Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

06/08/2019 à 00:06 - Les messages envoyés dans cette discussion et les appels sont désormais protégés avec le chiffrement de bout en bout. Appuyez pour plus d'informations.
06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*JIHADI*
_Umar faruk_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑

_NA_

_SAMIRA HAROUNA_


_My Happiness *Amnoor*, barka da fara sabon novel mai sunan *matar farko* (dandab'asa), wannan novel kam namu ne domin damu ake, matan farko ba ba kamar su o'o ba, ina nufin momyn D....tasan sauran, su kam d'ogalawa ne.😁 Allah yasa ki gama lafiya kamar yanda kika fara lafiya._


💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘
_My BK, nasan babu godiya tsakaninmu, to amma ya zama dole yaba kyauta, ina godiya BK ta Allah ya bar zumunci._
💘💘💘💘💘💘💘💘💘💘


🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾
_My Heenat, na rasa me zance ma, sai dai kawai nace Allah ya barmu tare, qauna ta gaskiya kam kina nunawa Sameera ita._🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾🎾

_💘Mamien mu *(Maman Labyb)*, gaskiya ke uwace ta gari wacce ko wace d'iya ko d'a zaiyi alfaharin samunki a matsayin uwa, yanzu haka har na d'an fara kishi da BK ina ji inama nice 'yarki , to amma ba damuwa zan zauna a matsayin 'kawa kuma rabin ran d'iyarki._💘


_DEDICATED TO_

*MA FAMILLE*

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛


_Bismmilahir-rahman-rahim_

1⃣


Da alama ranta a b'ace yake ga k'aguwa a zahirinta ya bayyana, sake kallon agogo tayi na karo ba adadi sannan ta kalli k'ofar douche d'in taja dogon tsaki tana magana k'asa k'asa "wannan wulak'anci dame yayi kama, sama da awa d'aya kina wanka, ki bani wani banzan serviette (towel) na rik'e kamar ke wata musaka ce."

Sake kallon agogon tayi sai dai kafin ta maido kallonta taji an bud'e k'ofar douche ana fitowa, da sauri ta kalleta amma saboda ganin santaleliyar budurwar ta fito daga ita sai d'an k'aramin silip (pant) d'inta ko soutien ( bras) babu yasa tayi k"asa da kanta, ita kam ko a jikinta takowa tayi ta zo gabanta ta karb'i serviette d'in ta d'aura a k'irji sannan ta karb'i dayan ta d'aura a kanta, gaban coiffeuse taja kujera ta zauna tana kallon madubi ita kuma mai aikin ta matso ta d'auki mai ta fara shafa mata, bayan ta gama ta shafa mata powder da pink d'in jan baki, ta fito mata da wani silp d'in da soutien ta bata ta saka sannan ta fito mata da riga da siket na atamfa, d'inki ne na yan zamani yayi kyau sosai gashi ya zauna a jikinta daram , mai aikince ta zuge mata zip d'in dake bayan siket d'in wanda ya kamata sosai komai nata ya fito masha Allah, d'an kwali ta kashe d'aurinshi sannan ta fito mata da sarka da yan kunnai da gani kasan sunji kud'i, sannan ta fito mata da jaka da takalmin da suka dace ta aje mata gabanta, sakawa tayi sannan ta d'auki turare ta fesheta dashi ita kam tana tsaye kamar gunki, tana kamalawa ko jiranta bata tsaya ba kawai tayi k'ofar fita abinta.


Binta tayi da harara tana fad'in "wannan zanso naga gidan aurenki , mijinki ne zai miki wannan hidimar ko kuma mai aiki zai samar maki."

Gyara d'akin tayi kamar yanda maishi zata buk'aci ganinshi sannan ta fito ta rufe mata d'akin.

Ba tare data kalli kowa dake kan table a manger (dinning) d'in ba taja kujera ta zauna, wata mai aikince dake tsaye kusansu ta matso ta fara zuba mata abincin, ta zuba mata fritte zata bud'a wani kwanon kawai ta d'aga mata hannu tare da kallonta cike da wulak'anci tace,

"Ya isa haka, ni ba jaka bace kamarku da zan zauna ina had'iyar abinci haka."

Ja baya tayi kanta k'asa bata kalleta ba ita kuma ta fara cin fritte d'in, mahaifiyarta ce tace "mu kike so mu fara gaidaki kenan?"

Cike da nuna an takura mata tace "ina kwana."

Mamar ce tace "nice kad'ai a wajen?"

Kallon saurayin da suke fuskantar juna tayi, amma ganin wani kallo da yake mata tare da murmushi yasa ta zabga masa harara, maida kallonta tayi ga mahaifinta, d'auke kai tayi ta kalli mahaifiyar tata tace "ki tabbatar min jiya bai shigo cikin maye ba, ni kuma saina gaisheshi."

A tsawace uwar tace "ke, ashe baki da mutunci, wannan ba mahaifinki bane da zaki fad'a masa haka?"

A wulak'ance ta kalli uwar tace "shi kenan mutunci ne yake sashi shigowa cikin gida a buge? kinga nifa karki b'ata min rai da safiyar nan."

Duk da k'ok'arin rik'e hawayen da tayi saida suka zubo, cikin muryar kuka tace "ba laifinki bane, kiyi yanda kike so."

Tana fad'a ta juya ta nufi d'akinta tana zubar da hawayen takaici, ita kuma ko kulata ba tayi ba bare taji ba dad'i, saima mahaifinta data kalla tace "zaifi maki kyau ki daina saka damuwa a ranki akan wannan da baisan kina yi ba."

Tashi tayi ta bar abincin zata fita ,mahaifinta ne kalleta a marairaice yace "kiyi hak'uri mana gimbiyata, nayi alk'awari ba zan sake ba."

Kallonshi tayi ta kalli saurayin dake zaune kusanshi tace "ka fad'awa wannan wawan watak'ila shi zai yarda da abinda ka fad'a, amma bani ba *Khairat*."

Fita tayi ta nufi wajen motarta, d'aya daga cikin jami'an dake kula da mahaifinta ne ya taho shima a gadarance ya karb'i jakar hannunta da makullin mota ya nufi motarta dasu, dan in baiyi ba to masifa zaisha amma ba k'aramin d"aci ba abin ke mishi, har zata shiga mota taji saurayin nan yace "nine wawan?"

A wulak'ance ta juyo ta kalleshi tace "to da wa in ba kai ba? da wani ne wanda ya fika zama wawa a duniyar nan? ai kai kad'ai ne namijin dake zuwa gidan wacce yake ikirarin yana so kuma ya zauna zaman dirshan har da mik'e qafafu."

Nunashi tayi da yatsa tace "wallahi harka gama wa'adin daka dibarwa kanka ba zan tab'a kallonka a matsayin mutum ma bare harna fara tunanin soyayya da kai, désolé."

Tana fad'a ta shiga motarta ta bar gidan cikin matsanancin gudu, shi kuma taushe b'acin ranshi yayi da har yanzu yana ji a jikinshi zata iya zama tashi, a ranar da kuma hakan ta faru zata gane wanene shi.

********************

Kafin ta fara gudanar da komai saida tasa masinger ya siyo mata fritte mai had'e da soyayyen nik'akk'en nama da jus d'in albasa da moutarde, tasa *Habiba* ta had'a mata kakkauran tea da zuma sannan ta fara wani sabon petis de jeûner d'in, tana fara ci Habiba ta sake shigowa cikin ladabi tace "madame, manager ne ke son ganinki."

Kallonta tayi a wahalce tace "uhum, kice ya shigo."

Juyawa tayi dan cika umarninta, takai wata lomar bakinta taji shigowarsu, amma jiji da kai yasa ta kasa koda kallonsu da ido, tsaye sukayi a kanta hakan yasa ta musu nuni da hannu akan su zauna, saida suka zauna sannan ta kallesu gaba d'aya ta kuma kalli manager tace "kai kad'ai aka ce kana son ganina, yana ganku ku biyu?"

"Eh madame, wannan shine wanda za muyi magana akan ci gaban daya kawo mana."

Sake kallon saurayin tayi wanda idonshi ke kan kallon yatsun hannayenta da take cin abinci dasu, jan lallen da suka sha da dogayen akaihu na kanti wanda suma ta lullub'esu da pink couleur d'in vernie, sosai suka birgeshi duk da dai ya tsani mai su d'in, maida kallonta tayi ga plate d'in abincinta taci gaba da ci har saida ta gama sannan ta d'auki bidon (gora) d'in ruwa ta zura hannunta ta tagar dake bayanta ta wanke hannu ta juyo da nufin aje bidon d'in ta d'auki lotus dan goge hannu, karaf idonta suka sauka akan gayen nan daya kasa d'auke idonshi akan kyakyawar hallitarta, da sauri ya d'auke idonshi tare da had'e fuska tamkar hadarin gabas, dan tunda ta fara aiki anan take tak'ama wajen mahaifinta ne ya lura tana da raini shi kuma ba zai d'auka ba, saida ta goge hannun ta tsaya ba yare data zauna ba ta kallesu tace "ina jinku."

Hannu manager yasa a jaka ya fito da takalma ya mik'a mata yana fad'in "wannan shine sabon sanfarin da wannan ma'aikacin namu ya fito mana dashi, shine nace kafin muci gaba da bugawa sai mun samu izininki."

Karb'a tayi bayan ya gama mata bayanin ta kallesu da kyau, tabbas sanfurin ya birgeta dan kuwa basu da maraba dana maza harda gidan babban yatsa, ga kuma tudunsu shima kamar dai na maza, ajesu tayi qasa ta cire na qafarta tasa wad'annan, su kam kallo suka bi qafar da ita yayin da saurayin ke ma qafar kallon qurilla wacce tasha jan lalle sai dogayen akaihu itama data saka masu kamar dai na hannuwa, ganin yanda suka zauna a qafarta suka mata kyau yasa ta cire ta zauna a kujerarta tace" kuje kawai ku ci gaba da bugawa, ku bar min wannan zanyi publié a Internet nasan zamu samu masu so."

Cikin farin ciki bayan sunyi godiya suka tashi zasu fita, muryarta ta tsayar dasu tace "fasahar waye?"

Juyowa sukayi manager kuma yace "wannan ne madame." ya fad'a tare da nuna na kusa dashi.

Saida ta fito da wayarta a jakarta sannan tace "meye sunanka?"

" *Umar Faruk*." ya fad'a a daqile.

"Zo nan." ta fad'a kamar ta kira yaronta.

Kamar ba zai zo ba saida manager ya sake cewa "madame na kiranka."

Takowa yayi tare da k'ara d'aure fuskarshi, saida ya tsaya gaban tebur d'inta yana kallon idonta, jujjuya kujerar ta fara yi tana juyawa da ita ta fara magana "karka bari mu sake had'a ido da kai da sunan had'arin kallo, karka sake bari na maka magana so d'aya har sai an maimaita maka, karka bari na sake jin raina ya b'ace a kanka, sannan karka sake kallon min bayana idan na juya."

Tsaye ta mik'e tare da d'aukar lotus d'in data goge hannu ta saka masa shi a aljihun gaban riga tace "ka aje min shi, gobe zan tambayeka."

Zaune tayi tace "zaka iya tafiya."

Saida ya gama mata kallon raini kafin ya gyara tsyuwarsa yace "idan baki son ana kallonki, to ki zama kamilar mace ta yanda ba zaki rinjayi shed'anun dake cikin zuk'atanmu ba bare har mu kalleki , ni kaina nasan nayi zunubi kuma dole na nemi gafarar ubangijina akan hakan, sannan ki sani ni ba d'anki bane da zaki takani yanda kike so, haka kuma talaucina bai k'ask'antar dani izuwa matakin dake kike k'ok'arin d'orani a kai ba, ina fata kin fahimta."

Yana fad'a ya juya bar bureaux d'in, ita kuma ta bishi da kallo tare da tunanin koya masa hankali.

Kasancewar bata jima da fara aiki a wajen ba yasa har yanzu akwai rashin sabo, yanzu haka tattara kayanta tayi Habiba ta biyota dasu ta nufi gida saboda bacci kawai take so tayi.

********************


Tunda ta shiga gidan taga guardcord (bodyguard) d'in mahaifinta kuma taji shiru dan haka ta shiga babban falon da zai sadata da nata d'akin, duk da ba bak'on abu bane a wajenta amma dai ta tsorata, tunda taji sautin tasan mahaifinta ne ke dukan mahaifiyarta, da gudu ta nufi d'akinshi ta jefar da jakarta, bata tsaya komai ba ta kutsa kai cikin d'akin ai kuwa bata tsaya ba wajen kaiwa mahaifiyarta d'oki , saman gadon ta fad'a ta rumgumo mahaifiyarta tana k'ok'arin kare jikinta, tunda ya ganta ya jefar da wayar hannunshi ya fara zare ido, yana kakkare jikinshi saboda daga shi sai gajeran wando, kama mamanta tayi suka sauko daga gadon ta d'auki rigarta a k'asa daya ketata da qarfi ta rufe mata jiki, tana rik'e da mahaifiyarta ta kalleshi sai k'yabta ido yake tace "wallahi idan ka sake dakar min uwa, to ka sani justice (kotu) ce zata rabani da kai, dan ba zai yiyuba ka dinga shak'o giyarka kana zuwa kana narkar min uwa ba."

Tana fad'a suka fita daga d'akin saida ta kaita har d'akinta ta d'auko mata riga doguwa ta sauya ta d'auko mata maganinta ta bata tasha sannan ta kwantar da ita tana rufeta tana fad'in "banga abinda kike tsinta a gidan nan ba da ba zaki barshi ba, amma da nayi magana sai kice saboda ni kike zaune, ni zan kula da kaina ki koma wajensu Mammie ki zauna."

Tana fad'a ta juya itama ta koma nata d'akin ta cire kayan jikinta ta watsa ruwa sannan ta d'auki kayan data fi jin dad'in zama dasu a cikin gida ta saka, wando ne na jeans fari tas sai dai iya cinyoyinta ya tsaya sai kuma riga ta dan sauko har cibiya amma k'ananan hannuwa gareta, kwance tayi ba jimawa bacci ya d'auketa.

*******************

Tana tashi bayan la'asar brush tayi kawai ta fito bata damu dayin sallolin dake kanta ba, a falo ta zauna saman lunstumemiyar kujerar dake kai tana kallon tv, mai aiki ce ta kawo mata abinci tana ci mamarta ta fito rik'eda carbi , zaune tayi tace "kinyi sallah?"

"Nayi." ta fad'a dan karta sake damunta.

_Wannan yarinya ba dai k'arya ba_

Haka suka kasance wunin ranar ba wani dad'i, sai dai takalmin data d'ora a internet sun samu masoya, anan wasu manyan 'yan kasuwa suka ce suna son dayawa akan sari, anan suka tsayar akan gobe zasu zo ma'aikatar tasu sai suyi magana, kasancewar manyan mutane ne yasa tace wa mahaifiyarta ta tasheta k'arfe takwas na safe danta shirya da wuri, cikin dare sosai tana kwance tana chat taji motsi a falo, lek'owa tayi abin mamaki *Mujahhid* ne yake shiga d'akinshi cikin tsananin maye tare da wata budurwa, tsaki taja tace "dubunka ta cika, wallahi saika bar gidan nan tunda bana ubanka bane."

Komawa tayi d'aki ta ci gaba da abinda take har bacci ya d'auketa da ecouteur a kunne tana sauraren wak'ok'i iri iri.

*********************


*Da safe* zaune take a tsakiyar wani faffad'an gado na alfarma cike da magagin bacci da har yanzu bai saketa tace "nifa wallahi kun takura min, wai dole saina tashi ne?"

Sake komawa tayi ta kwanta taja wata kakkabrar zanin rufa ta rufe, matar dake tsaye gefenta ta sake yaye zanin tana fad'in "dole ki tashi, ke da kanki kika ce na tasheki takwas daidai saboda bak'in da zasu zo."

Tana jin haka ta tashi firgigit tana zare ido tare da kallon mahaifiyar tata tace "k'arfe nawa yanzun?"

Tab'e baki tayi tace "08:20."

Ai kuwa kamar zata bige uwar haka ta diro daga kan gadon ta nufi k'ofar fita, ta bud'e k'ofar matar tace "ina kuma zaki je da wannan kayan?"

Ko saurarenta ba tayi ba kawai ta fice abinta, da gudu ta sauko daga matakalar benen, tsinkayar mahaifinta tayi a farfajiyar gidan d'aya daga cikin masu tsaron lafiyarsa ya bud'e masa mota yana daf da shiga, da gudu ta k'arasa tana kiran "papa, papa."

Tsayawa yayi ya juyo yana kallonta, sai dai bashi kad'ai ba harda masu tsaron lafiyarsa dake cikin tenue d'insu na sojoji su hud'u, kayan baccine wando iya cinyoyinta sai kuma k'arama kuma siririyar riga mai kamar puscier, abinka ga fara kuma doguwa kyakyawa, ba tare data kulasu ba kawai tace wa mahaifinta "papa, ku jirani na shirya saiku ajeni a service d'in."

"Motarki fa?" cewar papan

Juyawa kawai tayi ta nufi cikin gidan tana fad'in "bana jin tuk'i yau."

Ajiyar zuciya ya sauke dan babu yanda zaiyi dole ya jirata, yayin da jami'an suka bita da kallo iri iri suna kallon mazaunanta dake juyawa gwanin ban sha'awa.

Kasancewar tana sauri yau shi yasa bata jima douche ba ta fito cikin k'ank'anin lokaci ta shirya, doguwar rigar tattausan tissue (matériel), wacce ta kama jikinta sosai k'asa kuma ta bud'e, kallabin rigar kawai ta d'aura ta d'auki jakarta tasa takalmi ta fito bayan fessa tsadaddun turarukanta masu d'aukar hankali dayawa, duk da jan jan-baki ne ta shafa kad'ai amma hakan bai hana kyawunta fitowa ba sai k'ananun kitsonta da suka kwanta a gadon bayanta.

Tana fitowa matar na zaune a d'aya daga cikin kujerun falon ta kalleta, cike da nuna rashin jin dad'i tace "me yasa kullum kike burin mu dinga nanata kalma d'aya, yanzu ko nauyi ba kiji ki fita haka babu gyale bare hijabi."

Wata babbar fridge ta bud'a tana fad'in "kece kike sha'awar bawa kanki wahala da kike maimaita abu guda kullum."

Tana fad'a ta d'auki wani gateau da holandia yagourt ta fice abinta, tana zuwa jami'in ya bud'e mata gidan baya kusa da mahaifinta, shagalta da yayi da kallonta yasa bai bud'e k'ofar da kyau ba, cikin jin haushi ta daka masa tsawar da saida kowa ya zabura dake wajen tana fad'in,

"Imbecile, q'est ce que tu regarde?"

Da sauri ya bud'e mata ta shiga tana jan tsaki tana fad'in "sakarkarin banza kawai, ni banga abinda suke tsinana maka ba da har yanzu kake tare dasu, in banda k'yauyenci da shirme babu abinda suka sani."

Haka suka ja motocin, mota d'aya ce a gabansu sai kuma wata d'ayar a baya tasu a tsakiya, saboda tsaro.

Gâteau ta fara ci tana korawa da tana ci gaba da mita, shi dai mahaifinta saurarenta kawai yake,amma hankalinshi baya wajenta, har saida suka isa suna tsayawa a babban masana'antar ta sake kallensu tace "kenan babarku ce zata bud'e min k'ofar ko me?"

Wanda baya tuk'in ne ya fito ya bud'e mata, tana fita ta kalli mahaifin nata tace "idan kaje mashayar ka shawu son ranka, kaga saika shigo mana gida a buge."

Kallonta kawai yayi baice da ita k'ala ba, ita kuma ta wuce ta tunkari ma'aikatar, tana shiga ma'aikatan suka fara shan jinin jikinsu yayin da kowa ke gaisheta, sai dai babu mai sa'ar da zata amsa mashi gaisuwar , secretaire d'inta mai sunan *Habiba* ce ta karb'i jakar hannunta ta fara take mata baya tare da fad'a mata programme d'insu na yau bayan sun sallami bak'in, juyowa tayi a hassale ta kalleta tace,

"Ki soke duk wani programme na yau dan babu abinda zan iya, bak'in nan kawai zan gani na koma gida."

Shiru tayi suka haura sama a cikin acessaire in da zai sadasu da d'akin da bakin suke, tana shiga kallon mutanen ya dawo kanta in da kowa ke yaba kyawun fuskarta dana hallita da Allah yayi mata, bakin turawa ne duka ta mikawa hannu cikin sakin fuska suka gaisa kafin ta zaune kujerar dake tsakiyar sauran kuberun , saida kowa ya zauna mazauninshi harda secretaire d'inta ta zaune daga bayanta danta d'auki rahoton abinda zasu tattauna, sai lokacin kuma kallonta ya kai ga wata kujera da babu mazauninta, kallon habiba tayi tace,

"Wane sakarai ne anan da bai shigo ba?"

Cikin ladabi Habiba tace " *Umar Faruk* ne."

Za tayo magana suka ji an bud'e k'ofar wajen, ganin saurayin cikin hanzari yake yasa ta tashi tsaye cike da raini tace "sannu da zuwa yallab'ai."

Kallonta yayo ya kalli mutanen dake wajen, take ya fahimci abinda take nufi dan haka yace "je demande vos esxuze, je..."

Tsawar data masa yasa yayi shiru "yi mana shiru, kenan muna zaune nan dan ka zo ka bamu hak'uri, kai mahaukacin ina ne da baka san mahimmancin lokaci ba? kawai mutane jahilai daku babu abinda kuka iya sai tumasanci da banlag...."

"Ke, ya isheki haka."

Wannan maganar ita tasa tayi shiru bata shirya ba.....

Cikin b'acin rai ya ci gaba da cewa "me kika d'auki kanki? su waye jahilan? fad'a min matakin karatunki da har kike fad'a min haka, to bari kiji wallahi kika sake kirana jahilai saina fasa miki baki a wurin nan, ke in ba jahilce ke damunki ba me yasa zaki kira wasu da jahilai, kuma bari kiji aikine da nake a service d'inku zaisa kimin kallon banza ko? to na daina daga yau, saiki zauna ki cinye wurin idan zaki iya."

Yana fad'a ya juya ya barta nan tsaye sake da baki, a fusace ya bar wurin kayanshi ya had'a dake kan teburd'inshi yana shirin fita, ta baya yaji an dafa kafad'arshi, juyowa yayi ya sauke idonshi akan babban abokinshi....


*Luv you guy's*😍
06/08/2019 à 00:06 - Meerahgee❤: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*JIHADI*
_Umar faruk_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑

_NA_

_SAMIRA HAROUNA_


_DEDICATED TO_

*MA FAMILLE*

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛


_Bismmilahir-rahman-rahim_

_Manzo (S.A.W) yace "Imanin d'ayanku ba zai cika ba har saiya soma dan uwansa abinda yake so ma kansa."_ *Imamul Bukhari da muslim suka ruwaitoshi*


2⃣


"Faruk lafiya na ganka rai a b'ace?"

Cikin masifa yace "ina fa lafiya, wannan 'yar rainin hankalin tana nema ta b'ata min rai kawai dan tana ganin nan mallakin mahaifinta ne, ni dama tunda naga yarinyar nan nasan ba za ayi abun k'warai a wurin nan ba."

Wani murmushi yayi yace "Faruk, to yanzu meya faru kenan?"

"Me kuwa ya faru, na baro mata wurin,kuma daga nan gidanmu nayi dan ba zan iya aiki a k'arkashin yarinyar nan ba."

Da sauri ya rik'e hannunshi daga shirin rataya jakar da yake shirin yi yana fad'in "me kace? Faruk kana da hankali kuwa? kasan me kake shirin aikatawa?"

"To bari kaji in fad'a maka kuskuren da kake shirin aikatawa, wannan aiki shekara hud'u mukayi muna neman abinyi amma bamu samu ba, ka sani kafin mu sameshi munsha wahala sosai, bama wannan ba Faruk me yasa ba kayi tunanin mutanen da suka ci suke sha ta dalilinka ba, ko ka manta da irin nauyin dake kanka ne, sannan ka sani
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment