Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels


An dauko wannan littafi daga shafin www.dlhausanovels.com.ng ku ziyarci shafin na www.dlhausanovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from www.dlhausanovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT[7/9, 9:22 AM] Ameera Adam🌚: *ZAUJATU JINNUL-ASHIQ*


© *AMEERA ADAM*

Littafin kuɗi ne idan kina buƙata 300 ne ta Account 3090957579 Aisha Adam, First bank. Za ki turo evidence ta wannan lambar 0706 206 2624 Whatsapp only Idan kati ne 300 MTN.

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

https://chat.whatsapp.com/J0qrgC0rXNQ57u50VzeewR

FREE PAGE 1


Girma da nauyin cikin da ke jikinta kamar an kifa ƙwarya, bai hanata gudun da take yi na ceton rai ba. Gudu take zabgawa saboda miyagun hallitun da ta yi tozali da su, masu kawo mata farmaki da zimmar cafkar tsohon cikin da ya yi tsini tamkar zai fashe.

Zuwanta bakin wata bishiyar kuka mai duhun gaske ya bata damar tsugunnawa cikin haki, saboda ji take kamar bayanta zai ɓalle gida biyu saboda azaba, ajiyar zuciya take saukewa akai-akai kamar wacce ta shekara tana matsanancin gudu a tsakiyar rani. Dafe bayanta ta yi wani irin azabar ciwon baya da mara ya sarƙeta kamar ana tsaga marar tata da kaifaffiyar aska. Sannu a hankali ta waiga bayanta don ganin mummunar halittar da ke bibiyarta kamar yanda inuwar mutum take bibiyarsa. Kukan jarirai ne ya fara yi mata amsa kuwwa kamar saukar aradu a tsakiyar ka! Ta ko ina take jin sautin kukan na su kamar kunnuwanta za su tawatse.

Kuka haɗe da dariya ne suke ta shi a cikin dajin, zuwa can ta hango inuwar wata hallita na tunkaro ta, matsananciyar guguwa ce ke tashi bishiyoyi na kaɗawa da ƙarfa yanda kasan za su jijjigo daga jikin jijiyoyinsu.

Cikin wani irin gwamamman yare ta riski muryar inuwar tana cewa, "Sai kin halaka ke da abin da yake cikinki, kin zama halakakkiya keda tsiron da ke cikinki." Ba ta yi aune ba ta fara jin abu na bin ƙafarta zuu! A daidai lokacin da ta ji wani irin nishi ya taso mata.

Durƙushewa ta yi a wurin tana murƙususu, nan take wani irin kukan Jarirai mai haɗe da kukan Jaki ya fara karaɗe lungu da saƙon da ke cikin dajin tamkar zai tsage gida biyu. Sannu a hankali Jarirai suka fara rarrafowa suna zageta kamar ana zagaye wainar gero. Duk da halin da take ciki bai hanata yunƙurin tashi domin tseratar da rayuwarta ba, amma ina! Haihuwa ta tunkarota gadan-gadan nan take jaririn ya faɗo.

Sannu a hankali ya rinƙa bin duk wurin da jini ya zuba yana lasa shi da sauran 'yan uwansa Jarirai, tamkar waɗanɗa suke da'irar ƙungiyar asiri. Raihan da ke durƙushe da sauri ta zabura kamar wacce aka ɗanawa ruwan dalma, tana yunƙurin tashi nan take mabiyiya ta faɗo. Kamar yanda Kura take ƙishirwar nama haka suka afkawa Mabiyyar kafin wani lokaci tuni suka gama da ita.

Kamar haɗin baki haka suka waiwayi wurin da take tsaye, tamkar 'ya'yan Birrai haka suka fara tsalle suna ɗane jikinta har Allah ya basu nasarar hawa jikinta. Lokaci ɗaya suka fara lasar jikinta, ihu take kurmawa kamar zautacciya amma babu ɗaya daga cikinsu da ya yi alamun dakatawa. Daga can ƙafarta ta hango Jaririn da ya fito daga jikinta yana bin jinin ƙafarta yana lasa. A haukace ta ƙwalla ƙara tana ambatar sunan Mahaifiyarta kamar wacce ake zare wa rai.

Firgigit ta farka daga bacci tana sauke ajiyar zuciya kamar wacce ta ci gasar tseren gudu, jikinta rawa yake kamar mazari, ta haɗa gumi sharkaf kamar wacce take gaban maƙera.

"Barka da tashi ranki shi daɗe." Ba ta yi aune ba ta ji kalaman Mama Uwani a tsakiyar kanta. Da sauri ta ɗago ta kalle ta har lokacin jikinta rawa yake, sai da ta jingina da bangon gadon ta lumshe ido tana sauke ajiyar zuciya ta ce, "Yauwa Mama Uwani."

"Kina buƙatar wani abu?"

Girgiza mata kai ta yi tana murza idanu, hamma ta yi haɗe da miƙa sannan ta dubi Mama Uwani tana faɗin, "Mama Uwani ki haɗa min Tea kafin na fito." Cike da girmamawa Mama Uwani ya russuna tana faɗin, "An gama shalelen Uwani, gabanki gata bayanki gata. Duk abin da kika faɗa haka za a yi uwar ɗakina." Tana gama maganar ta fice daga ɗakin, Raihan miƙewa ta yi tana ɗan waƙe-waƙenta sannan ta faɗa toilet don ɗaura alwalar sallar asuba. Sai dai rana ta buɗe sosai wacce take nuni da gari ya waye tangararan don ƙarfe tara har da kwata a lokacin.

Sai dai har lokacin mafarkin da ta yi bai gama sakin jikinta, wani abin da ya bata mamaki bai wuce zuwan period ɗin ta ba alhalin ba lokacin zuwansa ba ne.

Mama Uwani tana fita bayan Raihan ta shiga toilet wata baƙar mage ce ta ratso daga bangon kusurwar ɗakin, idanunta jawur suke kamar gauta ga ƙarshen jelarta wani tafkeken kan maciji ne ban da sheƙi babu abin da yake yi. Kalle-kalle ta fara yi tana shine-shine sannan ta fara girgiza cikin wani irin yanayi, lokaci ɗaya ta fara rikiɗa zuwa kaloli daban-daban. Sai da ta rikiɗa zuwa kaloli sama da goma sannan ta dawo kalarta ta farko, ta buga tsalle zuwa kan gadon da Raihan ta tashi wanda har ya ɗan fara ɓaci da jini. Tana hawa kai ta fara lasa sai da ta siɗe shi tas sannan ta sauko cikin takun ƙasaita tana kalle-kalle, a hankali ta taka zuwa kan mudubin Raihan da ke cike da kayan shafe-shafe da turarruka kala-kala.

Girgiza ta yi lokaci ɗaya ta rike zuwa wata mummunar hallita mai siffar dorinar ruwa da ranƙwalelen ƙaho a goshinta, a hankali ta fara zuƙe mayuka da tururrukan da ke cikin kwalabe da robobinsu, nan take komai ya zama wayam babu komai a ciki. Wani irin ruwa ta shiga ɗurawa mai yauƙi sai da ta gama cika su sannan ta hura iska suka dawo tamkar mayuka da turarrrukan da ke ciki da farko. Mama Uwani ce ta tunkaro ƙofar da sauri wannan hallitar ta sake rikiɗewa zuwa mage wannan karon jelar rabuwa ta yi gida biyu dukkansu ɗauke da kan maciji. Tana jin alamun buɗe ƙofa da sauri ta ratse ta jikin bango ta ɓace daga ɗakin, sai dai takaicinta ɗaya da bata samu ta ƙarasa cimma abin da yake tafe da ita ba.

Mama Uwani jere kayan abincin Raihan ta fara yi, a daidai lokacin Raihan ta fito ɗaure da towel. Da murmushi Mama Uwani ta riƙo hannunta tana faɗin, "Ƴar gatan Uwani me kike buƙata bayan wannan?" Ɗan yamutsa fuska ta yi ta ce, "Babu." Mama Uwani cikin wani yanayi ta fara bin ɗakin da kallo, Raihan ta ɗan ja guntun tsaki tana faɗin, "Mama Uwani ki bani wuri bana buƙatar hayaniya."

Mama Uwani ba don ta so ba ta juya jiki a sanyaye ta fice daga ɗakin tana waige, fitarta ke da wuya Mommy na kawo kai tana ganin Mama Uwani ta ce, "Uwani yarinyar ta tashi kuwa?" Mama Uwani cikin ladabi ta ce, "Ta tashi hajiya yanzu na kai mata abin kari." Mommy bata tanka mata ba ta tura ƙofar ɗakin ta shiga, Raihan na gaban mudubi za ta fara shafa mai. Mummy ta kira sunanta tana ci gaba da cewa, "Raihan ba dai yanzu kika ta shi kika yi sallaha ba?" Raihan ta ɓata fuska ta ce, "Haba Mommy wai me kika mayar da ni, ni ba sallah ma zan yi ba period ɗina ya dawo." Fuska ɗauke da damuwa Mommy ta ce, "Period kuma, ina ce yau ko sati biyu ba ki da gamawa ba." Cikin rashin damuwa ta gyaɗa kai tana ci gaba da shafa mai, juyawa Mommy ta yi ta fi ce tana faɗin, "Gaskiya idan ya ci gaba da yi miki wasa dole mu je mu ga likita." Raihan ta tura baki gaba ƙasa-ƙasa da murya tana faɗin, "Kawai don period ɗina ya dawo sai ace sai na je wani Hospital ana zaune ƙalau." Turo ƙofar da aka yi ne ya sa Raihan waigawa a lokacin ta fesa turare tana saka wata doguwar rigar bacci, Mama Uwani ce ta sake shiga hannu ɗauke da kunun gyaɗa ta ajiye, Raihan na ganin haka ta saki murmushi mai sauti ta ce, "Mama Uwani dama kin yi kunu shi ne baki kawo min ba, ai kuwa da na cika cikina sai kin kwashe min tass kin ɗura min kunun nan." Ta ƙarasa magana tana zame towel ɗin jikinta don ita Raihan bata kunyar ko a gaban waye ta cire kayanta ko ta sauya wasu.

Mama Uwani na ganin haka ta fice daga ɗakin, Raihan na cikin saka kaya ta ji kanta na sara mara lokaci ɗaya jini ya fara bin ƙafarta ga wani irin raɗaɗi da jikinta yake yi ta ko'ina, nan take ta yanke jiki ta faɗi a wurin. Wani irin hayaƙi ne ya fara zirarowa ta jikin ƙofa har sai da ya zo gaban Raihan da ke kwance jini ya fara malala daga jikinta, lokaci ɗaya hayaƙin ya rikiɗa zuwa siffar mutum. Kallon kan mudubin Raihan ya yi yana girgiza kai cike da baƙin ciki, ɗaya bayan ɗaya ya fara zuƙewa mayuwan ciki da yake ganinsu da kalar ruwan nan mai yauƙi, kusurwa bangon ɗakin ya kalla ya ce, "Tabbas ba aikin kowa ba ne sai naki Mugaza, na lura kin fara wuce makaɗi da rawa amma ranki sai ya yi mummunan ɓaci." Tun bai rufe baki ba magen nan ta sake ɓullowa ta bango, har sai da ta zo gabansa ta yi girgiza cikin surar wata matashiyar budurwa ta ce, "Ka ga laifina don na nakasta mai shirin tarwatsa farincikina? Ko kana tsammanin zan zura ido ka ɗauko mini kishiya alhalin ka san wannan haramtacciyar al'ada ce a zuri'armu. Wani abin takaici ma ka rasa wacce za ka aura sai bil'adam salon ka ja mini abin kunya cikin ahalina, wallahi ba zan lamunci haka ba kuma wannan somin taɓu ne ka zuba ido ka gani." Tana gama maganar ta sake rikiɗa zuwa mage ta ɓace daga ɗakin, cike da takaici ya kalli gadon Raihan sai kawai ya fara kiran sunan Hidaya. Sai da ya kira sau uku sannan wata matashiyar budurwa ta ratso ta ƙarƙashin ƙasa mai zubin siffar Raihan babu abin da ya bambamta su har kayan jikinta. Wurin abincin Raihan ya nuna mata ya ce, "Ki maye gurbinta kuma bana buƙatar a samu matsala idan ba haka ba har abada ke da biyan buƙatar ƙudurinki."

Idanunta ne suka ciko da ƙwallah ta ce, "Wuskarbat min kalsusbima wakfit karmu linkasbu muzrabatu fisgatmuha warmi Jalkisu Mu'az." (Don Allah karka yi mini haka, ka san duk duniya babu wanda nake ƙauna kamar Yarima Mu'az.)

Ɗaukan Raihan ya yi da ke kwance ya saɓa a kafaɗa sannan ya kalli jabun Raihan da ke tsaye ya ce, "Dole ki ɗauki ɗabi'a irin ta Raihan hatta yare dole ki ci gaba da irin yarenta ba namu da muka saba yi ba. Na gaya miki idan aka samu matsala ke da Yarima Mu'az har abada." Yana gama maganar ya daki tsakar ɗakin nan take ƙasar wurin ta dare ya faɗa ciki hannunsa ɗauke da Raihan suna shigewa ƙasar wurin ta haɗe ta shafe kamar wani abu bai taɓa faruwa a wurin ba.


SHARE HILIS🌚

Daga yau za ki iya turo kuɗinki don karki bari ayi babu ke🤸🏻‍♀️🤸🏻‍♀️🤸🏻‍♀️

Ummou Aslam Bint Adam🌚
[7/9, 9:22 AM] Ameera Adam🌚: *ZAUJATU JINNUL-ASHIQ*


© *AMEERA ADAM*

Littafin kuɗi ne idan kina buƙata 300 ne ta Account 3090957579 Aisha Adam, First bank. Za ki turo evidence ta wannan lambar 0706 206 2624 Whatsapp only Idan kati ne 300 MTN.

*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*

FREE PAGE 2

https://chat.whatsapp.com/J0qrgC0rXNQ57u50VzeewR

A hankali Jabun Raihan ta fara bin ɗakin da kallon, miƙewa ta yi ta fara buɗe drowers ɗin kayan Raihan sai kuma ta bi hotunan ɗakin Raihan da ke maƙale a jikin bango tana kallo ɗaya bayan ɗaya, tana jin motsi ta koma wurin kayan abincin ta zauna. Kallon abincin take don sam bai burgeta ba cikin zuciyarta take mamakin irin abincin bil'adam don ita bata ga abin daɗi a ciki ba. Goggo ce ta turo ƙofar tana faɗin, "Rehanu! Ke Rehanu wai ina kika shiga ne tun jiya ban ji wulgawarki ba, yarinya sai iya shege don kin ga na damu da ke." Turus ta yi tana kallon Jabun Raihan da ke cin abinci tana yamutsa fuska, daƙuwa ta yi mata da hannu tana faɗin, "Kin ci ƙaniyarki Rehanu dama kina jina kika yi shiru to kin wulaƙanta uwarki Abu. Meye wannan ɗin kike ci kina yamutsa fuska kamar abinci?" Jabun Raihan a daƙile ta ce, "Gashi kuwa kin gani."

Goggo ta shiga ɗakin ta yi tsaye a kan Raihan tana faɗin, "Oho dai kowa ya raina uwar wani tashi ya raina, wallahi duk maganar da kika gaya min uwarki da Ubanki kika gayawa." A fusace ta ɗago tana duban Goggo da ke tsaye tana zazzaga ruwan masifa, farantan gabanta ta kalla tana motsa baki lokaci ɗaya ta cinye abincin ciki sai kwanukan, tana kallon Goggo kamar wacce ta basu umarni sai farantan suka yi tsalle zuwa gaban Goggo, wuƙar da Mama Uwani ta haɗowa Raihan don ta riƙa yankar farfesun ƙafar sa ce ta yi tsaye a daidai fuskar Goggo saitin idonta tana wani juyi, kamar za ta tsokane mata ido. Jabun Raihan ta kalli Goggo fuska ba walwala tana cewa, "Kika sake zagar mini iyaye sai na tsokane idonki, ke da sake gani har abada. Wannan kwanukan kuwa sai na basu umarni su yi ta ranƙwale miki kai har sai sun illataki." Goggo daskarewa ta yi a wurin, tuni fitsari ya jiƙe mata zani gumi sai yanko mata yake ta ko'ina. Tun Jabun Raihan bata gama magana ba, Goggo ta juya da gudu tana ƙawalawa Mahaifiyar Raihan kira, sai dai yadda ƙafafuwanta suka yi mata nauyi ya sa ta fice da rarrafe zanin jikinta kuwa tuni ya samu mutsuguni a bakin ƙofa.

Tana fita Jabun Raihan ta miƙe tana kaiwa da kawowa don gabaɗaya zaman wurin ya gundureta, abin da ya sa ta bi umarnin Huzaifa don biyan tata buƙatar amma ba don haka ba babu yadda za a yi ta amince da rayuwa cikin siffar bil'adam.

Huzaifa bai tsaya ko'ina ba sai cikin wani ƙasurgumin daji mai ɗauke da jajayen furanni, da jajayen ƙoramu. Komai na wurin ja ne hatta ciyayin da suke wurin, sai waɗansu korayen kifaye da su kaɗai ne suka bambamta da jajayen abubuwan da ke wurin. Kan wani jan dutse ya kaita ya kwantar da ita nan take ya fara gyara mata jikinta, kafin wani lokaci tuni ya gyara mata jikinta ya ɗauko wani ƙaramin jariri da ke kwance cikin wata ƙorama mai ɗauke da siffar kunkuru, sai dai kansa ɗauke yake da kawuna huɗu kowanne da surarsa. Akwai kai mai siffar jaki, agwagwa, mage da mai siffar kifi, a kowanne kai akwai manya kahunhuna guda biyu, daga jelar hallitar ɗauke take da tafkeken kan maciji. Yana zuwa ya ɗora shi a gefenta sannan ya ɗaga hannunta ya tura shi ƙarƙashin jikinta kamar yadda uwa take rungume jaririnta. Nesa da su ya koma yana sakin murmushin farinciki a fili ya fara faɗin, "Na jima ina burin haka ban samu dama ba domin gudin abin da zai ɓata miki rai, sai dai a wannan karon dole na ɗau wannan matakin domin haka ne kaɗai sai tseratar da ke daga kaidin Mugaza, idan ba haka ba duk yadda za ta yi sai ta halaka min ku. Ni kuma ba zan juri rabuwa da ke ba wanda ya nemi raba ni da ku zan iya hallaka shi ko wanene, ko da kuwa Mahaifina ne Jingas." Yana gama magana ya ɗaga dutsen da Raihan take kwance da jaririnta, naɗe su ya yi cikin wani kogon dutse sannan ya hura wani kogi da korayen kifayen nan suke ciki, nan take ruwan ya dare Huzaifa ya jefa su ciki ya sake hura ruwan ya haɗe gabaɗaya.

Mommy na daga falo ta fara jiyo muryar Goggo na ƙwala mata kira, da sauri ta nufi wurin da ta ji muryar Goggo tana zuwa ta yi turus ganin Goggo na rarrafe daga ita sai ɗan fatari. Da sauri ta sunkuya tana faɗin, "Goggo lafiya kuwa ko ƙafar ce ta motsa?" Tun bata rufe baki ba Goggo ta ci gaba da faɗin, "Abu ki dubi Allah da ma'aiki ka mayar da ni Albasu wallahi na yafe zaman gidanki, ki maida ni Albasu na mutu cikin aminci tun bata tsaface ni a gidan nan ba." Goggo na maganar hawaye da majina na zuba, a gefe ɗaya fitsari ne ke zuba don Goggo ta yi fitsari daga ɗakin Raihan zuwa babban falo ya kai sau uku.

A ɗan tsorace Mommy ta waiga tana faɗin, "Goggo lafiya kuwa wace ce ta zama matsafiya?" Goggo ta fyace majina da gefen zaninta ta ce, "Wa kuwa kika sani idan ba Rehanu ba. Wallahi yadda na ga tana tsafi ido biyu na ga Annabi haka..." Tun bata ƙarasa maganar ba Mommy ta fara waige tana katseta da sauri cikin ƙasa-ƙasa da murya.

"Goggo don Allah ki daina faɗin haka wallahi Alhaji yana gida kar ya ji abin da kike faɗa, kin san fa baya kawaici a kan yarinyar nan Raihan." Tana rufe baki Inno ta ƙaraso wurin tana faɗin, "Allah ya tonu asirinku, ashe gulmar Ɗana kuke da jikalleta to ahir ɗinku wallahi ke Zinaru ki yi ta kanki arziƙi kika zo ci ba zan miki baƙin ciki ba, gida dai gidan Ɗana ne ba a isa a sawa jikata ido." Goggo takaici ya sake cikata tana ganin kamar gori Inno take yi mata, don haka a zafafe ta ce, "Allah ya sa ni na haifi Abulle har ɗan naki ya aura, magana ce na gama ta yau za a mayar da ni Albasu don wannan sheɗaniyar jikar taki ba za ta sayar da kaina ina ji ina gani ba." Inno na jin haka ta yi zaman ƴan bori daɓar sai kawai ta fashe da kuka, da sauri Mommy ta koma wurinta tana rarrashinta amma fir taƙi yin shiru. Suna nan zaune Alhaji Abdallah ya sauko cikin dakakkiyar shadda ruwan toka da hula baƙa, kayan ba ƙaramin kyau suka yi masa ba. Tun kafin ya ƙaraso Mommy ta fisge ɗankwalinta ta rufawa Goggo, yana ƙarasowa ya ce, "Lafiya dai Inno mai yake faruwa?" Inno na jin haka ta rushe da kuka tana faɗin, "Audullahi ka dubi irin sitirar da ka yi wa Zinaru ita da ƴarta amma da yake sun samu wuri wai cin naman ka suke da ƴarka ɗaya tilo a gidan duniya. Don Allah ko don darajar haihuwa Abulle ai da ɗagawa yarinyar nan ƙafa ina dalili tana uwarta tana cin namanta?" Goggo ta ƙanƙance ido cikin masifa ta ce:

"Audullahi wallahi tun wuri ka san halin da kake ciki, kwarankwatsa dubi Rehanu ta shiga ƙungiyar asiri."

Kamar wanda aka zagi iyayensa haka Alhaji ya ɓata fuska sai da ya haɗiyi yawu mai ɗaci ya ce, "Goggo kin san wa kike faɗa kuwa? Raihan ɗina ce ta shiga ƙungiyar asiri?"

"Ƙarya na yi maka kenan Audullahi?" Goggo ta tambaye shi tana ɗage kai gefe. Shiru ya yi don ya san idan ya buɗe baki
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment