Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da suka
faru tsakaninta da dr shuraim da kuma
mataki na hudu da abida ta karanto mata.
Barr muazzam ya dubi aisha farida cike da
rashin fahimta yace to ni kamar ni ta yaya
zan yi mata biyayya? Kuma kamar baraka
wacce tayi biyayyar a baya bata ci riba ba,
sai da ta share shi ta fara samun saukin
wulakancin? Aisha farida tace ai a ganina
duk daya ne mu ukun. Yanzu kamar baraka
taci gaba dayi masa haka har lokacin da zai
karkato sosai, yana son zaman nata sai ta
dawo tayi masa biyayya sosai, tayi duk abin
da yake so, ta bar abinda baya so, ta nan
zai fara mantawa da nafisa. Ko kuma zai
fara kokonto ko ya rike matarsa ne, ya rabu
da waccan don na tabbata ba zatayi masa
biyayyar da baraka take yi masa ba. Saboda
wadannan dalilan nawa na farko kace babba
ce har ta dade da gama jam'ia. Na biyu
tasan yana sonta don haka zatayi ta jansa a
kasa kasan halin mata. Barr muazzam ya
gyada kai yace lallai kanwata na yadda da
tunaninki, kamar kina zaune a wajen duk
yadda kika fada haka ne. Aisha farida tayi
dariya tace kai kuma a bangarenka kaci
gaba da nuna mata ka sami wata bata
gabanka yanzu. Kada ka bari alakarku ta
rabe, ku cigaba da yawan haduwa ko bayan
ta dawo gidan a matsayin abokinta zaka ga
ta dawo. Kada ka fada mata da wasa kake
da wuri, kayi ta kyautata mata, kanayi mata
duk lallashi da tarairaya. Kayi ta yin duk
abin da kasan tana so, ka kiyaye wanda ba
taso tabbas zataji kai kafi dacewa da
rayuwarta, ko bata zo tace tana sonka ba,
zata nuna alamu. Barr ya gyada kai yayi
murmushi yace gaskiya ne wannan kinyi
hikima, Allah Ya sa mu dace. Bani lambarki
don muci gaba da tattaunawa a waya. Ya
zaro wayarsa daga aljihun, aisha farida tana
karanto masa lambar yana rubutawa har
suka cika. Sannan ya kira lambar ta shiga,
amma wayar tana gida. Aisha farida tace
idan na shiga ciki zanyi saving. Barr
muazzam ya zaro kudi daga aljihu, naira
dubu biyu ne 'yan dubu dubu guda biyu, ya
mika mata nan fa ake tataburzar, don aisha
farida ta tubure ba zata karba ba, shi
kumwa yace sai ta karba. Ko zubarwa zatayi
sai dai ta zubar. Sai da ta ga ya dage sosai
har ransa zai baci sannan ta durkusa ta
karba, tayi masa godiya suka yi sallama ya
tafi, tashiga gida cike da farin ciki kamar
kuwa yasan suna cikin tashin hankalin
rashin kudi, asibiti duk ya cinye musu
kudin. Cefane ma sai harhade harhade ake
yi, a dafa a ci ba dadi don kar a mutu.
Ciwon abida kamar da wasa, abu ya fara
tsananta hankalin kowa ya fara tashi, don
har hussaini yayi waya ya sanarwa da
iyayenta da 'yanuwansu na shagamu.
Babban likitoci yanzu take gani a asibitin
kashi, don ciwon ya wuce kananan likitoci.
Magani take dirka amma fa a banza, ko
alamun canji bata ji a jikinta. Daga nan sai
suka rabu da zuwa asibitin kashin ma, suka
dawo gida aka fara na hausa, wannan yace
sanyin kashi ne, waccan tace mayu ne.
Kowanne magani hussaini yaji sai ya karbo
ya kawo, burinsa matarsa ta sami lafiya.
Abinka da mai ilimi aisha farida bata son
wannan gwafje gwafejen magungunan
gargajiyar ko hussaini ya kawo ya bata, sai
ta boye bata bari tasha. Gara ma na
shafawa a gabobi tana shafa mata kamar na
sanyin kashi da aka karbo musu a wajen
sarkin ruwa na wudil. Maganin sanyi kashi
ne da man shanu ake kwabawa a shafa a
gababin. Sai man tafarnuwa dashi ma akace
ta dinga shafa mata a gabobi shima tana
shafa mata kullum da daddare kafin su
kwanta.
DUK KYAN TAKALMI 2* 11
Babu abinda abida ke iya yi, sai anyi mata
tana kwance kawai. Amma tana magana
radau kuma idan an bata abinci tana ci
sosai. Sai tsananin sanyin da take ji, sai tayi
ta makerketa duk da bargunan da aka lufga
mata, kuma a lokacin zafi ne. Ba asiha
farida da hussaini da 'ya'yan abida ba kadai,
duk wani mahalukin da yake da dison imani
a cuciyarsa hankalinsa sai ya tashi idan yaga
ciwon nan kuma ya tausaya mata. 'Yan
dubiya basa karewa layi layi mata suna
shiga, wasu na fitowa. Sai yanzu 'yan gida
da 'yan unguwa suke zayyano kyawawan
halayen abida. Idan akace yau asabar da
lahadi ce lokacin yaya hussaini yana gida
baije aiki ba, to mazan unguwa da abokan
aikinsa sai suyi ta tururuwar zuwa dubiya.
Kuma yawanci basa zuwa hannunsu haka ,
suna riko kayan dubiya kamar ayaba da
lemo, ko kayan shayi, wasu kuma sai su ba
da dan kudi suce a sayi magani. Aisha
farida ta labe tayi kuka har ta gaji, addua
take Allah Ya tashi kafadun abida uwarta,
ubanta, yayarta kuma kawarta, sannan
aminiyarta mai bata shawara. Aisha farida
ta tari yaya hussaini a bakin kofar dakinsa
ya shirya ya fito zaije aiki. Bayan ta gaishe
shi ta shawarce shi tana son ta kai abida
asibitin malam aminu kano a duba to ko
Allah zai sa a dace.
Hussaini yayi shiru can yace kina ganin aje
asibitin nan alhali na tabbatar ba ciwon
asibiti bane, tunda ga kasusuwan sun
kumvura suna ciwo, amma likitocin kashi
sunce basu ga komai ba. Aisha farida tace
ina ga ai ba bangarensy bane, wata kila
ciwon ba a jikin kashi yake ba, gara in kai ta
tunda can akwai likitoci manya manya zasu
gano ciown. Hussaini yace kinga abin da
yasa nace bana asibiti bane, idan tana bacci
sai tayi ta zabura har sai na rirrike ta cikin
dare. Aisha farida tace haka ne yaya, ai
asibitin ma suna da maganin razana da
zabura. Ya lalubo kudi ya bata yace suje,
Allah Ya sa adace. Aisha farida ta harhada
'yan kudaaden da take adanwa na masu
dubiya, misbahi ma dubu daya ya bata,
haka wani yayansu da yazo daga shagamu
shima dubu daya ya bata, taje ta hado
cefanen dambu ta shirya wa rabin ranta dr
shuraim. Bayan ta yi wanka ta fesa kwalliya
da wata doguwar rigarta bakai mai dankwali
(abaya). Sai ta shirya abida aka kirawo
musu mai adaidaita sahu yazo har kofar
gida. Sai da matan gidan suka taimaka mata
aka rirriko abida aka saka ta ciki domin duk
gabar da aka rike mata ciwo takeyi mata.
Sai ta dau kuka kamar wacce ake balla mata
kashinta don azaba. Aisha farida rike da
kwandon abincinta ta shiga adaidaita sahi
suka tafi. Ta dubi abida ta zubo da hawaye
don tausayi tace wannan dambun ne nayi
wa su dr shuraim in kai musu ko in kyale
su? Abida tayi murmushin karfin hali ta cije
baki saboda tsananin ciwo ta gyada kai tace
ki kai masa.
Mai adaidaita sahu ya kai su har bakin
GOPD kafin su sauka, sai aisha farida ta
shiga ciki da sauri tayi magana da maikatan
suka bata kujerar tura marar lafiya. Lebura
daya ta dauko kujerar ta biyo ta da ita. Nan
ma sai da aka agazawa aisha farida sannan
aka dora abida akan kujerar saboda tsabar
ragargazar da kashinta ke yi har kara zaka ji
yana yi bas! Bas! Idan ta motsa. Aka turata
aka shiga dasu wajen bude file kasancewar
duk ta sanu ba ta bi dandazon layi ba aka
bude musu, nan da nan aka mika musu file
din dakin likita. Nan ne fa za asha jira
sabida likitoci basu karaso ba, don haka
dole a sha jira akan bencina. Aisha farida ta
dubi abida wacce har yanzu take kan wheel
chair tace inje ofishin dr lukman in dawo,
zaki iya zama ke kadai? Abida tayi
murmushi tace kije a tsanake ki gama
abinda kike yi, kada ki damu don kin barni,
ni kadai zan zauna a cikin kabarina. Ni kadai
zan zauna babu mai tayani zama, saini sai
halina. Sai aisha farida ta runtse ido yayin
da kuka ya kcece mata, ta kasa magana
saboda jama'ar dake kallonsu. Cikin sanyin
jiki ta dauki kwandon abincin ta tagi.
Hawaye yake ya tsaya har ta kusa isa
ofishin dr lukman don haka ta sami lungu ta
labe tayi kuka har ya isheta, ta goge
hawayen ta fito. Amma kuwa kallo daya
zakayi mata kasan kuka ta sha, don
idanuwan sunyi luhu luhu.
A sanyaye take tafiya cikin nutsuwa ta
kwankwasa kofar ofishin dr lukman ta
shiga. Bata iske shi ba, sai wasu daliban
likitocu guda biyu ta samu suna zazzaune
suna jiransa. Bayan sun gaisa sai ta tura
kwandon abincin a lungun da saba ajiyewa,
sannan ta tambaye su inda ya tafi. Suka
tabbatar mata yace su jira shi yanzu zai
dawo, ba zai dade ba. Sai ta sami kujera ta
zauna tana zama sai taji an bude kofa,
yayin da gaba daya hankalinsu ya tafi wajen
kofa. Dr lukman ne a gaba, dr shuraim ba
biye dashi. Kowannensu da laptop dinsa a
rataye a kafadarsa. Idanuwan dr shuraim
akan aisha farida ya fara dira, yayin da ya
jima yana kallonta sannan ya dauke idonsa.
Ita kuma murmushi kawai takeyi tana mai
sunkuyar da kai tana jin kunya. Dr lukman
ya dube ta yayi dariya yace 'yar shagamu
daga ina kika diro? Na dauka ai da aka gama
karatu sai kika hada 'yan komatsanki kika
koma shagamu. Tayi dariya tace ina nan
yyayana, kai ka share ni ai ba ka nemana
gashi kuwa na taso takanas na zo in gaishe
ku. Dr lukman yayi dariya yace kin kyauta
'yar shagamu, ni daman nasan kinfi ni kirki,
to bari inje in sallami daliban dana zaunar
tun dazu suna jirana. Ya juya ya dube su
yace to ku taso muje lab din in nuna muku.
Suka bi shi a baya suka fice, sai ita sai gogan
nata dr shuraim kadai aka bari a ofishin.
Yana zaune akan kujera ya bude laptop
dinsa yana dube dube. Ta dubi
zankadediyar fuskarsa sai taji zuciyarta ta
hau dukan uku uku saboda tsananin kyawun
dataga ya kara yi. Ta fara tambayar kanta
da kanta “anya kuwa mutumin nan bai fi
karfina ba? Anya kuwa zan kai labari a
tafiyar nan? Anya kuwa hakata zata cimma
ruwa”? Sai bayanan abida ya fado mata
cewar babu abinda ya gagari Ubangiji,
samun dr shuraim ba wani abin wahala
bane idan har ta rike matakan nan guda
biyar. Ta silmiyo daga kan kujera ta gaishe
shi cikin wata kintsatsiyar murya bata mike
daga durkuson ba har sai da ya amsa mata,
sannan ta koma ta zauna. Tayi shiru kanta a
sunkuye a kasa, sai dai su biyu suna hada
ido in dai ta dago zata kalle shi, sai taga
shima ya dago ido ya dube ta.
Sunyi mintuna biyar cur babu wanda ya
sake magana a cikinsu. Sai taji muryarsa
kamar a mafarki ya ambaci sunanta. Yace
aisha farida, 'yar shagamu, 'yar acaba.
Wanne ne sunanki a cikin su. Sai ta dago ta
dube shi tayi masa lallausan murmushi ta
sunkuyar da kai ta sosa goshi alamar kunya.
Tace sunana aisha farida umar shagamu.
Yayi wani dan siririn murmushi yace kin
amsa sunayen uku daya kika cire, mai yasa?
Ta girgiza kai tace ai na daina hawan acaba
yanzu. Yayi murmushi yaci gaba da
daddanna laptop dinsa. Yace kinsan sunan
wa kike dashi? Sunan mamana ne aisha,
haka farida sunan kanwata ce wacce take
bina. Ya akayi kike amfani da sunaye biyu?
Aisha farida tayi murmushi tace mai suna
aisha ai farida ce duk daya ne. Yace okay
kenan ummata da farida sunansu daya ni
ban ma taba ji ba. Aisha farida tayi
murmushi tace haka ne, ai ba kowa ne ya
sani ba. Ya dube ta da wutisyar ido yace
baki da lafiya ne? Ta dago ido da sauri ta
dube shi cike da mamaki ta girgiza kai tace
lafiyata kalau. Ya girgiza kai yace shikenan,
naga kinyi kama da marar lafiya ne, ko kuka
kikayi ne? Wannan tambayar tasa ta sake
bata matukar mamaki, sai taji kamar a
mafarki. Tayi shiru har zuwa dan lokaci
sannan tace eh. Ya dago ido da sauri ya
dube ta sai ya cika da mamaki yayin da ya
maimaita amsar da ta bashi eh??! Yaci gaba
da duban laptop dinsa ya ma rasa tambayar
da zaiyi mata. Ta sharbe hawaye tace
yayata ce bata da lafiya sosai, har bata iya
tafiya ita na kawo asibiti. Yayi shiru na wani
dan lokaci sannan ya nisa ya ce me yake
damunta? Aisha farida ta zubo da hawaye
mai dumbin yawa tace an kasa gano ciwon.
Dr shuraim ya girgiza kai yace a'a bakuje
inda za'a gano muku ciwon ba dai, har
akwai ciwon da ba a ganewa, ko wanda
bashi da magani? Aisha farida ta matse
hawaye da hannunta ta dagi da jajayen
idanuwanta ta dube shi, ta girgiza kai. Tace
asibitin kashi na dala muka yi ta zuwa suna
bata magani, amma bata jin sauki. Sai ma
gaba yake. Shine yau na kawo tana, tana
GOPD a layi, likitocin ne basu karaso ba. Ya
tambaya cike da kulawa yaya take jin
ciwon? Aisha farida ta kwatanta masa duk
yadda ciwon ya fara har izuwa yanzu. Sai
yayi shiru can yace ciwon yayarki
rheumathoi athritis ne ko systemic lypus
erythramatosis. Aisha farida ta kalle shi
cike da rashin fahimta tace na'am? Ya
girgiza kai yace kada ki damu likitocin da
zasu duba ta yanzu zasu hada da likitan da
ya dace. Allah Ya bata lafiya. Aisha farida
tace amin nagode. Sai ta mike a nutse ta
duka tace zan tafi saboda kada likitocin
suzo a kira mu bata iya tafiya, nice zan
shiga da ita. Ya gyada kai yace okay, Allah
Ya ba da sauki. Ta fice cike da farin ciki,
tana fita ta dafe kirji tana ambaton Allah na
gode ma Ka, Allah Ka sake cika min burina
akan shuraim. Tana tafe tana fara'a tamkar
an biya mata kujerar makka. Sauri take ta
karsa wajen abida ta bata labari, amma da
ta tuna abida babu lafiya sai jikinta yayi
sanyi musamman data je ta iske abida ta
galabaita a inda take zaune, ta gaji da
zaman duk jikinta ciwo yaje. Hawaye kawai
ke fitowa daga idanuwanta. Ita kadai tasan
me takeji, sai dai duk wanda ya dube ta
yasan tana jin jiki saboda gaba daya
gabobinta a kumbure suke. Aisha farida ta
rike ta, ta gyara mata zamanta tana mai
lallashinta tayi hakuri likita yazo. Suna
zaune shiru aisha farida na ta sake
maimaito hirar da suka yi da rabin ranta, sai
tayi murmushin jin dadi ta waiwayo da
sauri ta dubi abida tana shirin ta bata
labarin dr shuraim sai taga mawuyacin halin
data ke ciki, sai taji hawaye ya cika mata
ido.
BABI NA GOMA SHA DAYA Aisha farida tayi
kuka, har ta godewa Allah a wannan rana ta
asabar saboda jikin abida ya matsa, babban
yayanta yaya lurwanu yazo da mota har
kofar gida, yace a bashi ita ya tafi da ita
shagamu ayi maganin hausa. Yaya hussaini
ya zama bashi da zabi kasancewar shima
yana ganin ciown bai yi masa kama da na
asibiti ba, don sunyi ta yin na asibitin babu
alamar jin sauuki, kullum ciow kamar kara
shi ake yi. Aisha farida ta dage wajen yi
musu bayani, sunki su fahimce ta, suna
ganin don ita 'yar boko ce kuma malamar
asibiti shiyasa take son a dauwama da na
asibiti don likitoci ba sa kaunar a hada
maganinsu dana gida. Sunfi karfinta, tana ji
tana gani yaya hussaini da yaya lurwanu
suka ciccibi abida tamkar 'yar jaririya da
kayanta aka saka ta a mota. Yaya lurwanu
ke tukawa, yaya hussaini yana zaune a
gefensa, yayin da ita kuma aka kwantar da
ita a bayan mota. Aisha farida ta mika
hannu ta tagar motar ta rike kumburarrun
yatsun abida a hankali yayin da hawaye ya
surnano daga idanuwansu su duka. Aisha
farida tace Allah Ya baki lafiya. Abida ta
girgiza kai tace ba zan dawo ba farida, ki
kula da 'ya'ya na, kada ki manta abu uku
dana fada miki. Ki zama mai yawan addua,
mai tsananin hakuri mai yawan kama
mutuncinki. Biyun kuwa ba yanzu zan fada
miki ba sai nan gaba idan ban mutu ba.
Yaya hussaini ya juyo da sauri yana kallonsu
ba tare da ya fahimci abin da suke ba, shi
da lurwan suka cika da mamakin jin
kalaman da marar lafiya ta ke furtawa.
Hussaini ya tambayi aisha farida meye
hakan kuma yake nufi? Zance me kuke yi?
Aisha farida ta goge hawaye tace a'a sako
take bani. Yace sakon me kuma naji ana
maganar soyayya? Ki koma gida ki kula da
yara, gasu can suna ta kuka, nima gobe
zandawo na bar miki dari biyar a daki akan
katifa. Idan anyi wa yara hutun makaranta
sai mu dunguma mu tafi shagamu, ni ina jin
ma gara ku kaura can kacokan, ni zan dinga
zuwa ina dawowa, gara mu hakura da
zaman kanon ma. Kirjin aisha farida ya buga
bamm! Don fargabar tana tunanin yaDda
zata rabu da rabin ranta dr shuraim. Ta
zame hannunta a hankali daga hannun
abida, sai abida ta dago ido ta dube ta, tayi
mata murmushi. Tace Allah Ya baki nasara
akan abin da kike nema. Kuka yaci karfin
aisha farida, ta rushe da kuka. Tace Allah ya
tashi kafadunki anti abida.
Nan da nan yaya lurwanu yaja mota ya tafi,
saboda suma sun fara jin hawaye yana zubo
musu don tausayi. Idanuwan yaya hussaini
ya cika fal da kwallah. Aisha farida ta kame
a inda take tsaye tana kallon motar har sai
da suka kure sannan ta juyo gida. A hanya
jama'ar unguwa sai sannu suke yi mata, da
kuma fatan Allah Ya ba wa abida lafiya.
Kowa ya tausaya wa aisha farida ganin
kukan da take sharba, idanuwanta sunyi
jajawur. Ita kanta tana so kukan ya tsaya,
amma yaki saboda tsananin kunar da take ji
a ranta. Ta kama hannun 'ya'yan abida su
hudun dukka maza, faruk, sa'ad, muhd, da
ishak idan taja hannun wannan sai wannan
ya arce da kuka. Da kyar matan gida suka
taya ta da kamo su ana lallashi da alewa da
biskit. Da kyar suka zazzauna a daki suka
daina kukan. Aisha farida ma tazo ta zauna
a gabansu tana kallonsu, ba tare da ta iya
musu magana ba. Abin duniya ya ishe ta, ta
rasa abin da yake yi mata dadi. Ji take
tamkar zuciyarta zata fashe. Tana ambaton
Allah kar ka kashe abida, ina son abida a
rayuwata. Wayarta ce tayi kara, ta mika
hannu a sanyaye ta dauka, ta duba wata
lamba ce bakuwa babu suna, sai dai lambar
ta musamman ce, saboda kusan lambobin
duk iri daya ne. Tayi ta kallon lambar amma
batayi mamakin wanda ke kira ba, domin
'yan ajinsu da dama suna karbar lambarta
su kira ta maza da mata. Saboda bata cikin
hayyacinta , don haka bata son yin magana
har wayar ta katse ba ta amsa ba. Can ta
mike ta fito tsakar gida ta jawo risho ta dora
ruwan zafi a karamar tukunya, ba tare da ta
san abin da zata dafa ba.
Ta dubi babban dan abida faruk tayi
murmushin karfin hali tace yaya me zamu
dafa yau? Maganar ma shi ma dakyar yake
yi, sai ya langwabar da kai yace wake da
shinkafa. Ta dubi sa'ad mai binsa tace kai
fa dan lelena mai zan dafa muku? Shima
yace wake da shinkafa. Sai ishak yace
shinkafa da miya. Mohd yace a'a tuwon
shinkafa da miyar taushe. Aisha farida tayi
dariya tace a'a su yaya sun fiku gaskiya, ku
rage min aiki tunda muna da yaji mai dadi
da daddare sai inyi mana tuwo. Tana zaune
a dokin kofa tana tsice wake sai wayarta ta
dau ruri. Nan da nan yara suka hau tseren
dauko waya, ana dambe dai kamar za a yar
da wayarta samu ta karba. Taba dubawa
taga lambar dazu ce, sai ta tabbatar ko
waye wannan mai kiran wayar tana da
muhimmanci tunda ya sake kira, don haka
nan da nan ta danna. Cikin nutsuwa tayi
sallama, taci gaba da sauraron mai wayar,
mace ko namiji? Muryar namiji taji ya amsa
da wa alaikumul salam. Tayi kasake tana
sauraon abinda zai fada mata, har yanzu
bata gane muryar ba. Amma daga dukkan
alamu ta taba jin kamilalliyar muryar. Ya
tambaya don Allah ina magana da aisha
umar ne? Ta amsa da eh aisha ce. Yayi
gyaran murya kadan yayi murmushi yace
farida kina magana da dr shuraim imarn ne,
daga nan asibitin aminu kano. Tsarki ya
tabbata ga Ubangijin talikai. Kalmar da
aisha farida ta fada kenan a cikin zuciyarta,
yayin da ta sulale ta durkusa gwiwoyi guda
biyu a kasa don mamaki da kidimewa. Ta
rasa kalma daya da zata furta, sai gumi take
jikinta yana bari, ta rasa inda take. Shin
mafarki ne, ko kuma idonta biyu?
Ya ambaci sunata har sau biyu. Farida!
Farida!! Tayi doguwar ajiyar zuciya, ta
lumshe ido ta amsa cike da ladabi, cikin
sassanyar murya na'am. Yace kina mamaki
ne? Kada kiyi mamaki. Na sami lambarki ne
daga wajen dr lukman jiya aiki ya hana in
kira ki, sai yau da yake weekend ne, ina
gida. Ta mike ta shige dakin abida ta turo
kofa ta datse saboda hayaniyar yara, ta
sami lungu ta shige ta takure kai kace sanyi
take ji. Ta gaishe shi cikin nutsuwa. Ya
amsa cike da fara'a ya tambayeta ya mai
jiki? Cikin sanyi jika tace da sauki. Yace yaya
maganin da take sha, tana samun sauki?
Tayi jim kadan tace tana sha dai, amma
ciwon kamar gaba yake tayi. Yace
subhanallah, to yanzu abinda za a yi, ranar
litinin ki kawo ta wajen zan hada ta da
likitan da ya kamata ta gani, wato
rheumatologists. Ba damuwa idan nayi
masa magana zai duba ta ko babu
appointment. Hawaye ya surnano daga
idanuwan farida, ta marairaice murya tace
ai bata nan, anzo daga gida an dauke ta,
wai na hausa zaayi. Babu yadda banyi ba su
kyale ta muci gaba dana asibiti suka ki.......
Bata rufe bakinta ba sai ta rushe da kuka
cikin wata irin sautin murya mai ban
tausayi. Dr shuraim ya zabura yace
subhanallahi, wannan suna so su jawo mata
ciwon koda, daman ciwon yana da alaka da
ciwon koda. Kada su sake su bata sassake
sassake ta sha, don akwai mummunan
hatsari wajen shan jike jike. Kuka kawai
farida ta keyi, ba tare da ta iya magana ba.
Yayi ajiyar zuciya ya ambaci sunata cikin
wata lallausar murya. Yace farida kuka kike
yi? Daman ke haka kike sarkin kuka ce? Na
hadu dake fiye da sau hudu kullum kina
kuka, meya damuwarki? Ta girgiza kai ta
goge hawaye tace babu abinda ban fada
musu ba, babu irin maganar da banyi ba
akan su kyale ta, suka ki. Mijinta ma tun ba
ya yadda yanzu har ya yadda. Yanzu ko nay
waya shagamu nayi bayani kada su bata
maganin hausa ba zasu saurare ni ba. Shine
nake jin tsoro kada su jawo mata ciwon
koda.... Ta sake barke wa da wani kukan
DUK KYAN TAKALMI 2* 12
Ya sake jan doguwar ajiyar zuciya yace kada
ki damu, mu dukka muslmaii ne, mun yadda
da Allah Shi ne mai warkarwa, ba magani
ba. Muyi addua Allah Ya bata lafiya, Allah Ya
tsare duk wani tsautsayi. Ya ya kike da ita
marar lafiyar ne, mamarki ce? Aisha farida
ta marairaice murya tace anti abida yayata
ce, kakanninmu daya, kuma tana auren
yayana da muke uba daya, itace marikiyata
tun ina karama, itace tamkar uwata, ubana,
yayata, kuma aminiyata mai bani shawara
akan duk lamurana. Sai yayi murmushi ya
lumshe ido yace amma kin iya kwatance
yadda mutum zai gamsu. Ko kon taba bata
labarin wani dr lukman da abokinsa dr
shuraim da suke cinye miki dambu da
danwake? Aisha farida ta kwashe da dariya
tace a'a baka bani izinin na sanar mata ba.
Yayi dariya yace nasan kin fada mata. Ta
sake tuntsirewa da dariya tace sai dai yanzu
na fada mata. Yayi dariya yace to Allah Ya
sauwake Ya bata lafiya sai anjima. Aisha
farida tace nagde Allah ya saka maka da
alkhairin, sai anjima. Ya kashe wayar yana
lumshe ido saboda jin dadin muryarta. Har
yanzu aisha farida sankare take a lungu ta
kasa sauke wayar daga jikin kunnenta. Ji
take tamkar mafarki take yi, yayinda
farinciki marar misaltuwa suka cika
zuciyarta, ta cika da mamaki marar adadi,
sai ta tuna da bayanan ABida da tace babu
abin da ya gagari Ubangiji. Idan bawa ya
roke Shi, yana amsa ma sa duk sanda Ya so.
Ta ajiye hannunta a hankali daga jikin
kunnenta ta dafe kirji taji sassanyayiyar
bugun da zuciyarta take yi. Ta daga hannu
sama tayi wa Allah godiya sai ta malale ta
kwanta akan katofa tamkar ruwa.
Ta jawo wayar da sauri ta duba lambar, ta
kayatu ita kanta lambar abar kallo ce, sai ta
sumbaci wayar. Ta dannan lambar ta kira,
bugu daya ta shiga ta fara ruri, sai taga an
kashe. Hankalinta yayi mummunan tashi,
nan danan ta zabura ta tashi zaune ta dafe
kirji, yayin da farin ciki datake yi ya koma
ciki. Ta fada a bayyane innalillahi wainna
ilaihir rajiun! Me ya kaini sake kiransa, gashi
ya katse? Shikenan zai tsane ni. Ta na
zaune ta hada kai da gwiwa tana tunani sai
taji wayarta tayi ruri. Nan da nan ta zabura
ta dauka ta duba, sai taga lambar dr shiraim
ce, tay sauri ta dannan gami da yin sallama
cikin nutsuwa. Ya amsa mata gami da cewa
naga kin kira ko? Ta lumshe ido tace eh
daman zan tambaye ka ne, ranar litinnin
dambun zan kowa muku ko danwake? Ya
girgiza kai tamkar yana gabanta yayi
murmushi yace a'a babu, ba sai kin kawo
mana komai ba, mungode. Ta marairaice
tace haba doctor meyasa, ni ina so na kawo
muku. Yace a'a ki bari sai wani lokaci, idan
muna bukata zamu fada muki. Yanzu na
kira ne naji halin da marar lafiya ke ciki,
don na damu nasan ciwon nan yana da
tsananin zafi, sannan na damu da yadda
naga kinta ta koke koke na kora najji halin
da kuke ciki. Tayi murmushi tace nagoda ka
kyauta, nayi farin ciki da jin kiranka. Ko zan
iya saving din lambarka don mu dinga
gaiswa. Yace ba damuwa, zaki iya. Tayi
godiya, shima yayi mata godiya, suka kashe
waayar. Tayi tsalle akan katifa ta dire don
murna. Ta dubi gabas da yamma, kasa da
sama tana tunanin wanda zata ba wa
wannan kyakyawan labari. Ta tuno abida,
taji yau dama abida na nan ta fada mata
yadda sukayi da dr shuraim. Taji hawaye ya
cika mata ido, ta fada a bayyane. Allah sarki
anti abida, Allah ya baki lafiya. Tana rufe
bakinta faruk ya shigo dakin da gudu ya ce
anty aisha ruwan da kika dora a wuta yana
ta tafasa tun dazu, har ya kusa ya kone. Ta
zabura da gudu ta fito don ita har ta manta
da shi, tabbas yaro yayi gaskiya , ruwa dai
ya gaji da tafasa har ya kusa konewa. Sai da
ta kara wani yayi zafi sannan ta zuba wake
da shinkafa suka dahu. Ta ba wa yara suka
ci, yayin da farin ciki ya kosar da ita, ta kasa
ci, yunwar ma bata ji. Bayan tayi sallahr
azahar sai ta dinga jero nafilfili ba adadi,
duk ta godiya ce ga Allah da ya kawo mata
dr shuraim.
A cikin satin nan haka take yini cike da farin
ciki, saboda ta sami dr shuraim, sai dai
matsala daya ce take

Please Login or Register in order to submit comment