Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

sai ki bud'e bakinki,idan ba ki shirya ba ki fice min daga office!"

Na d'ago na kalle shi, sai na ga tabbas wannan ba Habib d'ina bane,da gaske ya ke yau a gaban doctor Habib nake,sai na saka a raina ban san shi ba d'in,don haka na ce"ni ma ban sani ba".

"Kamar ya ba ki sani ba? Shekarunki nawa?" Ya tambaye ni,idonsa a kaina

"Ashirin" Na ba shi amsa.

Ya ce"ko y'ar shekara biyar aka yi mata fyad'e dole ta sani,bare ke da kin isa zaman aure! Ki na kokwanton anyi miki fyad'e,ta ya ki ka tsaida wanda kike zargi?"

Na lura dai da gaske Habib ya ke son k'ure ni,gwara ni ma na dawo masa Zinatu,don ya na shirin canza min suna da wata banzar barazanar sa,wai shi likita!

Na had'e rai na gyara zama na ce"kafin na shigo wurin nan ce min aka yi likita zai duba ni,ba lauya ba,kuma a zatona da doctor Habib na ke magana,ba barrister Habib ba".

"E hakane,amma wannan tambayar duka cikin aikina ne". Ya fad'a ya na had'e gira.

Na ce"tunda ka ga har sun kawo ni nan,ai ka san an zo gab'ar raba gardama kenan.Idan za ka duba ni bismillah kawai". Na k'arasa maganar zuciyata na bugu,don ina fargaba da takaicin wani gardi ya ga tsaraicina,musamman ma Habib d'in,wannan rashin darajar ina zan kai shi? Amma a fili ba za ka tab'a kawo haka nake tunani a raina ba.

Ya yi shiru ya na kallo na,tsawon sakanni,sannan ya jinjina kai ya ce" bismillah! Ga gado can je ki hau".

Gabana ya fad'i,duk da har yanzu zuciyata ba ta amince da zai iya duba ni d'in ba,ban nuna ba na dake na tashi na yi inda gadon ya ke,sai dai zama na yi ba kwanciya ba

Na d'an jima da zama,har na fara k'aguwa sannan ya k'araso wurin,ya janyo kujera ya zauna ya fuskance ni,ni kuma na sunkuyar da kai, don ba na son ya kalli k'wayar idona.

Tun kafin ya fara magana wani likita ya shigo,wanda na ke kyautata zaton shi ne me office d'in.

"Doctor ka kammala?" Ya tambaye shi,idonsa a kaina

Habib ya yi wani huci ya dafe kansa da duka hannayensa biyu.

Likitan ya janyo wata kujerar ya zauna a kusa da shi,ya ce"na fa kasa fahimta,a iya sani na ba ka harka da mata,wacece wannan?"

Kamar ba zai ba shi amsa ba,sai can ya ce"ita ce Zinatu".

Ko idona ne oho! Sai na ga kamar lokaci d'aya yanayin likitan ya canza,zuwa ga b'acin rai,ya yi min wani kallon da na kasa fassra shi a lokacin,sai daga baya,sannan ya kalli Habib ya ce"to me ya kawo ta nan d'in?"

Habib ya tashi ya je kan teburin ya d'akko masa takarda ya ba shi.Ko me aka rubuta a takarda tawa oho! Na dai ga ya kalle ni da sauri,kuma da alamun b'acin rai

Ya kalli Habib ya ce"yanzu ka duba ta d'in?"

Ya girgiza masa kai alamar a'a.Sai ya ce"ok,ka je kawai zan saita komai".

Habib ya yi masa wani kallo me wuyar fassrawa ya ce"kai! Matar da zan aura d'in za ka duba!?"

"Ai cikin aikina ne" Ya ba shi amsa ya na d'age kafad'a.

Habib ya kalle ni ya ce"ke tashi ki fita! Sai dai ku canza wani asibitin wallahi,ta ya wanda na sani zai duba min mata?"

Likitan ya dafa kafad'arsa ya ce"ok! Na fahimce ka Habib,amma ka sani ko wani asibitin aka kai ta ba ka da tabbacin mace ce za ta duba ta.Na yi maka alk'awarin ba zan duba ta ba,zan lallab'a ta ta sanar da ni gaskiya".

Habib ya yi shiru kamar me nazari. "Ka yarda da ni abokina,ka je d'in".

Habib ya kalle ni,sannan ya maida facemask d'insa ya fice.Na sauke ajiyar zuciya a b'oye,har yanzu zaune nake a bakin gadon

Likitan ya kalle ni da kyau ya ce" ke anyi miki fyd'en ko ba a miki ba?"

"Ni ma na kasa tantancewa fa" Na fad'a, ina juyar da kai gefe

Sai ya tab'e baki ya ce"yanzu ya kike jin jikinki?"

Na ce"ya na yi min ciwo kad'an,sai bacci da nake ji".

"Tun yaushe abun ya faru?"

"Jiya da daddare" Na ba shi amsa.

"Waye wanda ake zargi" Ya tambaye ni.

"Wani ne" Na fad'a

Ya ce"ko Salim da na gani a waje?"

"Shi" Na fad'a a tak'aice.

Ya ce"ok! To yanzu zan canza miki d'aki,sai na saka miki drip,idan ya k'are za a sallame ki".

Ina shirin yin magana ya tashi,ya na cewa na biyo shi.

Ba ni da zab'in da ya wuce bin umarnin shi.Zazzaune muka tadda su Abba,da alama har sun k'osa da jira,na tsaya daga d'an nesa,yayinda likitan ya k'arasa wurin su,Abba ya tashi da sauri ya mik'a mishi hannu suka gaisa ya na tambayar sa ya ake ciki?

Likitan ya kalli Salim sannan ya maida duban shi wurin Abban ya ce"fyad'en dai ya tabbata,sai dai Allah ya rufa asiri".

"Ban yarda ba! Wallahi akwai k'ulla-k'ulla a wannan abun!" Muryar Salim ta karad'e kunnuwanmu.

Gabana ya fad'i. Likitan cikin nuna rashin damuwa ya ce"me ye ya ba ka tabbacin hakan?"

Salim ya ce"duba yarinya ba sai likitoci biyu ba,likitan farko da ya dace ya duba ta ya jima a ciki,sannan ya fito kuma ina kallon shi,sam ban yarda da yanayinsa ba,kai ma kuma da ka shiga ka jima a ciki,to meye dalilin dad'ewarku a duba mutum d'aya kawai?"

Likitan ya kalle shi na y'an sakanni,har na fara fargaba sai ji na yi ya ce"amma dai ina tunanin ka san irin b'arnar da ka yi mata ko?"

"Ban gane ba!" Salim ya fad'a a hasale.

Likitan ya ce"likitan farko da ka ga ya fita,shi ne ya fara duba ta,kuma ya ga b'arnar da ka yi mata,shi yasa ya kira ni saboda na fi shi k'warewa a fannin d'inki,yanzu dai an gama gyarata,za mu saka mata ruwa,idan ya k'are kuma sai a sallame ta.Akwai magungunan da zan rubuta".

"Dank'ari!" Na fad'a a zuciyata.Amma lallai wannan likitan idan ya shiga wasan kwaikawayo zai samu abinci sosai, na ji wani farinciki ya rufe ni,sai dai fa na yi mamakin abin da ya sa shi wannan k'aryar har haka,kuma na sa a raina ba sai na ji dalili ba,ko ma menene ni kam ya taimake ni.

Salim ya ce"kai ka ga! Kada ka sake danganta ni da wannan,can za ta nemi wanda ya yi mata b'arna ba...".

"Kai!" Abba ya daka masa tsawa,Salim ya koma ya zauna fuskar nan kamar bai tab'a murmushi ba.

Abba ya ja likitan gefe,ban san dai me suka tattauna ba,ni kuma wata nurse ta zo ta rik'e hannuna muka shiga wani d'akin. Aka bani gado,ta saka min drip,ta ba ni magani na sha,har da lulllub'e ni da bargo,aikuwa bacci ya ce min mu je.

Ba ni na tashi ba sai bayan azhar,na duba wayata dake kusa da ni,na ga k'arfe biyu da minti ashirin,na tashi zaune,yanzu kam na ji dad'in jikina sosai,babu wani sauran bacci a idona,na tashi na shiga band'aki na d'auro alwala.

Ina fitowa na tadda Mama Saude a d'akin,ta dinga kallon k'afata kamar wadda aka ba ta aikin k'irga taku na,na san dai tsabar gulma ce take cinta,na had'e rai na k'araso na gaishe ta.

Ba ta amsa ba ta ce"oh! Zinatu ashe haka abu ya faru?"

"Uhm!" Kawai na ce,na d'auki d'ankwalina na shimfid'a a k'asa,na tada sallah

"To kin yi wankan tsarki ne?" Na ji tambayar tata a bazata.

Na juyo na kalle ta na sakan uku,sannan na tada sallata.Kafin na idar ta fita ta shigo da kwando me d'auke da kuloli,ta had'a shayi kofi biyu, ta ja d'aya gabanta,ta mik'o min d'aya,haka abincin ma ta zuba faranti biyu, ta gyara zama ta fara antayawa ba tare da ta min magana ba.

"Mama a ina aka samu wannan abincin?" Na tambaye ta,ina d'aukar kofin shayin

Ta ce"daga gidansu yaron aka kawo.Ai ya na nan ma,ya na jira a sallame ki, ya maida mu gida,wallahi yaro kyakkyawa me hankali da kirki,ni na san k'addara ce kawai kifta".

Na ce"Baba da Ummi sun sani?"

Ta na yagar naman kaza ta ce"yo kema dai zancen ki ke so,idan ba su sani ba ni taya zan ji har na zo jinya? Ai har da mahaifin yaron ma baban naki sun zauna,ban dai ji abin da suka tattauna ba tukun,sai mun koma gida".

"Ummi ta zo?" Na tambaye ta.

Sai ta tab'e baki ta ce"ta zo ina? A gabana Na'ima ta kira ta ta sanar mata,amma wallahi bud'ar bakin matar nan,sai cewa ta yi Allah ya ba ki lafiya.To dama waye dolenki idan ba ni ba? Wallahi na san na fi mahaifiyarki shiga tashin hankali,ke ni yanzu fargabata d'aya ,kar Habibu ya ji labari".

Ni dai na yi shiru ban sake tanka mata ba,ta na ta surutun ta,ni kuwa tunanin yanda za mu yi da mahaifana kawai na ke yi. So na ke ma ta bani space na samu damar kiran Nazifi a waya,amma ta zaune min.

Mu na nan zaune Salim ya shigo da sallama,Mama ta amsa ta na yi masa sannu,ni kuwa binsa da kallo kawai na yi,ina jin wata k'aunar shi, Kai! Gaskiya ina son Salim fiye da zaton ku.

Kallo d'aya ya yi min ya kauda kai,ya kalli Mama ya ce"kun ci abincin kuwa?"

Ta washe baki ta ce"mun ci abinci mun k'oshi".

"Ok! Za mu wuce gidan". Ya fad'a ya na d'aukar kwandon kayan abincin.

Ya fita,muka bi bayansa,sai kallon shi nake yi.Muna shirin shiga motar wannan likitan ya dakatar da mu,ta hanyar k'walla min kira,na dakata,shi kuwa Salim ya shige motar bayan ya bud'ewa Mama ta shiga gidan baya.

Likitan ya ce" kin ba ni mamaki".

"Na me kenan?" Na tambaye shi.

Ya ce"akan irin yanda na fad'i abin da ba haka bane,kuma ba ki nemi jin dalili ba".

Na ce"to meye dalilin?"

Ya ce"saboda ba na son tarayyarku da Habib". Na yi masa kallon mamaki

Ya d'ora"Sam! Habib bai dace da mace irinki na,ya na da hak'uri da halaye masu kyau,mace me hankali da hak'uri ce kawai ta dace da shi.Ya na yawan ba ni labarin irin yanda ya ke son ki,ke kuma ba ki damu da shi ba...".

"Kai dakata malam! Idan ka yi ne don ka raba ni da shi,to ka sani shi ka cuta ba ni ba,kuma tunda ka ga tun farko ban nemi jin dalili ba,idan da tunani ai za ka gane hakan dad'i ya yi min.Ba ni da lokacin ku!".

Ina gama maganar na wuce wurin motar na bud'e gidan gaba na shiga, ya ja muka tafi.


Gidan Babana mu ka je,na ji wata sabuwar fargaba ta kamani,Mama ta bud'e ta fita,ina shirin bud'ewa na fita,babu zato kawai na ji Salim ya...
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_


BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_


*&þFIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION&þ*


Page 20



Na ji ya kira sunana a sanyaye,na juyo na kalle shi ina jiran abin da zai fad'a,sai kawai ya tsaya ya na kallo na,ni ma na zuba masa ido son shin na ratsa duk wasu jijiyoyin jikina,wajan minti biyu muna a haka,sannan ya jinjina kai ya d'auke idonsa a kaina ya ce"je ki".

"Na gode" Na fad'a,sannan na fice na rufo masa motarsa,tsaye na yi ina kallon motar har sai da ya b'acewa gani na,na sauke ajiyar zuciya na shiga gida da fargaba.

A tsakar gida na tadda Mama,anti Na'ima,anti Halima,da kuma yayata ta Rijiyar lemo anti Maimuna,na yi sallama na k'arasa inda suke a sanyaye,da na gaishe su ma babu wanda ya amsa,ni dai na d'auki buta na shige band'aki,ina shiga na duba wayata,na dannawa Nazifi kira,bugu biyu ya d'auka ko sallama ban jira ya yi ba,na fara magana
"Nazifi me kuka yi min?"

Ya ce"ya ya? Da fatan komai ya tafi daidai,ban kira ki bane saboda kar a samu matsala".

"Wai da gaske an yi min fyad'e?" Na tambaye shi,cikin zafi-zafi.

Ya yi dariya ya ce"haba Zinatu! Zargi na kike yi?"

Na ce"ka ga kawai ka sanar min!"

Ya ce"wallahi Zinatu babu wani fyad'e da aka yi miki,kuma cikin mu babu wanda ya tab'a ki".

Na d'an ji dama-dama a raina, na ce"ta ya zan yarda da kai,bayan na ga kun canza min kaya?"

"Wallahi mace ce ta canza miki kaya,ba mu ba". Ya fad'a

Sai na yi mamaki,na ce" to wace ita? A ina kuka samo ta? Kuma jinin jikin rigar fa!?"

Ya ce"k'anwar abokina ce,kuma ta ina za mu samu jini? Zob'o ne muka zuba".

Har raina na yarda da zancen sa,ashe ya b'oye min wani babban abu,sai nan gaba za ku ji illar da suka yi min!

Na ce"to amma meyesa duka jikina yake ciwo? Kuma maganin bacci kuka bani ko?"

Ya yi dariya ya ce"ai dole jikinki ya yi ciwo,tunda ba ki tab'a shan irin k'wayar ba,ke ta ma fa sake ki da wuri".

Na ce"amma Nazifi meyasa kuka ba ni k'waya?"

Ya ce"to Zinatu gani na yi idan idonki biyu za ki iya kawo cikas wurin gudanar da aikin,ko kuma bayan mun kai ki,ki ji tsoro daga baya ki lalata aikin,amma wallahi babu abin da aka yi miki".

Na sauke ajiyar zuciya na ce"to shi ke nan,Nazifi na gode sosai, Allah ya biya ku".

"Amin matar oga J.S" Ya fad'a yana dariya. Na yi murmushi na kashe kiran.

Bayan na fito aka tisa ni a gaba,da fad'a kamar za a min ciki da hak'ora,ni dai ban wani damu da hayaniyar su ba,tunda dama na san ta zama wajibi,kuma ko dukana za a yi tunda burina zai cika ba zan damu ba.Bayan sun gama bambamin su,sai kuma suka sakko suna tambaya ta a inda na had'u da Salim har ya min fyad'e,na fad'a musu dama can saurayina ne,kuma ba halinsa bane,shi ma tsautsayi ne ya afka masa.

Anti ta katse ni da fad'in"to idan ma halinsa ne cutar y'ay'an mutane ai yanzu ya yi wanda ba zai kub'uta ba,don kuwa yanzu sati d'aya aka tsayar auren ku".

Na ji zuciyata ta motsa,sai na rasa farinciki zan ji ko akasin sa? Ni dai abu d'aya da na tsana yanzu bai wuce yanda y'an'uwana su ke yiwa Salim kallon macuci ba,na san alhaki a kaina,sai dai na kan ji dama-dama idan na tuna da anyi auren komai zai wuce...

Na tashi na shige d'aki,na kwanta,ina jiyo tattaunawar su,har aka kira la'asar.

Ina idar da sallar la'asar Baba ya shigo,ya kira ni,na zo na tsugunna kaina a k'asa,to shima dai fad'an ne babu k'akk'autawa,kuma ya tabbatar min ranar Asabar za a d'aura aurenmu da Salim, kamar yanda mahaifinsa ya tsara, ya ce min shi ma kuma ya amince don shi ne kawai mafita a gareni.

Washegari da safe Anti Maimuna yi min waya, ta ce na je gidan Ummi yanzu, na shirya na tafi ina ta fargaba.A d'akin Umma na same ta,na zauna na gaishe su suka amsa babu yabo babu fallasa,na yi shiru ina jiran ta inda za su fara tasu tijarar,jin shirun ya yi yawa na ce"Ummi ga ni".

Ta ce"ai na gan ki, me zan yi miki? Ko na kira ki ne?"

Na ce"Anti Maimuna ta ce na zo".

Ta ce"to ki kira ta ki tambayi wurin wanda za ki je,ni dai ban kira ki ba".

Na sunkuyar da kai na ce"don Allah Ummi ki yi hak'uri".

Ta ce"hak'uri ai ke ya kama Zinatu,ke da za ki zama MATAR SHIGE...".

Babu wanda ya sake yi min magana, har dai na gaji da zama na,na tashi na koma gida. Tun daga nesa na hango Habib a k'ofar gidanmu,na k'araso na yi masa kallo d'aya,ina niyyar shigewa ya zo ya tare hanya,sannan ya ce"Zinatu zan yi magana da ke".

Ban ce komai ba,na tsaya sauraron shi

Ya ce"yaushe ku ka had'u da J.S,har kuka yi nisa a soyayya ban sani ba?"

"Ba mu dad'e ba" Na ba shi amsa.

Ya ce"kuma da gaske ne ya yi miki fyad'e?"

Na ce"to kai meye matsalar ka da hakan?"

Ya ce"amma ai kin san ya kamata na sani ko?"

Na ce"saboda me?"

Ya ce"saboda ni zan aureki,kin ga kuwa ya dace na san komai game da matsalar".

Na yi shiru ina mamakin sa.

Ya d'ora da fad'in"saura fa sati biyu ya rage,zuwa gobe na ke son a buga invitation,sai ki lissafi abin da ki ke buk'ata,na baki kud'in,lokaci ya na k'urewa".

Daga haka ya tafi,ya bar ni tsaye da mamakin sa.



SALIM

Tunda ya maida su Zinatu ,gida ya dawo ya kwanta,zuciyarsa fal bak'inciki,ya san dai ko giyar wake ya sha bai isa ya kalli Abba ya ce masa ba zai auri Zinatu ba,shi a yanzu ba ma auren nata ne damuwarsa ba,yanda Junaina za ta d'auki lamarin kawai ya ke ji,ace aure nan da sati d'aya? Anya kuwa za ta yarda da shi?

Ya tashi zaune jin k'irjinsa ya yi masa nauyi,ya je ya d'akko lemo a fridge ya yi had'in k'wayoyin sa,ya fara kwankwad'a.

Ya na cikin wannan yanayin Baby ta zo ta same shi,kasa ajiye jarkar ya yi,saboda burinsa kawai ya shanye ya samu bacci ko zai samu nutsuwa.

Ta na k'araso wa,ta warce jarkar ta jefar,ta zauna ta fashe da kuka, ya dafe kansa ya na furzar da iska. Ta ce"Yaya..."

Ba ta k'arasa ba ya katse ta"wallahi Baby Zinatu sharri ta yi min,ban san komai ba".

Ta ce"na sani,kuma ko na sakan d'aya ban tab'a zarginka ba Yaya,wallahi na yarda shiri ne kawai,saboda son da take yi maka,ga shi har son ya na nema ya zama k'iyayya".

Ta d'ora da fad'in"Yaya shaye-shaye ba mafita bane,da wannan abun da ka zauna ka na sha da alwala ka yi,ka tada sallah ki ka yi ta karatun k'ur'ani,idan ma ba ka da nutsuwar karaton ka kunna ka yi ta saurara,za ka ji sauk'i a zuciyarka".

Haka ta yi ta kwantar masa da hankali har sai da ya nutsu.


HABIB
Da daddare Baba ya kira Habib,ya zo gidanmu,bayan sun gaisa Baba bai b'oye masa komai ba,ya zayyane masa halin da ake ciki,tunda a zaton sa shi bai sani ba,ya d'ora da fad'in "Habib na san ka na son Zinatu,amma a irin yanayin da ta shiga yanzu ya zama dole ka hak'ura da ita,shi wanda ya yi b'arnar shi ya dace ya aure ta,ya zauna da ita".

Habib ya ce" Baba,son da na ke yiwa Zinatu na tsakani da Allah ne,ba gangar jikinta na ke so ba,kuma idan ni d'an'uwanta bai yarda da aurenta a halin da ta shiga ba,waye zai yarda?"

Baba ya ce"ai shi mahaifin yaron ya tilasta masa auren ta,don haka babu wata sauran matsala".

"Shi ne ma babbar matsalar Baba" Habib ya fad'a.

Ya d'ora "wallahi Baba ina jin tsoron kar ayi masa tilas ya aure ta,ba da son ransa ba,kuma ya zo ya na k'untata mata daga baya.Ni fa na ce,na ji na yarda,zan aure ta a hakan kuma mu zauna lafiya ba tare da na nuna mata alamar na sani ba".

Baba ya sauke numfashi ya ce" wata sabuwa! To a gaskiya da farko na yi zaton idan ka ji haka za ka fasa aurenta,shi ya sa ma har na amincewa mahaifin yaron,amma yanzu zan sanar masa da na janye maganar,shikenan komai ya wuce,tunda itama ai da nata laifin".

Habib ya ce"to Baba na gode,Allah ya saka"

"Amin Habibu,ni ne da godiya, ka je ka cigaba da shiri" Baba ya fad'a.


Ina kwance na ji shigowar sak'o wayata,na duba da sauri ganin sak'on Habib ne

_"Zinatu son gaske nake yi miki ba na k'arya ba,don haka ba na jin wannan k'aramar matsalar za ta sa na fasa aurenki.Ki kwantar da hankalin ki,har yanzu akwai maganar aurenmu"_.

_"Habibu! Ba na son ka,kuma ba zan aure ka,Salim zan aura in sha Allah!"_ Na maida masa da amsa.


_"Wallahi sai kin aureni Zinatu,ko kuma ki yi danasani, da nadama mabayyabiya!"_

Ya maido min da amsa.
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_


BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_


*&þFIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION&þ*


Page 21


*BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE*

*I selling MTN data with this cheap price*

*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
10GB@===2,600
15GB@===3850
20GB@===5000
40GB@===9900
Dial *460*260# to check Data balance.
*Validity 1 month*

*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *Whatsapp OR
Call 08066268951*



Na tashi zaune ina sake kallon sak'on da d'umbin mamaki,lallai Habib ya na son wargaza min shirina,aikuwa yanzu ne zan d'aura d'amarar zabga masa madarar rashin mutunci,don wallahi ba zai sani na yi wahalar banza akan Salim ba,na kira shi bai d'auka ba,sai sak'on da ya sake turo min me d'auke da kalamar _"I love you "_. Ban samu bacci ba a daren har sai da na samawa kaina mafitar da ta dace.

Washegari da sassafe na tafi gidan su Ummi,na samu dai yau ta kula ni,ta yi ta min nasiha a tsanake,na tambaye ta Kawu Sabi'u,ta ce ya na d'akinsa ba ya jin dad'i,ta ce jiya ma shi ya yi ta tausar Kawu Ummaru,don cewa ya yi sai ya zaneni,na yi farinciki kuwa don dama wurin sa na zo,na ce mata zan shiga na duba shi.

Ina fitowa tsakar gidan na ga Kawu Ummaru ya na shirin fita,ya zabga min wata kafirar harara,na sunkuyar da kai na gaishe shi,bai amsa ba sai k'wafa da ya yi ya fice,na tab'e baki ina bin bayansa da harara sannan na yi sallama a d'akin da Kawu Sabi'u ya ke.

Ya amsa,ya min izinin shiga,na shiga da sallama kaina a k'asa,ko fuskata ba na son ya gani,saboda nauyin zancen da na zo masa da shi, kamar amarya haka na nemi wuri na rakub'e,ina sake jawo hijjabina,na gaishe sa na yi masa ya jiki,ya amsa,na yi shiru na d'an lokaci kafin na ce" Kawu dama wata magana ce nake son yi maka"

Ya ce"to Zinatu,ina jinki".

Na ce"dama akan zancen aurenmu da Habib ne".

Ya ce"to,wani abun ne kuma ya taso? Ba an ce ya yarda zai aureki a hakan ba?"

Na ce"e,amma ni Kawu wallahi na fi son na auri shi Salim d'in".

Ya ce"meyasa?"

Na yi kalar tausayi na ce"wallahi Kawu ni ina tsoron wulak'ancin da zai biyo baya,wannan abun da ya faru k'addara ce,kuma ni a yanda nake gani Habibu zai aureni ne kawai saboda mugunta,wallahi yanzu ba so na ya ke ba...".

Sai na ga ya had'e rai,ya ce"shi ya fad'a miki yanzu ya daina son ki?" Na girgiza kai,alamar a'a.

Ya ce"to kul! Na sake jin haka daga bakinki,babban rufin asirinki shi ne ki auri Habibu,don kuwa shi ne kawai zai iya zama da ke ba tare da wata tsangwama ba,saboda irin yanda ya ke son ki,kuma ke ma sai bayan auren za ki fahimci abin da ake fad'a miki".

"Ba za ku gane ba!" Na fad'a a zuciyata.Wani takaici ya rufeni,nan take kuma wata dabarar ta fad'o min,wadda nake kyautata zaton ita ce ma babbar mafita,amma ni da na tsaya duhun kai ban aiwatar ba.

Na tashi na fita daga d'akin,ina jin takaicin su na rashin fahimtata,sallama na yi wa Ummi,na tafi,kai tsaye bakin titi na yi,na siyi sabon sim na saka a wayata,na yi gida.

Ina zuwa k'ofar gida na tadda motar Salim ta na k'ok'arin tsayawa a k'ofar gidanmu.Na ji irin abinda na ke ji idan na gan shi a y'an kwanakin nan,tsayawa na yi har ya daidaita fakin ya fito,mu ka tsaya muna kallon kallo na tsawon minti biyu kafin na k'arasa inda yake,na gaishe shi ina sunne kai,ya amsa fuska babu yabo babu fallasa,sannan ya mik'o min y'ar jakar da take hannunsa ya ce"congratulation Mrs Muhammad Salim!".

Na karb'a ina mamakin maganar sa,tun kafin na bud'e jakar ya shige mota ya bar unguwar. Na shiga gida,har ina tuntub'e saboda sauri,ina shiga d'aki na bud'e jakar,wani abu ya caki zuciyata ganin abin da yake ciki,invitation ne me kyaun gaske,d'auke da sunana da na shi,na duba date d'in na ga kwanaki biyar ya rage aurenmu.

Na fad'a katifata ina yin siririyar dariyar farinciki,can kuma na rungume katin na fara hawaye.

Na jima a haka,sannan na zabura kamar an tsikare ni,na d'auki wayata na saka sabon sim d'in,na nemo lambar mahaifiyar Habib,sai dai duk rashin kunyata sai na ji ba zan iya aiwatar
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment