Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

acikin kabarinka, idan kana yinta da kyau, ina kara tunatar daku kuji tsoron Allah, domin duk abinda mutum ya aikata zeje yasamu abinsa yana jiransa. Alhamdulillahi, ina kyautata zaton Rahma agurin Hajjo, saboda takasance mace tagari, kuma tana ibada sosai, batada abokin fada, bata taba batamun ba, aduk zaman damukayi.

Allah yajikanta da rahma, Allah yasa sanadiyyar mutuwarta yazamo mana shiriya akan halayen mu marasa kyau. Zaku iya tafiya, hawaye ne kawai suke zarya afuskar Alh, shima yakasa tsaidasu, kowa agurin kuka, yakeyi, Jidda kuwa jitayi kamar tafada ma Dadynsu abubuwan datakeyi yaroka mata Allah shiriya,sede tanajin kunyar fadar irin laifinta agaban mutane, sede tayi alkawarin komawa islamiyya, domin neman ilimin dazata tuba dashi.( ni kuma nace Allah yasa ba tubar mazuru zakiyi ba Jidda, nasan dan adam da mantuwa).

Haka suka cigaba dazamansu acikin gidan gwanin ban sha,awa, Baba Mairo tana kokrin kula da Ameer dan yanzu yayi wayon sede kullum doloncinsa kara fitowa yakeyi, haryanzu ko zama befara ba, sbd kanshi baya tsayawa.
Falak da jalila sukeyi taya Baba mairo aiki dan surage mata wahala, Jidda kuwa dama bata iya girki ba sede gyran daki da falo, kuma shine aikinta. Zarah kullum cikin jin haushin irin yanda Alh, yakeyima Falak da Ameer take, gani take yanzu ,ya,yanta ma sune wararru agurinshi, kome yasamu yace Ameer, akwai wani katon mall daya bude. Suna Ameer yasa, bakaramin jin Ameer yake acikin ranshi ba, gani yake kamar yajawo girmanshi koze fara fita dashi yana tayashi aiki,

Hakan dayakeyi bakaramun kara wutar kiyayya yakeba azuciyar Zarah, kuma tayi shiru ne, kawai tana jiran dan lokaci, mutuwar takara nisa. Jidda andage dazuwa islamiyya duk da ba ajinsu daya dasu Falak ba, amma batajin kunyar shiga cikin kannanta.

Duk abinda bata ganeba, su Falak suke nuna mata agida, bata zuwa ko ina daga makaranta se gida. Al,amin bakaramin shiga tashin hankali yayi ba, saboda rashin Jidda, duk cikin yan matanshi, ita kadai yakema so metsanani, idan yakirata bata dauka, gashi dama can tahanashi zuwa gidansu,yarasa yanda zeyi yasameta, har kawarta Ameera yasa taje ta dubo mashi ita, amma koda taje tasamu Jidda ta tuba, tafara kawomata maganganun banza seda sukayi fada da Jidda, Haka tafito ranta abace. Data fadama Al,amin shima beji dadi ba, yasan tunda Jidda tadena yin harka shikenan bazata kara sauraronshi ba, haka yacigaba da kiranta, amma shiru.

Jidda ce zaune adaki, tadauko jakarta zata bama, Jalila kudi tasiyo mata, kati, murmushi tayi aranta tace wai yau nice dasiyan kati, lallai mata sunyi sanyi, dubawa tayi sede babu ko sisi aciki, tashi tayi taje gurin Umminsu tace Ummi dan Allah bani 500 Jalila tasiyomun kati.

Wani mugun kallo Zarah tayi mata, batasan dama cike take da ita ba, saboda wannan sabon halin data sake, gashi yanzu ko kudin datake samu hartana bata yanzu babu, gashi yau dan tabewa kudin kati ma suna gagararta.

Ummi ina magana kinyi shiru, Bazan bada ba, ko dole ne? Tunda rayuwar da kika daukarma kanki kenan, talauci ma yanzu kika fara, wata rana ma se kufin siyen turare sun gagareki, tunda dole se Alh, yazo gari sannan yake baku, suma kuma bawasu masu yawa ba, tunda yace bayason saba maku da kashe manyan kudi wai saboda gidan wani zaku.

Wlh kwandalata bazan baki ba, fita kibani guri. Amma Ummi bekamata kifadamun haka ba, kinmanta abunda nayi maki ada, amma yau saboda nace kibani 500 kike fadamun magana,,, saukar marin dataji ne yasata yinshiru.

Fita tayi tabanko kofar tanufi dakinta tana kuka, lallai tayarda sekana dashi kake zama wani abu agurin kowa. Wanka tashiga, sabulun nata ma yakare, ita kuma tafisonshi, dan Jidda babu abinda ta tsana irin taga jikinta yana baki, duk da bawata fara bace amma da tsiya takoma fara, haka tayi wanka da sauran sabulun daya rage tafito, manta ma saura kadan turarukanta duk sun kare, gashi bata saba da shafa turare daya ba.

Gaskiya bari Dady yazo gobe yabamu kudin siyan kayan shafa, bazan iya zama babu kudi agurina ba, wlh.

Saye suke akitchen suna girki, jalila tace wai ni Falak naji ko maganar Mal. Sameer bakiyi, kode harkin manta dashine? Hararta Falak tayi tace meye tsakanina dashi dazan tambayeshi.
Jalila tace ai naga kedin tadaban ce agurinshi, kozakicemun bakisan mal. Sameer yana sonki ba? Falak tace kede makaryaciya ce wlh, kawai daga muna mutunci dashi zakice yana sona, shida babu ruwanshi, da kowa, kilama yanada budurwarshi yar jami,a mezeyi dani. Jalila tayi dariya tace uhm kede fadi gaskiya gashi nan harkin fara kishinshi, ruwan dake hannunta akofi ta watsa mata, fita tayi tana mata dariya. Rufe ido Falak tayi, ita kanta tasan tayi missing mal. Sameer, ta dade da fara sonshi, sede bata son tafara fada mashi ya wulakantata hakan yasa tahakura.

Zaune suke afalon Alh, suna fira, jidda tace yauwa Dady wlh kayan kwalliyarmu sunkare, dariya yayi yace to Mamana yanzu kuwa za,a baku, koda yake kekadai zanba tunda nakine yakare, jalila da Falak sukace a,a Dady hadamu. Wata irin harara Zarah ta watsa ma, Falak jin yanda take wani zakewa kamar ba AGOLAH ba. Tsaki taja har seda yafito fili, kara gyarama Ameer zama yayi akan cinyarshi, ya kalleta yace yade da tsaki, murmushi tayi tace Allah Alh, kai ke kara shagwaba, yaran nan, yan matane fa amma ace haryanzu kaine zaka rika basu kudin kayan kwalliya, ai gara ma abama Ameer dina shine yaro.

Dariyar jin dadi yayi yace a,a ki kyaleni da yarana, suma agurina yarane, kuma hakkin uba baya sauka daga kan yayanshi harse ranar daya aurar dasu, hakan yake hana mata karbar abun hannun samari, wanda yawanci shine yake jansu zuwa ga halaka, kuma da wannan damar samari suke amfani gurin yaudarar yan mata. Dubu goma goma yabasu, yace suje su siyi abinda sukeso, dubu goma ya mikama Jalila yace ansa ki kaima Baba mairo, na ameer ne, shima asiya masa kayan dadi, wata 5 yaciro yace tabata itama tasiyi abunda takeso.

20k yamika ma Zarah yace kema uwargida ganaki, hadiye bacin ranta tayi, ganin yan kudin da yabata, bam bancin 10k ne tsakaninta da AGOLA, da kuma dan karamin yaro, wanda ada Alh, seyabata 50k kawai na kayan kwalliya, gaskiya dole ma tasake tsari, seta cire Falak Da Ameer azuciyar Alh, shima sena maidashi rakumi da akala.

Jidda ce tafito zata kasuwa dan su Jalila sunce se gobe zasuje, gashi driver bayanan, ita kuma bazata bari se gobe ba, tafiya take zataje bakin titin domin tarar abun hawa, se sababi takeyi, yama za,ayi 10k ta isheta siyan kayan shafa, to mema zansiya, 10k ai basu kai kudin man datake shafawa ba ma, bare akai gurin sabulai, da turaruka. Gaskiya dasake wlh,,,,, karar horn dataji ana yimata ne, yasata tsayawa, Al,amin ne yafito har yana tuntube ya iso gurinta fuskarshi dauke da murmushi. Bayan sungaisa yace haba Dear meyasa zakimun haka? Jidda tace muje cikin mota muntsaya bakin titi kada Dady yagammu.

Tafiya sukeyi hannunshi cikin nata, tawani lumshe ido, ita kanta tasan tayi missing Al,amin. Yace ina zakije haka cikin rana? Tace. Wlh kasuwa zanje siyan kayan kwalliya. Murmushi yayi yace haba ba girmanki bane zuwa kasuwa, ina laifinma kije mall aizefi. Aranta tace idan kudina sunkai shiga mall ko. Karya kan motar yayi zuwa wani babban mall, suna tafiya yana fadimata irin yanda yayi missing dinta, har suka isa.

Siyayya yayi mata takusan 100k, duk abinda batada shi seda tadauka, azuciyarta fadi take Allah nagode maka daka kawomun Al,amin dabansan yanda zanyi da 10k ba wlh. Haka suka fito suka shiga mota yakalleta yace Baby muje gidana mana nayi missing dinki fa, kallonshi tayi tace Dady na gari fa, kashe mata ido yayi yace just 1 hour plsssss, yana kamo hannunta, murmushi tayi tace ok badamuwa muyi sauri. ( Wa iyazubilla, Allah katsaremu daga sharrin zuciya, dason kudi, domin abinda yake faruwa kenan azamanin nan, rashin godiyar Allah, mutane basa taba godema Allah, daga abinda yabasu duk mun kadan dinshi, hangen nawasu shine yake kara dulmiyar damu zuwa ga halaka. Allah kacire mana son zuciya, ameen.)

Urs,
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)
08028525263
[5/29, 2:15 PM] Nabeela lady: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)

@ ( H, O,N,A)

Part 55.....60

Tundaga ranar Jidda takoma ruwa, fiye da baya, sosai Al,amin yake kashe mata kudi, dan shide Allah yajarabeshi da son Jidda, itama haka tana masifar sonshi, dan danan Zarah takara jawo Jidda jikinta ganin yanzu tana samun kudi fiye da da. Haka tafara zirya zuwa Zariya, itama kanta Asabe tayi murnar dawowarta, dan tasan zata cigaba da cin dadi, dan ita tasan abinda Jidda take aikatawa, kuma bata damuwa, dan itama tsohuwar yar duniya ce. Jidda har kasar waje tafara fita ita da Al,amin sbd yanzu arzikinshi yakara habaka, har waje yake zuwa saro kaya, kuma duk sanda zeje tare suke zuwa da Jidda, dan Jidda akwai gayu da gyara, bata wasa da kayan mata.

Zarah ce zaune adakin Asabe, tagama fadamata abinda takeso bokayayi mata. Asabe tace ai dama kyaleki nayi mutuwar tadanyi nisa, sannan inzo maki da irin maganar nan, segashi kinrigani, bara inkira Dije muje, amma ai baje yuwa ba ace AGOLA tafi masu gida. Kuma wlh wannan yaron damuke rainawa, idan har bakiyi da gaske be, wata rana zesaki kuka daga shi har AGOLAR.

Bayan Dije tazo ne suka fada mata abinda suka shirya, murmushi Dije tayi tace meyasa kukeson yin abu bakwa tunawa da mutanen gari, kunsan fa yanzu mutum ake kiwo ba dabba ba, akwai matsala 2 dazaku fuskanta idan har kuka aikata abinda kukace. Tafarko de idan kuka sa aka kori Falak da Ameer daga gidanki, mutane babu wanda zasu zarga seke, har Mijinki keze zarga.

Matsala ta 2 kuma idan har kuka kashe Falak da Ameer, wlh ina me tabbatar maki da kotu seta daureki, dan nasan mijinki baze taba yarda dakeba, dole yasa yan sanda su bincikeki,
Asabe tace wlh shiyasa nakesonki kawata, yanzu me kike ganin za,ayi? Gyara zama Dije tayi tace zanbada shawara 1 amma fa idan tayi maku, Zarah tace wlh kifada zatayi,

Nafarko de za,a kashe Ameer, amma ta hanya mafi sauki wanda babu wanda zeyi zargin kasheshi akayi.
Na biyu kuma, dole zaki mallake Alh, za,a kawar da kanshi daga Falak, tayanda zemanta da ita acikin gidan kome zakiyi mata baze ce komai ba, sauran yan gida kuma ke keda iko akansu, bakamar wannan tsohuwar munafukar, wadda kika yarda da ita sosai.

Se kuma Jalila, ita kuwa diyarki ce kinsan yanda zaki tafiyar da ita. Falak kuwa kada kiyi mata komai, hakan zesa kifita daga zargin mutane, Ameer dama kowa yasan beda lafiya. Amma Falak kimaida ta ita da almajira basuda bam banci, duk wannan dadi datakeji kihanata, Mairo takoma girki kawai, sauran aikin gidan sukoma kanta. Wannan kyawun nata kimaidashi muni, kuma kirabata kwana daki daya da Jalila,

Kimaida ta store tarika kwana ita da kwari sucinye wannan shegen jikin nata, duk wani kayan more rayuwa ki anshe su, kayanta ma zanbaki wasu tsofaffin kayana ki kaimata, tarika sawa, ko aike kasuwa yatashi daga kan driver yakoma kanta.

Kuma kicema Mairo tamaida rikon Ameer hannun Falak bazaki iya cin abincinta ba, tana renon yaro me zubda miyau. Daga karshe kuma kisamu dan kwaya ki aura mata shi, idan bahaka ba kina gani masu kudi zasu aureta, dan kinsan tafi yayanki kyau.

Shiru Zarah tayi, Asabe tace yanaji kinyi shiru, tobari infada maki, wlh ba,a samun duniya da tausayi, idan baki sani ba, nidin nan seda nakashe mutane 2 saboda kudi, kuma duk mazaje nane, nakuma gudu da dukiyarsu, Babanki ma........ Saurin hadiye maganar tayi tuna dawa take magana tayi. Babanki ma saboda irin Son danake mashi ne, yasani zuwa naroki ya aureni, kinsan tunda nake bantaba son wata halitta kamar Babanki ba. Shiyasa gashi nan muna zaune lafiya abummu. Murmushi Dije tayi jin irin saurin kwaskwarimar da Asabe tayi.

Dije tace idan har kika iya aikata abunda nace maki, kawai kihangoki cikin jerin manyan mata masu fada aji akaduna, yanzu ina kawarki Karima, bakince tunda mijinta yamutu ba, tabar garin tana can Abuja gidan kudi, batada aiki sefita kasashe, ina da bakinki kikecewa yanzu ko wayarki bata dauka saboda tayi kudi, wani lokacinma sese me aiki tadauka tace tana bacci.

Haba Hajiya kalleki fa, yanda kike da kyan nan rashin samun kudi masu yawa ne da hutu yarage maki kyawunki, yanzo dan kasuwancin dakikeyi ma kudin duk sushige gurin boka, yanzu haka kila bakida wanda zamuje gurinshi yanzu, dan kinsan aikinshi kamar yankan wuka ne shiyasa yakeda amsar kudi masu tsoka.

Zarah tace wlh, ashirye nake da inyi abinda yafi hakama matukar zansamu kudi, kuma arayuwata babu wadda na tsana kamar Falak, zanyi duk yanda zanyi in kunta tama rayuwarta, bazata taba fin yayana ba, ita Kuma Jalila nasan yanda zanyi da ita, kunsan babu abinda ta tsana kamar fushi na, ko kuma ince zan tsine mata, bakaramun shiga tashin hankali take ba, idan taji furucina ba.

Saboda tana zuwa islamiyya, kuma suna aiki da abinda ake koyamasu sosai, Mairo kuwa kubarni da ita, akarkashin ikona take, kome zanyi bazata iya fadama kowa ba, Alh, ne kawai zata iya fadamawa kuma shima zan mallakeshi. Dariya sukayi gaba daya. Suka tashi zuwa gurin boka.

Wata irin dariya boka yayi yace lallai Hajiya kinzo da babban aiki, kuma aikinki zeci kudi sosai, dan wannan karon zakisani karya maganata dan banayin aiki 2 alokaci 1, amma idan har zaki saki kudi bakida matsala.

Zarah tace boka kamar nawa ne kudinka? Aikin Alh, mesauki ne, zaki bada 150, shikuma Ameer nashi 200 ne, sekizabi 1 idan bakida kudi.

Zarah tace atemaka mun boka yanzu babu kudi sosai, amma ga na Alh, afara yimani aikinshi, se abani na Ameer dana koma bayan kwan 2 nayi maka alkawarin zanturoma Inna Asabe, kudin aikin Ameer takawo maka.

Dije tace boka atemaka mata, kasan yanzu munzama daya. Magani 2 yadauko yabata 1 yace wannan zaki saka ma Alh, acikin abinci, dazaran yaci kingama dashi, wannan kuma wuta zaki samu ko garwashi kifita waje kizuba kamar yanda hayakin nan zetashi sama baze kara dawowa ba, haka tunanin Falak zefita daga zuciyar mijinki, ko yaganta baze tuna amfaninta agurinshi ba.

Wani dan butum butumi yadauko yakama wuyanshi yasa zare yashake wuyan, yace wannan kuma Ameer, tundaga yau babu abinda zekara shiga cikinshi, kome yaci iyakarshi makoshi zedawo, nabaki nan da wani lokaci zemutu. Kuma daya mutu Alh, zemanta dashi, zakici duniyarki da tsinke, sauran kuma sekinje gurin me hukunci. Dariya yasa yace kutashi kutafi, Dije kije sebayan anbaku kudin kwa dawo, Zarah de bata fahimci abinda yake nufi ba.

Baba Mairo itadasu Falak suna zaune adakinta suna fira, ita kuma tana bama Ameer abinci abaki, Jalila tace wai gashi har yamma tayi amma Ummi bata dawoba, bansan meyasa yazu Ummi yawan zuwa Zariya ba, wanda ada batason zuwa.

Baba mairo tace keko tunda tana da mahaifi araye ai dole tarika zuwa. Aranta kuwa tana fadin Allah yasa bawani mugun abun bane yakaita...... bata karasa ba, Ameer yashiga amayar da abunda yakeci, cikin sauri ta dagashi tana sannu ka kware ko,

Ruwa Falak tamika mata tana fadin aishine yacika cin tsiya, ke kuma Baba mairo kita bashi abinci, karbar ruwan tayi tana fadin tunda beda baki aidole inrika bashi abinci akai akai, kodan ke abincin beda meki ba ne, Jalila tace kyaleta Baba mairo sotake shima yazama kamarta yar siririya,,,,,,,, ruwan Baba mairo tabashi, yana amsa yasake amayoshi.

Tadashi zaune tayi takara bashi, abun tunbe basu tsoro har yafara basu, jikinshi Bab mairo ta taba taji babu zafi, tace tomeke damunka Ameer haka? Jalila tace Baba kawai akira driver yakaimu asibiti tunda dady nenan nasan gobe zedawo.

Shiryawa sukayi suka kulle gidan suka ba megadi key din suka tafi, kafin su kai duk yajike Baba mairo da miyau, dan har miyan baya iya hadiyewa. Sunazuwa suka wuce gurin Dr, bayani Jalila tayi mashi, ruwa yadauko yabashi amma yamaidoshi.

Abu kamar wasa jikin yaro yafara rikicewa, tun likita yana daukar abun wasa, shima yafara shiga damuwa, daki yabasu aka kwantar dashi aka samashi karin ruwa da allurai, sannan yayi bacci.

Baba mairo babu wadda take zargi se Zarah, dan tariga data lura duk lokacin da taje Zariya sewani abu marar kyau yafaru akansu Hajjo, yanzu gashinan ta kauda Hajjo takoma kan danta, duk da tasan cewar itace tayi sanadiyyar maidashi dolo, yanzumma bata debe tammanin tanada sa hannu acikin wannan ciwon nashi ba.

Jalila takira dadynsu awaya tafada mashi, yace gashi nan yanzu zetaho, haka sukacigaba dazama, Falak se kuka takeyi, Jalila tana lallashinta, duk itama hawayen takeyi.

Koda Zarah tadawo, megadi yabata key, yace mata sunje asibiti kai Ameer, murmushi tayi aranta tace boka aikin ka nakyau, saurin shiga cikin gida tayi, kayanta kawai ta aje tadauko gawayi tadorashi akan electric burner seda yayi ja, sannan takashe, dauka tayi tanufi gurin part din Hajjo daga baya ta ajeshi, maganin tadauko tazuba aciki, nan take hayaki ua turnuke, sama yayi tayi har yacinye, kakkabe hannunta tayi tana fadin su AGOLA anzama baiwa. Saura kai Alh, Allah yamaidoka gobe.

Ciki tashiga tayi wanka tana saka kaya taji horn din. Alh, murmushi tayi tace wato kai game da anayi maka waya harkataho, nasan Jalilan banzan nan ce zata fada maka, kema zaki dawo kisameni ne,

Da sallama yashigo yace ah, Hajiya bada ke aka tafi asibitin ba? Yatsina fuska tayi tace nim yanzu nadawo daga Zariya, megadi yake fadamun, wanka nayi nake shirin tafiya, ok fito mutafi gaba daya. Falak ce takiraka ko? Shiru yayi yana kallonta, jin ankira sunan Falak seda kanshi yasara.

Murmushi tayi tace yanaji kayi shiru, Fala...... tsawar daya daka mata ce tasa ta yin shiru, meye haka wacece kuma wata Falak, kada inkara jin wannan sunan agidan nan, kema kika santa, Jalila takirani amma kirika fadamun wani suna, banaso, kiwuce mutafi.

Suna zuwa office din likita yawuce, bayan sungaisa Dr, yace agaskiya Alh, nakasa gano wace irin cutace ajikin Ameer, duk wani gwaji munyi mashi amma bamu sami wata cuta dazata nuna mana asalin ciwon shiba.

Abinda nake ganin zefi kumaidashi gida acigaba dayi mashi na hausa, dan gaskiya ina ganin ciwonshi kamar akwai aljanu aciki. Alh, yace hakane, nikaina nafara tunanin haka, tun sadda yafara zubar da miyan bakinshi, da kuma kanshi da baya zama, haryanzu fa Ameer baya iya zama. Bakomai nagode bara naje mutafi, dr, yace nacire mashi karin ruwan ma dan naga jikinshi baya bukatar ruwa, sede matsalar rashin cin abincin shi, idan har kuka koma gida yacigaba da mayar da duk abinda yaci, zan iya zuwa gidan, ko insa azo arika samashi karin ruwa. Godiya sosai, yayi mashi yatashi suka fita.

Tunda yashiga dakin Jalila da Falak sukayi mashi sannu dazuwa, ya amsa yace Jalila yagidan, tace lfiya lau dady, ko kallon inda Falak take beyiba. Baba mairo tagaisheshi ya amsa yana tambayarta Ameer da jiki.

Zarah farin ciki ne aranta, fal, ganin yanda yayi ma Falak, sukuwa basu kawo komai aransu ba, ganin halin da ake ciki, Alh, yace sutashi sutafi gida, ansallamesu, anan yayi masu bayanin da Dr, yayi mashi. Baba mairo tace idan ko haka ne, Alh, se akaishi gurin Malami. Zarah tace koma de menene kuwuce muje, gida. Kallon mamaki Baba mairo tabita dashi, haka suka wuce da driver ita kuma tabi Alh, aranta tana fadin dole yau kaci maganin nan ko aikina zefara dawuri.

Urs,
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[5/29, 10:23 PM] Nabeela lady: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!! Nah,
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)

@( H,O,N,A)

Part 60..... 65

Suna zuwa gida Baba mairo ta kwantar da Ameer, su Falak kuma suka wuce daki domin yinsallar magrib. Wucewa kitchen Baba mairo tayi domin dumama masu abinci tayi, shikuma Alh, tadora mashi abinci mesauki, daki takoma tayi sallah.

Bayan tafito ta koma kitchen tana hadama Zarah abincin Alh, Zarah ce tashigo kitchen, din, tace yau mairo jeki dakina kidauko mun wayata bisa gado, tana fita tayi saurin bude cooler din Alh, taciro magani tazuba, kokarin maidawa tayi azaninta, juyawar dazatayi taci karo da mairo tana kallonta mamaki dauke afuskarta.

Cike da duniyanci Zarah tace shigo mana Mairo naga kintsaya kina kallona, Mairo tace dan Allah Hajiya wane irin magani ne kika sama Alh, kinga duk abinda yasame shi ni za,a zarga tunda ni nayi girkin.

Murmushi Zarah tayi, tace bazan fada maki ko maganin menene ba, idan yaci kome yasameshi aka kamaki, zakiyi bayani, ido waje Mairo tace kirufa mun asiri dan Allah hajiya.
Zarah tace naji. Amma da sharadi, banaso kowa yaji wannan maganar, kuma daga yau duk abinda zance maki banason gardama kinsan de ni nakawoki gidan nan ko? Saboda haka kina karkashin ikona, banason shishshigi, ki tsaya amatsayinki na me aiki, daga yau banaso ki kara fitowa daga dakinki matukar Alh, na gidan nan.

Kuma daga yau, zaki maida Ameer hannun Falak, dan baze yuwa kina girki kuma kina renon kazamin yaro ba, aiki yanzu ze koma girki kawai, naruwanki da wanke wanke nasamu wadda zata rikayi mani harma da wankin kayana.

Inafatan kingane menake nufi, idan kinbi umarnina kicigaba dazama agidan nan, idan kuma kinki, zaki tafi kuma kibar amanar da Hajjo tabaki, dan nasan kafin tamutu tamika amanar yaranta agurinki.

Zabi yarage naki, kuma wlh idan kika kuskura kika rika shiga harkar Falak sekin barmun gidana. Zaki iya tafiya. Fita Baba mairo tayi tana kwalla, wannan wane irin sabon yanayine yashigo gidan nan, anya Hajiya bata fara shaye shaye ba? Ya Allah katsare bayinka kuma marayunka, tabbas Falak nasan rayuwarku zata shiga, kunci, sede bazan bari inyi abinda za,a koreni daga gidan nan ba, nasan idan natafi zakifi shiga damuwa sosai, kuma nasan wasiyar ummanki bazata bari kibar gidan nan ba, dasemu tafi tare.

Abincin tadauka takaima Alh, yana shirin zuwa yaga Ameer tashiga, tace ina kuma zakaje Alh,? Yace Ameer. Zan dubo, tace daga can nake yasamu bacci, kuma yaci abinci, kabarshi yayi bacci tunda yasamu yayi. To Alhamdulillah, Allah yakara bashi lfiya, wlh har hankalina ya kwanta, banason ciwon yaron nan.

Abinci tazuba mashi tana ta janshi ta wasa, sewani shige mashi takeyi, shi kuma duk ya rude, abaki tadebo zata bashi, ganin yana niyar yin bismilla, yasata fadawa jikinshi, dariya yasaka yana shirin yin magana tayi saurin saka mashi abincin abaki.

Taunawa yakeyi yana fadin Hajiya yaude naga alamar amarci kikeso musha, ko? Kara debowa tayi tasaka mashi yakarba, tana ta yimashi kwarkwasa, shikuma duk ya rude. Ahaka haryagama ci beyi bisimilla ba.

Yana gama ci yasha ruwa, ana take yai kanshi yayi mashi nauyi, rike kanshi yayi, kamoshi tayi ta dorashi bisa cinyarta tana shafa bayanshi, da haka haryaji kan ya lafa. Shiru yayi nawani dan lokaci, sannan yatashi yace zanyi wanka idan nafito se inje inga jikin Ameer. Bata fuska tayi tace nace bazaka jeba, kabari se gobe. Nan take yace to hajiya, inje inyi wankan ko?

Wani murmushi Zarah tayi, aranta tana fadin wlh dagaske maganina yaci, kai amma dole incika ma boka alkawarinshi. Kara daure fuska tayi tace zauna inason magana da kai, zama yayi yace inajinki. Kudi nakeso zansaro kaya. To to kamar nawa kike bukata? Dubu dari 5 nakeso.
Yace toshikenan yanzu na hannuna basu kaiba, tace ina check dinka? Yace yana nan, to kadauko karubutamun gobe se inje incira. Tashi yayi jiki na rawa yadauko ya rubuta mata, yamika mata, tace haba Alh, atsaye zaka bani kamar wata yarka, yace yi hakuri Hajiya, dukawa yayi yabata. Tace tashi kaje kayi wanka idan kafito kuma bance kafita ko ina ba, sallar isha,in ma kayita agida, idan kagama katsaya afalonka kayi kallo, idan kanajin bacci kayi kwanciyarka. Yace to Hajiya sekin shigo.

Fita tayi tana me cike da fari ciki tana shiga dakinta tace wlh, Alh, sekayi dana sanin yimani kishiya, sena maidaka abun tausayi arayuwa, daga yau bakai ba Ameer da shegiyar AGOLAR KA.


Juyawar dazatayi taci karo da Jalila tana gyara mata gadonta. Cike da firgici, tace Uban waya kawoki dakina? Jalila da tunda taji kalaman Umminta jikinta yafara rawa, kafin tayi magana hawaye sun wanke mata fuskarta.

Jawota tayi ta kwada mata mari tace ina magana shine zakimun shiru, wato labe kikemun ko, Jalila tace dan Allah Ummi kiyi hakuri, nibanji abinda kika ceba, kawai nashigo inamaki gyaran dakine.

Zarah tace idan ma kinji, bakiji karya ba, kuma zauna kibude kunnuwanki da kyau kije abinda zan fada maki, nasan sarai kinji maganar danayi, to haka yake bakiji karya ba, tunda Babanku ya auro uwar su Falak naji natsanesu, gashi nj bantaba haihuwar naminj ba, amma tana zuwa tahaifa.

Saboda haka idan harkina kishina, kuma kindaukeni amatsayin uwa, wadda ta tayi renonki tunkina jini harkika koma

Please Login or Register in order to submit comment