Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

LABARIN ALJANI YA TAKA WUTA Part 1.
Duk wannan kadan ne daga cikin cikin kaunar da
yarinyar take nuna masa yau kusan shekaru shida
kenan tun suna firamire, kullum aikin t kenan
taso shi ta kuma yi masa wahala, kuma duk
sanda zai koma makaranta ita ke zuwa da motar
gidansu ta mayar dashi, bayan yan kananan siye-
siye da take yi masa har kudi take bashi. Amma
kuma abinda bata saniba shine mafi yawa daga
cikin kudin da take bashi a shaye shaye da
yawace-yawacen banza suke tafiya,domin in har
kana neman shaidani a duk fadin makarantarsu,
idan ka sami Nuraddin ka kare."Badawiyya
kenan". Nuraddin yace gami da dan tattausan
murmushi."Nuri 'darling' kenan". Badawiyya
tace.Ga mamakinsa sai ya ga ta dauko tsohuwar
jakar da take cewa bazata dauka ba, ta rataya
kafada."Zo mu tafi dan Allah Nuri so kake muyi
rana?Nuraddin na gaba dauke da jakankunan
ledar biyu, ita kuma na biye dashi a baya dauke
da mushenzakaran jakar Nuraddin. Duk inda ta
wuce, sai tabar iskar gurin da madaukakin
kamshin turaren dake jikinta, tana tafiya iska na
kada siraran gashin kanta wadanda ke kokarin
fitowa ta ciki farin gyalenta mai raga-raga dake
lullube da kanta.Hajara ta fito daga daki a dai-
dai lokacin da yaran biyun suka ratso tsakar
gidan. Badawiyya tayi sauri ta durkusa."mama
ina kwana?""Lafiya lau Badawiyya", Mahaifiyar
Nuraddin ta amsa, sannan kuma ta dubi
Badawiyya. "oh 'yar nan bakya rabuwa da
wahala, ko yaushe dai sai kinyi masa wahala,
'Badawiyya ta sunkuyar da kai cikin
girmamawada alkunya tace a hankali."ba.... Babu
komai mama"."An gode to, Allah ya saka miki
Badawiyya." mahaifiyar Nuraddin tace da ita
sannan ta juyo ga Nuraddin."Ga wannan ka tafi
da ita, malam ne yace a baka, maganin tsautsayi
ce, yace duk inda zaka, ka rinka tafiya da ita," Ta
mika masa wata 'yar kankanuwar laya wacce aka
rufeta da jara fata.Nuraddin ya karba, ya dubi
Badawiyya suka yiwa juna murmushi, sannan sai
yara biyun suka juya suka tafi."Allah ya kiyaye
Nura." mahaifiyarsatace dasu."To mama saina
dawo.Koda yaran suka fice daga gidan saibabar
Nuraddin ta dubesu sannan ta Dubi Badawiyya ta
girgiza kai sannan tace cikin zuciyarta "kai
wannan soyayya ta yaran nan da ban mamaki
take, yanzu ace yarinyakamar wannan ta
makalewa wannan yaro wanda shi ba komai ba,
to, meyiyuwa dai shima farin jinin malam zai
biyo." sai kuma abinda bata sani ba shine farin
jini ma yanzu ya fara, domin kuwa bada dadewa
ba farin jinin zai sake hada shi da wata sabuwar
budurwar mai ban mamaki.*** *** ***Nuraddin ya
mika, sannan yayi wanikwakwaran fito ya dirgo
daga kan gado, ya dubi sauran gadajen dake
dakin babu kowa akansu sai gado daya wanda
Auwalu surajo ke kwance a kai yana karatu. Karfe
tarada rabi na dare, duk sauran daliban dake
daikin sun tafi ajujuwan karatunsu domin bitar
abinda aka koya musu.Nuraddin ya durkusa karka
shin gadonsa ya janyo akwatinsa, sannan ya
bude ciki. A lafe a kasan akwatin, kudin kusan
Naira dubu biyar duk Badawiyya ce ta bashi
kudin. Nuraddin ya zaro dari daga cikin kudin ya
tura ciki aljihun gaban rigarsa. Sannan ne yaji
motsia bayansa, yayi firgigit cikin sauri yarufe
jakarsa don gudun kada wanda ke shigowa yaga
kudin da yake ciki. Duk yake dai Nuraddin yasan
babu wani shege a cewarsa, daya isa ya taba
kayansa koda wasa ballanta nada sunan sata,
amma yasan in an tambaye shi dole shima ya
bayar, tunda ana bashi, wannan shiyasa baya son
asan yanada kudi da yawa."Mene ne na boyewa
ai mu dama ganin falleliyar babynnan ta
kawokacikin arniyar motar nan munsan da
karfinka ka dira.Nuraddin ya juyo domin ganin
mai maganar, duk da dai kafin ya juya ma yasan
duk daniyar ba mai muryar nan sai wazirinsa
Nafi'u {BOSS}."shegen duniya daga ina haka,
dakin karatu ko makaranta?" Nuraddin yace
sannan ya mika masa hannu suka tafa tas!
Kamar an mari jaki da faranti."wace irin
makaranta kuma banda wannan da muke ciki?"
Nafi'u boss ya tambaya lokaci guda kuma ya
zauna bakin gadon Nuraddin."Ku dubu allonku
daya nake nufi".Oh shet! Men, ai abin da ya kawo
ni kenan, ance kuwa fim din yau wani arnen
Indiya ne, ana fadamin labarin sai ka fado min a
rai, to ni sam-sam ban dauka ka bayyana ba to
shine hamza siyasiya ya ce min ai dazu yaga
bayyanarka kuma wai wata ba kyau din beby ce
ta kawoka,nan da nan na garzayo, domin yau duk
aljihun ka zamu shiga sinimar nan dan bai yiyuwa
fim din nan ya wuce mu". Nafi'u boss yace ya
dan tsagaita yana mayar da numfashi."to uban
shegen surutu ka gama tsarani din?""Ah! Haba
Nuri namu, kai kasan ai mu da kai haka muke".
Ya hada tafikan hannunsa biyu guri guda."wai ina
su Basiru logarizim ne?" Nuraddin ya tamba.Duk
suna can bayan 'central hall' kai muke jira kawai
yau duk aljihunka zamu shiga sinima kai harsigari
ma yau ba mai siya da kudinsa......

Aljani Ya Taka Wuta!..2
;
;
sunyi sanadiyar faduwar dalibai da dama
jarabawa, haka nan tun da suka shigo
makarantar basu da aiki sai shiririta, yau kusan
shekaransu shida kenan, wannan itace
shekaransu ta karshe a sakandiren. Da yawa
daga cikin su suna zuwa makarantar ne kawai
don ace sun gama, amma badan su sami sa
kamako mai kyauba. Ba kowanne mutum bane,
ba kuma ko wanne mai karfin zuciya bane zai
baƙin kungurumin dajin dake tsakanin makarantar
zuwa cikin gari ba, domin tafiyar kusan kilo mita
biyar ne zuwa cikin garin, an kuma ce zai hanyar
cike take da aljanu da kwumakwumai, amma
hakan bai tsorata su ba musamman Nuruddin,
domin shi ko babu mai zuwa zai gwab kama
hanya abinsa shi kaɗai, dole ne sai yaje. Anyi
musu nasiha sunkiji an horesu da bulala duk
banza kai har wa'azi na anyi musu. Malam
mahmud bashir malamin arabiyyane a
makarantarsu Nuruddin ya taɓa cewa dasu
watarana suna ɗaukar darasi " kuyi a hankali
yara, mun sami labarin akwai wasu takadarai
acikin ku waɗanda kullum kwanan duniya sai sun
shiga gari sunyi kallo a sinima, to ina
shawartarku ku da ku bari, ba don komai ba
kuma sai don lafiyar ku, kunsha da jin haɗarin
dake tattare da wannan dajin na irin kwankwamai
dake ciki, amma don taurin kai ku nace sai kun
fita cikin dare. To wallahi kuyi a hankali inba so
kuke watarana wani ya farka a cikinku da siririn
hannu shanyayye kamar lagwanin risho ba "
yaran suka fashe da dariya to amma nasihar
malam mahmud bashir tamkar zuga ce ga
takadaran yaran biyar. "kai rabu dashi ajawo,
muzai yiwa wa'azi da wani dogon gemunsa
kamar buroshin wanke kwalabe ". Nuruddin yace
da yaran su kuma suka bushe da dariya. Watanni
biyar kenan da faruwan hakan.
****
Cikin sinimar ya dauki hayaniya lokacin da
bangwaleliyar kalmar *{ THE END }* ta yiwa
kanta gurin zama a kan farin allon sinimar. Ba a
dade ba su Nuraddin suka fito, suka kamo hanyar
dawowa makarantar karfe daya da rabi na dare,
domin ranar fim biyu akayi a sinimar.Yaran biyar
suka keto cikin bakin daji, bakajin komai sai
hayaniyar yaran wadanda ke tafiya sunata
hayaniya gami da tada kura kamar shanu. Babu
alamar farin wata a cikin dajin, babu kuma wani
kwakkwaran sauti sai jefi-jefin kukan gyare dana
tsuntsaye nan da can."Kai ku tsayani na taka
kaya." basiru logarizim yace dasu."Gafara can
malam waye zai tsayaka, ka kwana ma a nan
mana waya damu da kai". Nuraddin yace
dashi."To kada ku tsaya din mana wata tsiyar
ce". Sauran yaran suka busheda dariya sannan
sukayi gaba suka barshi gurin tsugunne yana ko
ƙarincire kayar.Basu dade da barinsa ba, sai
basiru yaji motsi a bayansa yana juyawa sai
sukayi ido biyu da wata katuwar kyanwa baƙa ƙirin
da ita kamar kwanta. Idanunta jajaye suna sheki
kamar kwalba a cikin rana. Basiru ya dubi magen
itama ta dubeshi , iska taci gaba da karkada
ganyayyakin bishiyoyin dake zagaye sannan ya
rarumi wani bushashen itacen bishiya dake kusa
da shi ya nufo magen, amma sai taki
guduwa."Ah! Kaga marar kunya! Basiru ya fada
cikin karaji sannan sai ya ɗaga itacen yakai mata
duka. Tun kafin itacen yakai ga kan magen yaji
hannunsa ya yi sakh yayi lararraf dashi kamar
tsumma, babu nauyi, ga mamakinsa sai yaga
hannun yana motsewa a hankali a hankali har ya
koma kamar kaurin kyandir, sannan sai yaji
hannun nasa ya fado jikinsa tamkar dama ba a
jikinsa yake ba."wayyo Allah na shiga uku! Ah!
Ah! Ah! Nura! Dan Allah kuzo na shiga uku.....Na
lalace".Sannan sai wata kakkausar murya ta kece
da dariya, muryar babu dadin ji kamar muryar
jaki.Ihun da suka ji a bayansu, shiyasa su juyowa
lokaci guda tamkar sojoji yayin faretin ban girma
a gaban shugaban kasa."Kunji wannan shegen
kamar sunana yake kira, ihun menen...Sauran
maganar ta makale a fatar bakin nuraddin lokacin
da sukaji an sake ihun, a wannan karon har da
kuka. Yara hudun suka dubi juna sannan suka
dubi ciki duhun dajin inda suka baro Basiru. Kuzo
mu ko mu gano shi. Nuraddin yace da sauran ko
wannensu tsumayake, sun gama tsorata don haka
sai sukayi sororo kamar gumaka suna kallon
Nuraddin."ko bakwaji nane?
¤¤¤¤
A dai dai lokacin ne suka hangi basiru ya ratso
cikin duhun dajin yana tafiya yana hada hanya
kamar dan giya hannunsa na hagu a dafe
ahannunsa na dama yana kuka, sannan sai
kakkausar muryar mai kama data jaki ta sake
kecewa da dariya. Yaran suka fara waige
waigecikin firgici a tsorace sai dai kuma basu ga
mai dariyar ba, duk abin nan da akeyi, shi
Nuraddin ko ajikinsa, domin idan akwai wani
abuda ake kira tsoro a duniya shi baima sanshi
ba."yau ga shegantakar banza inba tsoro ba a fito
fili mana!" Nuraddin yace cikin karaji. Dajin ya
amsa kuwwar abin da yace.Cikin firgici, Nafi'u
Boss ya matso kusa daf da Nura ya dakeshi a
baya."Me...Menene kuma haka nura, so kake a
halaka mu a banza?" Yace bakinsa na
rawa.Nuraddin ya buge hannunsa gefe guda
sannan yayi sauri ya tari Basiru wanda ke tafe
yana tangadi kamar dan giya. Nuraddin na taba
shi sai basiru ya zube kasa yana kuka.

Aljani ya Taka Wuta!.....3
-
-
-
yana tangadi kamar dan giya. Nuraddin na taba
shi sai basiru ya zube kasa yana kuka, yamu
sashshen shanyayyen hannunsa ya fadi gefe guda
sharaf kamar mushen maciji.Wata sassanyar iska
ta fara busawatsakanin yara biyar gashi dai ba
lokacin sanyi bane amma iskar tafi iskar sanyi
sanyaya kashi da bargo. Nuraddin yaji gashin
jikinsa duk sun mimmike. Ko kusa ko alama,
dafarko Nuraddin bai tsorata da ihun da yaji ba,
to amma ba karamar girgiza yayi ba lokacin
dayaga hannun basiru ya tsotse ya yamushe
tamkar lawashin albasa a cikin rana. Ba karamin
bala'i bane ace 'yan mintoci kadan kuna tare
damutum kowa da hannayensa biyu, amma kuma
tsakanin wani dan lokaci ace hannunsa dayan ya
shanye ya zamama daya da rabi.Nuraddin ya
tallafi Basiru ya tashe shi tsaye sannan yace da
sauran kuzo mu tafi.Samarin suka bishi a baya
sumu-sumu ba magana. Fara tafiyar ke da wuya
sai karfin iskar yafara karuwa, saida takai ta
kawo samarin na tafiya da kyar sbd karfin iska.
Wannan al'amari shi yasa samari biyar din suka
dada rikicewa, tuni sun fara tunanin anya kuwa
zasu koma da hannunsu bibiyu? Kamar hadin
baki lokaci guda sai kowanne daga cikin yaran
banda Nuraddin goggoya hannayensu a bayansu
wai a tunaninsu yin hakan na iya kare
hannayensu daga shanyewa irin na Basiru. Abinda
yafi basu tsoro shineduk irin mahaukaciyar iskar
dake karkadasu tana wasa dasu kamar shanya
hakan baisa koda ganye daya daga cikin
ganyayen bishiyoyin dake wajen motsi ba. Hakan
shaya tabbatar musu cewa iskar sukadai take
kadawa a cikin dajin domin inhar basu kadai take
karkadawa ba yaya to ganyen bishiya baya
motsi?Adai dai lokacin samarin dake ratsawa ta
cikin iskar domin tsira daransu, sai kwatsam wani
abu ya bayyana a gabansu. Babu zato
babutsammani wani mai kamar bakin labule ya
ziraro gabansu. Saboda tsananin duhun dake
gurin idan suka juya baya basa hango bayansu.
Adai-dai lokacin ne kakkausar muryar ta sake
kecewa da dariya mai hargitsa hanjin cikin
mutum, awannan karon dariyar harda
kyakyatawa. Su Nuraddin sukayi tsumu suna
dube-dube ga iskar na kadawa amma gumi kamar
ruwa ake zuba musu a jiki, da zaka tsaga wani
acikinsu dazaiyi wuya ka sami jini ajikinsu
saboda firgici."kudaina waige-waige! Domin
kuwaduk wani waige-waigenku bazai iya hango
muku ni gaba dayana, sai daikuna iya ganin
tsakiyar kaina duhunda kuke gani a gabanku ba
duhu bane nice na tsare hanyar tsakiyar kaina
kuke gani haka bakin kirin".Kaukausar muryar tayi
shiru ga barin magana mummuna sannan sai taci
gaba da cewa. "daga yau saiyau, kada na kara
ganinku akan hanyar nan cikin dare, domin nan
hanyar mahaifina ce ba taku bace, in banda
rashin kunyarku ta bil'adama ina ku ina bin
hanyar sarkin sarakunan aljanun duniya. Zan
baku hanya ku wuce' sai dai kuma duk wanda ya
sake tunanin karan banin b tanan gurin to na
tabbatar masa cewa saina nannadeshi kamar
alkaki.Kamar budin ido kakkausar muryar nayin
shir duhu ya yaye iskar ta tsaya cak, sannan sai
dajin ya dawokamar yadda yake. Yaran suka dubi
juna jikinsu na diga kamar an narkasu sbd gumi.
In banda shanyayyen hannun Basiru da sai ka
rantse da Allah babu abinda ya faru.Yara ukun
suka dubi Nuraddin wanda ke rungume da basiru,
sannan kamar daman sun shawarcijuna sai suka
ruga da gudu suka nufi hanyar makaranta.Basiru
ya dubi yace yanzu kaima guduwa zakayi ka
barni?"Haba Basiru ah ko nawa hannun zata
shanye bazan gudu na barka ba. Bakomai Basiru
ka barni da ita zamu sake haduwane"."Tayaya
zaku hadu? Basiru ya tambaya har yanzu a
jingine yake ajikin Nuraddin."Bata ce kada
musake biyo hanyar nan ba, to wallahi ni banga
uban da ya isa ya hanani bita hanyar nan ba
tunda ba hanyar ubanta bace......Kafinya rufe
bakinsa, sai yaji muryar nan na cewa kayi a
hankali marar kunya idan baso kake na nanna
deka ba! Dajin.........Nuraddin ya dubi basiru
wanda tuni ya sume a jikinsa saboda tsoro. Don
haka sai ya sungumeshi kamardamin itace ya
dorashi a kafada ya kama hanyar makaranta
dashi. Yana tafiya shanyayyen hannun basiru na
dukan gadon bayansa. Fara tafiyar keda wuya sai
yaji mummunar muryar ta sake kecewa da dariya.
Daga nan kuma ba'a sakecewa dashi komai
ba."zaki yi dariya"! Nuraddin yace a fusace.
-
**** **** ****
Tun acikin daren da al'amarin ya faru labarin ya
iske duk kusan rabin makarantar, sannan kafin
tara na safiya ranar, labarin ya gama mamaye
cikin gari kamar wutar daji.Mutane sukai ta bada
labari iri-iri nagaskiya dana karya. A cewar wani
mai gadin makarantar wanda ke bada labari a
cikin gari, yace duk kusan yara biyar din
shanyayyen hannu suka shigo makarantar, kuma
wai kowannensu da ido daya yadawo, sannan
kuma ya dada da cewar wai duk agabansa aka
wuce da yara biyar din duk kuwa da
cewarrabonsa da gadin dare tun wancan satin da
ya wuce.A safiyar ranar aka tara daliban
makarantar gaba dayansu a gurin taron dalibai,
sannan malam mahmud malamin arabiya ya sake
yin nasiha gami da dada jan kunnen dalibai.

ALJANI YA TAKA WUTA 4.
Nuraddin ya yi mika, sanna ya yi wani
kwakkwaran fito ya dirgo daga kan gado, ya
dubi sauran gadajen da ke dakin babu kowa
akansu sai gado daya wanda Auwalu Surajo
ke kwance a kai yana karatu. Karfe tara da
rabi na dare, duk sauran daliban da ke
dakin sun tafi ajujuwan karatunsu domin
bitar abinda aka koya musu.
Nuraddin ya durkusa karkashin gadonsa ya
janyo akwatinsa, sannan ya bude ciki. A lafe
a kasan akwatin, kudi ne kusan naira dubu
biyar duk Badawiyya ce ta bashi kudin.
Nuraddin ya zaro naira dari daga cikin kudin
ya tura cikin aljihun gaban rigarsa. Sannan
ne to ya ji motsi a bayansa, ya yi firgigit
cikin sauri ya rufe jakarsa don gudun kada
wanda ke shigowa dakin ya ga kudin da ke
ciki. Duk da yake dai Nuraddin ya san babu
wani shege a cewarsa, da ya isa ya ta6a
kayansa ko da wasa ballantana da sunan
sata, amma ya san in an tambayeshi dole
ne shima ya bayar, tunda ana bashi,
wannan shi ya sa ba ya son a san yana a
kudi da yawa.
"Mene ne na 6oyewa, ai mu dama ganin
wannan falleliyar Bebinnan ta kawo ka cikin
arniyar motar nan mun san da karfinka ka
dira.
Nuraddin ya juyo domin ganin mai maganar,
duk da dai kafin ya juya ma ya san duk
duniya babu mai muryar nan sai wazirinsa
Nafiu (Boss).
"Shegen duniya daga ina haka, dakin karatu
ko makaranta?" Nuraddin ya ce, sannan ya
mika masa hannu suka tafa tas! Kamar an
mari jaki da faranti.
"Wacce irin makaranta kuma ban da wannan
da muke ciki?" Nafiu Boss ya tambaya
lokaci guda kuma ya zauna bakin gadon
Nuraddin.
"Ku dubu allonku daya nake nufi".
"Oh Shet! Men, ai abin da ya kawo ni ke
nan, an ce kuwa Fim din yau wani arnen
Indiya ne, ana fadamin labarin sai ka fado
min a rai, to ni sam-sam ban dauka ka
bayyana ba, to shi ne Hamza Siyasiya ya ce
min ai dazu ya ga bayyanarka kuma wai
wata ba kyau din Bebe ce ta kawoka, nan da
nan na garzayo, domin duk a aljihunka
zamu shiga sinimar nan, dan bai yiwuwa
Fim din nan ya wuce mu". Nafiu Boss ya
dan tsagaita yana mayar da numfashi.
"To uban shegen surutu ka gama tsarani
din?"
"Ah! Haba Nuri namu, kai ka san ai mu da
kai haka muke." Ya hada tafikan hannunsa
biyu guri guda.
"Wai ina su Basiru Logarizim ne?" Nuraddin
ya tambaya.
"Duk suna can bayan 'Central Hall' kai kawai
muke jira, yau kowa a aljihunka zai shiga
kallon fim, kai har sigari ma yau babu me
saya da kudinsa."
Cikin murmushi sai Nuraddin ya kama
hannun Nafiu Boss suka yi waje. Ko da suka
nufi kofar Hostel din, sai Nuraddin ya dubi
Nafiu ya ce. "Ah, yau zaka shigo da
mutuniyar taka ne?q
"Wa kenan?" Nafiu ya tambaya yana
kallonsa.
"Ladi dala-dala mana."
"Oh shege Nuri, ashe baka manta ba, kai ma
kasan ai dole ne na shigo da ita tunda ka
shigo gari."
Mintina biyar da yin hakan, sai samarin
biyar suka dunguma suka fice daga
makarantar zuwa cikin gari.
Wadannan samari biyar shedanun mutane
ne, domin Allah ne kawai Ya san iya yawan
daliban da suka dora akan hanyar banza.
Sunyi sanadiyar faduwar dalibai da dama
jarabawa, haka nan tun da suka shigo
makarantar ba su da aiki sai shiririta, yau
kusan shekararsu ta karshe a sakandiren. Da
yawa daga cikinsu suna zuwa makarantar ne
don kawaia ce sun gama, amma ba dan su
sami sakamako mai kyau ba.
Ba kowanne mutum ba ne, ba kuma
kowanne mai karfin zuciya bane zai iya
ratsa bakin kungurmin dajin da ke tsakanin
makarantar zuwa cikin gari ba, domin tafiyar
kusan kilomita biyar ne zuwa cikin gari, an
kuma ce wai hanyar cike take da aljanu da
kwankwamai, amma hakan bai ta6a tsorata
yaran ba, musamman Nuraddin, domin shi
ko da babu mai zuwa zai iya kama hanya
abinsa shi kadai, dole ne sai ya je. An yi
musu nasiha sun ki ji, an horesu da bulala
duk a banza, kai har wa'azai ma an yi musu.
Malam Mahmus Bashir malamin Arabiyya ne
a makarantar su Nuraddin ya ta6a cewa da
su wata rana suna daukar darasi.
"Ku yi a hankali,mun samu labarin akwai
wasu takadirai a cikinku wadanda kullum
kwanan diuniya sai sun shiga gari sun yi
kallo a sinima, to ina shawartarku da ku bari,
ba don komai ba kuma sai don lafiyarku,
kun sha fa jin labarin hadarin da ke tattare
da wannan dajin da irin kwankwamai da ke
ciki, amma don taurin kai ku nace sai kun
fita cikin dare. To wallahi ku yi a hankali in
ba so ku ke wata raba wani ya farka a
cikinku ya tsinci kansa da siririn hannu
shanyayye kamar lagwanin risho ba" Yaran
suka fashe da dariya.
To amma nasihar malam Mahmud Bashir
tamkar zuga ce ga takadiran yaran nan
biyar.
"Kai rabu da shi ajawo, mu zai yiwa wa'azi
da wani dogon gemunsa kamar burushin
wanke kwalabe"
Nuraddin ya ce da yaran, su kuma suka
bushe da dariya. Watanni biyar ke nan da
faruwar hakan.
BY NAZIR ADAM SALIH.

.............ALJANI YA TAKA WUTA CIGABAN
LABARI {5}.......
Nuraddin ya dubi basiru wanda tuni ya sume a
jikinsa saboda tsoro. Don haka sai ya sungumeshi
kamar damin itace ya dorashi a kafada ya kama
hanyar makaranta dashi. Yana tafiya shanyayyen
hannun basiru na dukan gadon bayansa. Fara
tafiyar keda wuya sai yaji mummunar muryar ta
sake kecewa da dariya. Daga nan kuma ba'a sake
cewa dashi komai ba.
"zaki yi dariya"! Nuraddin yace a fusace.
* * *
Tun acikin daren da al'amarin ya faru labarin ya
iske duk kusan rabin makarantar, sannan kafin
tara na safiya ranar, labarin ya gama mamaye
cikin gari kamar wutar daji.
Mutane sukai ta bada labari iri-iri na gaskiya
dana karya. A cewar wani mai gadin makarantar
wanda ke bada labari a cikin gari, yace duk kusan
yara biyar din shanyayyen hannu suka shigo
makarantar, kuma wai kowannensu da ido daya
yadawo, sannan kuma ya dada da cewar wai duk
agabansa aka wuce da yara biyar din duk kuwa
da cewar rabonsa da gadin dare tun wancan
satin da ya wuce.
A safiyar ranar aka tara daliban makarantar gaba
dayansu a gurin taron dalibai, sannan malam
mahmud malamin arabiya ya sake yin nasiha
gami da dada jan kunnen dalibai akan fita daga
cikin makarantar.
"ku guji fita yawace-yawacen banza marasa
amfani cikin dare, kuyi zamanku a makaranta ku
karanta littattafan ku yafi muku. Na tabbata indai
dalibi ba fita yayi ba to Allah subhanahu wata'ala
bazai baiwa kowanne aljani ikon cutar daku ba,
"wasu daga cikin dalibai sukayi kabbara. Lokacin
da malam mahamud yazo karshen jawabinsa.
Daga karshe aka yiwa su Nuraddin horo mai
tsanani, sannan aka basu gargadi na karshe
wanda daga shi idan suka sake laifi to korarsu
za'ayi.
"kai! Rabu dasu, wa zasu yiwa wa'azi"! Nuraddin
yace da Nafi'u (BOSS) lokacin da suke kan
hanyar ajujuwan karatunsu bayan an sallamesu
daga gurin asambili.
"Ni dai nasan wannan mai muryar jakin bata isa
ta hanani fita kallon film din yau ba don wallahi
canis za,a yi da 'American film' ballen kuma
wa'azin wani mai dogon gemu, 'yar bulalarshi
ashirin! Sufa sun dauka wai duka zai hanamu
abinda mukeyi ko? Nuraddin ya tambaya yana
duban abokinsa Nafi'u.
Nafi'u yayi masa irin kallon dazaka yiwa
kyankyason daya fada a cikin furaraka yace.
"kanka daya kuwa Nura"?
"to in ba daya bane ina na baro dayan ko kai da
kai biyu kake ganina? Nuradadin yace yana jijjiga
littafin dake hannunsa a dai-dai lokacin da suka
karaso kusa da ofishin shugaban makarantar.
"To inba haka ba mezai sa da hankalinka da
komai ka kai kanka ga halaka, aini wallahi ko
karatu dare na daina fita, haka kawai naje nima
hannuna ya yamushe tab! Ai idan ka ganni a
lahira to kaini akai bada kafata naje ba.
Nuraddin ya dubeshi ya fashe da dariya. "wallahi
bansan kai mugun matsoraci bane sai yau, yanzu
kai da haka kake da tsoro har ake kiranka da
Boss, to in dai hakane daga yau bani ba kai
domin bana abota da matsoraci".
"Wallahi tafi nono fari". Nafi'u yace. "Domin idan
mutum ya biye ta kai sai ya tsinci kansa a
kushewa kwanansa bai kareba.
"Ai me rabon ganin badi sai ya gani ko ana ruwan
kibiya daga sama da kasa.
Nafi'u ya girgiza kai kana ya dubi nuraddin dai
dai lokacin da suka kawo kofar ajin. "Kana nufin
yauma fita zakayi kenan"?
"Ai idan kaji fita daya kenan ma, kai dai tsaya
nan kana shirme, haka kawai ka bari wasu
kananan kwankwamai da muryar jaki su mayar
dakai laushi, ka jirani na dawo na baka labari".
Nuraddin ya juya abinsa zai yi gaba.
Nafi'u ya sa hannu ya rike rigarsa ta baya.
"Nura kaga fa wallahi........"
Bai karasa ba Nuraddin ya tankwabe hannunsa
yana zazzare idanu. "Kada ka bata bakinka Nafi'u
domin banga dalilin dazaisa ta shanyewa dan
uwanmu hannu ba mu kyaleta tunda tace kada
mu sake bi ta hanyar, to ni yau saina bi na
tambayeta dalilin shanewa dan uwanmu hannu."
yayi shiru sannan batare da ya dubi Nafi'u ba wai
kai Nafi'u (BOSS), to in gaskiya ne yau ka biyoni
muga iyakacin taurin kanka". Nuraddin ya wuce
cikin ajinsu ya bar Nafi'u nan tsaye yana kirga
takun sawunsa.
"Mahaukaci ne, tabbas mahauka cine. Babu
mamaki abinda ya faru jiya ya tabashi". Nafi'u
yace da kansa.
Nuraddain ya shiga ajin Nafi'u na
DOWNLOAD
DOWNLOAD
Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment