Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

ο»ΏBUDURWAR ZUCIYA 2020
Na Shamsiyya Adam
Bismillahir Rahmanr Rahim
Allah kamana dakyau don Annabi s a w

BUDURWAR ZUCIYA
Awani gari mai suna kainuwa. Garine maikyawun gine gine da ababan more rayuwa daban daban kasancewar garin cike yake da tarin attajirai damanya manyan 'yan kasuwa da masu aikin govnati. Akwai anguwar talakawa babbar anguwa anfikiran unguwar dasuna fukara'u
Munadaya daga cikin masu xaman anguwar fukara'u
Sunana Ismat 'ya ga malm musa da mama kareema inashekara 13 mahaifinmu yarasu lokacin kanina Ayman nashekara 8,bakaramin girgixamu rasuwar mahaifin namu tayi ba kasancewar ko lokacin dayake raye acikin talauci muke domin dakyar yake iyasamomana abin da xamu ci koda kwa sau 2ne arana, gashi yanxu yatafi yabarmu waxaibamu ga kawu bala baya taimakon su tundaran babanmu duk da kasancewar kawu bala daya daga cikin masu kudin garin. Amma baruwan sa damu yanxu shekarar Ismat 15,ayman kuma goma.

πŸ’šπŸ’šπŸ’šπŸ’šπŸ’šπŸ’šπŸ’šπŸ’š
Xaune take tana sawuta ga murhun dake gabanta, wanda ke dauke da tukunya 'yar madaidaiciya akai, tukunyar bayanta yayi baki sosai kuma ta tsufa dayawa daganesa ma bakace xata iya dafa wani abuba sbd lalacewa.
Wani kyakkyawan farin yaro nagani yafito daga wani daki dake ta bayan budurwar yanufo wajenta hannunsa dauke da tiren roba yakara so
Anty Ismat yunwa nakeji cikina sai ciwo yake tamkar xai fuje
Dago kai tayi idanunta jaxur sbd hayaki dayagama bule mata ido wasu siraran hawaye ne suka xubo daga idaniyarta
Karka damu Ayman ka kara hakuri ainakusa gamawa danagama xakaci kaji
Hannu yakai xaibude tukunyar sabd bayajin gaskiya tafadamasa
Tarike hannunsa sbd tasan bakomai aciki face ruwa kawai data xuba take ta dafawa mamansu tunsafe tafita don tanemo musu abindaxa aci kuma balallai tasamo ba tayi hakane sbd takwantarwa da Ayman hankli yaxata ko abinci take dafawa
Jikinta yafada yana sakin wani marayan kuka
Wai anty wannan wanne irin abincine tin la'asar akedafa shi baidafu ba har mangaruba, dan Allah anty kifada mun inbabune wlh yunwa tamkar takashe ni
Fashewa tayi dakuka mai karfi tana rumgumesa ajikinta sosai
Inna nillahi wa inna ilaihir raji un Allah kayanke mana wannan igiyar wahala tatalauchi don manxon Allah s a w. Ayman bakoma acikin tukunyar nan face ruwa sbd shine kadai ayanxu muke dashi Allah ya axirtamu. Yau donhaka Allahamdulillah Allah shine abin godiya abisa diikkan abin dayaxar tar
Hakane anty yanxu ruwan xamu sha
Eh saimu kukkurba daxafi xafi kamar shayi kaga xamuji dama dama, kuma kaga inna tafita tin axahar neman mana abinci ataskar Ubangiji kuma in sha Allahu baxamu rasaba,
Daukomana kofina maxa
Dagudu yaruga yadauko musu adaki taxuba masa itama taxuba suna fifitawa suna sha Ayman yakalleta
Anty wai menene yasa kawu bala baxai taimakemuba yakaimu gidansa
Rike baki tayi tana cewa
Kaiitab lallaima yakaimu gidansa fa kace, hum um baxai iyaba tunda kaga kyamatar mu sukeyi su duka 'yan uwan abban mu, kuma bansan nima meyasa ba amma bari mama tadawo saina tambayeta,
Sallama tayi tashigo dafara arta saibakar leda dake hannunta babba, dagudu Ayman da Ismat suka ruga gareta dukkansu tahada ta rumgume tana farincikin samunsu datai cikin koshin lfy
Oyoyo maman mu
Ayman yafada yanakara kankameta tamkar wani xai kwace masa ita
Allah sarki Ayman dina har yanxu bakuci komai ba ko Ismat?
munsha ruwan dumi mama ai
Ismat ta ce tana amsar ledar hannunta tare dayimata sannu daxuwa cikin nutsuwarta dakuma yanayin tausayawa ga maman nasu
Ismat kuyi hakuri dan Allah nafita nabarku bakuci komai ba kingani ma tindana fita nakefaman neman taimako nako nera 100,ne nasiyo mana ko kwaki ne madanjika musha damuxauna haka amma hakan sam baisamuba sai gabda mangarubar nan nasamu wani bawan Allah yabani sadakar dari 500shima kaya naga yadauko su aboot in motarsa data lalace masa abakin titi xaishiga unguwar tasu natafi dasauri natare sa ina kama kayana nace
Dako ne yace aa nace dan Allah yataimaka min nadaukar masa nakai masa indaxashi yadan bani lada ko kadanne dan Allah damamaki afuskarsa nagani ina mace kuma ina neman dako yagirgixa kai yana bani nadauka nabisa abaya harkofar gidansa sannan na aje yamiko min dari biyar nai godiya yace miyasa nake dako nace marayu ne dani navarsu kuma tinsafe basu ci komai ba yatausayama na yakuma nemi kwatancena akan xairinka aiko manada sadaka insha Allah naigodiya nataho abakin layi natsaya kantin inuwa nasiyo mana kwaki rabi da mai na 50,ragowar chanjin nasiyo mana taliya 'yar awo kwata
Mungode sosai mama Allah yasakawa wannan mutumi da alkhairi mafifici
Cewar Ismat tana sakin murmushi
Mayafinta mama ta cire tana cewa
Amin bari nawanke mana kwakin sai akwadanta yanxu aci
Aa mamanmu kawo kiga ninakwadanta baxai yuwuba kidawo yanxu daga wannan tafiyan akafaba kuma sannan kixo kina wahalar aiki aibanwa kaina da kuruciyata adalciba
Mama tai murmushi
Allah sarki ismat Allah yamiki albarka don albarkar ANNABI s a w. Bakomai hakkinkune akaina amma tunda kindage shikennan dauki kije saiki deba mana wanda xai ishemu yanxu ki aje sauran saikuma gobe
πŸ’š
Bayan kwana biyar alhaji sanam yayo musu aike da shinkafa kwano da jakar maggi sai500 sunji dadi sosai don haka mama bayan sallar mangaruba taje gidansa domin tayimasa godiya maigadi ne yace mata yana ciki tashiga sallama tayi kofar falon ya amsa tare da yi mata ixinin shigowa
Akasan falon taxube suka gaisa sai lokacin yakalle sosai data dukar dakai kasa yaga kyanta wanda yadauki hankalinsa mama dama ba tsohuwa bace macace kykkyawa wacce wacce baxata wuce shekara 33, doguwa maikira. Dayawa alhaxawan kainuwa nakawo mata hari amma tanaki sbda ba abin duniya take nema ba aa mutumcin yaranta dakuma tsoron matansu sbda batasan yasuke ba bataso kuma yaranta su samu tsamgwama ko kyara awajen kishiya shiyasa mataki aure ta gwammace taitaxama dasu ahaka suna nema ataskar Ubangiji maigirma
Dadama kuma wasu iskanci suke nemanta dashi ba aure ba, amma bata da ra ayin bakar rayuwa irinta.
Jin shurun yayi yawa yasa tadago kai daga dukar dashi datayi tana mikewa tsaye
Toh Alhaji ni xankoma mungode Allah yasaka da alkhairi ainaso ma nasamu maidakin naka mugaisa naigodiya
Yayi murmushi tare dakara kafeta da idanunsa masu daukar hankali
Uhum har xaki tafi dakin xauna nakawo miki ruwa ai andan kara gaisawa ko?
Ai nabaro yara shiyasa kumadama cewa nai bari naxo muyi godiya da aike mungani mungode mungode
Da amin ya amsa tanajuya baya yabita da kallo tare da lashe dikkan labbansa yana saki murmushi mai cike da ma anoni daban daban wadanda shikadai yabarwa kansa sani.
πŸ’šRanar alhamis bayan la asar yaje gidan yana xaune amotarsa saiga Ayman yafito yana gara gare gare bude murfin motar yayi yana kiransa dasauri yaxo yana gaidashi
Mamanka na nan
Ayman yadaga kai
Eh tana nan yanxu tadawo daga gidan wanki
Tohm jeka kace mata tayi bako alhaji sanam
Aikuwa dagudu Ayman yakoma yana samunta xaune kan karamar kujerar cikin gida tana yiwa Ismat kitso ita kuma banda rakin xafi xafi ba'abin datake, sabda batason kitso maman ce ke tilas tamata xama ayimata amma don ta ita ne sai kanta yayi wata biyar ba kitso, adankare don kuwa ko taxar arxiki baya samu daga gareta balle kitso, kuma gashi Ismat irin matannanne masu cukowar gashi mai roba marar tsayi sai uban yawa su tsefe yayi musu ham aka
Maman mu waikinyi bako alhaji sanam
Ayman kenan ya ida maganar sa yana karasowa gabansu
Kareema ta kallesu tana mamaki Alhaji sanam kuma mai basu taimako shine kuma yaxo gidanta tohm lfy kuwa Allah yasa dai lafiya
Ismat tace
Maman mu kamar fa sunan alhajin dayake aikomana da shinkafa da kudi ne
Shine nima ai mamakin danake dakuma naji shine dakansa Allah yasa lfy
Mama lfy mana kidaina tsoro dan Allah kikasani ko wani taimakon ne yakawo mana dakansa amatsayin mu na mabukata xai tunanin ko abincin mu yakare yanxu bamu dana sawa abakin salati
Mama taja wana dogon numfashi tana jan hijabinta dake jikin kauren kofar dakin ta tana sawa
Tohm Allah yasa bari naje saikixo soro kimasa shinfida kikawo ruwa
Tom mama
Tafice tana tunanin irin kallon dataga yanayimata ranar dataje gidansa yimasa godiya baison tagansa ba da alama akwai manufarsa akanta amma Allah xaimata tsari dashi
Takarasa inda yake jikin motarsa tare dayanke tunanin datake
Daddana waya yake sallamar tace ta katse masa game din dayake bugawa mai dadi ya amsa sallamar tare dasakar mata murmushi kasa tayi dakanta
"Lfy klau ya yara kuma?
Lfynsu klau alhaji ya office
Allahamdulillah
To madalla Allah yadada arxiki da girma
Amin malama
Yafada yana kara fadada murmushin sa dake kwance afuskarsa tundaya daga kai yayi toxali da kyakkyawar fuskar dayake marari,
Shuru ne yaratsa tsakaninsu kafin tace
Alhaji kashigo daga ciki
Yayi dariya har saida jerarrun hakwaransa suka fito reras farare tas dasu tamkar baitauna abinci dasu . Sbda abinda yake nema kenan maganar xatafi idan aka samu aka xauna anutse don haka tana yin gaba yabita abaya asoro tasamu Ismat tayi shinfidar kuma ta aje ruwa fiyawater leda biyu data aika Ayman yasiyo bayan mama tafita wajen alhajin.
Bakaramin birgesa kunyar mama take ba sambata iya hada idanu dashi koda yaushe kanta nakasa
Ya sunan malamar ne?
Tai murmushi cikin kunya batare data dago kaiba ta bashi ansa
Ni sunana kareema amma yarana sunakirana mama
Yasaki murmushi
Yayi kyau kareema nikuma dama kinsan sunana alhaji sanam mai atamfa toh agaskiya dai ni nagani ina kuma so nanu na yabawata akai, sbda yadda hankalina yakwanta da abindana gani din saidai bansaniba ko malamar akwai wani aciki koma anrigani, don daganinki hakan nan baxakirasa kyakkyawan tayi ba.
Yakai maganar yana kallon fuskarta yaga awanne yanayi ta fuskanci maganar sa tare da jiran amsarta,
Uhum tace tana satar kallonsa
"Badan karna xake ba dana tambayi wani abu Alhaji
Aa babu komai wllahi tambayi ko menene insha Allahu xanbaki amsa,
Tohm alhaji ni aganina wanne abune yamin saura ayanxu babu komi agabana daya wuce yarana danatake fatan Allah yaraya minsu abisa tafarki dan Allah alhaji sanam kayi hakuri ni yanxu babu wannan acikin rayuwata
Saidaya bari tagama maganar tukunna yaciga ba datasa,
Haba kareema wannan ai ba girmanki bane kwata kwata kidubeki fa shekarar ki nawa aduniya daxaki ce baxakiyi aureba sbda yara yaran naki har nawane? Toh ko sunkai goma duk kitaho min dasu gidana nixan iya daukar miki nauyinsu dadik dawainiyarsu, mutkar xaki aure ni ke nake so kareema kigane kuma komai na rayuwa baxaki rasa shi ba agurina indai kina bukata inasonki lokaci daya naji sonki yashiga jikina kitaimaka min.
Shuru tayi tana naxarin wani abu acikin ranta balaifi alhaji sanam mutum ne kyakkyawa bayan haka kuma batsoho bane don koxai girmeta baifi da shekara shida ba gatausayi da kyauta yanason talaka dakokarin taimakonsa, yanada kirki total dinsa bata ga makusar saba, amma batajin xata aminta da auren sa sbda batasan halin matarsa ba itakuma batasan tashin hankli ko kadan ko wani abu daxai takuri yaranta,
Kareema tunanin mekike yi?
Takallesa dasauri tana janye idanunta daga kansa,
Bakomai alhaji
Aa dakomai mana tunda gashi kinyi shuru kodai bakya sona kareema?
Ta girgixa kai alamun aa
Toh kodan bakisan wanene niba shiyasa kika kasa sakin jiki dani tohm bari nabaki tarihina
Bayan sunana dakikaji nidai abaya nataba yin aure dawata banufiya 'yar Lagos, sunan ta jamila shekarar mu shida da aure amma jamila ko batan wata bata taba yiba dik nabi nadamu nashiga tashin hankli sbda alokacin ina masifar son naga yarana ita kuwa sainaga daga gareta ko ajikinta ko kadan bata damu ba idanma na tuntubeta da muje hospital adubamu saitaki ta danne maganar har na hakura nasaki jamila 'yar boko ce akwai son kyale kyalen duniya da gayu dason kwalliya kwata kwata nafuskanceta ita batason haihuwa sbda wai yara xsu rinka sata magana kuma idanma tahaihu yanxu ai tsofa xatayi shikennan itakuma taxama chos,naimata nasiha naimata nasiha amma saita watsar sbda tayi nisa da duniya. Watarana ciwon ciki yatirniketa me tsanani kafin nayi wani yunkurin kai ta hospital jini yafara xuba daga kasanta nagigice nadauketa akidime nayi hospital daxuwanmu kuwa aka shigar da ita emagancy lokitoci sika rufa dubata cikin ikon Ubangiji kuwa jinin yatsaya ciwon yasauka ta farfado harxatamu tafi likita yaban sakamako tare damin bayani akan karnakuma bari tasha kwayar xubda ciki inva hakaba xata iya rasa ranta nan gaba asilar hakan nakallesa akai kaice yafadamin cewa eh wannan shine xubar war ta daciki na biyar kenan
Afasace najuya nadauketa da mari natafi raina abace tamkar xuciyata xatafito sbd jin irin mummunar aika aikar da jamila takemin akan abinda tasan shine mafi soyuwa agareni amma take xubdamin yabi rarayi naimata Allah ya isa yafi a kirga daga bisani nasaketa, wannan shine yasaka min tsoron mata har nakyale sauraron su nahakura da auren na tsawon shekara biyu sai yanxu da Allah yayimin katar dake gashi kema batabbas din xaki amince dani
Yabata tausayi sosai tana jin amincewa dashi har cikin ranta amma dole saitayi shawara da Ismat kafin tafada masa ta amince, sbda sai Ismat taga xasu iya tukunna sbd kar yanxu ta amince Ismat tace aa dalili kuwa shine Ismat batason shiga rayuwar masu kudi sbad gudun wulakanci shiyasa ko kawa bata da ita da maman su kawai take shawara abokin wasanta kuma Ayman.
Shikennan nixan koma naga naxo natsareki sai tunani kike tafiya
Tai murmushi
Labarinka alhaji yadan firgitani gwanin tausayi dama ashe akwai irin wadannan matan har yanxu Allah yakyauta sannan inaso kabani lokaci xan shawara da 'yata dik abinda muka yanke xakaji
Yayi dariya cike da farinciki ganin yadau hanyar nasara,
Tohm kamar yaushe ne xandawo danjin amsata kareema?
Kamar nan da kwana hudu ma
Kai kareema sunyi min yawa da tsaho sbda kinga banason abin yadau lokaci daxafi daxafi fa kinsan ake dukan karfe
Suka yi dariya atare
Tohm shikennan saikaxo duk lokacin dakake da dama
Haka kikace tohm shikennan gobe kwa xandawo
Takallesa dasauri tana xaro ido.
Taimasa kyau ahakan yadaga mata gira taikasa da fuskarta tana murmushi alhajin nan dan duniya ne tace acikin xuciyarta,
Rafas'yan dari bibbiyu yadauko guda biyu yana aje mata tana yabarsu amma bai saurareta ba yawuce tare da cusa hannayensa duka a aljihu
Kodata koma cikin gida xama tayi jagwab kasan dakin tana sakin kudaden hannunta akasa Ismat dake kokarin dora musu sanwar girkin dare tataho wajenta hankalinta amutikar tashe sbda taga aydda mama tashigo batason taga mamansu atashin hankali ko kadan
Maman mu lafiya kuwa kindawo kuma awannan halin mai alhajin yafada miki? Kudin waye wadannan?
Har yanxu kallonta mama kawai take kafin tasaki wani gwauron numfashi tana kwasar kudin
Wadannan kudin alhaji ne yabamu sannan kuma wani sabon xance Ismat tayani gani wai alhaji sanam yana sona aure na yakesonyi shine abinda yasakani atunani yanxu
Murmushi Ismat tayi tana rike hannun mama fuskarta cike da murna
Laaa wlh ni mama aganina babu wani abun damuwa Allah ne yaduba halin damuke ciki yaturo mana alhaji sanam rayuwar mu sbda musamu sassauchi kiyi addu ah kawai maman mu akan Allah yaxaba abin dayafi alkhairi
Amin shikennan tunda kince haka amma yace nanda kwana biyu xaidawo yaji amsar tawa
Ismat tai dariya ganin yadda jikin mamn tasu yayi sanyi
Bakomai mama saiki ce masa kin amince Allah yayimana jagora cikin lamarin
Amin Ismat kinada hankali sosai Allah yayi miki albarka
Amin maman mu
Yanxu cikin kudin nan irgi dubu biyu kije bakin titi kisayo mana danyan nama sai muyi miya kidauki dubu kisayo doya sai ai sakwara
Tohm mama ai yanxu kuwa xantafi dama anjima rabona danaci sakwara
Sukayi dariya Ayman kuwa yanacan waje wasa gurin yara,
πŸ’š
Kwana biyu kuwa cif ran lahdi saiyaxo bayan angaisa yatambayi ya maganarsu tace ta amince bakaramin dadi yaji ba kwana uku atsakani yaturo manyansa akayi magana da kanin baban mama dake xaune arigar shehu sati biyu aka daura auren ta da alhaji sanam tatare agidansa maicike da kayan more rayuwa domin wani abin ma bata taba ganinsa ba a duniyar ta, dakin Ismat acikin falon yake ba awani bangare yake daban daga shi sai dakin 'yar aikin gidan. Sbda Alhaji amarci ake so ayi mai rai da motsi.
Bayan wata shida dayin auren Alhaji yashaku da Ismat sosai fiye datunanin mai karatu domin kuwa abinsai kungani yadda yake ji da ita tare da kulawa maikyau tamkar shine mahaifin ta na asali
Kamar kullum yauma xaune suke afalo ana breakafast wanda yar aikin gidan ce tayi maisuna mardiyya, sbda Alhaji yace bai yarda mama tayi aiki ba bayadda batayi badashi yabar ta tasamu ladan hakan amma yaki yarda dole ta hakura ta kyale amma tare da Ismat da mardiyyan suke yin aikin.
Ismat ce tashigo cikin falon jikinta sanye da unuform din makarantar da daddy yasakasu ita da ayman duk da kowa tashi daban amma duk ta kudi ce,
Bayanta goye dajaka maikyau dakyalli kana kallon jakar kasan sai 'ya'yan gata ke iya samunta
Daddy gudmornng!
Hannunta yarike yana jawo mata kujera itama taxauna
Mornng my dota anshirya school din ne?
Kai tadaga tana fara hadawa kanta tea sbda tafara jin yunwa na mintsilinta,
Eh daddy maman mu antashi lfy?
Lfy klau Ismat yakika tashi
Allahamdulillahi mama
Takai maganar tana kallon daddy takalli mama kafin tamaida kallonta duka kan Ayman tace
Aa daddy yanaga Ayman bai shirya ba ko yau batare xaka kaimu ba
Yana sauke cop din tean dayagama sha yamike domin shiga ciki shima yashirya office
Toh nima dai hakana gansa tanbayi mamansa yar daddy kinsanfa kece tawaje na koke dayane xan iya kaiki inwuce office dina shi dirver yakaisa
Mama ta hararesu su duka aikwa suka kyalkyale da dariya
Ayman ya tura baki gaba yana kwantawa jikin mama xai kuka
Alhaji bana son sonkai fa dan autan nawa ake nunawa wariya shikennan ai taraku muke yau bayajin dadi sosai kabiya ta school din tasu kaba malaman nasu uxiri kar autana yakoma gobe su dakar min shi,
Ayya Allah yasauke shikennan meyake damunsa
Daddy yace yana matsawa tare da taba goshinsa
Kamar xaxxabine
Eh nima naji kansa ma daxafi kikai sa hospital bayan munfita Allah yabasa lfy
Amin alhaji kokaifa kaga ai naji dadi
Sukai dariya yakalli Ismat
Dota kisauri kiyi breakfast yanxu xanfito karki lt
Umhum tace tana maida hankali wajen cin wainar kwan dake gabanta da hadadden ruwan tea wanda yasha madara da milo don Ismat badaganan ba wajen ci takoshi ba wasa itakam xataci abinci harsai ta koshi shiyasa kuwa gatanan lukui lukui 'yar duma duma
Mama ce ta mike tana kwantar da Ayman kan kujera dayafara bacci tabi bayan daddy sbda ta taimaka masa ya shirya kamar yadda kullum tasaba tana shirya sa tsaf ko ta taimaka masa yashirya.
Yayi kyau tamkar wani matashin saurayi haka daddy yake koma idan yabuga wanka tana ganin futowarsa tare da mama tamike dayake dama takammala shitake jira
Woow daddy na kullum sabo wallahi
Yayi dariya tare da rike hannunta
Muje dota mai daddy sabo
Mama tai dariya
Ai indai Ismat ce akwai surutu duk da maganar ta tayau akwai kamshin gaskiya acikinta
Yakalli maman yana sakin wani asirtaccen murmushi mai narkar da xuciyar wanda yafahimci dan soyayya akayi
Karki dai kice komai domin kinfi ni duk wani qalitis nakyau dota kuma duk tafimu lafiya
Dariya sukayi suduka Ismat tatirje tana cewa
Sbda kaga nice 'yar lukuta ko daddy shikenan nima nadaina cin abinci dayawa
Sukayi dariya mama data rakosu bakin mata tajuya tana girgixa kai cike da farincikin chanjin rayuwa dasuka samu
Daddy nakaunar Ismat sosai har aransa yakejin baxai iya bada ita ga kowanne namiji ba matsayin mata sbda tsananin sondayake mata shikansa wani xubin idan yaxauna yana tunaninta da tunanin yadda take aciken nan bulbul saiya ji bakidaya hankalinsa yatashi watarana saiya koma gida darana wajen mama idan yasamu nutsuwa yadawo duk da idan yana tare da mama saiya rinka hakaito Ismat aransa dandanan kwa kuxarinsa yake karuwa yake samun kansa afarinciki mara musaltuwa,
Mama tana jindadin yadda daddy kaunar yaranta don haka yake karajin dadin xama dashi dakara sakewa dashi sannan kuma kullum kara kyautata masa take sbd ganin yadda yake kulawa da Ismat sunshaku sosai
Game da ismat ma shakuwar datayi da daddy komai fadamasa take duk labarin dasukayi dakawarta saita basa labari inta dawo
Yaukam amakaranta antashesu break sunfito gaban makarantar itada wata kawarta hussaina siyan milo wani saurayi yayi mata magana taki kulasa tatafi sai hussaina ce ta tsaya tabasa numban Ismat din ta kuma fadamasa sunanta yaji dadi yakuma godemata harda yimata kyautar 5k, daga ni dan manya ne cewar hussaina tana biyo bayan Ismat class.
Daddy ne yaxo daukarta tana shiga yarike mata hannu yafara tuki da hannu daya bakaramin dadi hakan yake masa ba yanajin dimin hannun Ismat sosai acikin nasa,
Takallesa fuskarta dauke da dariya
Daddy na yau nayi saurayi akofar makarantar mu kum..............
Mugun birkin daya jane yatsoratata dasauri ta hadiye sauran maganar sbd yanxu tagane tayi kato barar fadama daddy wannan xancan daba tabbas sbda bata saurari saurayin bama amma take dorarwa kuma daddy yana mata fada akan karta rinka kula samari sbda yanafadamata baruwanta da samari ita yarinya ce yanxu shikenan tadabawa kanta wuka
Kallonsa tai
Daddy dan Allah k.............
Wani mugun kallo yake jifanta dashi mai tsoratar wa fuskarsa dauke da bacin rai idaninsa dandanan suka sauya kala hannunta dake cikin nasa yamatse dakarfi tarintse idanunta jikinta narawa ko ina bashiri hawaye suka fara xubowa daga idaninta
Wayyo hannu na daddy xafi
Sakin hannun yayi yafara magana cikin bacin rai da wani tukuki daya ji yana taso masa daga kasan makoshi yana yo masa sama tamkar yafashe yakeji.fuskarsa kuwa kishinta ne axahiri yabayyana saidai rashin wayo dayake damun Ismat yasa bata fahimta
Dawa kukayi shawarar xaki fara kula samari dota eyyeee?
Ta tsorota sosai tadiririce domin
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment