Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels


Home / ZURFIN CIKI novels / ZURFIN CIKI book 1 part 1
ZURFIN CIKI book 1 part 1
Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 - 02:16
UUmmi tana tafe tana yan wakokinta, tareda gudu
hade da tsalle. cinikin ummi ne gudu, sam bata
tafiya a hankali.daga can gefe ta hango wata
yarinya wadda bazata wuce sa'arta ba.
tace,"yauwa,ga firdausin data tsokane ni" ta nufi
wurinta ,tasha gabanta ta rike kugu. "fiddausi wa
kike tsokana? fiddausi tace "ban tsokane ki ba
fa".cikin tsoro tayi maganar .ummi ta shako mata
wuya. ina jin lokacin da kika ce ummi tsiga.ban
ce ba inji fiddausi .ummi ta hankada ta tare da
cewa "Allah yaso ki." nikan garin da fiddausin tayi
ya tarwatse a kasa tace "kin gani ko? wallahi sai
kin biyani"ta soma kuka,ummi ta sheka da
gudu,sai gida. tana ajiye man gyadan data siyo ta
nufi ba daki don fitsari ya matse ta .umma dake
zaune tana fadin. "da mutum!da mutum!!" saida
ummi ta bude . Ganin yaya Abba tayi,da gudu ta
juyo ta fada dakin umma,jiki na bari bayan tayi
bol da dakakken yajin da umma ta daka zata
soya mai don cin abincin rana. sai kuma ta tuna
cewa bata tsira ba,don Abba tsaf zai binciko ta.ta
fito da gudu ta nufi dakin tsohuwa. tsohuwar tana
sallar azahar.ummi ta tsallake ta ta kutsa kasan
gado.nan ma tayi ciki da furar da tsohuwar keson
sha da zarar ta idar da sallah. Alhaji babba tasa
ya aiko mata da furar daga kasuwa.don tasha da
rana. Abba ya fito wanka ranshi a bace.dakin
umma ya nufa yana fadin "ummi ke ummi zonan"
Ya samu Umma tana tattara yajin da Ummi ta
zubar, tana fada. Ya ce, "Umma ban san irin
dukan da zan wa Ummi ba yau. Ta ce,"Abba ka
mata dukan mutuwa, na gaji da halin Ummi.
Yarinya sai ka ce 'yar fata? Ka dubata ta tafi
dakin Tsohuwa, don ta san zata hana a dake ta."
Ya ce,"Allah sai dai Tsohuwa ta yi ta fadanta,
amma ba zan barta ba. Ya juya zai tafi, suka ji
muryar Tsohuwa tana fadin. Ba zan yi fada ba, ka
kashe ta ka ji mai sunan Malam, ba na son ka
barta da rai. Ta dubi Umma" ke kuma Suwaiba
dama kin san ba za ki daraja sunana ba ki ka sa
a ka sa miki don kiji dadin ci min fuska?" Umma
ta ce," Ba haka ba ne Tsohuwa, Ummi ba ta yo
halinki ba. Ita fa rashin hankali ne da ita. Yayanta
fa ke wanka ta zo ta leka shi, nan kuma tazo ta
zubar min da barkono. Abba ya ce, "Umma don
Allah kiyi shiru ki kyale Tsohuwar nan, ai ita ta
6ata Ummin, duk abn da yarinyar nan tayi sai ta
hana a yi mata fada. Uhm duk fadanki yau sai na
dake ta, ba sunan ki ba in ma kece,"Tsohuwa
tasa kuka gami da salati. "Yanzu mai sunan
Malam ni ka ke fadawa haka?" ya ce, "An fada
miki." Umma ta ce, "kai Abba zan sa6a maka
jeka." Ta juyo wurin Tsohuwa, Don Allah kiyi
hakuri............... Maman Fiddausi ce tayi sallama
tare da Fiddausin suka shigo. Ran Maman
Fiddausin a 6ace, ta tsaya rike da gari a
hannunta ta dubi Umma. Ta ce, Umman Abba
dubi abn da Umminki tayi min don Allah, yarinyar
nan tayo nika da kyar," tun safe sai yanzu na
samu, amma ta zubar min." Abba ya ce, Kinga
halinta ko?" Tsohuwa ta ce, "Wannan ba matar
Bala ba ce?" Maman Fiddausi ta ce, "Ni ce." Ta
ce," To kije kije ki nemi wanda ya zubar da
garinki, Ummi ko fita ba tayi ba. Umma ta ce, "
Ta fita Tsohuwa, na aike ta siyan mai." Tsohuwa
ta ce," Tsokanarta a ka yi to. Umma ta amshe
abin garin ta zuba musu, sannan ta ce, "Don
Allah Tine kiyi hkr." Abba ya nufi daki. Sai da ya
shirya tsaf, sannan ya dauki belt ya nufi cikin
gida, dakin Tsohuwa ya shiga kai-tsaye kasan
gado ya nufa. Ya jawo ta, ta soma kurma ihu.
Daya ya lafta mata amma ta dane shi tare da
cukwikuye belt din tana ihu. Tsohuwa ta iso tana
dukanshi a baya, fadi take "Za ka kasheta ne?
Jama"a kuyo dauki. Haushin hakan yasa shi
damko kanta ya shiga zuba mata kola, ya
sirmiyota ya shiga lafta da takalminshi, tunda ta
hana belt din. Sai da ya mata tas, sannan ya fita
ya bar su, Tsohuwa na kuka Ummi na kuka. , Sai
da komai ya natsa ta leka ta jawo furarta don
tasha, sai ta ganta a zube. Ta ce, A" a ke ki ka
zubar min da fura?" Ummi ta ce, To ba shi ne
janyo ni ba Yaa Abban. Tsohuwa ta ce, "Ai ko sai
ya siyo min furata. Ta mike ta wuce Umma tana
rabon abinci, ta nufi soro in da dakin Abba yake
(Zaure) Ya fito yana rufe kofa, ta ce "Au za ka
fita ba? To ka sawo min furata da ka zubar. Ko
kallonta bai yi ba ya rufe kofarshi ya wuce. Ta ce
mishi "Aikin bana, in ba siyo min ba ubanka ai ya
dawo ko min dare ya sito min. Abba ya ce, Ku ku
ka sani. Ra ce, kaima ka sani, dan jakar uba. Ta
dawo ciki tana mitar ya cika bakin rai. Umma ta
ce, "Ina Abban? Tsohuwa ta ce, "Ya tafi, in bai
sai min furata ba ranshi zai 6aci yau a gidannan.
Umma ta ce "Ni bai ma ci abinci ba ya fita, ke
Ummi zo ki kira min shi, yunwa fa yake ji.
Tsohuwa ta ce, "Ba za ta kira shi ba, ya dake ta
sannan ta kira shi? Tunda bai barta taci da dadin
rai ba, shi ma ba ya ci ba.,, Umma tayi shiry,sai
haushin Ummi da take ji kamar ta shake ta ta
mutu. Ummi tayi wanka ta zura kayan Mkrnt,
tana saka sandal Umma ta ce, "Ina Ummi? Zo
nan." Ummi ta tafi tana cewa a ranta. "ALLAH
YASA DAKIN YAYA ABBA ZA TA AIKE NI, SAI NA
RAMA DUKAN DA YA YI MIN JIYA, DON YANZUN
DUK ME YA MIN SAI NA RAMA.........." Umma ta
katse mata tunani da cewa,"dauki shayin Abba ki
kai masa kada yayi latti,kai shayin ki dawo ki
dauki dankalin,yau shi kadai ma nayiwa dankalin."
Tace,"nifa?"umma tace "ke kina cin dumame
Abba ko ba ya ci,dan haka dan wanda ya rage
shi nayi wa." Ummi ta figi kayan tea din ta nufi
dakin Abba tana tura baki.tare da sallama bata
jira amsa ba,ta daga labule ta fada. Dabi'ar da
yake mata fada akai kullum,ya gama saka
singiletinshi kenan yana kokarin saka riga. Yace,
"wai ke wace irin majanuniya ce?ban ce miki in
kinyi sallama sallama sai na amsa za ki shigo
ba? sai kawai ta saki tiren,ruwan zafin ya zube
masa a kafa,dankalin ya watse kan rigar da zai
saka. tayo waje da gudu,sai dakin tsohuwa.ya
fito da sauri yana cewa,"umma ta kona ni! ta
kona ni!!" da sauri umma ta fito daga dakin Alhaji
babba,shima Alhajin na biye da ita yana fadin
"wacece ta kona ka?" Yace "ummi ce! ummi
ce!!."nan take Alhaji babba ya rike kafar yana tofa
mishi addu'a. Umma ta debo kullun kamu ta zuba
mishi,amma duk da haka sai da yan yatsun
kafarsa suka kumbura. tsohuwa ta fito daga daki
tana fadin,"kai ummi bata ji? wai ni meyasa aka
sa mata sunana?" Abba ya kalli tsohuwa cikin
takaici yace,"duk ba ke kike daure mata gindi ba?"
Umma ta shiga dakin tsohuwa ta janye kayan da
tsohuwa ta jera don kada aga ummi,ta janyota
tun daga dakin take kwallo da ummi har waje.
Alhaji ma yau har dashi aka zane ummi,tsohuwa
dai sai yan mitoci take yi,wai yanxu haka ma
bata sani bane. Abba dai ranar dai bai je
makaranta ba,haka nan da yamma sai da ya saka
ummi a dakinshi ya bata gwale-gwale sannan ya
zane ta. misalin hudu da rabi na yamma,Ahmad
abokin Abba yayi sallama a kofar gidan,Abba ya
amsa ya fito. Suna zaune kan dakalin kofar gidan
suna hira,sai ga ummi ta yanko da gudu tana
waiwayen baya. Ya ce,"zo nan."tazo yace,"kinyo
tsokanar fada ko?" tace,"a'a.yace in har tsokana
ki kayo zaki sani shegiya mummuna kazama. Ta
murguda baki,yasa takalmi ya jefeta,ta shige gida
sai ko ga wani yaro jiki duk kwata yayyanshi na
biye dashi. ya tambayesu,suka ce "ummi ce ta
jefa shi kwata"ya taso yaron har cikin gida ya
kamota dakin tsohuwa ya tsareta ta wanke ma
yaron jiki,ta kuma wanke kayan. sannan ya
zuzzuba mata kola a kai.tsohuwa tana ta yiwa
yaran fada,wai ita ma su daina tsokanarta Umma
ko lekowa bata yi ba,ya fito ya samu Ahmad yana
cewa "kayi hakuri na barka kai kadai." Ahmad
yace,"ba komai" sai Abba ya zauna sannan
Ahmad ya dube shi. Abba wannan kanwar taka
kuwa bata da Aljanu? Abba yace,"ba kowa
akanta,sai iskanci." Ahmad yace."a'a,kai dai ku
kaita ayi mata rukiyya." Abba yayi dariya,sannan
yace kasan Allah ba kowa akan ummi,saboda
Alhaji karami ya taba yin wannan tunanin. ya
dauke ta yakai ta rukiya bata da komai."Ahmad
yace tabdi!,gaskiya in ta isa aure duk wanda ya
aureta akwai aiki babba a tare dashi. Abba ya
ce,"wane mahaukaci ne ma zaya dibar ma kansa
ummi?"Ahmad ya ce,"sai ai muku hadin ggida..."
ya kaima Ahmad naushi a gefen ciki,Ahmad ya
kauce yana masa dariya. Abba ya ce,"ka cuce
ni,ace in auri ummi ai sai na hada kayana na bar
garin nan. nan. Ahmad ya s heke da dariya har
da rike ciki.sannan ya ce,"don me? Abba ya
ce,"to wannan yarinyar ba sai ta hada maka
gobara gida ba?gata kazama ga muni." Ahmad ya
ce,"kama dai kuke yi." Abba ya bata rai,"Ahmad
bana so.in har da gaske ina kamada ummi ba sai
na koma ciki an sake haifana ba. Don Allah ni
tashi ma ka tafi,don wallahi da don kai bane kake
fada min haka da sai munyi rigima,na tsani
ummi,bana sonta sam! Zaune suke a kofar gidan
Alhaji babba kan katuwar tabarma,sun jere abinci
suna ci. kullum Alhaji babba da Alhaji karami nan
suke zama tamkar tagwaye,suna matukar kama.
mafi yawancin lokuta ma kaya iri daya suke
sakawa,domin Alhaji babba duk kayan daya saya
tare yake sai musu. haka nan hula ko
takalmi,haka nan matansu baya
bambantawa.shima Alhaji karami duk da bai kai
samun babba ba yana koyi dashi. Alhaji babba ya
kalli karami yace,"Aminu ya zancen makarantar
bashir?" Alhaji karami ya dubi wansa ya ce,"Alhaji
bashi fa ya fadi jarabawa,jiya na tsare shi da
maganar sakamakon jarabawarshi yace bai duba
ba,saida yaji nace zan hada shi da Abba suje
sannan yace min yaje wai duk ya fadi. Alhaji
babba yace,"Ash sha! sai ya maimata shekara
kenan?"Alhaji karami ya ce,"to in ma ba zai
maimaita ba Alhaji shi ya sani,ba sahura ta bata
su ba? shi Abba ai ba haka yayi ba,ka dubi fa
yadda yaki aikin kanikancin nan,uwarshi ta zuga
shi wai yayi karatu kadai yayi aikin gwamnati.
kullum haka sahura take kitsa ma yaran."Alhaji
babba yayi yar dariyar takaici,sannan yace"in
banda abin sahura yadda kasan nan tamu ta
zama waye zaici alwashin aikin gwamnati? ina ce
masu digree ne ke yawo ba aiki?" "har masu
masters." inji Alhaji karami.ya tashi zaune daga
kishingidar da yayi,yace dubi misalin dan
abokinnan naka Alhaji buhari." Alhaji babba ya
ce,"kwarai kuwa,mas'ud ba.yanxu ma fa kasuwa
yake zuwa,sai yanxun yake koyon kasuwancin."
Alhaji karami ya ce,"to daya dora shi a kasuwar
fa tun farko?shi yasa na fada ma sahura ta bar
yara su hada da sana'ar hannu. Donni dai yaro
kamar bashir yanxun ba zan dauki kudina in ba
shi ba."Alhaji babba yace,"shi yasa kulum nake
kara son Abba,yaron nan da kanshi yace min in
kai shi shagon dinki. Har naki suwaiba ta
ce,"Alhaji ka kai shi in ya iya sana'ar hannu ko
bai samu aikin gwamnati ba zai rike kanshi da
sana'ar nan." Alhaji karami ya ce,"to ai kasan ita
suwaiba tasan abinda take yi.amma sahura sai
addu'a." Sallamar Abba ce ta katse su,ya zauna
can gefe sannan ya gaishe su,duk suka amsa tare
da tara hankulasu gurinshi. Ya mika ma Alhaji
babba kullin takarda tare da cewa "Alhaji gashi
maganin (ulser)ne" Alhaji babba ya amsa ya
ce,"Abba sarkin amsa magani, a gurin wa ka
samo wannan kuma?" ya ce,"Ahmad abokina na
raka ya amso ma babanshi,shine nace bari in
amso muku" yace to Allah ya saka da
alkairi."Alhajikarami yace"dame ake sha?" Abba
ya ce,"da madara peak." suka ce"to" daya mike
zai shiga gida Alhaji babba yace ya shige da
kwanikan abincin. yau kam Abba bacci yake ji da
wuri,don haka ya baro shagon dinkinsu wanda ya
kan kai goman dare a ciki ya nufo gida. Ya bude
dakinshi ya shiga ya cire riga sai singileti da
gajeren wando na jeans.ya nufi ciki don ya kama
ruwa ya kuma yi wa ummanshi sallama. tsakar
gida ya sameta zaune ta zabga tagumi,inda
abinda Abba ya tsana shine,yaga ummanshi cikin
damuwa. da sauri ya isa wurinta,"umma
lafiya?"ta dube shi "ina fa lafiya,ummi ce tunda
tayi sallar isha'i ta fice kusan awa guda zance
jiya ka mata dukan fita wasan dare?" Abba yace
"to wai me za'a yi wa ummi ne ta zama irin
sauran yara?" umma tace,"addu'a ce Abba,kuma
muna yi kullum." ya juya cikin bacin rai,layin su
Amina kawarta ya nufa,don bata wuce can.duk da
cewa Amina bata kaita rashin ji ba. can din kuwa
ya sameta,ta tara zugan yayan layi sai tsokanar
fada suke yi,ita ce shugaba. wata falwaya Abba
ya samu ya jingina yana kallonsu,don yana iya
tunkararta su diba da gudu. shi kam ba za ya iya
guje-gujen nan ba,duk wanda yazo wucewa sai
sun tsokane shi,wani su jefe shi,wani kasa zasu
watsa masa su gudu wani kuma rigarsa zasu ja.
c can wani shida budurwarsa sun zo wucewa ta
fizge ledar hannunsu ta watsar,sannan suka ruga
da gudu. tayo gurin da Abba ke tsaye bata zaci
da mutum a gurin ba,sai dai taji anyi caraf da
ita.sai da Abba ya zabga mata koso a tsakiyar
kai har tayi fitsarin wuya,sannan ya tasata har
gurin mutumin data yaga ma ledar. suna
tsugunne suna tsintar lemunsu da ayaba ya
ce,"malam ga wadda ta yaga muku leda." da
zafin nama mutumin ya mike,Abba ya
ce,"gata"mutumin ya shakota yace yau sai naga
ubanki." Abba ya ce,"ko kara ka kai gidansu nine
zan hukuntata,don haka gata na kawo maka
kanwata ce kuma naga lokacin data tsokaneka."
jikin mutumin yayi sanyi ya ce,"na gode bawan
Allah,taje taci albarkacinka." Abba yace "daka
nade ta." mutumin yace,"ba komai,ke kuma ki
canza hali ke mace ce." Abba yace nagode"
sannan ya tasa ta zuwa gida. Bokiti ya cika da
ruwa ya dora mata,,umma rasa bakin magana
tayi daya sanar da ita tsokanar daya tarar da
ummi suna yi. Daga karshe ta ce,"Allah ya
shiryaki,abind ya sameki kada ya sami sauran
dangi. Alhaji kuwa daya sameta dauke da bokitin
tana kuka tana fadin "yaya Abba na tuba,bazan
sake ba." ya ce,"uwata bakya ji ne fatan Allah
yashirye ki."ya nufi dakinshi.tsohuwa takaicin
Abba ne ya hanata fitowa tayi magana. nata
ganin,ummi bata wuce fita tayi wasa da
kawayenta ba,a cewarta ba laifi ba ne. amma an
bi an tsangwami yarinya,an hanata walawa.sai da
Abba ya gaji dan kanshi sannan ya sauke mata
ruwan. Sannan ya mammaka mata
takalmi,sannan ta shige dakin
tsohuwa.tsohuwana daga kwance ta dubeta.
"yaga dama ya kyaleki?kai mai sunan malam
akwai mugunta.zo ki kwanta." cikin kuka ummi
tace,"kayana sun jike,bokitin ruwa fa ya dora
min."tsohuwa tace,"barshi da halinsa,ace mutum
ba zai sake ba?" ummi tace,"ai sai na rama,shima
din sai yayi kuka."tsohuwa ta ce,"a'a,kada ki
soma zancen ramakon nan.kin san ko kin rama
ke ce zaki kwan ciki." ummi ta ce,nifa sai na
rama."tsohuwa ta ce,"baki gaji da shan wahala
ba kema da shegiyar gaddama,ga zanina nan
kikin raki ciro ki daura kizo ki kwanta." ummi tayi
lamo bayan tsohuwa tana tunanin dame zata
rama abinda Abba yayi mata jiya.har bacci yayi
gaba da ita waiwaye............. SULAIMAN shine
asalin sunan Alhaji babba,Aminu kuma shine
Alhaji karami. tsohuwa itace mahaifiyar su,kuma
su kadai ne yayan data haifa.Asalinsu yan
zamfara ne a kauyen daji a karamar hukumar
kauran-namoda. malam Idris mahaifinsu shine ke
zuwa yawon fatauci,har Allah ya zaunar dashi a
garin kano,da matarshi Habiba. sunzo da
yayansu guda biyu,sulaiman da Aminu.sun yi
karatun muhammadiyya mai zurfi,amma basuyi
karatun boko ba. sannan ya dora sukan harkar
kasuwanci,Allahya albarkaci kasuwancin Sulaiman
inda harkoki suka bude mishi cikin kankanin
lokaci. matsalar shi daya rashin boko,malam
idrisu mahaifinsu yana daya daga cikin wadanda
basu amshi boko ba lokacin da tazo. Don haka
sam bai saka yayansa ba.Sulaiman ya auri
Suwaiba wadda suka dauki watanni suna
soyayya,ita yar unguwar sheka makaranta ce.
Amma asalinsu yan Daura ne jihar Katsina.kafin
aurensu sai da yayi gini a unguwa uku gidaje
guda biyu iri daya. Ya ce Aminu kaninsa ya zabi
gida duk da cewa a lokacin baiyi auren
ba,wannan abu yayi wa mahaifisu dadi. yayi ta
shiwa Sulaiman albarka,don haka sai aka rufe na
Aminu,yayin da sulaiman ya tare a nasa da
matarsa Suwaiba. / ZURFIN CIKI book 1 part 2
ZURFIN CIKI book 1 part 2
Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 - 21:40
Kwanci tashi 5yrs ta miqa suwaiba bata taba ko
batan wata ba. awannan yr ne mahaifinsu ya
cimma 1yr da rasuwa. saida aka watse makoki
danginsu na qauran-namoda suka koma. sannan
sulaiman yace da aminu, to ni xan dauki tsohuwa
in maida ta gidana,kai kuma aminu ka fito da
mata kayi aurenka dan mu xauna kusa da juna.
tsohuwa ta saka kuka tace wannan yaran nidai
da ka barni na xauna da gidan xai xama kufai.
sulaiman yace tsohuwa kiyi haquri, sai a saka
haya.aminu yace haka xa ayi. daqar tsohuwa ta
yarda dan tace ita wannan gidan mutuwane xata
rabata dashi, dan gidane me tsohon tarihi a
gurinta. ta ce gidan da mijinta ya rasu gidan da
ya kawo ta tun tanada jajayen sawunta. suka dai
lallabata. lkcn da aminu ya gabatar da sahura a
matsayin matan da xai aura, tsohuwa ta tuma ta
ce ba ta laminta ba, don kuwa kowa yasan
mahaifiyar sahura gun masifa. sanna sahurace ta
gajeta. aminu sai ya watsar da mgnn auran
gabaki daya har tsawan lkc. sulaiman yanata
roqan tsohuwa ta amince, dan ya lura aminu yayi
nisa. Ba yadda tsohuwa ta iya, dole ta amince,
aka sha biki ta tare gidan aminu. mai hali dai
baya fasawa, dan sahura batasan hulda da
suwaiba da surukarta, gashi daga kawota ko
2mth bata yiba ta kama fada da yan unguwa. a
cikin 3yrs sahura aka samu ciki. lkcn sulaiman ya
samu xiyarta qasa mai tsarki shida tsohuwa dan
sauke farali. sunyi addu'a allah ya bashi xuri'a
shida aminu.suna durowa gida suka samu lbrn
cikin sahura, murna a gun sulaiman tamkar
matanshi ne keda cikin.lkcn haihuwa tahaifi da
namiji murna gun yan uwa biyu ba'a magana,
anyi shagalin suna inda yaro yaci sunnan mahai
finsu wato idris shine suke kiranshi abba. Sannan
Ahaji Sulaiman ya biyama qaninshi kugeran
makka daga nan ne aka samu ahj Babba da ahj
qarami tun abba yana jariri ahj babba da
matanshi suke dawainiya dashi Sahura ba taso
saidai ba yan da xaitai da ita. domin alj qarami
na gama shirin fita xai saba shi sai gidan sai yayi
kukan nono ake maida shi, saidai tayi ta mitar
cewa anriqe mata yaro gidan,sahura dai in an
kawoshi bata isa taxoba dan tasan tsohuwa
tafita danja.duk da gugar xana da haibaici da
sahura take antayo ma suwaiba ta katanga ko
inta je gidan, baisa ta daina dawainiya da abba
ba. cikin hakane sahura wata ran sahura ta tashi
da xaxxabi mai tsanani da amai, shine taje asibiti
ganin likita ya tabbatar mata da tana dauke da
ciki.ko da ta fadama alj qarami ba qaramin murra
yayi ba ita kuma ta batarai, yace tunda abba
yana tafiyan shi ko ina ayaye shi. Da yamma
bayan yadawo kasuwa ya shiga gaida tsohuwa
shine yake gayamata xa'a yaye abba. tace
saboda me? ku barshi yayi 2yrs. sai yace ai uwan
tanada juna biyune, shi yasa, daman sha waran
da nakesan fada maki shine xanba yaya shi
kyauta har abada.tsohuwa tace kai amma ka
kyauta. Washegari da safe shine ma yayi ma
abba wanka tana kwance ya shirya shi, sannan
yace mata ta hada kayanshi duka dan xan kaishi
gidan ahj babba gaba daya. tace kana nufin kayi
kyauta dashi gaba daya? yace ea. tace tabdi!,ba
xai yiwu ba. infishari banxane kaxa tayi mana. su
wa yace kada su dage su samu nasu dan? nima
wahala nasha na haifi dan, ba shago na bude ya
fito ba....sam bai kulata ba, ya hada kayan yaran
ya fita. ya shiga gidan ahj babba da shi. dakin
tsohuwa ya shiga, nan ya samu ahj babba suna
gaisawa, yace yauwa, dama gurinka naxo yaya.
abba ya sauka daga jikin babansa yaje jikin ahj
babba da gudu, ahj ya dauke shi ya rungume. Ahj
qarami ya keqa ya kira suwaiba,ta shigo ta xauna
sai ahj qarami ya soma jawabi da cewa. tsohuwa
ina san ki xama sheda, yaran nan na ba yaya da
suwaiba har abada.ahj babba yasake rungume
yaran a jikinshi wani saban son shi ya ratsa shi.
idanshi suka kawo qwalla, suwaiba ta sa kuka
tace mun gode da wanna abu da ka yi mana.
Allah ya bamu ikon riqeshi da amana. ahj babba
yace bani da bakin da xan maka godiya, saidai
ince allah ya qara xumunci. ahj qarami yace haba
yaya dana nakane, saidai inasan abba ya xama
xaka kai daya. tsohuwa tace allah ya maku
albarka daku da yayanku, kaima allah ya baka
haihuwa. sukace amin. Sahura kuwa mijinta na
fita da yaro, itama ta xari hijabi ta nufi gidan
iyayanta, ta shaida ma mamanta cewan aminu
yayi kyauta da danta, kuma yaba mutanan da
basa qaunan ta. nan da nan uwar tahau masifar
cewan ba xai yuyu ba, ai dole ya baki danki.
shiko uban cewa yayi ai ikon sane, dan haka
baiga laifinsa ba dan yaba dan uwansa dansa.
sannan yace ,ta tashi ta koma. uwar tace ba xata
koma ba, ya ce ta xauna. bai sake bi ta kansu ba,
ya ci gaba da harkokinsa. shiko ahj qarami cewa
yayi baxai bita ba, lokacin da ya dawo ya samu
batanan, sannan bai fadama dan uwansa ba har
aka kwana. sukuma su suwaiba basu fahinci
sahura batanan ba dan ba hurda suke ba, saida
kukaxo cin abinki ahj qarami bai futo da kwanu
ba. sannan wan yace iyalin naka bata nanne?
yace yaji tayi, niko baxan bita ba. ahj babba yace
akan wani dalili ne? ahj qarami yace ban sani ba,
na dawo gida ban ganta ba. da safe ahj babba ya
tashi gaba sukaje gidan, sahura ba kunya tace
danta takesan ya dawo mata dashi, inhar yana
san xama da ita. Ahj babba yace, indai danta ne
xai maido shi. ahj qarami yace shi kuma inhar sai
an dawo da dan to ya haqura da auranta. kuma
na cikin ta ma inta haife shi xaixo ya ansa ya
qarama wansa inya so yaga yadda xatayi. duk
juyin da akayi yaqi yarda daga qarshe ma tafiyan
shi yayi. ubanta yace da ahj babba kaima jeka
yadda suka so haka xasu yi. satinta guda taka
abincin kirki gagaranta yake yi, ita kuma uwan ta
daina samun wani abu daga gun sahurar ke kawo
mata. dan haka suka yanke shawaran ta koma,
duk da haka saida ya shareta na kwana uku
sannan ya sakar mata. haka ta haqura saidai
tasha alwashin dun runtsi sai danta ya dawo
hannunta. sannan ta kulla sabuwan gaba da ahj
babba da suwaiba kuma tace duk tsohuwa ce
takitsa abin. abba yana samun kulawa tare da
tarbiya mai kyau.sahura ta haihu ta sake samun
da namiji aka samasa bashir, daga nan haihuwa
akai akai.. Tun abba yana qarami ya koyi wasu
halaiya na ahj babba. da farko, sallar
asuba,axahar, laasar, magrib da isha. ahj babba
kan tasa abba suje masallaci da rana kuma
umman sane ke turashi. ranan jumaa ahj na
dawowa gida dan ya tafi dashi. dan haka sallah
ta xauna ma abba da xaran
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment