Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation

⚱⚱⚱⚱
*TSANTSAR BUTULCI*
⚱⚱⚱⚱


*NA*
*BINTA UMAR ABBALE*
*®BINTUBATULA👄*


```Marubuciyar```

```NANA KHADIJA```
```YARO DA KUDI```
```GIMBIYA BALARABA```
```LOODING....```

_*TSANTSAR BUTULCI*_



*NA FARA DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN K'AI*



_*Arashi*_

*WANNAN LITTAFIN K'AGAGGE NE DAGA NI MARUBUCIYAR BANYI DOMIN WANI KO WATA BA WANDA YAGA YAYI DAI-DAI DA RAYUWARSA TO A RASHIN SANI NE*



*BAN YARDA WANI KO WATA BA YAYI AMFANI DA WANI B'ANGARE NA RUBUTU NA BA,BA TARE DA IZINA NA BA, AYI HATTARA*




*WANNAN LITTAFIN NA KUD'I NE, NAIRA D'ARI BIYU IN MUTUM NA BUK'ATA SAI YA BI WANNAN NUMBAR KAMAR HAKA*
08089965176
07084653262



*UP*
*UP*
*UP*
*KUNA RAINA, BINTA UMAR FAN'S HAK'IK'A BANI DA ABUNDA ZANCE DA KU SAI FATAN ALKAIRI*

*GAISUWAR KU DABAN TAKE, DOMIN BAKWA GAJIYA DA YI MIN COMMENT*

*UMMAHANI "YAR MUTAN BAUCI*

*NANA AISHATU " YAR MUTAN KATSINAWA*

*PREETY "YAR MUTAN BARNO*

*ZAINAB " YAR MUTAN KATSINAWA*

*MAMAN SUDAIS SAKWATTO*

*HAJIYA INDO AMADU*

*FAUZIYA MA'AWIYYA*

*RAHAMA ALIYU*

*MAHILLA UMAR*

HAK'IKA BAZAN TAB'A MANCE KARAMCIN KU GAMI DA FATAN ALKAIRIN KU A GARE NI, NAGODE SOSAI DA ADDU'AR KU.

KUYI HAKURI WANDA BAN FAD'A BA KUMA KUNA RAINA SOSAI ANA MUGUN TARE🤝🏻



_ZAMANI WRITERS ASSOCIATION_
_________________________
*KUN CANCANCI YABO DA GODIYA A GARE NI*

*1 HUSAINI ATK 80k*

*2 ZAINAB ABDULLAHI,SHAXXI*

*3 NASMATU "YAR MUTAN ARKILLAH*


HAK'IKA BANI DA BAKIN GODIYA A GARE KU SAI DAI IN CE ALLAH YA K'ARA MUKU LAFIYA DA NISAN KWANA, MUNA TARE IYA WUYA🤝🏻




_ALHAMDULILLAHI INAI WA D'AUKACIN AL'UMAR MUSULMI MURNAR BABBAR SALLAH UBANGIJI ALLAH YA MAIMAITA MANA YASA MUGA NA SHEKARU MASU YAWA, ALLAH KA SHAFE MANA ZUNUBAN MU, AMEEN_



_*WANNAN PEGE D'IN NAKI NE*_


*HAUWA S ZARI'A*
(Maman Usuwan)

*ALLAH YA K'ARA HIKIMA DA AZANCI*





*BISIMILLAHIR-RAHAMANIR RAHIM*






*🅿1&2*







Wani babban gida ne me d'auke da d'akuna masu ciki da rumfa-rumfa za su kai bakwai, kana ganin gidan kasan gidan yawa ne kuma da ka gani me gidan me tsohuwar dukiya ne, a zamanin sa, bene uku ne a gidan d'aya a soro biyu a babban tsakar gidan, tsakar gida babban gaske ne ga wasu manyan bishiyu na dirimi a gidan har guda biyu, band'aki na futsari uku ne haka kuma na bayan gida uku ne,bayan na tsakar gidan a kwai wasu a bene guda bibbiyu. Kana ganin benen kasan na samari ne saboda yadda suka barbaza takalmansu da gajerun wandunansu, fulas din abuncin su, da kwalaben lemo gami da robobin ruwa da ledar pure watar duk ga sunan a watse a barandar benan me d'auke da d'akuna biyar.

Kicin d'in na kalla naga wata k'atuwar tukunya a kan murhu ana ta da huwar abunci "yan matan gidan ne suke ta kai kawo tsakanin kcin d'in da d'akunansu, ko wacce da aikin da take banda mutum d'aya, Rabi'a kenan,tana kwance can k'arshen rumfar su tana karatun wani k'aton novel na turanci sai mutsu-mustu take tana lumshe ido ita kad'ai, k'anwarta ce tazo ta tsaya a kanta tana zumbura baki tace" Ke Rabi'a Mama tace"Kizo ki daka mata citta da kanin fari ki d'ora mata shayi kin San yau littinin tana azimi"

A fusace Rabi'a ta aje novel d'in hannunta tace"Wallahi zanci uwarki Sumayya, kin raina ni ko? Ke me ya hana ki d'ora mata shayin da zakice dole sai ni"

Buga cinya Sumayya tayi,tace"Yo ai bani bace Mama ce ta aiko ni, kuma wallahi bani kika zaga ba kanki kika zaga ehe!
Da sauri Rab'ia ta mik'e zata kai mata duka, tayi waje da gudu tana dariya gami da tsalle-tsalle tana murgud'a mata mazaunanta,
Ta kalmi Rabi'a ta d'auka ta jefe mata tace"Shegiya "yar lukuta kawai"

Da gudu ta k'arasa kusa da Mamansu Hajiya Zulai kenan tana zaune kan dadduma tunda ta idar da sallahr la'asar take zaune tana lazimi, tayi saurin yin gyaran murya ganin yadda Rabi'a tayo kan Sumayya tana k'okarin dukanta da takalmi, rike'hannun Rabi'a tayi tana d'an hararata, Rabi'a ta gane hukuncin Mamansu ko da ido ma tana yi, girgiza kai tayi ta bar gurin tana fad'in za ki shigo hannu ne yarinya Allah sai na zane ki"
Gwalo Sumayya tayi mata tana dariya ta d'ora kanta kan cinyar Maman nasu.

Hajiya Gaji ce ta futo daga d'akinta da murmushi a fuskarta ta kalli Sumayya tace"Ke kam kinji kunya, kullum kina nad'e a cinya kin girma baki san kin girma ba wai ke "yar shagwaba'a"
Bubbuga k'afa Sumayya tayi cikin shagwab'a tace" Ni Mama a k'yaleni inci lokacina nice fa duk "yar k'arama a gidanan, a k'yaleni in suburbud'a sha'anina"

Dariya Hajiya Gaji tayi tace"Dube ta don Allah,da baki kamar gidan tsutsa ya iya fad'ar suburbud'a"

Murmushi Hajiya Zulai tayi da carbi a hanunta k'okarinta taga ta kammala laziminta ta shigarwa Sumayya domin yanzu Hajiya Tabawa ma ta futo d'orawa zatayi kan abunda Hajiya Gaji take wa Sumayya suyi mata taron dangi wanda yake sata kuka.
Zumbura baki Sumayya tayi tana kauda kanta.

Hajiya Gaji ta wuce bakin rariya tana dariya.



*TUSHEN LABARI*

ALHAJI MADO GWADABE
Shararran d'an kasuwa ne, me dukiya taban mamaki wanda yasha gwagwar maya a harkar kasuwanci inda ya tsaya da k'afafunsa a wancan lokacin da turawan ingila yake harkar atampah da yadika irin na maza da d'ankwali na mata, mutum ne shi me nasibi shiyasa ko wane gari kayansa suke zagawa idan yaje ya dawo zai rarraba kaya cikin sauk'i da rahusa kafin kace kwabo kaya sun k'are, kamfaninsa biyu a ingila wanda ake atampah d'aya a chana ana d'ankwali, sosai mutane suke ci a karkashinsa, mutum ne shi me k'arfin zuri'a, mutane da dama na cewa gado yayi saboda mahaifinsa Gwadabe ya haihu sosai da sosai wasu sun mutu wasu sunanan a raye shi Mado ya taso bai san ubansa ba domin ya kasance dan amaryasa ne, wanda ya kasance shine k'arami a cikinsu,yana a
Da she kara d'aya a duniya mahaifin nasu ya rasu.



_Tab'a ka lashe_
*ZAN CIGABA INSHA ALLAH SABODA MASU BUK'ATA KAFIN IN DA TURAWA GROUPS SAI WANDA YA BIYA*
*200*
[14/08, 13:13] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation

⚱⚱⚱⚱
_*TSANTSAR BUTULCI*_
⚱⚱⚱⚱


_*NA*_
_BINTA UMAR ABBALE_
*®BINTUBATULA👄*


_*MARUBUCIAR*_

```NANA KHADIJA```
```YARO DA KUDI```
```GIMBIYA BALARABA```
```LOODING......```
_*TSANTSAR BUTULCI*_




_*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION🤝🏻*_
____________________
_*We are here to educate,motivate and entertain aur Reades*_
_______________________






_*BISIMILLAHIR-RAHAMANIR-RAHIM*_



*🅿3&4*



A k'alla Gwadabe ya haifi "yaya arb'in da bakwai tare da mataye iri-iri kasancewar shi mutum ne me aure-aure shiyasa ya tara " yaya da yawa mace d'aya sai ka same ta da "yaya goma, ko goma sha biyu cikin mantan nasa guda hud'u harda me " yaya goma sha biyar, Mado ne kawai bashi da d'an uwa saboda da kan babarsa Gwadabe bai k'ara auran wata mata ba, gashi lokacin ya tsufa sosai,kuma mahaifiyarsa ta dad'e bata haihu ba.


To mutane suna cewa Mado ai gado yayi saboda mahaifinsa yayi aure-aure shine shima yake yi saboda yaga yana da kud'i, lokacin da zaiyi auran fari ma da mata biyu ya fara, kuma suna haihuwar fari ya k'aro wani auran inda ya auri mace d'aya itama da tsohon ciki ya cikashe ta hud'un babu abunda ya dame shi.
Yanzu haka yana da "yaya ashirn da bakwai mata da maza, wasu iyayensu ma basa gidan.

Yana da " yaya maza goma sha hud'u inda mata suka kasance su goma sha uku, matayensa uku ne suka rage kasancewar amaryarsa ta futa ta dalilin babban d'ansa me suna Habib, wanda yanzu haka yana can ingila kan harkokin mahaifin nasu shi da k'aninsa Auwal me bi masa kenan,

Fafur!Habib ya hana mahaifinsa k'ara wani auran tunda amaryarsa ta futa yace"Har indai yarinya zai je ya d'auko to gwara kawai ya hak'ura da auran domin yanaji yana gani ba zai yarda yaje ya d'auko musu yarinya k'arama ba tazo tana zagin iyayensu, waccen ma kafin ta futa sai da ya sumar da ita dalili ta zagi Hajiya Tabawa matar mahaifin nasu ta uku, sosai yaran gidan maza da mata suka taso da tarbiya da nutsuwa uwa uba ilimin addini da na boko dai-dai gwargwado kowa najin magana, banda Sumayya ta gagari kowa a gidan maza da mata, mussaman yanzu da ta samu sakewa Yaya Habibu bayanan sai tak'i zuwa makaranta haka duk za'a d'ad'e a gidan babba da yaro duk su tafi banda ita, daga taga lokacin makaranta yayi sai ta shige k'uryan d'akin su tayi kwanciyarta kan gadon k'arfen Mama ta shige loko sosai ta saki labule, haka za'a k'araci nemanta a hak'ura sai taji gidan yayi tsaitt! sai ta futo tana sharb'a gumi tana sosa soshe irin na rashin gaskiya.

Nan Hjy Gaji zata kamata ta murd'e mata kunne tai ta fad'a tana cewa"Wallahi ko don wannan abun naki da kikeyi zan tursasa Yayanku ya dawo domin shine maganin ki,haka zaki zauna babu karatu,shashashar yarinya kawai"
Zumb'ura baki take kawai taje ta d'ane karfen baranda tana sufa tana kyalkyala dariya sai kace wata shashasha, haka take yi ni tana wasa a gidan, babu ruwanta,da zuwa makaranta sai taga dama, har inda kaga tana himmar zuwa makaranta to tabbata Habibu yazo gida,nan ne zaka ga ta nutsu tana abu simi-simi kamar me gaskiya ko tsokanarta akayi a gidan bata ramawa Dan kar ya dake ta, saboda in yazo gurin baya tsayawa ya bi ba'asi zane ta yake ciki da bai yace"Ai itace bata da gaskiya,sai dai tayi kukanta ta gaji, Mama kuwa haushi duk ya isheta duk ranar da Habibu ya dake ta yini take bata kulashi ba,sai dai yazo ya karaci maganarsa ya tafi.
Haka "yan matan zasu dawo gida kowa na bitar karatun da akai masa a makaranta amma banda Sumayya, magariba nayi zasu shirya su tafi makarantar magariba, nan ma sai ta tsiri baccin k'arya, Rabi'a tai ta tashinta tana ji tayi shiru mamansu tace tak'yale ta kawai tayi tafiyarta, haka zasu tafi Rab'ia na jin haushin yadda Sumayya ta maida kanta koma baya cikin " yan uwa, lafin su dawo kuwa ta fakaici idon matan gidan mussaman insun shiga sallah,sai taje ta bud'e miya ta tsamo nama ta tsuguna kchin din tana ci, sai taci me isarta sannan zata gudu gurin Babansu Alh Mado kenan d'akinsa na can benen soro dake d'akuna uku ne sai ya d'au d'aya Habibu ya d'auki d'aya shima Auwalu ya d'auki d'aya, to can gurinsa take guduwa tayi kwanciyarta har sai garin Allah ya waye sannan take sakkowa tana zumb'ure-zumb'uran baki.
To duk me girki a ranar in taga an tab'a tukunya tasan Sumayya ce,haka zata k'araci fad'anta ta hak'ura saboda in tace zata bita saman tayi mata fad'a zasu iya b'atawa da me gidan domin ba'a tab'a masa shalelensa,ko kayan kasuwa ya siyo duk yawansu ita yake bawa yace ta raba musu, in ta sakko k'asa sai tasha na sha taci na ci sannan zata raba musu ragowar Rabi'a tai ta dukanta, ita kuma tana b'are baki tana kuka, babansu najin kukanta,zai lek'o ta taga yayi ta fad'a haka zasu hak'ura su k'yale ta.

Babbar yarsu Zainab tana aure a Kaduna tana da yara bakwai, Ihisan ce babbar "yarta kuma duk itace mace sauran duk maza ne.Ihisan Aminiyar Sumayya ce sosai in tazo Hutu. haka zasuyi ta tsula siyarsu

Sai Khadija ita kuma tana Aure a jibi'a can katsina kenan yaranta uku duk maza

Sai Aisha ita kuma shekararta biyar da aure Allah bai bata haihuwa ba, tana can abuja can take aure






*_Wannan book d'in na kud'i ne naira d'ari biyu kacal in mutum na buk'atar cigabansa ga numbar ta nan_*
08089965176
07084653262
[15/08, 15:16] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation

⚱⚱⚱⚱
_*TSANTSAR BUTULCI*_
⚱⚱⚱⚱


_*NA*_
_BINTA UMAR ABBALE_
*®BINTUBATULA👄*


_*MARUBUCIAR*_

```NANA KHADIJA```
```YARO DA KUDI```
```GIMBIYA BALARABA```
```LOODING......```
_*TSANTSAR BUTULCI*_




_*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION🤝🏻*_
____________________
_*We are here to educate,motivate and entertain aur Reades*_
_______________________


_*Wannan littafin na kud'i ne, naira d'ari biyu in kana buk'atar sa ga numbar nan*_

08089965176
07084653262



_*BISIMILLAHIR-RAHAMANIR-RAHIM*_



*🅿5&6*



Rabi'a da Suwaiba ne cikin k'uryan d'akin Hajiya Gaji, suna hira k'asa-k'asa Sumayya ta zo ta lab'e bayan labule ta kasa kunne tana jin abunda suke fad'a

Rabi'a tace"Wallahi Suwaiba aure nake so, na gaji da zaman gidan nan gwara ayi min aure kawai in je in mori k'uruciyata,bakiji yadda nake ji ba in ina karanta novels duk sai in dunga jin tsigar jikina na tashi, humm kin san shekaran jiya a gidan k'awata Nusaiba na wuni wallahi baki ga yarda suke soyyaya da mijinta ba,a gabana fa naga yana tsotsar bakinta, wallahi ji nayi ina ma nice"
Hannu Suwaiba tabata suka tafa suna dariya tace"Ba sai ki fad'awa babanmu aure kike so,nasan halin baba aure zai miki da Ansar d'in ki"

"Humm nasan da haka ai,kin san babbar damuwa ta wacce tasa na hana Ansar zuwa gidanan shine, Wallahi ina bal'in jin tsoran masifar yayanmu, kin sam shi babu abunda yake so muyi a yanzu idan ba karatu ba,ni kuma wallahi aure nake so"
Rabi'a ta k'are maganar tana sauke ajiyar zuciya kana kallon yanayin ta kasan da gaske take.

Suwaiba tace"Bake kad'ai ba,Allah nima da zan samu tsayyayen miji aurena zanyi babu ruwana da wani karatu," Tafawa sukayi a karo na biyu suna k'yalkyala dariya.
Motsi sukaji a falo gabansu ya fad'i a hankali Rab'ia tace"Allah yasa babu wanda yaji Suwaiba ce ta d'aga labule a hankali tana lek'owa,kawai sai ta hango k'afar Sumayya bayan labule, tana k'okarin guduwa Suwaiba ta rik'eta tam!tana janta tana turjewa, fad'i take"Wallahi naji abunda kuke fad'a sai na fad'awa yayanmu,ko in fad'awa Babanmu, tabd'ijam,wai aur....da sauri Rabi'a ta rufe mata baki suka jata da k'arfi suka kaita d'aki.
Turje-turje take tana k'okarin kwantar kanta ta gudu sun rik'eta sosai, Rabi'a tace"Haba k'anwata ta kaina, bani ce fa nace ina son aure ba labarin k'awata Nusaiba nake bawa Suwaiba, don Allah kar ki fad'awa kowa kinji"
Kamar zatayi kuka ta k'arashe maganar.

"Oho miki,ni dai sai na fad'a ehe!ai naji sanda kike cewa wai mijin Nusaiba yana tsotsar bakinta, kema kina so,sai na fad'awa yayanmu in ya dawo wai kina so mijin ki ya tsotsi bakin ki"

Cikin rawar murya Rabi'a tace"Ayya Sweet Sistar na, nace miki fa bani nace, labari ne kawai a novel irin Wanda nake karantawa don Allah kar ki fad'a kinji, na miki alk'awarin zan baki wannan mayafin nawa da kika CE kina so"

"Oh"Oh to me yasa kike karanta novel d'in ai Mama ta hanaki,ni dai babu ruwana sai na fad'a"
Sumayya tafad'a cike da kuruciya

Suwaiba tace"Wai ke dan kinga ana lallab'a ki shine kikewa mutane botsare-botsare, wallahi dukan ki zanyi,yanzu kije ki fad'a d'in"

Zumb'ura baki tayi tace"Tabd'ijam ni babu me dukana in kyaleshi sai ruwan sama"

Hannu Suwaiba ta d'aga zata mare ta a fusace, Rabi'a tayi saurin rik'ewa tana girgiza mata kai.

Ita kuwa Sumayya b'are baki tayi zatayi kuka,Sumayya tace"Ko in baki kud'i,nawa kike so"
Sanin halin jarabban san kud'i irin na Sumayya yasa Rab'ia ta yanke wannan shawarar.

Aiko da sauri tace"Na yarda ki bani Dari da hamsin, bazan fad'awa kowa ba"
Da sauri Rab'ia ta d'auko jakar makarantar bokonta ta ciro naira hamsin a tsakiyar littafinta na engilis tace"Gashi nan itace dani,ranar Monday zan cika miki d'ari, shikkenan ko"?

D'aga kai tayi ta karb'i hamsin d'in ta b'oye k'arkashin siket d'inta, tana kallon su tace" Yaya Suwaiba kece shaida ko, Allah idan bata cika min kud'ina ba sai na fad'a"

Suwaiba tace"Eh nice shaida da kaina zan karb'a in baki in za muje makaranta"

Zumb'ura baki tayi ta juya ta futa tana muskura mazaunai.

Da kallo suka har ta futa, Rab'ia tace"Wannan yarinyar munafuka ce,wallahi ashe tana kallon sanda muka shigo d'akin shine ta biyo mu ta lab'e tana jin abunda muke cewa"

Dariya kawai Suwaiba take,harda kwanciya k'asa tace"Ai tuntini na dawo daga rakiyar yarinyar nan wallahi, Sumayya,humm duk inda kika d'auke ta ta wuce nan"

Itama Rabi'a dariyar take tace"Shegiya "Yar lukuta kawai tana fama du d'uwawu kamar an d'ora turmi"

Kwanciya sukai d'akin suna ta shek'a dariya, Hajiya Gaji ta shigo d'akin ta gansu suna dariya tace"Ku kuma fa kuna dariya kamar wasu shashashai.



_*Tab'a ka lashe*_
[16/08, 17:15] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation

⚱⚱⚱⚱
_*TSANTSAR BUTULCI*_
⚱⚱⚱⚱


_*NA*_
_BINTA UMAR ABBALE_
*®BINTUBATULA👄*


_*MARUBUCIAR*_

```NANA KHADIJA```
```YARO DA KUDI```
```GIMBIYA BALARABA```
```LOODING......```
_*TSANTSAR BUTULCI*_




_*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION🤝🏻*_
____________________
_*We are here to educate,motivate and entertain aur Reades*_
_______________________






_*BISIMILLAHIR-RAHAMANIR-RAHIM*_



*🅿7*




Had'a baki sukayi gurin cewa "Babu komai Hajiya"Girgiza kai tayi tana k'okarin sakko da samira dake kan kwabarta tace" Yanzu naga Sumayya ta futa Allah yasa ba tsokanarta kukayi ba,kun San halinta fad'anta baya rabuwa, haka kawai baza Ku jawo mana fad'an Alhaji ba, yana gida bai futa ba mutuk'ar yaji kukanta, to kuma sai kunyi kuka"

"Laa Wallahi Hajiya ba ita muke tsokana ba, labarin wata " yar ajinmu nake bawa Suwaiba"
Rabi'a ce tayi Wannan maganar cikin wayance wa.

Hajiya Gaji tace"A to!ni dai na fad'a muku"

Sumayya ce ta shigo d'akin da gudu,tana dariya hannuta rik'e da biscuit d'an hamsin tace"Hajiyarmu kizo ga Yaya Khamis yazo yanzu"

Cikin fara'a tace"A'a lallai muna da babban b'ako a gidanan lale maraba, maza je ki ce ya shigo"

Har ta juya zata futa,tayi saurin dakatar da ita,ta hanyar kiran sunan ta"

Sumayya taja ta tsaya tana k'okarin bud'e ledar biscuit d'inta

Had'e fuska Hajiya Gaji tayi tace"A'ina kika samu kud'i kika siyi biscuit ko rok'onsa kikayi daga zuwansa.

Girgiza kai tayi,tana zare ido tace"Sama na hau gurin babanmu na karb'o kud'i" Hajiya Gaji tace"Mak'aryaciya kawai ba yanzu na sakko daga saman ba,bacci yake ko tashinsa kikayi"?
D'aga kai tayi tana zumbura baki.

"Wuce ki bani guri kuma ina fatan kin gaida Yaya Khamis d'in"
D'aga kai tayi ta futa tana zumb'ura baki.

Khamis na zaune kan dadduma dake falon, kansa a sunkuye, ya d'ago kansa yana kallon Summya da ta futo daga d'akin, ganin tana zumb'ura baki, yasa ya saki dariya, yace"To uwar shagwab'a zonan ke dawa kike toro baki gaba,sai kace shantu"
Kuka tasa tana buga kafarta cikin sangarta tace" Ya Khamis bana so, ni bakina baya kama da shantu"

Dariya yake kyalkyalawa yana binta da wani mayen kallo, bubbuga k'afarta da take yasa dukkanin sassan jikinta motsawa, mussaman mazaunanta,duk da take yarinya "yar shekara sha biyu hakan bai hana bayyanuwar hallitar ta,saboda macace mai girman jiki sosai ga shinan har tafara k'irgar dangi sunyi tsaye Carr!a cikin rigarta, gurin cikar k'afa da shara b'a ba'a magana a cike suke dam!


Wani irin kallo yake mata me tattare da zallar sha'awa sosai yake son lafiyyan jikin yarinyar da alama za'a huta a jikinta"


Hajiya Gaji ce ta futo fuskarta cike da fara'a tace"Lale maraba da Hamusu, sannu da zuwa"

Gyara zama yayi yana me d'auke idonsa daga kan Sumayya,yace"Sannu Hajiyarmu fatan mun same Ku lafiya "

Hajiya tace"Lafiya lau muke Hamusu ya harkokin?ya mutan gida,su Hajiya Laure"


"Wallahi duk sunanan lafiya, ai jiya nima na dawo shine nace bari in shigo mu gaisa kafin mu fad'a kasuwa koma duk harkoki su da baibaye mu"


"Ai kuwa ka Kyauta sosai da kazo muka gaisa Allah yayi maka albarka, Allah ya dafa muku,a dukkanin abunda kuka sa a gaba"


"Ameeen" Ameeen
Ai munyi Waya da Habibu yace" Yana kan hanya insha Allah a satin nan zai dawo"


Hajiya Gaji tace"Ka rabu da shiriritar wannan, ko jiya sai da nasa Abdulsamad yayi masa waya abunda ya fad'a maka da ban da wanda ya fad'a mana"
Dariya Khamis yayi yace"Wannan karon dai da gaske yake, insha Allahu mu tsammace shi a satinan,don haka ma bazan koma Maidugiri ba,sai ya dawo nan zan zauna"

Hajiya Gaji tace"To Allah yasa da gaske yake,ai naga alama shi babu abunda yasa a gaba sai neman kud'i shikenan yawo daga wannan k'asa zuwa wannan k'asa"

Cikin murmushi Khamis yace"Haka abun yake Hajiya fatanmu dai kuna yi mana addu'a su kud'i ai dole a neme su Ku dan su Ooo gatanan a tsaye"
Ya k'arashe maganar yana dariya"

Hajiya ta tayashi dariyar ,tana fad'in "Aikwa dai,wannan sarkin kashe kud'in, bata da aiki sai ciye-ciye" tafad'a tana mik'ewa da niyar futa,tace"Bari in sa a kawo maka abunci"

Suwaiba ta kira tace"Kuna jin yayanku kun kasa futowa Ku gaidashi ko"

Kusan a tare suka futo kai a k'asa suka gai dashi cikin girmamawa,suna mutuk'ar ganin girmansa,kamar yadda suke ganin girman Yaya Habibu saboda bashi da babban aboki kuma amini kamarsa"

Hajiya tace"Ko zo muje Ku kawo masa abunci"
Bayanta suka bi,duk su biyun suka bar Sumayya da Khamis d'in a falo.

Tana can gaban tv tana k'okarin kunnawa,yace"Zonan Sumayya, barin abunda takeyi taje ta tsaya kansa, cinyarsa ya nuna mata wai ta zauna.

Duk da yarintar ta tasan hakan ba dai-dai bane saboda haka sai ta mak'e kafad'a alamar tak'i.




Karku manta wannan book d'in na kud'i ne naira 200 ga me buk'ata ga numbar nan
08089965176
07084653262
[17/08, 04:26] 80k: https://m.facebook.com/Zamaniwritesassociation

⚱⚱⚱⚱

DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5

Please Login or Register in order to submit comment