Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[5/16, 5:52 AM] Aunty Fauzah Yar Amanah: *ZAN FASA KWAI*


*NA*

*HADIZA BARA'U GIDAN IKO*


_Hakkin Mallakar na gidan iko ne_



*Page 1*



*_________________________________*

*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*_________________________________*




*_Da sunan Allah me Rahama da jinkai ina godiya ga Ubangiji da ya yarda Zan fara sabon littafi na me suna ZAN FASA KWAI Ubangiji ka tsareni rubuta abinda ya kauce da tuntuben alkalami kasa ya zamo wa azi da izna_*



*Gaisuwa ga masoyan GIDAN IKO na kusa da na nesa Ina gaishe ku*



*_Sai Uwata haj Saliha abubkar abdllh Zaria gaisuwar ta muddin Rayuwa ce Allah ya dafa_*



"Talai Wai Ina Talai ta shige don tsohon wulakanci ta barni ina ta yage bakin kiranta?
Tsohuwar ta taho da sauri tamkar zata kifa saboda Jin Kiran uwar gijiyar ta akalla tsohuwar zata haurawa shekaru sittin koma fiye ta taho da sauri har tana cin tuntube kadan ya rage taci da kasa.

Ta wurgo Mata harara lokacin da take zubewa agabanta.
"Gani hajiya kiyi hakuri Ina bandaki naji kina Kira tun jiya Wallahi ciki ke murda min sai faman zagayawa nake......
"Ai nayi Zaton samun wuri ne yasa Kika fara nuna min kinaji Ina kwakwazon kiranki kikayi min kunnen uwar shegu dama ba Dole ciki ke rude Miki ba komai Kika samu wawab kin abkawa ciki sai kace jaka? Wani Abu ya daki zuciyar tsohuwa talai Jin Wai yau ita take Kira da jaka Amma ya ta iya tunda Ubangiji ya zano abincinta akar Kashin wannan Mata me masifar izza wadda ko saboda izzar tata ne ma aka rada Mata suna da izzatu? Ta katseta da wata tsawa tamkar zata fasa Mata dodon kunnen

"Da Allah Ni tashi ki Kai min jakata mota Kika sakani gaba kamar kin samu wata TV"
Tsohuwar ta Mike da azama ta dauki jakar ta hannu wadda Isa da izza ke Hana Mata dauka Wai sai an Kai Mata duk in zata fita.

Tabi bayan tsohuwar tana sababi inda tsohuwar kamar zata fashe da kuka saboda Jin abinda ake fada Mata ba Diya ba jika ma tayi da ita Amma saboda kawai tana Yar aiki sai ake sauke Mata kowane kalar wulakanci tamkar ita ta kawo talauci duniya.

Ta bude mota ta saka Mata jakar ta juyo zata dawo ciki inda ta maido ta. "Na sallame ki ne kike kokarin juyawa? Wai talai me kike daukar kanki ne a gidan Nan? Akwai gadon tsohonki aciki ne? Tsohuwar ta rusuna tana Bata hakuri

"Nace akwai gadon tsohonki aciki? "A a Babu hajiya na tuba ki yafe Ni nayi Zaton kin sallame Ni ne Amma ba Zan sake ba .
Ta wurgo Mata harara
"Idan na dawo na samu wankin tile din Bai fita ba sai kin sauya shi wallahi duk wata sai an biyaki kudinki Amma saboda kin kware a ha inci wankin tile ma sai kinyi cuta
"Zan kiyaye hajiya adawo lafiya
Taja tsaki taja motar ta fice tana sababi

Tsohuwa talai ta juyo ta soma aikin wankin tile tamkar zata sabunto shi yadda ya faro har dai ta tabbatar ya fita kafin ta Kama wankin kayan hajiyar inda Kuma ciwon cikin da tayi magana ya kayar da ita abin tausayi tsohuwar amai da gudawa ya sarketa ta Fadi Kan shinfida tana kwara amai zawayi na bin shimfidar inda harira ta me aikin girka abinci ta kawo Mata agaji da Dan ruwan gishiri ta Kuma tsabtace tsohuwar cikin ikon Rabbi Kuma amai da zawayin ya tsaya sai dai ta kwantsame Abu ga tsoho amai da zawayi ba Dadi

Sai San maraice hajiyar ta dawo inda ta iske talai akwance Babu lafiya Amma sai me? Sai sababi da masifa Wai lambone musamman da taga wankin da talai din ta fara ciwo ya kaita kasa Aiko ta SHIGA zubar da ruwan tijara Wai akan Dole sai talai ta taso ta wanke Mata kayanta

Harira ta kalleta "kiyi hakuri hajiya wallahi Bata da lafiya kwance ta wuni amai da gudawa ke damunta Bari Ni na karasa wankewa......
Ta zabgowa harira wata ashar
"Na tambaye kine gwana yar ka iya? Kauce daga Nan ko yanzu ranki yayi Baki Yar iska me shiga shirgin wani....

Tsohuwa talai ta taso tana daura Dan kwalinta ta fito dai dai da shigowar hajiya Mama uwar me gidan wadda tazamo dodan izzatu saboda masifarta

Tsohuwa talai ta Yi Mata barka da zuwa inda izzatu ta Sha jinin jikinta
Hajiya Mama ta amsa inda take duban talai.
"Baki da lafiya ne talai? Wallahi kuwa hajiya amai da gudawa ne....
Ta dubi izzatu fuska ahade tasoma zazaga masifa...

"Kuma shine saboda Rashin sanin kimar Dan Adam bakiyi tunanin kaita Asibiti ba saboda ba uwar ki bace? Ke Wai wace irin Yar iskace ne ? Maza ki sa akaita Asibiti ko ruwa akara Mata me aiki Ba baiwa bace sun taimake ki ba kadan ba tunda ke agidan ku Basu koya Miki komai ba

"Kiyi hakuri hajiya Bari asa akaita ko kyamis ne.....
"Asibiti za akaita ke in kinji naki ciwon kyamis kike zuwa? Talai tace hajiya ai naji sauki ma ba sai munje ba.....

"A a talai kuje ko ruwa akara Miki Baki ga yadda Kika kwaltse ba? Haka ko akayi direba ya dauki talai zuwa Asibiti inda aka Kara Mata ruwa da magunguna suka dawo gida Inda hajiya Mama ta balle hancin tsiyar da ya kawo ta gidan Dan nata

"Ina da labarin duk irin cin Kashin da kikewa masu aiki izzatu kin mace ko wacece ke? Don me Zaki samu mutane kiyi ta cin zarafin su don kawai suna muku aiki? To Bari kiji abinda ya kawo Ni gidan nan yau shekarar ki goma Sha biyu Nan gidan Amma ko batan wata bakiyi ba to na gaji da gafara sa Banga kaho ba a yau nazo da magana wadda zanyi akan ke da mijinki don haka maza ki Kira min shi yazo yanzu Ina jiran shi..........
[5/16, 5:52 AM] Aunty Fauzah Yar Amanah: *ZAN FASA KWAI*


*NA*

*HADIZA BARA'U GIDAN IKO*


_Hakkin Mallakar na gidan iko ne_


*Page 2*


*_________________________________*

*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*________________________________*



..Hawaye ya tararowa izzatu Jin abinda hajiya Mama ke Fadi wata zuciya ta kuleta taji kamar ta tashi ta rufe hajiyar da duka sai dai Babu hali hajiyar zaune take da kuturinta.

"Kukan banza ne kike kukan wofi. Yanzu Nan daga gidan saminu nake Ina shiga yara suka taho suna min oyoyo abin farin ciki duk inda na waiga Yan dugwi dugwi ne ke hawa da sauka ajikina shi wannan haka zai lalace akan ki ba zaiyo aure ba ? To maza ki Kira min shi kice Ina jiranshi...

Ta wurgowa hajiyar harara kafin ta bude Baki cikin gadara da izza ta fara magana

"Hakan da kikayi yayi kyau hajiya ku sama mishi mafitar da zata bulle dashi don nagaji Nima magana ce kawai banyi ba to tunda har Anzo inda Kika gaji hajiya zanso ayau koma yanzu ki tsinke igiyoyin aurena sai ki kawo mishi wadda zata Rika haihuwa duk wata .......

Hajiyar ta dago Mata hannu "kar ki sake ki zageni don na Fadi gaskiya.....
"Ba Zan zageki ba hajiya Amma Nima ba Zan yarda ki fada min maganar da zata dameni ba kija bakin Ni Kuma Zan fassara Miki kowane kalar ciwo Zan fada Miki kalar maganin tunda na kula shekawa jaki shayi aikin banza ne ba iya Sha zaiyi ba....

"Ki Fadi komai damar kice Amma na rantse Miki sai an kawo wata mace agidan Nan wadda zata haifa Mana yara wallahi na gaji da sai dai kici ki kasayar

"Ai hajiya Ni tuni na gano kece Baki gano ba kice Rabon a bankado abinda zai saka zuciya tashi Baki taba tambayar ko shi Dan naki ne ke da matasala ba sai dai Ni kuke kallo? To za ayi duk yadda kike so tunda watan da za ayi magana ya Kama wallahi za ayi magana

Don haka yanzu sai kiyi hakuri baya gari Yana can kasar waje neman lafiyar da zata bashi Yan dagwai dagwai din da kike magana idan ya dawo sai kizo kuyi maganar kafin lokacin Ni na Dade agidan mu tunda nayi kawaici nayi hakuri ba ku San nayi ba to Ak ya dawo Ni kuma ya sallame Ni

Hajiyar tayi shiru tana tauna maganar izzatu kar dai matsalar daga AK din ne na Rashin haihuwar? Karfa allura ta tono garma Kai Bata zaton hakan Kuma ko daga gareshi ne ai akwai magani sai agwada.

Da haka hajiyar ta taso inda talai tayi Mata rakiya har wurin motar ta suka tafi ita Kuma ta juyo inda Kuma izzatu tace dawa Allah ya hadata ba da talai ba?

"Kinje kun zageni ke da hajiya to in zata burgeni Mata hudu ya kamata ta aurowa ak haihuwa Kuma sun Dade basu haife mishi singa da kasuwar kurmi ba
Haka tayi ta sababi tamkar zata aro Baki ta hada da nata talai dai ta wuce daki ta barta

Kwana biyu tana cikin takaici da bakin cikin da hajiya Mama ta guma Mata inda take ta jiran zuwan me gidan don ayi ta ta Kare Wai ramamme ya zagi maye

Ya Kira wayarta yake sanar da ita kanwar shi asma,u ta haihu har gobe ake suna hajiya Mama ta kirashi ta sanar dashi inda ya bukaci ta dauki kudi dubu hamsin ta kaiwa asmau kudin aski
"Gaskiya ba zanje ba ak sai dai na tura talai ko harira Amma Ni dangin ku nayi wuri na aje su gaskiya saboda nagane basa kaunata........

"Babu komai tunda har Kika iya fada min kinyi wuri kin aje dangi na na gode.......
Dit ya tsinke wayar inda Kuma taji lallai Bata kyauta ba kamata yayi ta amsa mishi da to in yaso sai ta tura wani kawai don haka sai ta Kira wayar tana bashi hakuri cikin kissa da kisisuna har tana fadin tayi kuskure yayi hakuri da haka suka aje wayar t

Washe gari ta nufi gidan Asma u inda ta tabbatar ba zasu kwashe da marar arzikk ba musamman dangin shi dake da burin yada Mata bakar magana to yau Suma zata nuna musu uwar su ma dai dai take da ita bare su kanan shegu

Da haka ta fice ta iso gidan sunan Wanda ya ciki ya batse da Yan uwa da abokan arziki ta fito mota tana shakar iska dai dai inda ta hade fuska don kar su Raina ta.......
[5/16, 5:52 AM] Aunty Fauzah Yar Amanah: *ZAN FASA KWAI*


*NA*

*HADIZA BARA'U GIDAN IKO*


_Hakkin Mallakar na gidan iko ne_


*Page 3*



*___________________________________*

*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*__________________________________*




...Sanye take da leshi me kalar ruwan kasa me cizawa wato coffee brown kafarta sanye da takalmi me tudu Wanda ya Kara Mata tsayi hannunta cike da warwaraye da zabban zinariya yayinda kwalliya ta taimakamata afuskar ta don in baccin kwalliyar to da ba zata kallu ba ahalayya Kam taci sunan ta izzatu don izgili da dagawa ba a magana hakama Bata Faye shiga mutane ba saboda tana ganin ta zarce hada kafada da mutane musamman idan Basu da kumbar Susa don kuwa mijin da take aure eng abdukarim fitaccen Dan kwangilar dake samu kwangila daga gwamnatin tarayya Wanda sunan shi ya tumbatsa aduniya shine barazanar ta da homar ta sai dai inda matsalar ta take shine tsayin shekaru Bata haihu ba inda har dangin shi ke yada Mata magana da habaici da arashi karshe ma said ga hajiyar shi da kanta ta wanko kafarta ta wanke ta soso da sabulu inda itama ta daura damarar yakar duk Wanda yace Mata kulle zata ce mishi Cass

Ta shigo gidan sunan inda ta iske ana ta sabga ta dauke kanta tana hura hanci
Da yawan Matan dake gidan suka bita da kallo suna kallonta awatse itama tana musu kallon sai dai aganni abarni ko Kuma bakin ciki ya kashe mutum.

Kai tsaye ta shiga dakin me jegon Wanda yake cike da Yan uwa da dangi
Tamkar wadda ta shigo cikin wata najasa haka take ta shakar hanci tana dauke Kai inda asmau take kallon ta tana mamakin daukar kanta

Bata gaishe da kowa ba ta jawo kudin ta mikowa asmau
"Gashi inji AK yace akawo Miki Yana Miki barka ta Mika mata tana dauke Kai.
"Madallah na gode inji asmau ta fada tana Miko Mata jariri
Shafa tace "Kai Yaya ak ya soma rage kyauta ba kamar da ba.......
Samira ta karbe da fadin
"Yaya eng ba zai rage kyauta ba wata Kil dai sauran kudin ne sukayi dimuwa Yar gidan ikon tashi ta na baza irin wannan ikon Allah yaushe zaiyi abin kuzo ku gani? Samira tace Ni wallahi Ina tausayin shi bawan Allah kowa da danshi Amma shi Babu Kuma an rufe mishi idon ganin gaskiya.....
Ke dai Bari Yar uwa sai dai aci akima katon Kashi a hau mota ashiga gari ana hura hanci Ni wallahi har gobe mamaki nake yayun mu sunyi Rashin dacen Mata mu Kuma mazan mu sunyi dacen Mata....

"To ko kina da Sha awa ne akan yayan naki shafa? Cewar izzatu da tagaji da Jin shaguben su
"Me kike nufi da ko Ina da Sha awa? Inji shafar,
Izzatu tace
"Wai ko ki aure shi nake nufi tunda Ni na tsare muku gaba na tsare muku baya tunda kina haihuwa kawai sai ki kaso auren ki kizo kuyi Maja Kinga sai kema ki biyo layin masu sa ar mijin harma ki yi abinda nakeyi.

Sai suka harzuko Mata su duka tamkar zasu cinyeta.
"Me kike nufi da wannan maganar? Dama kinzo don kici Mana fuska ? To aikuwa Wallahi jikin ki zai gaya Miki zakuma ki Gane karyar iskanci kike...

Izzatu ta Mike tana aje jaririn
"To Bari agano Yan iska tsakanin Ni da ku ai a yanzu dai dai nake da uwar mutum ma da uban shi bara ku gayyar na gayyaro
"Eh kice dama da abinda ya kawo ki yau har hajiya ta samu tukwaicin zagi gareki ? Sai saka soma musayar yawu har an daura damarar dambacewa inda shafa ta rarumi izzatu suka soma dambe har suna yagawa juna sutura inda a karshe sukayi Mata taron dangi har suka fasa Mata goshi . Inda gidan suna ya hautsine wasu suka shiga tsakani izzatu ta taho da Alwashi kala kala Alwashin karshe shine rabuwa da ak

Kwana biyu da yin hakan me gidan ya dawo daga tafiyar da yayi ayadda taso ba zata Kuma kwana gidan ak ba Amma wani Abu da ta kasa ganewa shine ak kwarjini ne gareshi Koko son shi ne takeyi da har in tayi arba da shi take mantawa da kanta? Ganin ak yasa taji ko za a dawo da bara bana ba zata Rabu da ak ba

Ta tarbeshi cikin salon kissa da kisisina Wanda take siyeshi har ma ta mantar dashi tunanin wata ya mace.
Washe gari ya fice zuwa gaishe da hajiya Mama inda acan ya karbo umarnin hajiyar na ya karo aure ko Kuma ita tayo mishi

Ya dawo inda ta kula da Yana cikin damuwa duk da Bai fada Mata ba Amma ta San kwanan zancen don haka sai kawai ta fada mishi yadda sukayi da Hajiya. Ya dubeta
"Ni kamar Ni ace za ayi min aure ai kamar an sarawa matar da aka aura min aiki.
Ta Sha mur tana hade fuska
"Nifa har yanzu kaki fito Dani duhu akan gwajin da akayi Mana Amma ko baka fada min ba na san an samu matsala ta bangarenka don da akaina aka samu matsalar da tuni ka bi bayan hajiya ka karo aure shine ka rufe min har kana tsallake kasa neman lafiya to kasani Nima hakuri na ya Kare tunda hajiya ma tazo har gida taci min fuska akan hakan bare su shafa dake fasa min goshi
Lokaci yayi da ya kamata ka fito ka fada musu gaskiyar magana akan Kaine me matsalar don su sakar min Mara nayi fitsari idan Kuma na gaji da mugun halin su sai ka sauwake min auren ka kawai.

Yayi murmushi Yana dubanta
"Wa ya fada Miki magani naje nema India? Yo har sai an fada min ga Abu abude? Ai na San halinku ne maza na Rashin adalci da Akaina aka samu matsalar nan da tuni ka samawa kanka mafita to Nima na gaji

Ya Kuma yin murmushi " to haka din ne Allah ya bamu lafiya Amma Ina so ki sani Ni haihuwa da ake ta maganar ta akaina ban wani damu ba saboda na San komai Allah NE ke yin shi idan Ina da rabon haihuwa Zan haihu idan Kuma bani dashi auren ne kawai ake da ikon yi min Amma haihuwa Babu me ikon bani ita in ba Allah ba So ki bar damuwa hajiya Kuma kiyi Mata uzuri Dole ne taji tausayina Amma ko ita ki Bari Zan fahimatar da ita zata Gane sai dai ki sani ba Zan lamunci Raini gareta ba duk abinda zatayi Miki saboda kin rabeni ne idan Kuma kina sona Dole ki girmam min mahaifiyata don su shafa in sukayi Miki zanci mutuncin su Amma akan hajiya komai zai iya faruwa
Ta dubeshi cikin Jin haushi da takaici

"Kana nufin sai don Ina sonka sai in Bari hajiya ta takani akan abinda ba laifina bane?
Shima ya dubeta cikin Jin haushin abinda take kokarin fada akan mahaifiyar shi........
[5/16, 5:52 AM] Aunty Fauzah Yar Amanah: *ZAN FASA KWAI*


*NA*

*HADIZA BARA'U GIDAN IKO*


_Hakkin Mallakar na gidan iko ne_


*Page 4*


*_____________________________________*

*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*_____________________________________*





.........."Me kike son ce min ne"? Ko hajiya Bata haifeni ba nayi Zaton girmanta zaisa ta ci albarkacin sa bare kuma Ni da kaina. To kar ki Fara don Zan iya jure komai akaran kaina Amma ba Zan jure ko kallon banza ga hajiya ba bare ki nuna Mata yatsa.......

"Ohooo sai nice za a iske gida azageni in Kuma shiga sabgarsu su zageni saboda Ni ban San yanci ba ko kuma shago aka bude na fito ko Kuma daga sama na fado? "To na rantse maka Babu shegen da Zan Kuma yarda ya taka Ni in zuba ido in kyale shi don yanzu Kai nakewa Alfarma ba kamar Ni da suke zaton kayi min Alfarmar ba sai Kuma ka shirya sanar dasu Kaine da matsala ba Ni ba.

Ya dubeta "Ina fatan cikin shegun da ba Zaki yarda su taka ki ba Babu hajiya? Kiji ki Kuma kiyaye Babu wani Abu da hajiya zata so ko ta sani Wanda ba zanyi shi ba don bani da wani fata ko buri sai na in rabu da ita lafiya. Ko auren take so nayi zanyi don zanyi biyayya agareta sai ki kiyaye.

Tayi wata kwafa ta shige daki ta barshi da yi Mata rakiya da ido kafin yayi murmushi kishi manya kowace mace da kalar nata abinda ma yake tambaya shine shi kishi dabi a ce ko hali ne?

Tunda sukayi haka sai izzatu ta fito da sabbin salo tamkar wadda ake zugawa Amma dayake Allah yayi mishi hakuri sai yayi Mata uzuri akan cewa maganar hajiya ce ta sa ta daukar Kai

Sati biyu Yana gida Yana kallon idon mikiya a tashar farin wata shafa ta shigo ita da wata budurwa me shegen kyau ya tashi zaune inda izzatu ke kallon su awatse
Suka zauna suna gaishe da shi inda ko kallon izzatu Basuyi ba
Bayan sun gaisa shafa tace
"Dama hajiya ce tace na kawo maka lubabatu gata nan kanwar mijin asiya ce idan Allah ya yi sai ku dai dai ta".

Lubabatu ta sunnar da kanta kasa cikin Jin kunya inda yaji wani Abu marar Dadi in Banda hajiya yaushe zata turo mishi yarinyar har gida Mai makon ma ace yaje ya ganta.
Izzatu da take kallon su cikin kaskanci ta tofa albarka cin bakinta.

"Wane irin aure ne haka marar daraja da sanin kimar Kai? In ba lalacewa ba lubabatu yaushe za a turoki gidan mutum maimakon shi ya iskeki gidan ku in dai ba zubarwa Kai daraja ba?
Shafa ta dubeta
"Ai Rashin daraja ya Kare ga ci kasayas? Babu komai indai ta samu shigowa ai tayi daraja.....
Ya dago Mata hannu cikin fusata
"Ashe kema kin iya wannan iskancin irin na su Samira da asmau? Akan idona kike fada Mata haka?

"To Yaya bakaji abinda tace ba? ....
"Tashi kuje Zan zo in samu hajiyar muyi magana....
Shafa ta finciki hannun lubabatu suka fice daga gidan

"Gaskiya ba Zan boye maka ba ak indai aure ake Shirin Yi maka Ni Kam sai dai ka sauwake min aurenka don ba Zan iya zaman hakuri biyu ba, ba zanyi hakuri da Rashin haihuwa ba Kuma inzo inyi da kishiya da dangin miji abarni inji da Abu daya

Bai tankawa maganar ta ba ya ci gaba da kallon shi inda wayar shi tayi Kara ya duba ya dauka da sauri inda ake sanar dashi batun kwangilar da aka bawa wani Dan kwangila ne wato Kabir mashi Wanda aka karbo aka bashi don anfi yarda da aikin shi fiye da Kabir mashi din don
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment