fad'in"don Allah ka taimakeni,ko da shara ce ko wanke-wanke"

Ya ce"zancen kike so"

Na tausasa murya na ce"don Allah ko kyauta ne ni zan dinga aiki,idan ya so duk wata ka dinga rik'e albashina,na bar maka...".

Ban k'arasa ba ya tareni"ok, ba sai ta kai nan ba,zan iya baki aiki,amma fa ba wanda kike zato bane idan za ki iya duk wata za ki samu kud'i fiye da zaton ki,amma nima za ki na bani wani abun k'arshen wata"

Na yi saurin fad'in"e na yarda, in dai a wurin nan ne".

Ya ce"a anan ne ba matsala.Wurin namu b'angare biyu ne,akwai wurin da masu kud'i suka fi zama idan sun zo cin abinci,to za mu saka ki a cikin wa'inda za ki na kai musu abinci,wasu kuma sukan buk'aci wata ta zauna ta tayasu fira,ke wani ma idan firar ta yi dad'i har ya buk'aci ki raka shi wani wurin,to ta nan ne ake samun kud'i daga hannunsu,ga kuma albashinki me tsoka,dad'in dad'awa ma ku da kayan gida za kuna zuwa,amma fa sai kin kula da kwalliya mai d'aukar hankali".

Na jinjina kai bayan na gama sauraron sa,na ce"babu matsala zan yi".

Ya ce"yawwa! Amma dutyn dare za ki na yi,saboda na ga kina da kyau sosai,Allah yasa dai za ki iya aikin".

Na yi murmushi na ce"kar ka damu zan iya.Yaushe zan fara zuwa?"

"Tun daga yau" Ya bani amsa,sannan ya tambayi cikakken sunana,na fad'a masa,ya tashi ya rubuta a wani littafi,mu ka yi musayar lambar waya sannan ya ce zan iya tafiya.

Na yi masa godiya,na fito daga wurin ina jin wani farinciki sosai.

Yanzun ma ba gida na yi ba,kasuwar sabongari na wuce na yi siyayyar kayan kwalliya kala-kala da turaruka masu k'amshi,domin inganta aikina.Gidan Ummi na wuce kai tsaye,bayan na gaisheta na tashi na yi alwala na yi sallar azhar,don lokacin k'arfe d'aya saura kwata, ta zubo min abinci na ci kad'an na tashi zan tafi,ta ce min"kin ga kayan naki kuwa?"

Na gyad'a mata kai,alamar e,ta na murmushi ta ce"Habib ya yi k'ok'ari sosai,Allah dai ya baku zaman lafiya".

Ban amsa ba na fice ina yi mata sai gobe.


To daga nan kuma gidansu Kamisu na wuce,wani a k'asan layinmu da mu ke mutunci da shi,na yi sa'a kuwa ya na nan,zaune akan benci na tadda shi a k'ofar gida,na zauna a bencin nesa da shi,ina tambayarsa ya garin

Ya ce"normal wallahi,kin yi wuyar gani, sai jiya nake jin ashe auren ya kusa?"

Na yi murmushi na ce"haka aka ce".

Ya ce"a,ban gane haka aka ce ba?"

Na yi y'ar dariya na ce"share kawai,kamar na ji ance k'anwarka ta na yin lalle ko?"

Ya tab'e baki ya ce"wai Nana? Ko yanzu ma shi na fito na barta ta na yi"

Na ce"yawwa! So nake don Allah, d'an kad'an za ta yi min"

Ya ce"ok,mu shiga to"

"A'a,ta fito dai ta min,sauri nake".

Na fad'a ina d'akko wayata da ta fara ringing. Habib ne me kiran,na d'aga,bayan mun gaisa ya ke ce min yau zai shigo da daddare,na ce masa a'a sai dai da yamma,don ina da abin yi da daddare,ya amince muka yi sallama

Na kalli Nana dake tsaye na ce" yawwa Nana,kinga ba me yawa bane,da na iya rik'e lallen ma da kaina zan yi, harafin (S) kawai za ki zana min babba a nan"

Na yi maganar ina nuna mata bayan hannuna.Nana ta zauna a benci nima na zauna,ta zana min kamar yanda na buk'ata,sannan ta cike tsakiya da jan rani,hannun ya yi kyau sosai kuwa,na mik'a mata d'ayan na ce shi kuma ta zana min J.S,nan ma ta zana min,sannan ta saka min a y'an yatsuna ,na yi mata godiya na ce ta zuge jakata ta d'auki d'ari biyar,ta ce a'a na bar shi,ta shige gida.

Kamisu ya kalli lallen ya ce"amma Zinatu na ga dai sunanki daga Z ya fara".

Na yi murmushi ina kallon hannun da na shanya shi s titi na ce"hmm! Share kawai Kamisu,wai ka ji y'an drugs sun k'wamushe Salisu ko?". Daga haka mu ka shiga wata firar.



Da yamma Habib ya zo kamar yanda na ba shi lokaci,ya kwashi surutun sa ya k'ara gaba,don ni kam duk rabin hankalina ya na ga yanda aikina zai kasance,ya ce dai da daddare amma ban san ko k'arfe nawa ake tashi ba,yanzu idan za a kai dare sosai wace k'aryar zan yi wa Baba akan fita ta kullum? Wannan tunanin ya d'an sanyaya jikina,amma fa bai canza min k'udirina ba.


Ana fara kiran sallar isha'i,ina kammala shirina,doguwar riga na saka dama duk ta fi burgeni cikin kayana,na zauna na rangwad'a kwalliya,na nad'e kaina da mayafi kalar takalmin da zan saka,na baza turare bayan humrar da na yi wankanta,lokaci-lokaci nake kallon k'unshin hannuna na yi murmushi, kamar dai an bani tabbacin yau zan had'u da shi,na saka takalmina me tudu,na rayata jaka y'ar k'arama na fito

Mama Saude da ke kwashe tuwo ta bud'e baki ta na kallona,na tsuke fuska ina shirin wuceta na ji ta ce"Allah me iko! Zinatu wannan kwalliyar fa? To ko dai dawo da bikin yau aka yi bani da labari?"

"Wurin dinner k'awata zan je" Na fad'a don kar ta had'ani da Baba,na fice daga gidan cikin sauri-sauri.
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_


BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_


*&þFIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION&þ*


Page 7




Ina zuwa manager ya had'ani da wani,ya kaini b'angaren da aikina ya ke,ya na ta yaba kyauna,ni dai binsa kawai nake ina k'arewa wurin kallo,wani holl ya kaini,na ga y'an mata wasu na girmesu wasu sun girmeni,ga kuma sa'annina duk sun ci kwalliya su na zaune,wasu na fira,wasu na danna waya. Wata ya nunawa ni ya ce ta koya min yanda zan gudanar da aiki.Ta matso kusa da ni ta na murmushi ta fad'a min komai,sannan ta d'ora da fad'in"akwai Oga Salim,shi ne me wurin,shi ma ya na zuwa wataran,kuma be cika cin abinci ba idan ya zo,shi ya fi yin shaye-shayen shi,da yake d'an shaye-shaye ne".

Sai na ji kalmar shaye-shayen har cikin raina,na ji ban ji dad'i ba a ganina Salim ya wuce ana danganta shi da wannan kalmar mara dad'in ji,to amma ya zan yi? Tun da halinsa ne dole a fad'a

"Allah ya shirya shi dai" Na fad'a ina sauke numfashi

Ta ce"hmm! Ai ni idan ya zo har na tsani a turani kula da shi wallahi"

"Kula da shi,sai kace wani jinjiri?" Na fad'a a zuciyata

A fili kuma na ce"to ya ake kula da shi?"

Ta ce"ai idan mutum ya shiga ba ya barin d'akin har ya tafi,saboda kai za ka rik'e masa d'an farantin da zai dinga karkad'e tokar sigarin da zai sha,kuma kai za ka had'a masa lemo da maganin tarin nan,idan zai ci abinci sai ya fad'i wanda yake so,ka kawo masa,ga shi ba ya son kallo,sai dai ka duk'ar da kai,ga warin taba shiyasa duk muka tsani a tura mu idan ya zo"

Na jinjina kai,ina mamakin wannan mulki irin na Salim,sai dai sosai hakan ya min dad'i,ko banza zan jima ina ganin shi,kuma zan samu hanyar shigar da kaina cikin sauk'i,na yi farinciki da ba sa son zuwa,ni kam ba warin sigari ba ko na giya ne zan jure.

Muna nan zaune aka yi kiran mutum uku,ni dai ina ta raba ido da fargaba,tunda na ga abun zab'a ake yi,kuma na ga kwalliyata duk ta fi tasu kyau,hakan ya b'ata min rai kad'an.Me kiran mutanen ya na sake shigowa kiran wata na yi sauri na tashi ina fad'in"kai! Ni ce zan je"

Ya ce"ai ke da Oga na yiwa tanadi,amma taho idan kin matsu"

Na yi saurin komawa na zauna na ce"a'a,shikenan zan je wurin ogan"

Ba a jima ba kuwa ya ce na fito,Oga ya k'araso.Na tashi na bi bayansa,sai kuma na ji wata fargaba ta dira a zuciyata,na fara hasashen watak'il Salim ya na ganina zai koreni daga aikin,wannan tunanin ya sanyaya min jiki,haka dai mu ka k'arasa har wani d'aki,ma'aikacin ya ce na shiga yanzu zai shigo

Na hau bin d'akin da kallo bayan na shiga, kujera ce zaman mutum uku,sai wani k'aramin firji da kuma wata loka y'ar k'ara,ga tebur a gaban kujerar me d'auke da k'aramin faranti me kyau sai walwali ya ke,wanda na ke kyautata zaton shi ne na zuba tokar tabar,sai da na kalli teburin da kyau sannan na lura da zanen harafin (J) me kyau sai k'yalli ya ke yi,na kai hannu na tab'a ina tunanin abin da J d'in take nufi.

Ina jin motsin bud'e k'ofa na yi saurin zama a k'asa,nan gaban teburin ina sauraron yanda zuciyata take bugu.

"Assalamu alaikum" Ya yi sallama ya na shigowa,na amsa cikin kashe murya wai ko zan burgeshi

Bai kalli inda na ke ba ya zo ya kwanta rigingine a kujerar,ya fara danna waya

"Ina wuni" Na gaishe shi.

Sai ya juyo ya na kallona,ko so ya ke ya ganeni oho,ya min kallon sakanni ya juya ga wayarsa sannan ya ce"lafiya k'alau".

"Za a kawo wani abun?" Na tambaye shi a d'arare.

Ya yi shiru kamar bai ji ba,sai can kuma ya ce"ina zuwa".

Ganin ya bawa banza ajiyata ya na ta harkar wayarsa sai nima na zuge jakata,na d'akko wayata,na tank'washe k'afa na shiga y'an danne-danne na

Wajan minti talatin mu na haka,sannan ya tashi zaune ya ajiye wayar ya kalleni ya ce"bud'e lokar can ki d'akko min sigari"

Na tashi tsam,na je na bud'e sigarin ce a ciki da yawa,da maganin tari suma kala-kala,sai wasu k'ananun robobi masu murfi,wanda ban fahimci abin da yake ciki ba,gida d'aya na d'akko,na duk'a na ajiye a teburin cike da ladabi

Ya d'auka ya zaro d'aya,ya kunna ya fara zuk'a,ni kuma na d'auki farantin na matso kusa da tebur d'in sosai,sannan na sunkuyar da kai. Ni sai na ji kamar hannuna ya ke ta kallo,ko tsarguwa na yi oho!

Sai da ya shanye su duka,ya na kad'e tokar a farantin,hannuna duk ya sage amma hakan bai sa na ji ina son barin kusa da shi ba

Kamar daga sama na ji muryarsa"Zinatu ki ke ko?"

Gabana ya fad'i,don da na yi zaton bai ganeni ba,ashe ya gane.Na d'ago na kalle shi a d'an tsorace na ce"na'am".

Sai ya kalmashe yatsun sa wuri d'aya sannan ya ce"me yasa ki ke bibiya ta?"

Na yi saurin fad'in"na rantse da Allah ba bibiyarka na ke yi ba Salim,ka fahimceni".

Ya kalleni na y'an sakanni,sannan ya ce"ta ya zan yarda ba Junaina ce ta turoki ba?"

Na ji dam! Na fara nazarin wacece Junaina? Sai kawai sunan na shi ya fad'o min (J.S) to ko dai J d'in ta na nufin Junaina,amma wace ita d'in? Kuma meye alak'ara su?

"Ki na shirya k'aryar da za ki fad'a kenan...". Ya katse min tunani

Bai rufe baki ba na yi saurin fad'in" a'a wallahi,ni ban san wata Junaina ba, kuma ba ni da wata alak'a da ita,babu wanda ya turo ni".

Ya jinjina kai sannan ya ce"ok! To ko dai so na ki ke yi?"

Na ji wani dam! Har numfashina sai da ya tsaya na sakan d'aya,to meyasa zai min wannan tambayar haka kai tssye? wannan ai k'ure ne kuma wace amsa ya kamata na ba shi? Na fad'a masa an kusa aurena,ko kuma na ce masa son shi na ke yi? Kai! Ba zan yi masa k'arya ba,ni dai burgeni ya ke kawai,amma ban sani ba fa ko ya ya kamu da so na ne,kar na je na yi abin da zan yi danasani

Muryarsa ta katseni
"Da ke na ke magana"

"Eh" Na fad'a a tak'aice.

Sai na kalle shi, jin ya yi shiru,na ga hannuna kawai ya zuba wa ido,ban ankara ba na ji ya rik'o hannun nawa me d'auke da zanen J.S,ya k'ura ido ya na kallo na y'an sakanni sannan ya wurgar da hannun ya fara magana

"Me yasa d'azu kika yi min k'aryar burgeki kawai na ke yi? Ba ke ce kika fara furta min kalmar so ba,amma na yi mamakin salonki,kin san meyasa?"

Ni dai na yi shiru kaina a k'asa,na kasa ba shi amsa

Ya ce"ok! Shikenan,ba sai kin ji ba".

Na yi saurin d'agowa na kalle shi,saboda har ga Allah na so na ji dalilin,amma kamar an d'aure bakina na kasa yin magana

Ya tashi tsaye ya na jan d'an bak'in gemunsa da ya k'ara masa kyau ya fara magana"ba na sonki,kuma ba zan tab'a son ki ba"

Na ji wani dum! A k'irjina

Ya d'ora"ke ba ma ke ba,duk duniya babu wata mace da zan so bayan Junaina,ita kawai na ke so kuma ita kad'ai ce matata in sha Allah! Ko na auri wata macen sab'anin ta to fa sai dai ta yi zaman amsa sunan matar aure kawai,don ko gangar jikina ba za ta samu ba bare kuma zuciyata".

Ban san lokacin da na fara kuka ba,sai da na ji d'and'anon gishiri a bakina,na ji wani dunk'ulallen abu ya zo ya tare min mak'oshi,raina ya b'aci sosai,zuciyata ta yi bak'a k'irin,cikin y'an sakannin na fahimci tabbas son Salim na ke yi,da kuma kishin sa me k'arfi.

"Kin gama aikin ki,za ki iya tafiya"

Ya fad'a ya na d'aukar wayarsa,ya saka a aljihu zai fice

Da k'yar na tattaro yawon bakina na had'iya,wai ko zan iya had'iye abun da ya tokare mak'oshi na,sai na samu damar magana.
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_


BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_


*&þFIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION&þ*


Page 8



"Na yarda zan yi zaman amsa sunan matar auren,in dai aurenka ne!". Na fad'a kamar wanda ya bani zab'i

Sai ya juyo ya min wani kallo me kama da harara,ban damu ba na d'ora da fad'in" ban damu da gangar jikinka ba,ko ban samu zuciyarka ba babu matsala,ganinka ma kawai zai wadatar da ni".

"Don Allah!" Na fad'a ganin ya tsaya kallona.

Sai kawai ya buga tsaki ya bar d'akin.Na jima zaune a wurin ina hawayen rashin gaskiya,to rashin gaskiya mana,idan ba haka ba har yaushe na fara son Salim da zan ji yanda na ji yau don ya fad'a min ba zai tab'a so na ba? Duka fa ban dad'e da sanin shi ba, ko gidansu ban sani ba bare iyayenshi.Kuma ni da na ke shirin yin aure nan da sati shida me ya kaini jefa kaina a irin wannan matsalar?

"K'addara!" Zuciyata ta ba ni amsar da ta gamsar da ni

Ina nan zaune a wurin manager ya turo k'ofar ya shigo d'akin,ya buga min wata kafirar harara kafin ya ce"wallahi yau da kin sa an kore mu daga aiki sai mun sa an rushe gidan ubanki! Shegiya me bak'ar k'afa,daga zuwanki yau kin b'ata ran Oga,har ya na zancen zai rufe gidan..."

Bai k'arasa ba na zabura na mik'e,hankad'ani aka yi? Tsalle na yi,iska na bi,duk ban sani ba amma ni dai idan na ce k'arasawa ta wurin shi na yi sakan d'aya na yi k'arya,na wanke shi da wani zazzafan mari,don har hannuna sai da ya d'auka,ina huci kamar zakanya na ce"k'arya ka ke yi wallahi! Ubana ya fi k'arfin ka,kuma kai k'aramin d'an iska ne,iskancin lungu ka ke yi,ka biyo ni eriyata ka gani don ubanka!".

Ina gama maganar na fice daga office d'in,zuciyata na tafarfasa,ni na yi zaton ma zai biyoni wallahi,amma sai na ji shiru,watak'il hak'uri ne da shi,ko kuma ya ji tsorona ne oho! Shi dai ya sani

Adaidaita sahu na tare na shiga na fad'a masa inda zai kaini,duk da hasken da ke titi tarwai bai hanani gane dare ya yi ba,na share hawayen da suka zubo min,na kifa kaina da guiwa ban d'ago ba har sai da me adaidaita ya ce min an k'araso

Sauka na yi,ina shirin duba jaka na d'akko masa kud'insa,jaka ta ce d'aukeni inda ki ka ajiyeni,sai yanzu na tuna ko jakata ban tsaya d'auka ba,tana office d'in Salim,takaici ya rufeni kamar na saka kuka na kalli me adaidaita na ce"ka ga na manto jakata a inda na je,don Allah ka yi hak'uri na tsallaka,naje gida sai na d'akko maka".

"Kutt! Amma dai kin san ko yaro ba zai yarda da wayon ki ba ko? Malama sallameni tun ranki bai b'aci ba!" Ya yi maganar ya na fitowa daga ciki ya murtuke fuska

Muna tsaye muna jayayya sai ga hannu d'aya ya zo wucewa.Hannu d'aya abokina ne,tsabar k'arfin sa ne yasa ake ce masa hannu d'aya,don ance duka d'aya yake wa mutum ya baje

Na yi farinciki kuwa,na k'wala masa kira daga inda muke,ya k'araso cikin takunsa na masu k'arfi ya na k'ara bubbud'ewa ya ce"kai! Zinatu tamu,me ki ke yi a ta nan da daddare?"

Na kwashe duk yanda muka yi na fad'a masa

Ya yi wa me adaidaita wata dank'a,ya matse wuyansa ya ce"kai! Har ance maka za a kawo maka kud'inka amma ka tsaya ja da ta wajanmu?"

Ya fizge daga rik'on ya ce"ai hakki na ne,dole ta ba ni,ba wani shege wallahi!"

Hannu d'aya ya ce"kai! To da alama ba ka da iyalai,idan kuma akwai to maza ka musu waya ka sanar da su inda za su zo su kwashe ka"

Sai ya karkace ya zaro wuk'a y'ar k'arama ya cakumo shi

"Na shiga uku! Ni fa ban saka ba don Allah kar ka sa caka masa"

Na fad'a cikin rud'ewa,don har rik'e hannunsa na yi.

Mai adaidaita ya rud'e ya shiga ba shi hak'uri, sai ya hankad'a shi kusa da ni ya ce"au! Ka ce kai shege ne? To duk'a ka bata hak'uri".

Ba shiri ya zube a gabana ya na bani hak'uri, har abun ya bani dariya,na shiga yinta

Hannu d'aya ya ce"za ka ware ko sai na maka d'ayan? Don dai hakkin ka ne da yau babarka ba za ta ganeka ba,k'aramin d'an iska!"

Shi dai bai tanka ba ya shiga mashin d'in ya ja shi a miliyar.Wannan abun shi ya d'an wanke min zuciya ya rage min damuwa,muka jero da Hannu d'aya ina fad'a masa inda na je.


Na yi mamakin ganin gidanmu a bud'e,tunda na san Baba da wuri ya ke rufe k'ofa,na tura na shiga da fargaba.A tsakar gida na tadda Baban ya na zaune ya zuba tagumi,na yi sallama na zo zan wuce shi sum-sum

"Zinatu!" Ya kira sunana da alamun fushi

Na dawo ina d'an rage tsayina na ce"na'am Baba".

Ya ce"daga ina kike?"

Na yi shiru kaina a k'asa

Ya nisa can ya ce"wata rayuwar kuma ki ke shirin shiga ko Zinatu?"

Lokaci d'aya na gane inda zancen sa ya dosa,kuma na ji babu dad'i a raina,da k'yar na bud'e baki na ce"a'a Baba,daga wurin aiki na ke wallahi".

Bai kulani ba ya shige ya je ya rufe gidan,ya dawo ya shiga d'aki.Ni ma na yi d'akina,ko kaya ban canza ba na kwanta ina tunanin ta yanda zan samu jakata da wayata.

Ni dai ba zan koma wurin ba,musamman yanda na mari manager, sai dai na tura Hannu d'aya ya amso min,amma kuma ina tsoron manager ya sa a kama shi fa,da dai wannan zulumin bacci ya kwasheni.

Da asuba bayan na idar da sallah,na je na gaida Babana,ya amsa babu yabo babu fallasa,har zan tashi ya na ji muryarsa ya na cewa"Zinatu! In dai na isa da ke,to daga yau kar ki sake fita ko k'ofar gida,har sai ranar aurenki,ko Habibu ne ya zo ya shigo cikin gida".

Gabana ya yanke ya fad'i,nan take zuciyata ta shiga bugu don kuwa na ji Baba ya na bani umarnin da ba zan iya yi masa biyayya ba

"Amma Baba jiya na manta wayata a wurin aiki,yau zan je na karb'o". Na fad'a kaina a k'asa.

Baba ya min shiru kamar bai jini ba,har tsawon lokaci,ganin haka na san ba zai yi maganar ba,watak'il ya amince ne ko kuma ya yi fushi da maganata,ni dai na tashi na koma d'akina na kwanta ina ta nazari.




Salim gida ya wuce kai tsaye,zuciyarsa na tafarfasa,ya kwana biyu bai shiga irin wannan halin ba,ya na takatsantsan da duk wani abu da zai sa ya tuna farkon had'uwar shi da Junaina,shi yasa ko kad'an ba ya shiga sabgar wata macen.Duk da Junaina ta na cikin rayuwar shi har yau,har gobe ma amma ba ya son tuna farkon k'ulluwar alak'ar shi da ita

Baby ce ta shigo d'akin,kallo d'aya ta yi masa ta san ya na cikin damuwa,ta k'araso ta zauna a kujera ta ce" akwai matsala ne Bros? Me ya ke damun ka?"

Ya yi shiru ya na kallonta,sai ta d'age kafad'a ta ce"ai na sani,wannan yarinyar ba za ta tab'a barinka ka ji dad'in rayuwa ba,ta hana ka aure,kuma ita ta k'i ta aureka! Ka duba fa ka ga yanda ta maida kai,ta na son haukata ka,ta maida kai d'an maye,amma ka k'i rabuwa da ita,meyasa?"

Ya sauke numfashi da k'arfi ya ce"a'a Baby,da gaske na rabu da Junaina,farincikin ki shi ne nawa.Wata ce yanzu ba ita bace".

Baby ta share hawayen da ya zubo mata ta ce"da ka damu da farinciki na da tuni ka yi aure Bros.Ka fito Ammi ta na kiranka".

Daga haka ta bar d'akin ta na hawaye,ya tashi ya bi bayanta ya na jin damuwa sosai da hawayen y'ar'uwar tasa.


K'arfe takwas na safe Ummi ta aiko wata y'ar mak'otan su,na zo ta na kirana,na d'an tsorata da kiran,ina tunanin watak'ila an fad'a mata an ganni jiya da daddare,haka dai na shirya wajan k'arfe goma na tafi gidan

Tun zuwana jikina ya yi sanyi,ganin damuwa a fuskar Ummi,na gaisheta ta amsa babu yabo babu fallasa,na tashi na je d'akin Umma na gaishe ta,wai ko zan d'an y'antu a wurin Ummi,na dawo na zauna na sunkui da kai kamar a gaban malamina na ke.

Shiru na d'an lokaci,sannan Ummi ta ce"wai ke Zinatu me yasa ba kya jin magana? Ni fa gabad'aya na rasa inda ki ka sa gaba,ban san me ki ka d'auki rayuwa,ki fad'a min abin da ya ke ranki!"

Na yi shiru,idona ya ciko da k'walla.Ta d'ora da fad'in"jiya Ummaru ya ke fad'a min ya ganki a kamfani wai kin je neman aiki,da wa ki ka yi shawara Zinatu? Ko mahaifinki ne ya tura
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment