Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[4:21PM, 11/19/2016] Fadeela lamido: 💘💍💍MIJIN MARAINIYA💍💍💘


story
&
Written
Fadeela Lamido
Mmn yazeed📝


Bismillahir rahmanir rahim

1-3

Zaune take a dan ma tsakaicin gidan su tana ta faman share hawaye wata dattijuwan mata ce ta fito daga daki tana fadin , kin fara ko, dama ke idan tsohon munafunci ki ya tashi ba mutunci gareki ba, wlh uwarki ta bar miki mugun gado, ki zauna kiyi ta kuka salon iya ta ce ana miki wani abu, matsuwa tayi ta rike mata kunne tace ai baki ga komai ba safna sai rada na koreki gidan nan , zakiyi kuka, yadda uwar ki tasani kuka ta tura min bakin ciki kema sai na tura miki bakin cikin da zai kashe ki .

Safna taji zafin wannan ruko, fitsari ne yake bin kafafun ta, tace goggo dan allah kiyi hakuri , indai kuka ne na daina.
Kar ma ki daina dan jakar ubanki, tashi maza ki wanke kafafunki ki dauki rake , kuma karki dawo gidan nan sai ya kare.

Jiki na rawa safna ta mike ta dauki bukiti taja ruwa a rijiya ta shiga bayi, cikin sauri safna ke wanka dan gudun fadan goggo.

goggo na tsaye safna ta fito da bukitin wanka a hannun ta goggo ta bita da harara , da sauri tashiga dakin ma haifiyar ta, wanda a yanzun ita kadai take kwana acikin sa, cikin sauri ta jawo ledan kayan ta, ta fara cirowa tana dubawa duk tsun mukara ne , masu dan kyan goggo ta kwashe tayi kyauta dasu, haka dai ta dauki daya daga ciki ta saka, tadauki raken goggo ta kama hanya.

tafe take tana hada hanya domi ita bata iya tallah ba sai dai idan mutun ne yakira ta ,haka tai ta tafiya ko nera ba tayi ba, ta gaji ta koma gida.

goggo na zaune a tabarma ita da yaran ta guda biyu iro da salma, safna ta shigo , goggo ta mike yanzun nan dawo min da raken nan kikayi , iro tashi kaba yarinyar nan kashi rashin duka ke damun ta.

Kamar jira yake yamike da sauri ya fara kai mata duka daga kar she ma dukkan su suka taron mata wannan na duka wannan nayi , sai da suka ga bata iya motsi suka bar ta

WAIWAYE
malam musa mutumin kirki ne matan sa biyu goggo itace uwar gida, sai mahaifiyar safna wanda suke kira Inna, tunda malam musa ya auri goggo ta haifi iro bata kara haihuwa ba dan haka iya mahaifiyar malam musa ta matsamai ya kara aure, duk inda malam musa yaje neman aure ba a bashi saboda masifar matar shi, wata rana malam musa na cikin tafiya akan tsuhuwar mashin dinsa yaci karo da wata bafulatana batafi shekara sha biyar ba tana tafiya tana kuka, tsayawa yayi ya tam baye ta lfy take kuka, sai da ta share hawaye sannan tace wata yaya tace tayi aure a binni tunda mijin ya tafi da ita har yau bamu sake ganin ta ba, shine muka fito neman ta su baffah suka ce na jira su karkashin wata bishiya tunjiya har yanzun basu dawo ba, malam yace ina ne garinku , kame kame takama malam dai yagane bata san sunan garin su ba, goya ta yayi abayan mashin din sa dan su kara duba wajan ko iyayan ta sun dawo, suna zuwa suka duba babu kowa awajan , dan haka malam musa yace ma wani abukin sa dake zaune a waja bayanin cewa ko da iyayan ta sun dawo ya kawo su gidan shi.

malam musa gidan iya ya wuce da yar fillo saudatu dan yasan halin matar sa, iya ta kar beta hannu biyu tare da mamakin wauta irin na filani, sai da saudatu tayi shekara biyu awajan iya ba labarin iyayan ta ,dan haka iya ta matsawa malam musa ya auri saudatu, malam musa yabi umarnin ma haifiyar shi dan shima yafara tunanin haka.
bayan an daura musu aure da wata uku goggo ta sake haihuwan salma itako amarya saudatu sai da ta shekara biyu sannan ta haifi safna , saudatu tasha wahala a gun goggo dan ma tana samun kariya agun malam safna nada shekara sha hudu tafiya ta kama malam zuwa kauyen su iya dan kai masu ziyara, iya tace atafi da saudatu tunda bata taba zuwa ba.

lokacin safna nazuwa makarantar primary tana aji shidda dan haka suka barta gun goggo, bayan wani dan lokaci da tafiyan su labari ya same su, motar da suka shiga ta kone kurmus babu wanda yayi rai, haka su kai ta kuka a yanzun haka shekaran su daya da rasuwa inda goggo tahana safna makaranta sai tallan rake.

Abduljalal
wani matshin yaro ne me ji da kanshi daka ganshi kaga dan gata bazai wuce shekara ashirin da bakwai ba, dogo ne sosai yanayin tsawan shi sai ka zaci ya wuce shekarun shi haka fari ne tas, bashi da yawan fara,a.

Idan kaga jalal na dariya to da ummin sa ne , ko kuma cikin abokan sa, zuwa yayi ya samu ummin sa zaune a falo, yaje ya fada jikin ta yana fadin ummi yinwa nake ji.

ummi tace jalal karfa ka karya ni, wai kai baka san ka girma bane.
haba ummi wanni girma nayi ne, kodan kinga kin samu wata.
tace ba haka bane jalal ya kamata ka fahimci cewa ka girma yanxun fan ba da bane, ga abinci nan kaci , karani gida hajiya sahura.
cokali daya ya kai bakin sa yace ummi na gaji zo ki bani abaki.
gargiza kai ummi tayi ta matso ta fara bashi abaki sai da ya koshi yace ummi bar shi haka na koshi.
sai da ummi ta shiga ta gama gyara wa sannan ta fito, ta samu jalal na zaune a falo kanan kaya ne a jikin shi yayi kyau sosai, idan kaga jalal da ummin sa sai ka rantse yayar sa ce, jalal ne ke jan motan ba, suna tafiya suna hira .
sunyi nisa sosai sun shiga unguwan su hajiya saratu abduljalal ya hango wata yarinya tana tafe tana kuka ga kuma rake akan ta, yace ummi ji wata yarinya yar karama an daura mata talla, yanzu dan Allah ummi wa zai sha wannan raken kofa kan kare shi ba,ayi ba.
ummi tace kai kake ganin haka jalal kazamai yan uwan ta zasu sha.
jalal na kawowa kusa da yarinyar ya tsaya ya kira ta da gudu ta karaso, yace me yasa meki kike kuka?
tace idan na koma gida raken nan be kare ba duka, duka za,ayi min, jalal ya tausaya mata ya kalli jikin ta yaga shedan bulala, yace ummi zan saya raken nan.

da sauri ummi tace amman dai ba a mota ta zaka zuba wannan kazamin raken ba.
yace sai ta bawa almajirai , ya sunan ki ya tam baye tace safna sai da ya maimaita sunan sannan yace raken na nawa ne?
tace nera dari, dari biyu ya ciro ya mika mata, tamiko hannu zata karba , ummi ta daka mata tsawa taja baya da sauri, jalal yace ummi me tayi ?
yaro ban yadda ku hada hannun da yarinyar nan ba ka aje mata akasa sai ta dauka
[1:22PM, 11/23/2016] Fadeela lamido: 💘💍💍MIJIN MARAINIYA💍💍💘


story
&
written
Fadeela Lamido
Mmn Yazeed📝


4-6

Jalal yace haba ummi ai ba taba ta zanyi ba, bata kawai zan yi.
ummi tace ashe tsaftar ka ta banza ce , idai ka bawa yarinyar nan da hannun ka kuwa.
juyawa yayi ya ajewa safna kudin akasa, da saurin ta ta tsuguna ta dauka tana ma jalal godiya, ummi ko hararar ta kawai take.

bayan sun dawo gida ummi ta lura jalal fushi yake da ita, dan haka ta bishj har dakin sa, tace jalal me ya same ka, kake ta fushi?
abduljalal be iya boye wa ummi komai dan haka yace ummi yarinyar nan ce take bani tausayi, ummi da,a kwai yadda zanyi dana tai make ta.
ummi hada rai tayi tace yaro halin ka yana bani mamaki in banda abinka ina ruwan ka da yayan talakawa da har zaka damu kan ka, akan wata banza yarinya kazama, da kikiya.
ummi bazaki gane ba nasan da dady ne zai fahimce ni, ummi raken nera dari ne fa akanta, ummi kuma gashi yarinyar kyakyawa da ita.
zoro ido ummi tayi tace yaro kai ne kuwa, kaga yarinya mumuna kace kyakyawa ko dai gamu kayi ne, to naji kyakyawa ce me kake nufi yan zon.

ummi ni ba abinda nake nufi kawai dai inason ki tai maka mata ne.
kaga jalal karna kuma jin manar yarinyar nan abakin ka, ta mike da sauri tabar wajan.

itako safna zuwa tayi gurin wasu almajirai tana raba musu, iya na daga gefe tana kallon safna, saida ta gama ta juya zata tafi iya ta kwala mata kira , ai tana ganin iya ta roga da gudu ta kamkame ta, cikin rudu iya ta daga kan safna tace a ina kika samu rake kike rabawa Jama,a? Safna ta kwashe labari kaf ta fadawa iya, salati iya ta shiga yi, tana fadin ina can zaune za,a lalata min jika, wanne dan iskan ne, yabaki kudi?
iya nima ban san shi ba kawai gannin su nayi amota.
be miki komai ba dai ko?
ba abinda yayi min, iya tasa keyar safna tayi tace muje na samu goggon taki, in kaskiya ne ta daurawa salma mana.


suna shiga iya ta fara fada taita fada tundaga ranar rokon safna yadawo hannun iya, safna dadi takeji sosai agurin iya babu ta kura, iya duk ta. hada dan kudin da take da shi ta mai da safna makaran ta, haka iya tai ta wahala da safna ana haka safna ta gama primary schools, gashi iya nason safna ta ci gaba da karatu kuma bata da kudi Dan haka ta fara toya kosai a kofar gida, iya bata barin safna tazo gurin tuyan kosan ta sai dai aikace aikacen cikin gida duk da cewa iya ba wani karfi gareta ba, amman safna ta murje tayi kyau kamar ba ita ba.

a yanzun safna tana J S2 dan haka iya ta fara tunanin aurar da safna dan duk da cewa safna bata wuce sha bakwai ba, itako safna babban burin ta shine ta tayi karatu me zurfi.

ana cikin haka rashin lafyya ya kama iya dan kosan da take yi ya gagara, safna ta rasa ya zatayi , tana kuka ta nufi gidan goggo, ta gaya mata iya babu lafiya.
fada ta fara tana fadin aiga irin ta nan, kina nan muna neman kudi tazo ta dau ke ki, sai yanzun da ciwo yakama zaki taho to bamu da kudi, wacce ki bani waje karna kara ganin ki gidan nan, haka safna ta juya tana tafe tana kuka.

haka safna ta dawo ta samu iya kwance cikin amai, ta shiga gyara wajan bayan ta gama ta fara tunani yadda zata samo ma iya abincin da zata ci, tashi tayi ta fita ta gama bulayin ta bata somo komai ba ba yadda zatayi dole ta koma wurin goggo sai da ta gama zagin ta sannan ta bata ragowar tuwan jiya da sauri ta nufi gida tana ta sauri , tun kafin ta isa kofar gidan ta hango muta ne tana shiga gidan kara kamkame tuwan ta tayi ta sheka da gudu tana shiga taga an lulube ta da zani, safna fadawa tayi jikin ta tana kuka.

Wata makociyar su iya ta taho ta dafa safna tace kiyi hakuri safna ki daina mata kuka Allah ya karbi abinsa kuma ya fimu santa dan haka sai muraka ta da.ardu,a haka safana taita kuka har aka kai iya makwanci ta safna bata bar kuka ba.

bayan anyi bakwai da yamma goggo ta hada kayan ta ko salama batawa safna ba ta wuce gida, gidan iya kuwa safna ce ka dai aciki sai ta tsince kanta cikin matsanan cin tashin hankali, haka safna ta kwana ita kadai acikin gidan, safna na tashi hankalin ta kara tashi yayi musamman da ta leka dakin iya taga wayam dan haka ta tsoguna abakin kofar iya ta saki Kara.

makociyar iya baba dije taji kukan safna aguje ta zagawo tace Ina goggonki .
safna tace ta tafi tunjiya
au yanzu nan nufinta baza ta rike kiba, lalai abin nata babba ne, tashi ki hada kayanki na rakaki .

cikin tashin hankali safna ke hada kayan ta tana ganin ita meye amfanin ta tuda ba iyayen ta iyar ma da take takama da ita ta tafi ta bar ta itama da mutuwar kawai tayi.

suna shiga gidan goggo suka same ta tana tankadan garin tuwo, tana ganin safna ta hada rai, bayan sun gaisa tace yazaki tafi kibar yarinya ita daya acin gida.
cin sauri goggo ta fara rantse rantsan ita sam bazata rike safna, baba dije ta fahimci da gaske ta keyi tace to naji to me zai hana ki kaita gun dangin iya.
cinkin sauri goggo tace ina naga kudin motan da zan kai ta.
kwance haban zanin ta tayi takwaso gudin wajan duk ta mikawa goggo ta sannu ta karba harda fadin yauyau zan kai ta.

goggo bata tashi kai safna ba sai gaf da mangariba tace dauko kayanki mutafi , safna ta dauki kullin kayanta suka kama hanya, motar cikin gari suka hau , safna tace azuciyar ta dama motar garin su iya acikin gari ake hawa ,take farin ciki ya rufeta ko banza yau zataga gidaje masu dan banan kyau .
suna isa aka sauke su garin kamar rana saboda fitilun da suke haka ko,ina gidaje kuwa fadan kyansu bata lokaci.

suna ta tafiya taki karewa ita dai safna bin goggo kawai take suna zuwa gurin wata katuwar bishiya, goggo tace safna zoki zauna anan naje na dawo , haka banzayen kakannin ki sukama uwarki har ta mutu bata kara saka su a idon taba.
[2:05PM, 11/24/2016] Fadeela lamido: 💘💍💍MIJIN MARAINIYA💍💍💘


Story
&
Written
Fadeela Lamido
Mmn Yazeed

7-9

Itako safna bata fahimci me goggo ke nufe ba dan bata da wannan labarin , haka tai ta zaman jiran goggo har ta gaji tun tana ganin wucewan mutane daidai har ta daina gani dan haka tsoro ya shige ta, mikiwa tayi tabi hanyar da goggo tabi , tana tafiya tana dubawa ko Allah zai sa su hadu da goggo.

wata mota ce ta shigo layin tun daga nesa motar ke hasko ta, dan haka ta tsora ta , motar na zuwa kusa da ita ta tsaya, wani dake cikin motar yace yace ke ina zaki da daddaren nan, kisan ko karfe nawa kuwa?
cikin kuka me ban tau sayi ta girgiza kai wanda ke mazauni direba yace kabir ina ruwan ka da ita ne kasani ko aljana ce yanzun 12:15 pm fah ,yace yarinyar ar zikice za aganta a waje awannan lokaci, kabir yace kuma fah haka ne aboki na, motar su kaja suka mike layin.

Safna ko babu abin da take ban da kuka, gaba tayi kadan ta samu wani dan dutse ta zauna sautin kukan ta kawai kake ji awajan wasu samari ne suka zo wucewa su uku irin yan shaye shayen nanne sun sha sun bugu daya daga cikin su yace kai kunga wata baby danya, da sauri suka isa wajen ta suka fara ja mata dan karamin hijjabin dake jikin ta safna ko kuka take tana kokarin guduwa amman Ina sun riga sun rike ta dukkan su ukun har sun yaga mata riga dama bawani kwari ke gare suba suna kokawan kwance mata zani .

wan,nan motar ta dazun ce ta sake dawo ,mutun daya ne acikin ta sabani dazun da suke su biyu jin uhun yariyar yasa shi tsayawa ya haska su da fitalan motar yaga abinda ke faruwa da sauri ya fito yafara takawa zuwa wajen yana musu tsawa cikin fada ya daga murya sosai .

daya daga cikin su yace kai kuzo mu gudu yaya abduljalal ne da gudu suka kwasa abduljalal ya matso kusa da ita ya tsoguna ya dauko hajjabin ta ya mika mata ta karba ta saka kuka kawai take abduljalal yace yanzun ina zaki?

tace goggo nace tabar agun wata bishiya tace na jirata kuma naga ta dade bata dawo ba, sheni na biyo hanya ko zan ganta.
cikin mama jalal yace kina nufin mahaifiyar ki kece abarki a titi.

a,a kishiyar mama tace.
yace to ke ina mamar ki?
cikin kuka tace suyi hatsari har baba na sun rasu.
Jalal ya tausaya mata sai dai har yanzun be gama yar da, da yarinyar ba yana ganin kamar dai ta fito yawo ne, ya juya yace Ina yan uwan ku suke,
tace nibasan kowa daga cikin dangin muba kakata kawai na sani itama ta rasu jiya akayi bakwai, shine akace ma goggona takaini gun dangin kakata, shine ta barni tace najira ta tadawo.

hankalin jalal ya tashi ya rasa yan zun ya zai yi da yariyar nan gashi dare na dadayi , zuwa yayi yabude motar sa ya shiga da gudu safna ta biyo shi tana fadin dan Allah karkabar ni anan.
ai bazan barki a nan ba ya bude dayan gefen yace shiga mutafi , bayan tashiga ta zauna jalal yace ya sunan ki?
tace sunana safna.

Jalal ya sake maimaita sunan safna da sauri yafara neman fitilan motar haske ya baiyana yace safna bake bace shekarun baya na saya rake wajen ki, dama ke ma rainiyace.
cikin kuka tace eh.
Yace to kibar kuka safna insha Allahu zakiji dadin rayuwan ki , jan mutan yayi ya fara tafiya yana tunani yadda zasu kwashe da ummin sa.

lokacin da ya isa gida me gadi yabude mai ya shiga yarasa yadda zaiyi da safna dan yasan yanzun ummi batayi bacci ba saitaga dawowan shi , kilama yanzun tana kallon shi, dan haka dibara tafado mai yace safna inazuwa bari naje nadawo.
cikin sauri safna ta rokoshi tace dan Allah karka gudu ka barni kaima.

cikin kwatar da murya yace bazan guduba safna yanzun zan dawo ai nan gidan mune da guduwa zanyi ai bazan shigo dake cikin gidan muba, ban so ne ummi na ta ganki daddaren nan saboda kartayi wani tunani daban kuma nasan tananan tana jiran shigowa ta, sabo da haka kijirani yanzun nan zan dawo.
Gyada mishi kai kawai tayi amman bata son ya bar ta anan.

yana shiga ya samu ummi sai zagaye falon take da sauri shi yaje ya rungume ta, hannu ta tasa ta tukude shi.
abinda
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment