Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ngH
Na SDY JEGAL
Ebook creat by Shuraih Usman
Ebook publish by www.hausaebooks.com.ng
Ebook din nan yazo maku ne daga shafin www.hausaebooks.com.ng
Kuna ziyartar shafinmu don samun sababbin littatafai
Ga duk wanda ke bukatar ebooks nashi ya samu shiga cikin wepsite namu sai ya turo mana da littafin ta Email namu hausaebooks@gmail.com

[10/28,
1:22 PM] +234 803 325 6478: 🍒 *BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng* 1-5🍒 Tana
bacci taji saukar ruwa saman kan ta, take ta zabura tana
rabon ido. Shegiya sai asamu damar tashi, waye bawan
ki, koni Zan fita rafi d'ebo miki ruwanne? Nan ta tashi ta
nufi buta da niyyar alwala, take ta Kai Mata duka, tana
cewa wallahi ba zaki tab'a ruwannan ba har sai kinje rafi
kin d'ebo, kuma in kika bari na taradda ke can na lahira
zai fiki jin dad'i, shegiya Mai Kama da aljanu. BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng ta
tashi tana kame-kame ta d'auki tulu ta fito daga gidan,
koda ta fito wani gurin ko sallah ba atada ba, ga kuma
yanayin gari da sanyi. Koda ta fito yana rakub'e k'ofar
gidan, nan ya mik'o Mata hannu ya karb'i tulu yace
muje. Tace Murtala da ka basshi, kaga kullum in ka
rakani d'ebo ruwa baka samun sallar subahin, kuma
kaga tana da muhimmanci da kuma d'inbin lada. Nan
yayi murmushi yace ba komai BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng, wataran in mun
dawo ina samun masallacin malam Atiku, kuma kinga ke
Mace ce bai dace Ana barin ki fito wa da subahin ba. Nan
take idon ta suka kawo ruwa tasa gyalen ta ta goge
hawayen, tace na rasa me na tare ma Gwaggo lami,
kullum da kalar azabar da nake fuskan ta. Murtala yace
kiyi hak'uri komi yayi farko zaiyi k'arshe, watarana sai
labari. Yace muje kar ki dad'e ki dawo ta hauki da duka.
Nan suka Kama hanya sai rafi, ya mik'a Mata ledar
hannun shi yace tayi sauri tayi sallah zai cika Mata tulun.
Tayi alwala ta zazzage kayan Ashe hijab ne da dadduma,
nan ta shimfid'a tayi sallah a gurguje ta gama, ta ninke
kayan ta saka a Leda. Nan ya d'auko Mata tulun suka
nufo hanyar gida, tace Murtala ka kawo tulun in d'auka
kayi sauri kaje ka samu jam'i, sai in k'arasa gida. Yace to
kije da kayan gida mana. Nan ta gwalo manyan idon ta
tace wallahi Gwaggo zata iya yan kani akansu, kaje dasu
kawai nagode. Yace Mata Ina ganin Maigari zai tura ni
sokoto ne sayen wasu kaya kuma k'ila zanyi kwana biyu
can. Kinga ba kida abin sallah in kin fito, kuma babbar
damuwa ta ba Wanda zai raka ki rafi. Nan tashin hankali
ya bayyana ga BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng jin kalaman shi, sai ga hawaye
shar sun wanke fuskar ta. Nan dai ya samu ya rarrashe
ta kan cewa kamin ya wuce zai San abinda zaiyi akai. Jin
tada sallah masallacin Mal Atiku yasa yayi saurin wuce
wa saboda ya samu jam'i, ita kuma ta wuce gida. ®
*SDY* *JEGAL* [10/28, 1:22 PM] +234 803 325 6478: 🍒
*BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng* 5-10🍒 Shigar ta gidan keda wuya Gwaggo lami
ta sauke tulun daga saman kanta kamar abin arzik'i, sai
ta hau ta da jibga tana fad'in shegiya kullum na aike ki
rafi sai kin yi tsaye-tsayen ki saman hanya. Kuma kinsan
Zan d'ora ruwan kunu, kina yimin bak'in cikin abinda
Zan samu. Jin turo k'ofar gidan ne had'e da sallamar Mal
salisu yasa ta rik'o hannun ta tana fad'in sannu BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng,
Ina fatar bakiji ciwo ba, tashi in gani. In har da sabo
BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng ta saba da wannan makircin na gwaggo duk
azabar da take ga namata in har Baban ta na gida to zata
yita tarairayar ta tamkar k'wai. Nan malam ya k'araso da
saurin sa ya tada BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng yana Mai duba jikin ta, yace me
ya sameki? Nan Gwaggo ta karb'e tana Mai cewa "kasan
halin ta da son aiki, tana sauri ne zata d'auki tulu zuwa
rafi taci Karo da ice shine ta fad'i. Mal yace BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng ki
dinga yin abubuwa a hankali duk da nasan ki da
natsuwa. Tace to Baba, tana Mai kakkab'e jikin ta. Yace
tashi kiyi wanka kamin Gwaggon taki ta gama kunu. Ta
ebi ruwa duk da taga mugun kallon da Gwaggo ke binta
dashi, ta wuce toilet saboda in har zata tuna yau kwanan
ta hud'u rabon ta da wanka. Dama in har ta samu wanka
gidan to Baban ta ke gidan. Hakan ta fad'a ta darji jikin ta
da ita kanta kejin tsamin shi. Koda ta fito Gwaggo ta
dama kunun, agurguje ta d'auko wasu kod'add'in kaya
Nata Zane daban Riga daban ta saka. Shigowar Gwaggo
taji, nan take ta zabura. Nan ta Kai Mata rank'washi ga
Kai, tace wallahi dakin dawo sai kin ebo ruwan da kika
d'iba, wato gaki y'ar gata Mai uba ko. To wallahi bud'e
kunnen ki da kyau kiji abinda Zan gaya maki, duk kika
kuskura yau kika dawo min da ragowar kunun wallahi na
lahira sai ya fiki jin dad'i, shegiya Mai Kama da mujiya.
Nan BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng ta fito daga d'akin jikin ta na rawa, ta d'auki
bokitin kunu ta fita zuwa in da take Kai kunun. Cikin ikon
Allah kamar ita ake jira mutane Nata zuwa saye, saboda
BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng akwai farin jini ga Sana'a. Hakan ta had'a kan
kud'in ta tayo hanyar gida, nan ta had'u da Murtala suka
gaisa. Yace yau baki ajiyemin kunun ba? Tace na jika
shiru ne, na zata ka wuce sokoto d'in. Yace wallahi
tafiyar ce bata yuyu ba inaga sai wani sati, don haka
gobe Zan zo muje rafi tare, nan tayi murmushi tace baka
gajiya Murtala, nagode sosai da kulawa. Nan ya rako ta
har suka kawo k'ofar gida sannan ya wuce. Tana shiga
gida ta damk'a ma Gwaggo kud'in, sannan ta durk'usa ta
gaida Baban ta, har ta tashi zata wuce akurkin d'akin da
take zama. Yace zo kisha kunu y'ar Baba, hadda k'osai na
fita na siyo muna. Nan ta zauna suka karya tare da
Baban ta, nan yace to zai fita kasuwa sai ya dawo. Tana
shiga akurkin ta ta zauna kenan, sai ga Gwaggo ta fad'o
tamkar wadda aka jefo. © *SDY* *JEGAL* [10/28, 1:23
PM] +234 803 325 6478: 🍒 *BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng*10-15🍒 Gwaggo na
shigowa d'akin ta hau ta da jibga, wato ke gaki y'ar gata,
har da mik'e k'afa kisha koko da k'osai tare da uban ki, ni
sai dai bani kad'an ga hannu. Wayyo Gwaggo kiyi hak'uri
bazan k'ara zama da Baba in karya ba. Rufemin bakin ki
shegiya Mai Kama da aljanu, tashi maza kije rafi ki d'ebo
min ruwa na da uban ki yasa kika iba kika yi wanka, ke ga
Mai tsafta ko, ta koma kaima rank'washi ga Kai. Nan ta
zabura jiki na rawa ta fito ta d'auki tulu. Gwaggo tace zo
nan, nan ta Fara yarfe hannu tana dire k'afa k'asa tamkar
Mai jin fitsari. Tsawar da ta daka Mata ne sai gata gaban
ta durk'ushe bata shirya ba. Nan ta Kama Mata kunne ta
murd'e sai da ta sako fitsari kad'an, tace wallahi muddin
kika fita kika dad'e sai na kusa yanka ki a gidannan. Kinga
ga tukunyar wake can saman wuta tana jiran ki zaki fita
talla. Nan ta tashi tana rawar jiki tana kuka, sai murza
kunnen ta take yi Wanda take ji tamkar zai cire daga
mazaunin shi. Tana fitowa taga k'awar ta lantana waje
tana jiran ta suje rafi. Lantana ta tarbo ta ta karb'i tulun
daga hannun ta, tace har Zan shiga gidan Ku naji waccan
masifaffiyar matar na maki kashe di, shiyasa na dawo
daga waje na tsaya. Kinsan ni bama shiri da ita, don Ina
Mai tabbatar miki in Ina shiga gidan ku watarana sai an
karb'e ta hannu. Nan BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng tayi murmushin dole, tace
ni abinda ma keban mamaki da ita, wallahi gaban Baba
sai ta dinga tarairaya ta tamkar ta had'i yeni. Lantana
tace gaskiya inni ce sai na gayama Baban abinda take
yimin. BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng tace da wataran sai ta yanka ni, kesan bata
da imani Ko kad'an. Haka suka yita tad'i har suka je rafi
suka dawo. Lantana tace kiyi sauri ki d'auko wake da
shinkafar ni ko Zan d'auko alale sai muje tallar. Tace to
Allah yasa kar in taradda wani aiki, da saurin ta ta fad'a
gidan. © *SDY* *JEGAL* [10/28, 1:23 PM] +234 803
325 6478: 🍒 *BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng* 15-20🍒 Sun fito suna tafiya suna
tad'in matsalar Gwaggo lami, kowa da abin Sana'ar shi
saman Kai. Dai-dai zasu karyo kwanar inda suke ajiye
abinci saiga mota ta karyo aguje, nan ta kwashe BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng
ita ko lantana ta samu ta kauce. Ai ko Mai motar ya fito
da sauri ya nufosu, daka kalli BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng kasan tana cikin
tashin hankali. Gashi duk man waken ya b'ata Mata jiki,
kuma ta d'an goge a gwuywar hannun ta da kuma yatsan
ta dake fitar da jini. Mutane sun taru saman kanta ana
duba jikin nata, amma ita cewa take yi ta shiga uku yau
sai Gwaggo ta yanka ta, nan lantana ta k'araso kusa Gare
ta tana fad'in ya jikin naki? Tace ki taimaka min lantana
yau zata kashe ni, ta d'ora hannu a ka tana na shiga uku.
Nan Shureim ya bita da kallon mamaki, yace baiwar
Allah ki bari agani in baki ji ciwo ba. Ta bishi da kallo
tana cewa zata kashe ni wallahi. Lantana ta Kama ta ta
mik'e amma daka ganta kaga zararra, nan ta ja ta suka yi
gefe, shima Shureim ya bisu. Nan yake basu hak'uri kan
kuskuren da aka samu, ya d'ora da cewa wallahi akasi
aka samu Ina sauri ne. Lantana tace ba komai bawan
Allah sai dai gaskiya akwai Matsala babba, nan ta kwashe
komai ta gaya Mai. Yace ba matsala, Ina ne chemist d'in
garinnan sai muje ayi Mata dressing d'in raunin da taji.
Lantana ta bashi amsa da cewa yana kan hanyar da ya
biyo, can baya kad'an. Yace to Ku shiga mota muje a
duba ta. Nan lantana ta zaro ido tace kaje mu zamu biyo
bayan ka, amma ya zamu yi da wa'annan kayan? Yace
kinga waken ya zube duka ba abinda zai amfanu daga
ciki kawai Ku had"a kayan Ku, nan ya Kira yara yace
lantana ta raba masu alalen. Bayan sun je an Mata
dressing d'in ciwukan ya basu kud'in da shi kanshi bai
San adadin su. Nan suka had'a kayan su suka yi mar
godiya suka nufi hanyar gida, shi ko yana k'ara basu
hak'uri. © *SDY* *JEGAL* [10/28, 1:23 PM] +234 803
325 6478: 🍒 *BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng* 20-25🍒 Gidan su lantana suka
zarce, suna shiga Inna Habiba ta buga taslima tace me ya
faru BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng kika yi wujiga-wujiga haka? Lantana tace
wallahi Inna wata k'addara ce muka gamu da ita, nan ta
kwashe komi ta gayama Inna. Inna tace ai anyi arzik'i,
tunda abin ya tsaya iya nan, injin jikin naki da sauk'i?
BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng tace eh Inna sai dai yatsana dake min zogi. Tace
to Allah ya sauk'ak'a, ta d'ora da cewa gaskiya kun samu
mutumen arzik'i, saboda y'an birnin nan ance
wulak'anci ne dasu. Lantana tace gaskiya Inna wannan
yanada mutunci, kinga ma kud'in da ya bamu ina ga har
sunfi k'arfin kayan mu. Nan Inna ta karb'i kud'in ta Saki
baki bayan ta irga, tace yo ni duka alalen d'ari uku da
hamsin na d'ora maki, kefa BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng? Tace duka cemin
tayi Inna kawo k'asa da d'ari takwas sai ta b'allani. Inna
tace to kinga shi dubu biyar ya Baku, nan suka zaro ido
suna kallon Inna. Tace yi sauri BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng kisa kayan ki ruwa
ki wanke in suka bushe kisa ki wuce gida. Tace Inna
banni a hakan in naje gida na wanke. Inna tace ga kud'in
na cire nawa na alale wa'annan sai ki kaima Gwaggon ki.
Tace a ah Inna ki ajiye muna gurin ki nida lantana, ni Zan
wuce gida. Nan ta d'auki kayan ta ta nufi hanyar gida,
jikin ta sai b'ari yake yi, tana shiga ta hango Gwaggo
zaune gaban murhu tana hura wuta. Taje gurin ta tace
Gwaggo barka da gida, bata ko ansata ba saita mik'o
hannu alamar ta bata cinikin, nan ta damk'a Mata, ai ko
sai ga haurun Gwaggo waje sai dariya take yi. Tace hala
wani dan arzik'i kika had'u dashi ya yi maki juye? Nan ta
bata labarin abinda ya faru, har tana nuna Mata ciwukan
da taji had'e da maganin da Shureim ya bata. Take ta
warce maganin har tana had'awa da yatsan ta da akayi
mata dress d'inshi. Nan ta Saki wata k'ara takai zaune
dab'ass. Gwaggo tace da kisha wannan maganin k'ara in
saka shi wuta, shegiya Mai shegiyar fuska, aini naso ace
da motar ta d'auke ki kar ta dire ki sai lahira in huta da
jaraba. BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng na nan zaune tana kuka jikin ta duk ya
fara tsami saboda ciwon da gab'ob'in ta keyi, ga kuma
yatsan ta da takeji tamkar zai gundule. Gwaggo tace tashi
maza ki b'ace min da gani, kin tsare ni da idon ki masu
Kama dana mage. Tana d'aga hannun ta zata kai Mata
duka, sai ta tsin kayo sallamar Malam. © *SDY* *JEGAL*
[10/28, 1:24 PM] +234 803 325 6478: 🍒 *BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng*
25-30🍒 Hannun ta sauke ta ringa goge Mata jikin ta, tace
BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng ki dinga kula da hanya kina tafiya a hankali. Nan
Malam ya k'araso yana fad'in meke faruwa? Gwaggo tace
wallahi wani Mai mota ne ya kad'e ta, duk tayi b'arin
kayan kaga jikin ta duk Mai ne. Tace sannu kin ji tashi ki
cire kayan in wanke maki. Tace basshi kawai Gwaggo Zan
wanke. Malam yace y'ar Baba garin yaya hakan ta faru?
Nan ta kwashe komi ta gaya Mai, Gwaggo ta d'ora da
cewa ai mutumen yana da mutunci don ya biya kud'in
har chemist ya Kai ta. Nan Malam yace ni dai wannan
tallar na soke ta, banga abinda na rage ku da shi ba a
gidannan, y'ar Baba na neman halaka garin yawon talla.
Ko yanzu da Allah bai tak'aita ba da sai dai mu rasa ta.
Nan Gwaggo ta d'ora hannu saman Kai ta fasa kuka, oh
ni lami! Naga ta kaina. Babu komi dama nasan duk
dad'ewa sai an goran tamin rashin haihuwa. Yarinyar
nan tun tana k'arama nake wahala da ita, sai yanzu da
zanci moriyar ta za a nuna min bani na haife taba. Kuma
duk Sana'ar nan da nake yi ita nake ajiye ma kayan d'aki
koda auren ta ya tashi. Ita dai BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng ta bita da kallon
mamaki, in har da sabo ta saba da wa'annan abubuwan.
Ganin take yi duk duniya babu makirar macce sama da
lami. Malam yace kiyi hak'uri lami, BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng dama y'ar
kice halak malak, kuma ban rai nama kulawar da kike
bata ba. Allah ya saka maki da mafificin alkhairin sa, kiyi
hak'uri kin ji lami. Nan ya Kama hannun BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng ya Kai ta
d'akin shi, yace bara in Kai maki ruwa kiyi wanka zaki
d'an ji damar jikin ki. Ya cika roba da ruwa ya Kai Mata
toilet, tana shiga ya d'auko kayan da ta cire yasa ruwa.
Gwaggo ta taso tace kawo Malam in wanke. Yace jeki
huta Zan wanke, gashi na b'ata maki rai. Nan tayi
murmushin mugun ta, tace ai ba komai Malam ya wuce.
Bakasan ya nake jin BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng a raina bane shiyasa, haka
nake jin ta tamkar ni nayi nak'udar ta. Nan dai suka yita
hira har ya wanke kayan ya shanya. BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng na fitowa
Gwaggo ta bita da kallon zamu had'u ne. Nan ta fad'a
d'aki jiki sai rawa yake Mata, ga zazzab'i ga tsoron gamon
ta da Gwaggo. © *SDY* *JEGAL* [10/28, 1:24 PM] +234
803 325 6478: 🍒 *BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng* 30-35🍒 Shureim na shigowa
gidan Dad d'in shi na saukowa daga stairs, yace Dad na
Kai mashi kuma jikin nashi da sauk'i sosai. Dama na gaya
ma wannan tsohon ba wani ciwo ke damun shi ba face
kwad'ayi. Dad yace son ubanka ne Mai kwad'ayi ba
mahaifina ba, nan Shureim yayi dariya sosai. Mum tace
Kai dai kayi rok'on Allah mahaifan ka su kai tsufan shi da
nagartar shi, suna tare da Kai. Shureim yayi murmushi,
yace Mum yau naga ikon Allah. Wallahi yarinya na kad'e
da mota kowa ya taru ana jimamin abinda ya faru,
amma yarinyar nan kukan waken da ya zube take yi.
Mum tayi murmushi tace kai mutumen k'auye sai a
barshi, baiwar Allah yana yuyuwa shine hanyar cin
abincin su. Yace Ina tunanin wadda ta d'ora Mata tallar
kamar kakar ta ce ko kuma kishiyar mamar ta. Mum
tace wasu mutanen basu da imani, duk yada aka basu
amana sai sun yi zalinci, Allah dai ya shige muna gaba. Ya
amsa da Ameen, har ya tashi zai shige Mum tace Lateefa
tazo muna Hutu d'azu, tana ta Neman ka. Nan ya had'e
fuska yace yayi kyau, kawai ya wuce d'akin shi. Koda ya
watsa ruwa ya fito daga toilet ya taradda ita zaune
saman gado. Tace S.S kimba kwana dayawa, in har bani
nazo ba Kai ka Saki zumuncin. Sai da ya k'ara had'e fuska
sosai, sannan ya cemata get out of My room. Jin
maganar da yayi cikin tsawa ya bata tabbacin bada wasa
yayi maganar ba. Nan take ta fito falo taga Mum zaune
na kallo ta fad'a saman jikin ta tana kukan sangarta.
Mum tace waya tab'a min ke Latee? Shureim yace Mum
har yaushe Zan gaya ma yarinyar nan ta daina shigomin
d'aki ba excuse, na gaya Mata duk abinda take so ta Bari
sai na fito falo muyi maganar. Lateefa tace gaskiya ni
nagaji da wulak'an cin Kimba, yau Zan tattara kaya na in
koma gidan mu inda Nafi gata da tarairaya. Bayan ta
wuce fuuu d'aki, Mum tace haka kakeso ko son? Yace
wallahi Mum don kun sangar ta tane, kamar wannan
k'atuwar zata rik'a yiwa mutane Abu tamkar y'ar sha
biyu. Mum ta karb'e da cewa sai ka bita d'akin ka rarraso
ta ko zata sauko. Yace Mum ni rashin tarbiyar Latee ne
bata yimin ba, haba dube ta ta saka wasu kaya tamkar
gidan inyamurai. To ka rik'a yi Mata a hankali zata gane,
cewar Mum. Nan ya haura sama ya tunkari d'akin da
take sauka in tazo gidan, yana tura d'akin zai shiga da
k'arfi ya janyo k'ofa yana maida numfashi. Sai da ya
k'wank'wasa k'ofa ta bashi iznin shigowa sannan ya
koma. Koda ya shiga ta saka kayan ta, dama abinda ya
fitar da shi Karon farko, koda ya shiga ya taradda ita
daga ita sai bra da mini siket. Ya samu wuri ya zauna
yace "Latee kiyi hak'uri, ba wai bana son kusanci na dake
bane, shigar da kike yi ce bana so. Kinga bai dace ace
duk yanda kika so hakan kike zama ba, dubi ko yanzu
shigar da kika yi. Ya nuna ta da yatsa yace dube ki wai
wannan Riga ce kika saka, cibiyar ki sake gaban ki ma
hakan, siket ke kan ki baki samun tafiyar walwala, haba
Latee ya Kama ta ki gyra d'abi'un ki. Nan ta bishi da kallo
cikin muryar ta ta sangar ta tace nifa Kimba kasan bana
iya d'aura Zane takuramin yake yi. Yace to ki rik'a saka
dogayen riguna mana ko kuma irin Pakistan haka, tunda
sune Riga da wando. Yace kishirya mu fita in siya miki,
amma fa ba zaki Bini hakan ba ace an ganni da Wata
k'abila, yana maganar had'e da murmushi a fuskar shi.
Tace yanzu Kimba nice k'abilar? Ta had'e fuska tana buga
k'afa sai wani turo baki takeyi. Yace yi hak'uri k'anwa ta
tashi muje, nan ya nufi trolley d'in ta ya duba kayan ba
wasu kayan arzik'i a ciki. Da k'yar ya samu wani dogon
wando ciki, ya koma d'akin shi ya d'auko wata suit d'in
shi ya bata yace ta saka. Yana falo zaune ta shirya ta fito
da dama ba laifi, ta d'ora wata hula saman kan ta. Nan
Mum ta bita da kallo tace sai Ina Latee? Ba Kimba ne ya
yita yimin fad'a ba, har da cemin ina Kama da k'abila.
Nan Mum tayi murmushi tace k'yale shi Latee ai kinfi shi
kyau shiyasa yake k'yashin hakan. Tace Mum za muje
shago ne wai zai yimin sayayyar kaya ne, kinsan saura
k'iris ya zama ustaz, duk yada ka saka kaya bakayi dai-dai
ba. Nan ya bita da harara yace komai zaki ce kice, amma
ba ke ba saka k'ananan kaya a gidannan. Nan dai suka
fito Mum tace sai kun dawo amma fa kar Ku fita ka yita
takura ta. (Masu kiran ojoro wannan ya isa ko ak'ara?
_lolx_😜) © *SDY* *JEGAL* [10/28, 1:25 PM] +234 803
325 6478: 🍒 *BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng* 35-40🍒 Gwaggo na shigo d'akin ta
hango BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng lullub'e cikin Zane jikin ta sai kyarmar
sanyi yake yi. Duk da hakan saida ta Kai Mata rank'washi
ga Kai, tace zaki tashi ne kuma zamu gamu dake, Mai
Kama da bebin roba. Mal ya shigo yace ya jikin nata?
Gwaggo tace da sauk'i sai dai akwai zazzab'i, sannu kinji
y'ar Baba. Yace bara inje chemist d'in hamisu in Kira shi
yazo ya bata magani, in ya dace ayi allura duk ya
had'ama ta da ita. Yana fita Gwaggo tace tashi zaune,
hakan tayi k'arfin hali ta tashi sai addu'a take jerawa a
zuciyar ta na neman kariya da muguntar Gwaggo. Kamar
addu'ar ta Kama ta sai kuma tace koma ki kwanta zamu
had'u ne in kika samu sauk'i, sai ta juya ta fita daga
d'akin, Saida BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng ta Saki ajiyar zuciyar da ni kaina sai
da na jiyo ta. Jin sallamar malam shida hamisu ne ya sa
Gwaggo tayi saurin dawowa d'akin, saboda tana tsoron
kar asirin ta ya tonu cewa an bada magani ta karb'e ta
k'one. Bayan sun shigo ne ya duba ta sai yakai duban shi
ga malam yace ai d'azu Wanda ya kad'e ta da mota yaje
da ita guri na har magani an bata, naso in had'a Mata da
allura tace bata so. Nan BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng ta Kai duban ta zuwa ga
Gwaggo, suna had'a ido da ita ta watsa Mata mugun
kallo cikin sauri ta kauce fuskar ta. Nan ta Kama in-ina
tana fad'in immm ina.. Nidai, Baban ya bita da kallo yace
ki natsu y'ar Baba ki gayamin ina maganin. Cikin muryar
ta tsoro da kuma zafin ciwon da ke damun ta, tace Ina
ga Mai motar ya manta ne ya wuce da maganin don bai
bani ba. Hamisu yace lantana fa ta karb'a da kanta. Cikin
ran Gwaggo tace wannan shegen Mai bin k'wakk'wafi
tamkar d'an jarida yana so ya tona min asiri. Tsinkayo
muryar BAHIJJAH daga www.hausaebooks.com.ng tayi tana cewa ai bayan mun fito ne ya
karb'a yace zai duba in maganin bai lalace ba, daga
hakan inaga mantawa yayi bai bamu ba, nima mantawa
nayi. Nan Gwaggo tayi wata b'oyayyar ajiyar zuciya,
hamisu yace to yanzu bara ayi Mata allura sai abata wani
maganin. Nan idon ta ya kawo ruwa tace "Baba bana son
allurar abani magani Zan sha. Yace kiyi hak'uri y'ar Baba
ayi allurar bana son zazzab'in nan ne, kuma kinsan yada
zazzab'i ke wahalda ke. Nan ma Gwaggo tasa baki
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5

Please Login or Register in order to submit comment