Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

had'a kai da gwuiwa,hawaye suka min sallama,na jima a haka ina nazari kafin na tashi cikin sauri,kamar an tsikare ni

Wanka na yi,na shirya cikin dogon hijjabina har k'asa,na zari jaka da wayata na fice.Sai dai ina tsayawa a bakin titi don jiran abin hawa,kawai na ga Baba ya sakko daga adaidaita,na d'an ji fargaba da kunyar sab'a umarnin sa sun kama ni,amma na dake cikin zuciyata na ce"sai dai ka yi hak'uri Baba,addu'ar ce dai za ka yi ta min".

Kafin ma ya k'araso inda nake,har na fad'a adaidaita,ban zarce ko'ina ba sai Zoo road, Allah ma ya taimake ni me mashin d'in ya san wurin,don haka ban sha wata wahala ba aka kaini har k'ofar shagon Junaina.Babu laifi wurin da girman sa,ya burgeni tun daga k'ofar,na saita kaina na k'ara nutsuwa ina kallon kaina daga sama har k'asa,wai na tabbatar babu wata makusa,kamar dai wadda zan gana da shugaban k'asa ko wani sarki

Tun kafin na k'arasa ta glass na hango wani matashi daga ciki,ya kafeni da ido kamar ya sanni,na tura k'ofar na shiga sallama d'auke a bakina,shi kad'ai ne a ciki don iya hange na ban ga alamar Junaina ba,ko kuma masu siyan kaya,matashin ya tashi da sauri ya amsa sallamar,ya fara washe baki ya na min sannu da zuwa,da alama dai ya na da rawar kai kuma sam bai burgeni ba,don haka na had'e gira na ce"Junaina nake nema".

Ya turo min kujera tare da fad'in"wallahi yanzu ta fita,amma ba za ta jima ba,ki zauna bari na kira ta a waya".

"Na gode" Na fad'a bayan na d'osana na zauna a kujerar,sannan ya d'auki waya ya kirata.Ya dinga k'ok'arin ja na da fira ni dai kawai ina bin sa da e,a'a,a haka har kusan minti ashirin,ni dai har na fara k'osawa sai ga ta ta shigo da sallama

Na yi saurin d'agowa daga kallon wayata,na zube idona a kanta,fara ce tass,ba don kar ace kishi nake ba ma da na ce har da k'arin mai a hasken,ba ta da wani dogon hanci,sai manyan idanu kamar k'wai,bakinta d'an k'arami don nawa ya fi nata girma,wando ne a jikinta da riga iya gwuiwa,ta nad'e kanta da mayafi,sai wani uban glass da ta maida shi goshinta,y'ar siririya ce kamar yanda Baby ta fad'a min

"Wa alaikumus salam" Na amsa ina yi mata murmushi

Ta k'araso ta ja kujera ta zauna,ta na kallo na ta ce"ke ce me nema na?"

Na ce"ni ce".

Ta ce"to Allah yasa dai lafiya"

Na yi murmushi na ce"in sha Allah ".

Ta jinjina kai ta na sake kallo na daga sama har k'asa ta ce"to ina sauraron ki"

Na d'an kalli matashin nan,na ga mu ya ke kallo, sai na ji nauyin yin magana a gabansa,don haka na kalle shi na ce"bawan Allah ko za ka iya bamu wuri?"

Junaina ta ce"Sani jira mu a waje mana". Ya tashi ya fita ya na waige na.

Na maida hankalina kan Junaina na ce"sunana Zinatu,don Allah wata tambaya na ke son yi miki da farko".

"Uhm" Ta ce kawai.

Na ce"na san duk tarihin soyayyarku da Salim.Don Allah me yasa kika k'i amincewa da auren shi har yanzu? Ko ba ki san yanda yake k'aunar ki ba?"

Sai ta yi shiru na y'an sakanni ta na kallo na,sannan ta yi murmushi ta ce"shi ne ya turo ki da wannan tambayar?"

Na ce"a'a,Salim ba shi da masaniyar zan zo wurin ki,kuma ba a bakinsa na ji tarihin soyayyarku ba".

Sai ta jinjina kai ta ce"ina son Salim, amma ni ban shirya yin aure yanzu ba,shi ne kawai dalili"

"To me yasa?" Na yi saurin tambayar ta

Ta ce"saboda ban shirya kashe rayuwata ba".

"Kisa kuma?" Na tambaye ta da mamaki

Ta yi y'ar dariya ta ce"e mana! Ai ita mace da zarar ta yi aure to rayuwarta ta zo k'arshe,shi ya sa nake son na gama cin duniyata da tsinke kafin aure,tunda ina da dahir d'in me yi min son gaskiya,kuma zai jirani duk tsawon lokaci".

Na yi shiru ina mamakin kalaman ta.Ta d'ora"menene dalilin zuwanki wurina?"

Kai tsaye na ce"son Salim nake,kuma na zo ne na rok'eki ki bani wasu shawarwari don na samu kan Salim cikin sauk'i".

"Me!?" Ta fad'a da d'an k'arfi ta na zaro ido.

"Shi Salim d'in ya san ki?" Ta tambaye ni

Na sauke numfashi na ce"ki nutsu don Allah, Salim ya san ni,amma bai amince da ni ba.Ni ki yanke kud'in da zan biya ki kawai ki fad'a min abin da ki ke yi masa ya ke k'aunar ki don Allah".

Sai ta jinjina kai,amma da alama dai hankalin ta ya tashi,ta ce min"ok! Gobe bayan magriba ki dawo,kafin nan na yi shawara".

Na yi mata godiya na fito daga wurin,kaina duk a d'aure,ni dai ban yi zaton Junaina ta na son Salim ba,amma a yanda na gani a idonta kam tabbas tana kishin Salim sosai.Na hau mashin na koma gida,gidan Ummi ma na wuce,don ina jin tsoron had'uwata da Baba, na yi sallahr azhar na ci abinci,na kwanta sai bacci.



Yau da wuri ya dawo daga kamfani,ransa duk a b'ace ya ke, don ya san Baby ce ta je ta kaiwa Zinatu wayarta,yau da wani ne ta yi masa haka ba ita ba,babu abin da zai hana ya yankar masa tikitin rashin mutunci,fuska a murtuke ya shigo gidan,bai tadda kowa a falo ba,ya fi zaton suna kitchen, don haka ya shiga kai tsaye da sallama,a zaune ya ga Baby ita kuma Ammi ta na tuk'a tuwo,ya d'an saki ransa bayan sun amsa sallamar ya ce"Hajiya Ammi,ke da y'arki ne ku ke yin tuwo?"

Ammi ta yi murmushi ta ce"na ke yin tuwo dai,fira kawai take taya ni,kuma ni na ce ta zauna ta huta".

"Aaaa,lallai y'ar gatan Amminta" Salim ya fad'a da d'an murmushi.

Baby ta kalle shi,ta na nazartar sa ta ce"sannu da dawowa Bros,ya aiki?"

"Aiki babu dad'i,zo mana sister mu yi sirri" Ya fad'a ya na shirin fita daga kitchen d'in.

Ammi ta ce"lallai fa sirri,idan ta yi tsami dai za mu ji".

Baby ta tashi ta na dariya ta ce"ai Ammi babu abin da zai yi tsami,indai tsakanina da my bro ne". Daga haka ta fito ta yi hanyar d'akinsa,kamar yanda ta ga ya yi can.

A zaune ta tadda shi,ya had'e rai ba kamar d'azu ba,ta k'araso jiki a sanyaye ta zauna nesa da shi,don ta lura da yanayin sa tun shigowar sa gidan,ta share ne kawai

"Akwai matsala ne bros?" Ta tambaye shi

Ya ce"ina wannan jakar?"

"Na kai mata abun ta" Ta yi maganar ta na bud'e hannu alamun ko a jikinta.

Ya sauke numfashi ya ce"haba Baby! Me yasa za ki kai mata da kanki? Kuma idan ma dole sai kin je da kanki ai sai ki takura min na kaiki"

Ta turo baki ta ce"to ba kai ka ce ba ka san gidansu ba?"

Ya yi shiru ya na kallon ta,ya na shirin magana ta riga shi "don Allah Yaya zan rok'e ka wata alfarma,duk da na san ba zan samu ba ma". Ta k'arasa a sanyaye

Salim ya ce"ina jinki"

Ta tashi ta dawo kusa da shi ta zauna,don nuna masa muhimmancin maganar,ta fara"ni dai a yanzu burina kayi aure,ka samu nutsuwa,ka manta da Junaina.Yaya! Zinatu ta na matuk'ar k'aunar ka,wallahi irin wannan macen ya dace ka aura,don na san a yanda take son ka ko ka auri Junaina daga baya za ta jure komai,Yaya Junaina fa ba son ka take ba,wallahi cutar da kai kawai take yi,da za ka bawa wata macen dama ta hanyar auren ta za ka tabbatar da hakan...".

"Baby kin san yanda nake ji a zuciyata kuwa? Ke ba ki san so k'addara bane ko?" Ya katse ta

Ta yi murmushi ta ce"alhamdulillah! Tunda har ka riga ni sanin k'addara ne,to kamar yanda ka ke ji d'in nan,ita ma Zinatu haka take ji fa,yanda Junaina ta zama k'addarar ka,haka itama ka ke k'ok'arin zama tata k'addarar..."

Ya katse ta da fad'in"a'a,ban yarda ba,ita ce ta d'orawa kanta!"

Ta yi saurin fad'in "kenan kai ma kai ka d'orawa kanka? Idan amsar e ce kenan mutum shi yake zab'arwa kansa k'addara ko? Kai me yasa ka zab'o wadda za ta wahalar da kai?"

Ya yi shiru, ya rasa abin fad'a,sai ta cigaba"wallahi Yaya na ga k'aunar ka k'arara a idon Zinatu,har kuka ta dinga yi duka saboda kai,me zai hana ka gwada saka ta a rayuwarka ko na d'an lokaci ne ka gani?"

"Na riga ki wannan tunanin" Ya katse ta.

Da mamaki ta ce"to amma me ya sa ba ka aiwatar ba?"

Ya ce"na gwada aiwatarwa,sai na tadda matsala,yarinyar ba ta dace da ni ba gaskiya, ba ta da hali".

Baby ta ce"subhanallah! Wane hali ne da ita? Kuma Yaya kai da ka ce ba ka san ko gidansu ba,ta ya ka san halinta?"

Ya yi guntun murmushi ya ce"bari na fad'a miki gaskiya, yarinyar nan akan gab'a ta zo min,dama ina son in yi aure, ba don ina buk'atarsa ba,sai dan na farantawa Abba rai,yanda yake ta lallab'a ni akan zancen auren nan,shi yasa na yanke shawarar zan yi,amma sai na samu me so na sosai,yanda bayan auren za ta iya jure kowane irin k'alubale,don Junaina ko cewa ta yi na saki matata zan saketa".

Ya nisa,sannan ya cigaba"a ranar da ta bar jakarta a d'akina,a ranar na yanke hukuncin auren ta,kuma ta na barin wurin bayan ta mari manager na shiga adaidaita sahu na bi bayanta,a gabana ta kira d'an daba ya zare wuk'a zai cakawa me mashin d'in,Allah ya taimake sa suka k'yale shi,kuma dama marin da ta yi ma ya sa ni kokwanto akan tarbiyyar ta.Washegari na dawo unguwar,na yi bincike akan yarinyar,na farko da na tambayi manyan unguwa mutum biyu,suka tabbatar min da yarinyar ba ta da tarbiyya,ta na mu'amala da maza..."

Baby ta katse shi"maza kamar ya?"

Ya ce"maza dai wanda kika sani,kuma na tambayi wasu samari su ma sun tabbatar min da hakan,to tun lokacin na san yarinyar ba matar aure bace,shi yasa na fasa". Baby ta yi shiru ta na nazari,sannan ta ce,
"Amma Yaya babu wani taimako ko nace uzuri da za ka yi mata? Ta na son ka"

Ya ce"ni kuwa na yi mata taimako,kin san matakin da managerna ya so d'auka kuwa? Da na samu labari,na gargad'e shi indai ya sake na ji wani abu ya same ta,sai na yi shari'a da shi".

Sai ta rasa abin cewa,ta ce"Yaya sallar magriba". Ta bar d'akin jiki a sanyaye,amma sam ba ta yarda da zancen yayan nata ba,kuma za ta yi bincike.



Sai bayan la'asar na koma gida,na tadda Baba a k'ofar gida shi da wani mak'ocinmu,na gaishe su,kaina a k'asa na shige gida,na zauna ina ta tunanin k'aryar da zan yi masa idan ya ritsa ni.Ga mamaki na,sai na ga Baba ya bawa banza ajiya ta,aikuwa na ji dad'i sosai na ce watak'il ya sassauta hukuncin ne.


Washegari ko minti biyar ban k'ara ba akan lokacin da Junaina ta bani,yau ta na nan kuma ita kad'ai ce a wurin babu wannan matashin,bayan mun gaisa ta kawo min lemo da ruwa,ni dai ban sha ba,burina kawai na ji ta bakinta.

Ta nisa ta ce"ke dai yanzu idan na fahimce ki,ki na son sanin duk abin da Salim ya ke so,da kuma wanda ba ya so,abin da yake burge shi,da wanda ba sa burge shi ko?"

Na ce"e hakane,idan da dama ma har kalar abincin da ya fi so,da wanda ba ya so".

Ta yi wani murmushi ta ce"za ki ji komai,amma fa akwai sharad'i".

Na ce"na amince da sharad'in ki,fad'a min kawai".

Sai ta yi y'ar dariya ta ce"y'an mata da sauri haka?"

"Zan iya yin komai don Salim ya aureni" Na fad'a ina murmushi

Ta gyara zama ta ce"kin ga yaron da ki ka gani jiya anan? Abokina ne, shi yake taya ni jire wurin nan,kuma gidanmu d'aya da shi,to jiya ya fad'a min ya na son ki,kallo d'aya ya yi miki ya ji sha'awar ki ta kama shi"

Sai ta yi murmushi ta ce"ai ban ga laifin sa ba,kin had'u Zinatu.To a tak'aice dai ya na son kwanciya dake ko sau d'aya ne,wannan shi ne sharad'in idan kin amince ko yau a shirye yake,ni kuma da kun kammala zan ba ki bayanai".

Tunda ta fara magana wani abu ya zo ya tokare k'irjina,na ji kamar na tashi na yi ta fesa mata mari.Ni kam ko da wasa ban tab'a sha'awar aikata wannan mummunan abun ba, to ta zarge ni ne ma wai da take kawo min wannan tayin?

"Ki bani lambar ki,idan na yi shawara zan kira ki" Na fad'a ina mik'a mata wayata.

Ta saka min lambar na karb'a na yi mata godiya na tafi.
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_


BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_


*&þFIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION&þ*


Page 12



Lokacin da na k'arasa gida har an yi sallar isha'i,tun daga nesa na hango Habib zaune a bencin k'ofar gidanmu,na rage sauri na dinga d'aga k'afa kamar ba na so,kallon shi kawai nake yi cikin tausayawa,indai abin da na ke ji a zuciyata game da Salim,shi ma Habib haka ya ke ji game da ni,to kuwa tabbas zan tausaya masa,sai dai ba zan iya sadaukar da farincikina akan na wani ba.

"Barka da zuwa gimbiyata". Ya fad'a bayan na zo dab da shi

Na zauna a bencin nesa da shi na ce"daga ina haka?"

"Daga gida nake" Ya bani amsa

"A yi hak'uri dai a min uzuri,na karya dokar sarauniya,ina fatan za a tausayawa raunanniyar zuciyata wurin yi mata hukunci. Na ji kin ce kin tafi hutun amsa kira,kuma ban sani ba ko har yau ba ki dawo ba,shi yasa ban kira ki ba na yi gaban kaina na zo". Ya k'arashe maganar a raunane,wai a dole na ji tausayin shi

Na k'ura masa ido tun daga kanshi,har yatsun k'afarsa,har yau na kasa gano makusar Habib,ya na so na sosai ga shi d'an'uwana,ko bai b'ata bakinsa ya fad'a min ba,na san zai kula da ni da soyayya idan ya aureni,ya na da hak'uri sosai duk wani laifi da nake yi masa da gangan ya na sani ya ke sharewa,ko wani bai fad'a min ba na san idan na aure shi zan ji dad'i.Amma sai dai kash! Kwata-kwata Allah bai d'iga min son shi a zuciyata ba,a da na amince da shi ne saboda ina ganin ni fa duk duniya babu wani namiji da zan so da aure,ashe lokaci ne bai yi ba,ni kuma GAJEN HAK'URI na ya sa ni saurin zab'ar Habib, ashe sarkin zuciyar tawa ya na dab da bayyana,gaskiya na yi garaje.

Ban san hawaye na ke yi ba sai da na ji muryarsa ya na fad'in "subhanallah! Zinatu lafiya kuwa? Me ya ke damun ki? Ko ba ki da lafiya ne?"

Na share hawayen cikin dakiya da jarumta na ce"Yaya Habib, ina son magana da kai ta fahimta,Allah yasa za ka fahimce ni".

Ya sake tattara hankalin sa wurina,alamun damuwa k'arara sun bayyana a fuskarsa ya ce"me zai hana? Zan fahimce ki Zinatu, ki fad'a min don Allah"

"Idan na tambaye ka,ka na so na ban yi maka adalci ba, na san duk duniya babu wani namiji da ya ke so na sama da kai Yaya Habib,amma a wane mataki ka ajiye so na a zuciyarka?"

Ya sauke numfashi har yanzu dai da alama bai nutsu na ya ce"Zinatu,ba iya son ki nake ba,har da k'aunarki,k'auna me tsanani ma kuwa,kuma kin kai mataki na k'arshen k'arshe a zuciyata".

Na d'auke kaina daga kallon sa na ce "idan na fasa auren ka ya za ka ji? Ma'ana idan k'adddara ta sa na auri wanin ka..."

Ban k'arasa ba ya katse ni,a sanyaye"amma me ya kawo wannan maganar?"

"Ka fara bani amsa kafin ka ji dalili" Na fad'a har yanzu ban kalle shi ba.

Cikin raunin murya ya ce"Zinatu ni musulmi ne,na yarda da k'addara me kyau da akasin ta,wallahi ina tunanin irin yanda zan ji,da kuma yanda rayuwata za ta kasance idan ban aure ki ba, saboda ke kad'ai nake so.Amma hakan ba zai sa na kasa yarda da k'addara ba,tunda na sani wani ba ya auren matar wani,kuma duk da ke kad'ai ce a zuciyata,amma a kullum ina sake neman zab'in Allah".

Jikina ya yi wani mugun sanyi,gaskiya Habib ya na da hankali,kuma na san har da ilimin addini a wannan kyaun zuciyar nasa,ina ma ace shi ne Salim! Da zan bugi k'irji cikin dubunnan mata na ce na fi kowace mace dacen miji,sai dai kash! Zanen k'addara ba ya gogewa,don kuwa har yanzu ban ji son Habib a raina ba,sai dai tausayin shi,kuma wallahi ba zan iya sadaukar da farincikina ba akan shi,sai dai ya yi hak'uri ya d'auki tasa k'addarar kamar yanda nake shirin rungumar tawa

"Akwai wata matsala akan maganar aurenmu ne Zinatu?" Ya tambaye ni

Kamar na yi masa k'arya sai dai na daure na ce"Yaya Habib ko a cikin maza kai namiji ne,ka had'a abubuwa da dama wanda duk mace me hankali za ta so ta same ka a matsayin abokin rayuwa,sai dai ni har yau na kasa jin son ka a zuciyata saboda ba ni da hankali..."

Ya yi saurin katse ni da fad'in"a'a Zinatu,kar na sake jin haka daga bakinki,ki na da hankali,wannan ba laifinki bane laifin zuciyarki ne,shi ya sa ake son mutum ya dinga addu'ar Allah yasa ya fi k'arfin zuciyarsa,zuciyarki ta fi k'arfin ki,da ace kin fi k'arfin ta za ki iya yi mata tilas ta so abin da hankalin ki ya ke baki daidai ne".

Wasu hawaye suka zubo min,na share na ce"wallahi har zuciyata,na so na yi wa mahaifana biyayya don na faranta musu,su yi alfahari da ni ko da sau d'aya ne a rayuwa,amma rafkananniyar zuciyata ta gaza bani had'in kai.Ka yi hak'uri Yaya Habib na fasa auren ka,saboda ko da na aure ka ba zan tab'a iya baka farincikin da ya dace namiji nagartacce irin ka ya samu daga matarsa ba".

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Ya furta kawai

Shiru na tsawon lokaci sannan ya ce"Zinatu na sani dama can ba kya so na,amma na tabbata yanzu akwai dalilin ki na fasa aurena,me ya sa? Don Allah kar ki b'oye min".

Gaskiya ban ji zan iya ba shi labarin Salim ba,don haka na girgiza masa kai alamar a'a sannan na ce"ka d'auka hakan k'addara ce kamar yanda ka sanar da ni ka yarda da ita.Ni dai yanzy alfarma d'aya nake nema a wurin ka, wannan alfarmar idan ka yi min ita ce kawai za ta sani na tabbatar da k'aunar da kake yi min,kuma zan rik'e ka a zuciyata masoyi na gaskiya,na yi maka alk'awarin duk sallolina biyar na kowace rana zan yi maka addu'ar Allah ya baka mace ta gari,kuma Allah ya cire maka so na a zuciyarka".

"Wace alfarma ce wannan?" Ya tambaye ni,jikinsa duk ya yi sanyi

Na gyara zama ina fuskantar sa na ce"Yaya Habib so na ke ka fad'awa manya ka janye maganar aure na,don Allah ka yi min wannan".

Ya saka yatsan sa a baki ya ciza kafin ya ce"haba Zinatu! Me yasa ki ke da son kanki da yawa? So ki ke ni aga laifina fa kenan,ki na so a saka ni a jeren masu sab'a alk'awari kenan? Kuma da wane idon kike so na kalli mahaifanki?"

"Ka na nufin ba za ka iya yi min wannan alfarmar ba,a matsayina na wadda ka ke kira farincikin ka?" Na tambaye shi muryata na rawa.

Ya tashi tsaye ya ce"e,ban yi miki k'arya ba Zinatu,ke ce farincikina,amma ba zan iya yi miki wannan abun da kika nema ba,gaskiya sai dai ki yi da kanki.Kuma ki yi tunani kafin ki yanke hukunci,so da yawa mutane su na son abu kuma abun ba alkhairi bane a rayuwarsu,kuma sai su k'i abun da shi ne alkhairi a duniyarsu da lahirarsu,shi ya sa istihara take da amfani,ki je ki yi ta istihara ki nemi zab'in ubangiji,idan still kin ji ba za ki iya aurena ba,sai ki sanar musu da abin da kika yanke,ni ma zan saka ki cikin addu'o'ina in sha Allah, Allah ya mana zab'in alkhairi".

Ya na gama maganar ya buga mashin d'insa ya tafi,ni kuma na tashi na shiga gida ina kukan rashin gaskiya.

'Dakina na shiga na fad'a a katifa,na fashe da kuka sosai,ni ma na san ban yi wa Habib adalci ba,to amma ya zan yi? Haka k'addarar mu ta zo mu duka ukun,da ni, da shi da Kuma Salim,duk Allah ya jarabce mu da son maso wani.

Bayan na gama kuka na sai tunanin sharad'in Junaina ya dawo min,a gaskiya ina son Salim kuma ko da na ke ganin zan iya yin komai a kansa abun bai kai na aikata zina ba,to na saida mutunci na don ya aure ni,na je masa fanko kuma na saka ran zan yi wata daraja a idonsa? Ai idan na yi hakan na yaudari kaina,kamar an ba ni umarni na d'akko wayata na dubo lambar Junaina na doka mata kira

Ta d'aga da sallama ta na kiran sunana,ban amsa ba na fara magana"Junaina wannan sharad'in ya yi min girma,gaskiya ba zan iya ba,idan akwai wani ki fad'a".

"Za ki yarda da romance? Ina nufin ki yarda ya biya buk'atarsa ba tare da ya kusance ki ba". Ta fad'a kai tsaye kamar me bani shawarar na yi azumi ko sallah

Na yi shiru,ina tunani duk zina ai sunan ta d'aya ne,ko ta ido ma an ce ana zina bare kuma wannan babban abun

"Idan fa kin ga ba za ki iya ba,babu dole" Muryarta ta katse ni.

Mu na cikin wayar kiran Baby ya shigo,na yi saurin ce mata"zan kira ki anjima".

Na katse kiran,na d'auki na Baby na k'irk'iri murmushi me sauti na yi mata sallama.

Ta amsa sannan ta ce"da fatan kina lafiya matar Yaya Salim"

Na ji zuciyata ta motsa,na yi y'ar dariya na ce"Baby kenan,to Allah ya tabbatar".

Ta ce "Amin".
Sannan ta yi jim ta ce" amm...Zinatu ina son ganin ki gobe,akwai magana me muhimmanci da za mu yi da ke akan Salim,ina tunanin na samo mafitar da za ta shigar da ke wurin shi ta hanya me sauk'i".

"Da gaske kike!?" Na fad'a da d'an k'arfi,farinciki ya mamaye zuciyata

Ta ce"e,goben ki zo shagon gyaran jikina da yamma"

Na yi mata godiya na ce zan zo mu ka yi sallama.Tun kafin na ajiye wayar na ji muryar Baba ya na k'wala min kira

Gabana ya fad'i,don na san yau dama tara ni ya ke yi,na saka hijjabi na fita kaina a k'asa kamar malama,na je na tsugunna nesa da shi a tsakar gida na ce"Baba ga ni".

Ya ce"Zinatu da gaske dai ban isa da ke ba ko?"

Muryata na rawa na ce"a'a,wallahi ka isa da ni Baba".

Ya ce"to indai kin yarda ni ne na haifeki,daga yau kada ki sake fita ko k'ofar gida sai da izinina!"

Ban ce komai ba,sai gyad'a kai da na yi alamar na amince,na tashi na koma d'ak'i na fashe da kuka.




HABIB=Ø%Þ
Babu me son Habib don Allah?
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_


BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_


*&þFIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION&þ*


Page 13



Bacci kad'an na samu a daren,ina ta tunanin yanda zan yi na yiwa Baba biyayya,ba na son b'ata masa rai,amma kuma Baby ta buk'aci gani na goben,kuma na san ba zai yiwu na ce ita ta zo ba,tunda k'aruwa ta ce ba tata ba,na so ma na ce ta fad'a min ta waya sai kuma na ga rashin dacewar hakan,ta na ta k'ok'ari a kaina,ai sai ta ga kamar ma ban damu ba,itama ta janye jikinta.Ga tunanin yanayin da na saka Habib a ciki,watak'il ya na can a cikin damuwa ta dalili na.Ita dai Junaina na ajiye buk'atar su a gefe,don ta yi kad'an
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment