Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

 [23/06/05, 12:30pm] Yusrah Musa
Abubakar📝
🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊🕊


💰'DAN MILLIONAIRE💰
('Dan miloniya)


WHATAPP NO: 📱+2349055273614



YUSRAH MUSA ABUBAKAR
Mrs Al'ameen Ahmad ce.


(*)(SHORT STORY)(*)



📚 LITTATTAFAI NA
👑Yarima Abdul-maleek
🌹Rayuwa biyu
🍇Safreeyyah
🎉Haskena sauban
🎀 Mina-Umer
🌷Karuwar boye
💰'Dan millionaira.

Ga me bukatarsu ya tuntube ni ta wannan number👉 09055273614 littattafai na free book ne ga duk wani masoyi na a duk inda yake afadin duniya I love u with all my body and heart💞.


💫ANNURI WRITER'S ASSOCIATION💫
🏡 home of hospitality and 🕊harmony.


In the of Allah the most benefits and the most merciful we love our nabeey s a w we like him and peace be upon him ameen🙏👏.



Some say hello some say hay but in islamically said assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatihu.


Tofa reader's na kumin afuwa wannan karon son kai zan nuna sosai first page na yan group dina ne Annuri ina alfahari dasu may Allah help them any where they are amin.



Page 01 to 02

Wani irin 'kayataccen ginannen gida ne wanda hatta fetin gidan gwal aka nike akai fetin dashi da safe ne amma ko'ina 'kyal'kyali ne ke fita a jikin bangon gidan da dare kuwa har dauke ido yake .



Tsararran palor ne dankarere daya sha kayan alatu na more rayuwa iri daban daban wanda wani abin ma na'ura ce ke sarrafa aikin sa ba mutum ba.


Zaune suke su uku samari ne guda biyu fitattatu na ajin farko yan gayu tsaf dasu kyawawa farare tar dasu kamar larabawa sai mace a tsakiyar su wacce kallo daya zakai mata kasan itace mahaifiyar wadannan zukakan samarin.



Amma kana ganin fiskokin su kasan akawai matsala domin a samarin wanda yafi hasken ransa a mugun bace yake kallo daya zakai masa ka fahimci haka .


Saidai bacin ran bai hana kyansa bayyana ba da kuma annurin fuska.


Cikin fad'a matar ta kalleshi tana cewa "kasan Allah Al'ameen ka fita idona na rufe idan banda shashanci me zakai da wannan banzar yarinyar wacce ba yaren kaba ba jinsin kaba 'kabila tubabbiya yar wata kasar ba zaka je ka yayo min masifa ba duk yan matar kasar ka da jihar ka saika haura wata uwa London to bari kaji bada yawu na ba ban amince ba kuma ko bayan raina ka aure ta ban yafe maka ba sai ka zaba koni ko ita".



Cikin tsananin firgici da tashin hankali wanda ta kira da Al'ameen ya dago kyawawan idonsa yana kallon mahaifiyar tasa jin furucin da take akan wacce bazai iya hada sonta da kowacce mace ba bayajin zai samu madadinta.


Iya kallon da yake mata ya tabbatar mata da cewa Abni ce numfashin sa bazai iya rayuwa ba tare da ita ba wanda hakan yai matukar firgita ta.



Cikin 'kunar rai ta mike bata sake cewa komai ba jin yawun bakin ta ya kame yasa da sauri tabar gurin zuciyarta na turiri da zafin al'amarin yaron nata wanda ta damu dashi .


Dafa shi dayan yayi cikin tausaya masa da halin daya tsinci kanshi na jarabtar soyayya yace "Al'ameen dan Allah kayi hakuri da halin mami tunda bata son wannan baturiyar ka daina furta koda sunanta ne a gaban ta domin mami idan ta fadi magana bata sauyawa kaifi daya ce nasan baza ta taba bari ka aure ta ba".



A damuwance Al'ameen ya dago yana kallon dan uwan nashi yace" ni da kaina na fada mata cewa babu kyau karya alkawari a addinin musulunci saboda ni tabar nata addinin ta musulunta bata yarda tayi imani ba saida na mata alkawarin zan aure ta sakamakon nima ina sonta yanzu me kake tunanin zata dauke ni idan nace tayi hakuri na fasa auren ta wanne irin hali zata shiga dan Allah ka taimaka min".


Kai Sadiq ya jinjina shikenan 'kani na zan taimake ka insha Allahu tamkar ka auri Abni ne domin bana son rasa ka kuma na fahimci itace bugun zuciyar ka".


Wata karamar yarinya ce tazo da gudu tana kuka ta fada jikin Al'ameen cikin rashin walwala yace" momy na me akai miki"?.


Da yatsa yarinyar ke nuna wajen dinning tana cewa he spoiled my shirt".


Kallon farar rigar ta ta yai ganin duk miya ya bata ta yasa ya kalli wajen dinning din wani yaro ne tsaye rike da spoon a hannunshi karasowa gurin yai yana cewa small dad ban sani ba na shafa mata miya a jikin rigar ta sorry sister".


Kafada ta make wallahi bazan hakura ba saika biya ni riga ta kona rama".


Zare mata ido yaron yai yana cewa baki isa ba tunda na baki hakura kuma bazan wanke rigar ba ".


Kuka ta kara fashewa dashi cikin lallashi dason raba rigimar hayaniyar da suke Al'ameen yace" muje na sai miki wata momy na rabu dashi".


Goge hawayen fuskarta tai tana dariya suka fita daga palon yayin da Sadiq shima ya mike yana cewa Ameer meye abin bata ran kaga kada kayi kuka muje kaima na saya maka".


Tsalle Ameer yai yana rungume Sadiq yace thnk dady " rike hannunsa yai suka fita wanda mami najin kara tashin motoci yasa taja tsaki cikin takaici tana bude window ta daga labule tana kallon su har suka fice daga gidan".


Sauke numfashi tai tana cewa amma wallahi Al'ameen sam bashi da hankali ina yabar ajin nasa wata shegiya take neman mayar min dashi shashasha duk yabi ya susuce akanta ko yar uban waye ita a London nata isa ta rabe muba duk kudin su saita raba su kota halin 'ka'ka.


Fita tai daga nata part din tana shiga wata kofa ta bude bedroom tare da lekawa tace" wato Afeeyah baki da hankali ko sai ulcer ta kama ki zaki gane gata ake miki tsabar iskanci kisa waya agaba ki manta da komai bari dadyn naku ya dawo zansa ya karbe wayar ne".



Cikin shagwaba wata budurwa dake kwance a wani makeken gado ta dago tare da cewa kai mami bafa wani abu nake ba kuma indai breakfast ne nayi tun karfe bakwai".


"Hum haka ne da gaske kinyi"?.


Eh mami nida wafer na karya ba abinci naci ba".


"To yayi miki kyau ki fito haka zama ni daya a palon ya ishe ni".


Shikenan to muje mami yadda kika ce haka za'ai mikewa tai suka fito tare yayin da mami ta danna wani karaurawa dake palon".


Da sauri wasu masu kaya iri daya su biyar suka shigo palon cikin ladabi jikin su na rawa suka durkusa tare da gaishe da ita bata amsa ba sai wani kallo datai musu tana cewa.


"A cikin ku wadanne banzayen ne masu lura da dinning mikewa hajar tai tana cewa mune nida ma'u ".


A tsawace mami tace sannu yayan talakawa wato daula tasa zaku fara shagala da abinda ya kawo ku uban waye ya zubar da miya akan farin carpet din can"?.



Zaro ido hajar tai wallahi hajiya ban sani ba tunda mukai servingg dinku ban sake fitowa ba".


"Saboda gaki isashshiya ko ke nana baki karanta musu ka'idojin gidan nan bane domin ba irin kowanne gida da suka sani bane sai wane da wane".


Nana dake shirin magana mami ta katse ta rufa min baki nan gaba aka sake samun kuskure daga wadannan 'kazaman new comer bazan daga miki kafa ba".


Hakuri nana ta taba domin marar abu baya zuciya sannan ta mike da kanta ta gyara dinning din da komai tana komawa bangaren ma'aikata ranta duk ba dadi ta gaji da wulakancin da mami ke mata".


Koda dare lokacin da daddy ya dawo haka mami ta cika ta kumbura tai fam taki sakin ranta akan lamarin dazu".


Kallonta alhaji Mustapha yai cikin mamaki domin da ba haka take ba yace" uwar gida ran gida ya akai ne naga kina fushi meya faru".


Kamar jira mami take ta ture plate din abincin gabanta tana cewa nida Al'ameen ne mana yana neman dora min hawan jini ya kashe ni lokaci na baiyi ba".


"Tofa meya miki haka auta na akwai hakuri kodai kece da tsokana"?.


"Kaji irin abin ko babu dama a fadi laifinsa a gaban ka saika wanke shi tas ".


"Ba wannan ba fada min meyai miki".


"Ranta a hade tace wai dan Allah kaji shi da wani hauka yaje wata kasar ya hadu da yar arna ta kaishi church sun burkita masa kwakwalwa ya dawo ya susuce".


"Subahanallahi da yaushe wani abu kika ga yana yi wanda ya saba hankali"?.


"Yo meye ma baiyi ba alhaji dazun nan na gama cin kaniyarsa akanta ala dole ita yake son aura duk Nigeria baiga wacce tai masa ba saiya debo mana masifa da bala'i sun zuge mana jini".


"Gaskiya ka sameshi ka masa fada tunda ni na gaza yaki fahimta ta".


"Ok yayi shikenan karki damu uwar gidan Mustapha Aminu zan same shi as you wish kamar yadda kike so".


Murmushi mami tai cikin farin ciki yauwa alhaji yanzu naji magana nina manta sunan shegiyar yarinyar ma sunan kalar amai"😣.


Ki daina rage mata alhakin data deba a cocin tunda kince kirista ce".


Allah wallahi abin ne da haushi duk gayun sa da tsananin kudin ka maimakon ya nemi yar shugaban kasa nasan duk inda yaje neman aure da gudu za'a bashi".


Kai alhaji Mustapha ya jinjina yana mamakin mami daga anyi magana saidai ta ambaci kudi💰😂.

BY MRS AL'AMEEN AHMAD CE.


💰'DAN MILLIONAIRE💰


#Comment
#✅ote
#Fallow.


💫ANNURI WRITER'S ASSOCIATION💫
Home of hospitality and harmony.

Yusrahms Abubakar

Mrs Al'ameen Ahmad ce.

Page 03 to 04.
Sati biyu da faruwar haka Al'ameen na zaune shi kadai a palor yaji wayarsa na kara wakar da Abni ta dora masa ce tun a London .


Yana kallon screen din wayar saida gabansa yai mummunar faduwa ganin sunan Abni din baro-baro.


Bai daga ba saida ta katse ya kira ta amma abin mamaki data daga saiya kasa ce mata komai kawai yai shiru yana sauraronta".


Jin yayi shiru yasa tace dear lafiya kwana da yawa wayar ka a rufe kasan irin tashin hankalin dana shiga kuwa please kada ka sake".


Sauke ajiyar zuciya yai muryarsa kamar yana mura yace fatan kina lafiya ina mom da saira ko kina ma'aikata ne kamar naji hayaniya".


Dariya tai domin tana da yawan fara'a tace a'a kawai dai zan baka mamaki ne".


"Kamar ya wanne iri"?.


"Idan nace maka ina kasarka Nigeria zaka yarda ".


Zuciyarsa na harbawa sosai kamar zata fito waje yace zan yarda amma da gaske kike kina Nigeria"?.


Allah dear ina nan Abujan ku ba nan kace state naku ba na rako daddy na ne wani aiki baifi sati zamuyi ba".


"Ok you are welcome".


"Thank dear amma yanzu ina ne zan same ka domin na sanar da dad dina zamu zo gidan ku"?.


A firgice da karfin gaske har saida ya tsora ta yace "what you mean........

"Yes ta katseshi batare daya karasa ba tace ka sanar dani addresss din gidan ku".


Babu yadda ya iya dole ya tura mata kamar yadda ta bukata tare da dafe kansa cikin damuwar mezai iya faruwa".


Fitowar mami kenan ganin a yadda yake yasa ta fasa wucewa ta tsaya tana cewa "lafiya meye ya faru na ganka a haka kodai wannan banzar yarinyar kad'anin kake tunani da wahalar da kanka a kant..........


Bata karasa ba taji anyi sallama da wata irin murya da ba hausa ba kanaji kasan yare ce".


Juyawa mami tai ganin mace tsaye bakin palor fara tar jawur baturiya yasa cikin kaduwa tace" wace ke ya akai me kike nema anan din"?.


Dan murmushi tai idonta nakan Al'ameen da shima ita yake kallo tace "barka da gida mah suna na Abni Jonah daga London nazo gurin dear ne" ta fada tana nuna Al'ameen.


Wata irin zabura mami tai tana jefar da glass cup din hannunta ya fadi ya tarwatse idonta kamar zasu fito waje dan razana tace".

"Me Abni Jonah wato kece wannnan matsiciyar yarinyar da kika lashe kurwar dana ko baya ganin ko wacce mace saike shine yanzu kika biyo shi har kasar sa ki cinye shi ko mayya "?.


"Kallon Al'ameen Abni tai tana tambayarsa akan me mahaifiyarsa take cewa".


Kafin yai wani yunkuri mami tace ubanki nace tsinanniya la'ananniya harda me nace da yake ya zama sako tumaki saiya fada miki jaka kawai".


Cikin takaici Al'ameen yace wai mami me kikeyi haka haba dan Allah ki daina zagin ta ".


Bazan daina ba kazo ka dake ni saboda na zagi wannan shedaniyar arniyar".


Mami ki daina kafurta ta musulmace fa"?.


"Au a haka shine ta sako wannan dan mitsitsin hijab din kila ma wanda take zuwa coci ne".


Fahimtar da Abni tai kamar bata samu karbuwa agurin mami ba ganin yadda take magana da fada duk da batasan me take cewa ba yasa ta kalli Al'ameen ba tare da nuna wata damuwa ba tace" suje waje ko gardan suyi magana".



A tsawace mami tace idan ka fita ka bita ban yafe maka ba saina tsine maka wallahi,".


Iya rudewa yayi cikin yanayin ladabi Abni ta roki mami cewa ta kyale suyi magana amma mami tace ya fita ya gani".


Dafe kansa Al'ameen yai jin lokacin guda yayi mugun sara masa da hanzari Abni ta karasa tana tambayarsa lafiya"?.


Wata hankada mami ta mata wanda saida ta buge da kujera cikin tsawa tace fice daga nan idan ba gidan ubanki bane bakadaddiya karuwa wato a gaban nawa ma fayde zaki masa"😨😱.


Abni zatai magana mami ta sakar mata wani zazzafan marin dayasa ba shiri ta fita a palon da gudu tana kuka".


Al'ameen dake numfashi dakyar muryarsa na rawa yace mami me kika aikata kin aibata kin zage ta kin mare ta me tai miki dan Allah mami meyasa kika tsani Abni ni kuma baki tsane niba domin nine ita itace ni kowa ya kita ya kini".


"Ai kai yanzu na fahimci mahaukaci ne bakasan ciwon kanka ba idan ba mayya bace kalli mana kafin tazo kana irin wannan numfashin ne shashasha ana maka gata da yake idonka ya rufe baka gani".


Barin gurin tai yayin da Al'ameen yake yunkurin tashi yabi bayan Abni ya kasa.


Abni na zuwa hotel inda suka sauka ita da dad dinta tasha wani marin a gurinsa yana huci yace dole soyayya dashi kina neman kashe kanki ga samarin ki can ki zabi daya mana Abni ina kika kai tunanin ki,"?.


Kuka Abni ta fashe dashi tana rungume mahaifin nata tace kayi hakuri dad Al'ameen na sona kada ka raba mu nima ina sonsa ba laifinsa bane".


Cikin tausayawa daddyn ta ya rungume ta shima yana cewa shikenan naji yi shiru haka na gama komai a cikin kwana biyu saboda ke gobe zamu tafi".


Zaro ido tai tana mikewa tsaye zatai magana ya girgiza mata kai yana cewa".


"Bazan barki ki sake komawa wannan gidan ba kada ki batawa kanki lokaci Abni auren ki da yaron nan bamai yuwuwa bane".


A rude tace dad zai yuwu dan Allah ka kara min lokaci zanji da komai"'.


"Na sake baki lokaci amma wannan shine na karshe idan aka sake samun matsala bazan daga miki kafa ba".


Murmushi tai eh dad thank you na yarda".

🌹 Mrs Al'ameen Ahmad ce.


Yma Dutse new world🌎 new life🌲 and new style💈 sabuwar duniya🏙.


NAJA'AT MUSA ABUBAKAR
ZARAH MUSA 'DAN ADAN THIS PAGE IS FOR U I LV💝 U EVERYTHING ABOUT YOU IS SO GOOD BUT ONE THING IS WRONG THAT YOU ARE NOT MIND.



Page 05 to 06
Wani karamin kauye wanda yake cike da mutane iri daban daban wani gida ne daya sha fenti harta waje kamar yana cikin gari gidan yayi kyau sosai kana gani kasan me gidan nada abin hannu a kauyen.


Wata mace ce ta fito daga daki tana rawa tayi daurin kwalin soke irin ture kaga tsiyarnan tace.


"Ahayye nanaye yan gidan nan ku fito kuyi kallo Zainabu abu na me 'kashin arziki ce ba irin su o'o da ba'a da farcen susa ba".


Jin shiru yasa tace Salamatu kina ina ne kodai bakin ciki ya kashe ki a daki lallai kina da aiki ".


Fitowa wata farar mata tayi daga wani guri da hayaki ke fita wanda kana gani kasan dakin girki ne ta kalli waccan dake rike da atamfa tana cewa".


"Akan me zanyi bakin ciki saboda Zainab ta samu atamfa kowa ai da nasa rabon Allah ne ya bata".


Dariya Saude tai tana tafi tace tofa masu tawakkali kamar gaske kina magana a salihance nan kuwa zuciyar bakin kirin take"".


Murmushi Salamatu tai an fada miki kowa irin ki ne ni abin wani bai dame niba Fatima bata rasa kaya ba".


"Humm karyar banza kayan gida ba badan ubansu meyin suturar bane idan ta samari za a biye wata rana saidai ta fita yawo tsirara".



Salamatu dake shirin komawa kitchen tace Allah ya kiyaye kedai tunda kinbi son zuciya ki taka a sannu ina gargadin ki".


Kugu saude ta rike jimin munafikar mata koke kika samu duniya yarki tai farin jini haka sai kinci kudin samari".



Sallama wata budurwa tai tana sauke fantekar dake kanta tace gaskiya nifa na gaji da wannan tallar ehe "'.


Baki saude ta bude ke baki da hankali yi kasa da muryar ki kada salamatu taji tai min dariya dama yanzu ita da shegiyar yarta suka gama kukan bakin cikin atamfar da ilya ya kawo miki ".


Dariya Abu tai lallai ahe bakin ciki zai kahe su dan wallahi yace saniyarsa ta haihu idan ina dan zai bani".


Da sauri kamar wani zai rigata Saude tace kice kina so dan ubansa tunda bashi da hankali ki wanki gara😂.


"Ai dama taliyar murjin da kika dafa min yau shi kadai ya saye ta".


Zaro ido saude tai sadaka yayi a dandalin".

Baki Abu ta tabe a'a kawai yaji da manjan ya juye a cikin fantekar ya cinye shi kadai sai yar kadan daya bawa wani almajiri🙊😹.


Saude tace kaji jakin mutum wannan kada ayi auren ya kasa rike ki mahaukaci ne shi zai cinye taliyar rabin kwano da kofin wake".


Hade rai Abu tai nifa ina sonsa ki daina zagin sa yace min gobe zai turo iyayensa".


Cikin murna Saude ta rafka guda tana cewa abin yazo yar albarka ta kusa tafiya daki bari muntarin ya shigo muyi magana".


Mikewa Abu tai tana cewa nifa yunwa nake ji saude dake kirga makudan kudin da ilya ya baiwa Abun tace ki buda daki yana nan a langa".



Kai Salamatu ta girgiza tana daga kitchen tana tuka tuwo tace Allah ya shirye ku kada wata rana kuci kudin matsafi".


Kwanan Al'ameen goma baida lafiya gashi yana so ya koma gurin aikin sa amma babu dama dole ya hakura zuwa wani lokaci idan yaji ya dawo daidai".


Daddy na zaune kusa da Al'ameen bayan Sadiq ya duba shi ya daura masa ledar ruwa cikin lallami yace.


"Aminullahi meke damun ka Sadiq yace min har yanzu bugun zuciyar ka bai dawo daidai yadda yake ba ka fada min matsalarka".


Sauke ajiyar zuciya Al'ameen yai domin maganar dazai fada ba lallai daddyn nasu ya amince ba yace.


"Dan girman Allah daddy ka dube ni da idanun rahma ka tausayawa zuciya ta ka fahimcr cewa danka ya fada cikin jarabtar soyayya kamin maganin damuwa ta".


"Me kenan zanyi maka Al'ameen ka fada min kada kaji shakka niba mami bane babu abinda zai gagara".


"Daddy na roke ka ka duba Allah ka amince min na auri Abni yarinyar nan ta sadaukar da rayuwar ta saboda na samu farin ciki ta kula dani lokacin da bansan kowa ba a London.



Ta musulunta saboda ni ta yarda zata aure ni ta zauna dani sannan mahaifanta basu nuna min kiyayya kamar yadda mami ta tsane taba.


Da tazo gidan nan ta rako mahaifin ta mami ta zage ta ta aibata ta ta kafurta ta sannan ta mare ta amma batai zuciya dani ba saboda tana sona".


Cikin mamaki daddy yace ita Aishan ce ta mare ta ".


"Eh daddy wai tazo har gida zata cinye ni".


Murmushi daddy yai kuma an fada mata mayun 'kiri da 'kiri suke kama mutum su cinye shi yanzu dai me za'ai".


"Daddy abin da za'ai shine zan aure ta ina sonta da ita zan zauna dan Allah daddy ka fahimce ni itace komai nawa banajin zan samu madadin ta".


"Ok yanzu kana so aje nemar maka auren tane "?.


Eh daddy wannan shine damuwa ta ka taimaka min".


Hannunsa daddy ya rike karka damu zan yi kokari akan hakan zamuje london cikin satin nan domin kudi ba sune kwanciyar hankali ba".


Tashi zaune Al'ameen yai ba shiri yana cewa a satin nan na gode daddy Allah ya kara daukaka".


"Amin daddy yace yana kallon yadda lokaci guda fuskar Al'ameen din ta washe da farin ciki".



Lokacin da mami taji wannan maganar kuka ta fashe dashi na bakin ciki tana cewa yanzu alhaji tsakani da Allah aura masa arniya zakai karya fa take bata sallah".


"Shine damuwar ki"?.


Shiru mami tai tana goge idanunta da sukai jawur saboda kiyayyar Abni.

Ganin taki magana daddy yaci gaba inda rashin sallah shine matsalar me sauki ne zata musulunta tunda tana sonshi kuma ba haramun bane danya aure ta".

"Dan haka ranar monday jibi kenan ki shiri za muje london nema masa auren ta kiyi fatan itace alkairi a rayuwarsa".


Hannu mami ta dora akai tana sake zunduma wani ihun cikin burgima tace wallahi bada yawu naba kuma ko kofar gate bazanje ba balle naje wata london gurin shegun arna naje su bawa gunki jini, na".


"Bazai auro min wata baturiya ba saidai ya mutu baiyi aure ba".


"Aishaa" daddy ya fada a tsawace tare da nuna ta da yatsa yace.


"Idan ke bakya sonsa ni ina sonsa kuma na amince ya auri wannan baturiyar tunda itace zabun ransa kece zaki zauna masa da yan mata da kike kawo masa"?.


"Shashancin banza kin girma amma kina shiga daji bakisan kaddara ba na biye miki kina neman kashe min yaro kamar ba kece kika haife shi".


"Saiya aureta idan har matarsa ce saiki dau mataki kuma umarni nake baki ki shirya tafiya ranar monday nan da kwana hudu na gama yanke magana".


Yana fita ta mike da gudu tana shiga part din Al'ameen yana zaune ruwan ya kusa karewa tana zuwa cikin karaji da ihu da yage yage kamar me ciwon hauka ta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On DAN MILLIONAIRE
avatar
zainab-ibrahim-8

3 months ago

Reply

Thank

avatar
zainab-ibrahim-8

3 months ago

Reply

Than

Please Login or Register in order to submit comment