Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

min...,


yanzu dai kawo wani abun da zamu zuba a mota mutafi kamusu


Innalillahi yanzu oga nura ni zaku yiwa abin da kukewa wa'yanda basu waye ba tab lallai shiyasa nace ku kaini gurin d.p.o kuma billahillazi inga mutum acikin gida sai na karta mai rashin mutunci mabayyani wallahi



kai sajan bala kofur musa ko bita ku kamo mana kowaye zasu yi bayani ne


Saramai suka kai suka ce to


Baiwar Allah dan Allah kisa baki ɗana aka kama ya saci garin kwaki wallahi yunwa ce da matsi na rayuwa yasa yayi haka kuma na maƙocina ne


tausayi ya bawa Magaji tace


"Kar ka damu baba sajan bala na nawa ya ɗauka...?,


na dari biyar sai kuɗin beli dubu biyu


kallon bangon policetasion ɗin tayi tace

"naga ansa beli free ne....,


sosa kai yayi yace



"Kawo abin da zaki kawo kiyi gaba mu sake shi....,


Dubu biyu ta bashi ta ɗauki dubu biyu ta bawa baba godiya ya shiga yi mata yana sa mata albarka fita tayi su sajan suna binta abaya can gurin me awara ta hango dinana nunawa su sajan shi suke ji yayi an cabki wandon sa cikin bala'i ya ɗaugo yace



"Wanne dan durin uwar.....kafin ya ƙarasa sukai ido huɗu da sajan bala....,


Haɗa rai yayi yace

"to me nayi mai nayi maka ba dpo yayi mini tsakani dakai ba....,


dungure mai kai yayi yace


"Uwarka kai min shige mu tafi...,


tirjewa ya fara yi da be lura da magajiya ba sai yanzu yace


"Magajiya dake za'a haɗa baki aci zarafi na....?,

Dinana kuɗina dubu sittin aka ɗauke min suwa ye ke tare dani in baku ba..,


Gaskiya ne yanzu na fahimta sai yau na gane maganar hausawa da suke cewa zuciya bata da ƙashi inban da haka in taɓa gani nayi sata banni da ɗan taɓe taɓen mata anan nafi kauri amma saboda ido wa ka raina shine ina gaban buɗurwata kika sa aka tuzarta ni....



Da hallacan muje tafiya suke suna ta faɗa sa mukulli tayi ta buɗe gidan hanka ɗashi su kofur sukai kahu yana zaune yana jan jarbi tashi yayi ya saki salati ganin wayan nan annobar yace


"Falmata amma dai wayan can yan Allah ya shirya za'a kama ban dani ko...,


shigowa tayi tace



"a fito min da kuɗina hankalin kowa ya kwanta in kuka ƙi wallahi sai kwanan cell gobe sai gidan gyaran hali....,


Rabi da take zaune dafe da fashashshan ƙai tace



"Innalillahi magajiya ki rufan asiri yanzu ina zan sa kai na wallahi fata ta bata son cizon sauro kinsan dai ance ciwon ya'mace na ya'mace ne su tafi da dinana da bulama yake kowa yauwa kun manta ba a tawo da manjagara ba ina kyautata zaton shi ya ɗaukar miki...,


To ɗan shegiya wa yace maka ina tsoron su gani billahillazi na kama ka sai na cire maka raini dake tsakanina dakai...,


zaro ido rabi tayi ɗaurin ƙanta ta cire tana fifita dashi.....✍️


gidan magajiya yasha babban da labarin da nake kawo muku kudai ku kasan ce da alkalamin

*Oum yasmeen matar mijinta*




GIDAN MAGAJIYA


Wannan littafi kirkirarre ne banyi da nufin tozarta wani ko wata ba duk wanda yaga yayi dai-dai da rayuwar'sa to ya ɗauka arashi ne......


Ku fitar mana da littafi ku karanta kuna nushaɗi kusan cewa Ubangiji zai barku wallahi hakkin mune Ubangiji bazai taɓa barin kuba muna amsar kuɗi ne saboda mu rage raɗaɗin typing hannun mutum duk ya ƙage ke ki karanta a kwanciyar hankali wata shari'ar sai a lahira🗣️


https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k


Kuyi following ɗin channel ɗina domin na kusa dena posting a ko ina sai a channel



Episode 5




Shege wanda Ubangiji ya la'anta billahillazi zamu haɗo a way

Ku dakata kuɗina nake muku magana kun mai dani mahaukaciya tagumin da uwani tayi ta cire tace



"Yanzu falmata bazaki bi wannan abin a hankali ba ayi bincike....,


Banza tayi mata kamar ance kalli can inda ta zauna tana al'wala sai ga kullin kuɗi da sauri ta ɗauka farke baƙar ledar tayi kirga kuɗin ta fara kuɗin ta cas ba abin da yayi ciwon kai...hamdala tayi ta soke a kugu tace


"yan iskan karya....,


Wallahi Allah ancu ce ni haka kurum kin ɗora mana sharrin sata gaskiya magajiya ki canza hali tun kafin Ubangiji yayi ƙuliƙulin kubura dake wallahi

Cewar rabi....


takaici ne ya kama xuby ta ɗauki mayafin'ta ta tasa a ƙafaɗa tace



"To su kofur sai ayi gaba nan gurin baku da rabo....,


harara ya gallamata yace


"to yar hau ke wallahi kike yaye ni tun kafin insaki a bayan kanta....,


Ka dade baka sakani ba tana kaiwa wannan ta fita shigiya da kafa yawa katafila kina wani rausaya kamar matatciyar bishiya da take shirin waɗowa

Rabi ya faɗa yana wani murguɗa baki dinana da takaici ya ishe shi yace



"Magajiya wallahi zan san zaman da zanyi dake.....,


Ka dena zuwa gidan nan daman me kake tsinana mata

taɓarya ya ɗauko ya biyi rabi da ita da gudu ta fita sallamar su kofur tayi suka fita akan dokin kofa ta zauna ta zuba tagumi ta shiga tunanin rayuwa jin maganar Sama'ila tayi yace



"yaya yunwa nake ji....,


da sauri ta ɗago tace


"Sama'ila ɗauki kuɗi a kan katifa ta ka siyo mana taliya ka biya gurin masu siyar da pieces ɗin kaji ka siyo cinya da kirji na dubu biyu.....sai ka siyo mana kayan miya...ka kaiwa uwani ta girka mana,



kahu da yake zaune yace



"Falmata kice yau me yar gaɓa za muci a gidan nan....,



kallon kahu tayi wanda take wa kallon kamar mahaifiyar'ta wani zubin halin sa ke ja masa tace



"Eh....,


gyara kwanciya yayi yace



"To Allah yayi albarka ya bayyana fatima....,


jindaɗin addu'ar sa tayi tace


"Amin.....,

Sama'ila ne yace


"Yaya yaushe za mu koma damaturu....,


kama haɓa tayi tace

"Ka rufa mana asiri so kake muje ayi dabgen mu....ai ko a mafarki bana fatan Allah ya maidani Maiduguri ai mun ga tashin hankali.....,


Shiga ɗaki yayi ya ɗauko ya fita Radio kahu bulama ya ware har maƙota anaji kwanciya yayi a katifa Yana jin labarin duniya kamar haka


Ayau ne shugaban rukunin Company AK SARDAUNA CONSTRUCTION sannan director general ma Hukumar DASS bayyana cewa insha Allahu sun kusa gama titin da zai kai ka har zuwa katsina tun daga nan kano kuma ya bawa wa'yanda ta sanadiyar haka suke samun tsaiƙun tafiya yayiwa wakilin mu ƙarin bayani


Waccan gwamnati ta bami aiki ba tare da tabiya mu bu shiyasa na dakatar da aikin amma wannan sabuwar gwamnati ta taka rawar gani gurin biyan yan kwangila hakkinsu

Inda yana gama wannan jawabi ne jirginsa ya ɗaga zuwa babban birnin Chaina

Ga zantawar da mukai da al'umma mene ra'ayin ku game da titin da shugaban ƙasa ya ɗauko tun daga kano har i zuwa hanyar da zata sadaka da Katsina nazeer lawan gare Ka

Sunana nazeer lawan nine me kawo rahotanni ga hirar da mukai da wasu matasa

A gaskiya mu ba wannan muke buƙata ba a inganta harkar lafiya da tsaro dan an gyara mana titi mutane ba kwanciyar hankalin da za suje su amfana da titin kullum ana bin mu ana kashe mu



Wakilin rahotanni yace


"Kar ka manta direbobi sun sha bin hanyar nan suna haɗari saboda rashin kyahun hanyar....,


ba rashin kyan hanyar bane yake sa haɗari ka bincika kaji yan fashin dare ne suka assasa haɗarin

Kai me zaka iya cewa game da ci gaban da aka samu tsawon shekaru takwas ana aikin titin nan aka tsaya sai yanzu me girma shugaban ƙasa ya fitar da kuɗi domin a ci gaba da aikin nan


hakan ya da yayi abu ne me kyau Allah ya ƙara mai nisan kwana ya bashi ikon sauke nauyin mu

To godiya muke nazeer lawan

a wanni ɓangaran kuma ministan ilimi A'isha AK sardauna ta halarci taron shugabannin makarantun kama daga kan primary secondary college university insha'Allah zata jajirce ganin harkar ilimi ta gyaru a ƙasar nan inda ta faɗi jimullar yaran da basa zuwa wa makaranta.....


a fusace magajiya taje ta kashe radiyo bacci ne ya fara ɗaukan bulama firgigit ya farka yace



"magajiya lafiya.....?kika kashe min Radio...,


Kahu sai yau she zaka kagane ka dena sauraron wannan ƙanzan kuregen ne


tasho zaune yayi yace



"Falmata labarin duniyar ne kanzan kurege lallai kinji hausa....,


komawa tayi ta zauna tace



"Kahu ka faɗamin abu ɗaya a aka faɗa da ka amfana dashi mu talakawa ba wannan ne a gaban mu ba a inganta mana tsaro rayukan mutane nawa a kullum suke salwanta....? muna tsaka da bacci aka kore mu aka yanka wasu daga cikin mu yara ƙanana suka zama marayu...mata nawa aka kama aka yi musu fyeɗe sannan aka yi musu kisan hulakanci....yara da yawa sun na ƙasa so muke akawo mana ƙarshen wannan zaluncin ba wannan shirman banzan ba a kawata titi su haukan titin adin gayi musu jiniya turawa su zo.....

zuga suna aiki a kasar su su hau kan gada su shiga su ɓulla yawa wasu kurege kahu dan amfanin kansu suke gyara titi badan amfanin mu ba wallahi kahu ace zan shiga siyasa kuma a zaɓe Ni sai *NAKAWO KARSHEN WANNAN ZALUNCIN......*


Allahu akbar ba shakka malama falmata ai kamata yayi ki tara mutanan ki ki musu faɗa kafin kizo kan shuwagabani...,


ɗaki ta shiga hawaye na bin kuncinta karewa ɗakin kallo tayi duk irin daular da take ciki tana ji tana gani ta baro'ta tabar abu mafi muhimmanci a rayuwar'ta jin maganar mahaifinta tayi ta dawota sabuwa fil tana amsa kuwa a kunnanta


Bazan shiga ƙungiyar ku ba saidai in Ku kasheni bazan zaɓi farin ciki na ba in sulhuntar da rayukan musulmai ba....karya kuke wannan abin da kuke ba jahadi bane cin zarafin Musulmi ne......✍️

*Yan aljanna a dinga yi min sharing Allah ya bawa kowa abin da yake nema duniya da lahira*


GIDAN MAGAJIYA

oum_yasmeen

✧⁠☆typing....

✷⁠✷✷✷✷⁠✷⁠✷⁠✷

EPISODE:.6

https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k


Kanta ta dafe dayake tsananin mata ciwo zama tayi salamar Sama'ila ce ta dawo da ita duniyar da muke tashi tayi ta ɗauro alwala salla ta haɗa azahar da la'asar ko tsayawa addu'a bata yi ta fito


Lokacin uwani ta gama shan wahalar hura huta ta ɗora tattasai sauke tukunyar tayi ta zuba ruwan wanka ta tsaya agurin tana girgiza kafar ta jin motsin sauke tukunya a sukwane uwani ta fito daga bayi tace


"Wanne shegen ne ke buɗamin tukunya....?,


shiru tayi ganin magajiya girgiza kai tayi ta koma alwala ta ɗauro shiga ɗaki tayi

sauke ruwa magajiya tayi ta zuba a botiki mai da tukunyar da ta sauke tayi
Sannan ta juya ruwan a botiki

shiga daki tayi ta ɗauko kwandon wankan ta ta shi ga bayan gida


✧✧✧

******CHAINA SHANGHAI PUDONG

miƙe ƙafafuwan'sa yayi akan Centre table sosai yake jin daɗin karanta jarida wayar sa ce tayi ringing gaban sane ya waɗi ganin wacce take kiran shahada yayi ya ɗaga kiran cikin ladabi yace


"Assalamu alaiki Barka da war haka hajiya....,

Bata tsaya amsa gaisuwar'sa ba balle sallamar'sa ta zarce da cewa

Asif ya kukai da kai wata fa ba ƙoƙarin cika banji ko ɓatan wata wannan juyar tayi ba


lumshashun idanuwasan ya buɗe ya maida su yawa na masu jin bacci yace


"Ki hakuri hajiya komai nufi ne na Allah..,

ai kafin ya ida zancen'sa tace


"Wallahi wata na cika sai kai aure....dan mu dangin mu irin haihuwa ne damab tun farko kafiyar ka ban ga abin so a silindar gas ba ba kyan fasali amma ka nuna kafiya dangin turawa ai su tun yaro na ciki suke kashe mai kwaikwayon haihuwa....kaf cikin ahalin mu kowa na haihuwa ban da kai ƙannan na baya wanda akai musu aure bayan auran ka daga me ya'ya biyar sai me huɗu....dole inga jikan babban ɗana....,

cije lips ɗin'sa yayi besan wacce tsana hajiyar sa tayi wa aysha ba duk da wani zubin da laifin aysha ƙasa yayi da muryarsa yace


"hakan ma baza ta faru ba insha Allah zaki ji kyakkyawan sakamako....,

Allah yasa ta kashe wayar ba tare da taji me zai ce ba

jikin'sa a sanyaye ya ajiye wayar ɗaga kansa sama yayi kallo ɗaya zakai mai kasan buzune ga hutu da ya ratsa fatar'sa har ɗaukan ido ji yayi karanta jaridar ya ishe shi tashi yayi dogune ga jikinsa duk a murɗe laptop ɗinsa ya janyo ya zauna duba saƙone ya shiga yi

wani sako ya gani Niheela M.S banza yayi da saƙon ya ci gaba da duba masu mahimmanci wani saƙon ne ya sake shigowa dafe kansa yayi dake tsakanin

ciwo buɗewa yayi kurawa rubutun ido yayi yana karantawa

_assalamu alaika amincin Allah ya tabbata a gare ka ya wanda zuciya'ta take so ina fatan a yau in sami a bin da na dade ina jira a ko wanne lokaci ina tsammanin ganin saƙon ka duk da nasan kana tarun aiyuka_

*daga masoyiyar ka ta har abada NIHEELA M.S*


takaici ne ya kama shi waya ya ɗauka cikin ba da umarni yace


"Zan turo maka wani email kai min bincike a kansa....,

Okay sir kashe wayar yayi ɗaya wayar'sa ce tayi ringing ɗauka yayi ganin my love CE ɗauka yayi ya kara a kunne batare da yayi magana ba tace


"Honey nayi kiwar ka....,


Shafa lallausar sumarsa yayi yace


"hmmm yanzu in nace ki biyoni cewa zaki aikin ki.....,

gaban tane ya waɗi karfa yace ta biyo shi bazata iya tafiya wata ƙasar ba ba aikin'ta ne ya akai'ta ba tace


"Ak aikin al'umma ne duk randa nayi ritaya zan buɗe Foundation ne in nemi guri in zauna in kula da kai sannan in Allah yayi min nuɗifin'sa sai kaga na haifa mana baby's masu kama da daddy su....,



ajiyar zuciya ya sauke ya gyara zama yace


"Aysha lokacin karfina ya kare a lokacin buƙatar sanyin idanuwa nake wa yanda zan kalla naji dad'i.....,


iska ta furzar me huci ta gyara zaman'ta tace


"A kullum ƙara zamar min wani fure kake wanda yake yaɗo baza ka taɓa jin ƙasa ba kai mazajene a cikin maza me isa wani zubin kake da saurin karaya....?,


rufe laptop ɗinsa yayi yace



"Aysha bakya tsoro rashin kulawar dakike bani a masu farauta ta su sami nasara....?,


Dariya tayi ta juya sitiyarin motar ta tace


"Zuciyar ASIF ba ko wacce mace face matar'sa na baka duk wata yarda....,


Murmushi yayi har ana iya gano jerarrun haƙoransa yawa sankara saboda haske da ɗaukar ido yace


"yanzu ina aiki in ajima muyi yawa....,


Okay nima ina kan hanyar zuwa gida wallahi na gaji gobe na kiraka tana kaiwa nan ta kashe wayar...

bin wayar yayi da kallo duniyar tunani ya lula

inda ake ni kuma ta tawo kanon dabo

NNDC Quaters


Tun daga farkon layin zaka san cewa unguwa ce ta masu hannu da shuni wani ɗan kareran estate in aka yi rubutu a jikin baƙar gate din gidan aka rubuta...SAUDAUNA ESTATE da ruwan gold wata mota ce ash ta fanno a guje horn ɗaya mamallakin motar yayi ba shiri masu tsaron estate ɗin duka buɗe mai.

ko daidai ta parking be tsaya yi ba ya fito a fusace duban ma'aikantan gidan yayi ya shiga surfa musu ashar yace


"She gu munafukai har da ku....har ni za a sa a kulle min gida bazan shiga ba....


Ƙwafa yayi tare da cewa


Ai duk da laifin yaya har mace ta dinga juya shi kamar ni za a mai da min da kaya na guest house bakomai Zan yi maganin yar kutumar....uba


Cikin isa Hajiya jamila ta iso tsawa ta dakawa ma'aikatan gidan da su ka daina komai suka tsaya suna kallon'sa kama hannunsa tayi suka fara tafiya

har hadadɗan floor ta zama yayi tsayawa tsaye tayi ta fara kai kawo ba tare da tayi magana ba haka shima sai ajiyar zuciya yake sauke wa can da ta gama isar ta tace


"Me ya dawo da kai.....?,



Mom yan zu abin da ake min a gidan nan yayi dai-dai kenan


Tsawa ta daka mai tace


"Faisal cewa nayi me ya dawo da akai....?har kana faɗa da kasƙantantun mutane abin yayi min ciwo lokacin da talatu a faɗa min ka dawo har ka tusa yan aiki gaba kana zagi.....,


Au yanzu na fahimta har da ita ke nan a sahun munafukan gidan nan


Zama tayi tace

"Har yanzu baka ban amsar tamabayata ba....✍️,

Iya comments din ku da sharing iya yawan read more ɗin ku



*GIDAN MAGAJIYA*

*_Ban yarda wani ko wata ya yi min amfani da shashina na wannan littafin ba masu dai haɗa document ku haɗa ko sa shi a website amma ban da mai damin da shi audio wannan hakkina ne kubar min kayana_*

https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k

EPISODE 7


Yanzun nan na dawo daga Company na tarar waccan me kama da taliya me sirisiri ta sa a kwashe kayana amai damin guest house wai ta gaji da halina me ruwanta da ni ban da shi yayan ya nuna mata bani da daraja ai bata isa tayi min haka ba...amma ba damuwa zan saita mata zama


Gauran numfashi ta sauke tace


"Faisal da ace ka zama mutumin kirki da nafi kowa jin dadi kalli a yarda ka dawo daga kai sai three-quarter sai riga me ƙaramin hannu ga wannan uwar sarƙar ko nauyita baka ji ...,

ɗaga sarƙar huyansa yayi yace


"Mom wannan kinsan kuwa kuɗin'ta ai fashion ce wallahi kowa ya ganni ba raini...,

cikin takaici ta buga Centre table tace

"Wallahi duk halin da nake ciki kai ke jamin Faisal da ace ka zama mutumin kirki zan kwatar maka hakkin ka amma yanzu fa....kalli muna wani yunkuri za a gane mu bamu da kataɓus da ko shiga jikin'sa kayi mu samu wani sirri amma ka tsaya shashanci...,

tashi yayi ya buge rigar'sa yace


"Mom faɗi wani abun ba wannan ba nifa ina kaunar ɗan uwana ato baki isa ki haɗani da shi ba matar'sa ce matsala ta da dai ita kike so mu haɗa hannu mu kifar da ita nayi....yana kaiwa wannan ya fita


kiran shi ta shiga yi amma ko wai wayowa be ba naushi ta kai wa iska idanunta sun ƙaɗa sun yi jaaa kai kawo ta shiga yi


__ __ __ __ __


Hajiya yi ce ko kin kora mai bayani haba kullum ai ta abu ɗaya mace ba mace ba sai aukin hura hanci yawa yar gidan me kuɗin duniya cewar Jidda


Tsiran ta zuga ta tauna bata ƙarasa cinyewa tace


"Kyale ni dasu jidda wallahi zan maganin su very soon zan nema mai yar gidan girma wallahi....,


da dai yafi amma Ni wannan aunty Ayesha ban ga mafaninta ba

Ai ke ke kina da amfani shegiya munafuka wai me kike so jidda ki zama kullum sai tusa hajiya kike a gaba kina hure mata kunne gaskiya be dace abin da kuke ba


Hamza Hamza fito fili ka zageni damam tun shekaran jiya nake lura da kai sai cika kake kana batsaiwa dan na taɓa yar gwal ƙarya na fada kullum sai dai taitayawo yawa yar bijilanti ni daman da aka zo neman me bijilanti na bada sunan izzatu ai a lokacin da ta musamin sa'a taci ban zubar mata da haƙora ba.....ta rasa na tarɓar miji

Allah ya huci zuciyarki amma ki duba ki dena biye wa zancan jidda

Salati ta saki tace


"wato ni gani mara hankali ko tana hure min kunne nagode Hamza....,


ajiyar zuciya ya sauke ya rusuna yace


"Allah ya ja da ranki hajiya ba haka nake nufi ba kinga jidda yarinya ce be kamata tana shiga hurumin da bana'ta ba ASIF iya ƙoƙari ya yi matar nan tasa matsalar ta ɗaya bata son wani ya raɓi mijin'ta bata shigowa dangin'sa to mu rabu da ita ita duniya hankali take koyawa mutum kar kije ki ɗauko mana kara da kiyashi....,


Allahu akbar masha Allahu Hamza ashe daman ka iya wa'azi ka tsaya kana gogawa da takardu maza ga hanya nan koma inda ka fito dole inga
ya'yan me sunan malam ace sardauna guda ba ya'ya....

tashi yayi be ƙara ce wa ƙala ba tujarar hajiya ba salla take ba waya ta ɗauko tace


"Jidda nemo min number Akram...,


karɓa tayi ta fara nemo mata kee dakata ki lura sosai kai ki kirawo min wannan me fuskar shanu


waya jidda ta ajiye tace


" Na fasa tun ɗazu nake miki abu kike kushewa ke kira shi...,

janyo jidda tayi tace


"haba yar jikallena acikin jikokina daga ke sai sardauna ku nafi so....shiya nake son ganin ya'yan'sa....dan ma ya tsotso nonon baƙin hali zuri'ar Fulanin daji...masu yin kiddinafin...,


haɗe rai tayi ta ƙarɓa ta fara duba wa bugu ɗaya biyu be ɗaga ba tsaki Hajiya ta ja tace


"Ko ubansa ina kira yaƙe ɗaga min balle shi maza kiramin Kabiru....,

kamar an hullo ta ahak ta shigo auzubillahi minal tsari Inteesar lafiyar ki ko gamo kikai...?

hajiya ya faɗa tana zaro Ido dafe da kirjin'ta

gyara zama inteesar tayi tace

"Hajiya umma ce ta biyo ni....,

da sauri hajiya ta tashi riƙe hannun inteesar tayi suka fara tafiya bin bayan su jidda tayi har shashin umma dake kofar kitchen hannunta riƙe da muciya bata lura da hajiya ba tace


"Wallahi inteesar sai naci ubanki ni zan haɗa kulli kina tsalle tsalle ki ɓarar min...,


A'a wallahi ubanta yafi ƙarfin ki ci shi saidai kanwar uwarki jimmai dubai ita za ki ci ubanta in banda iskanci ki biyo tatsitsiyar yarinya da muciya yawa kin kama ɓarawo anya ZARA'U kina son shiga aljanna kuwa


ƙasa dakai umma tayi tace


"Yi hakuri Hajiya bazan ƙara ba...,


Kima ƙara wallahi gun wayan nan mala'ikun duniyar (Dass) zan kai ki su sauya miki halitta su sassamaki wallahi


Iska ta furzar me huci tace


"Yi hakuri insha Allahu zan kiyaye...,


taɓe baki Hajiya tayi ta gyara zaman glass ɗin'ta tace


"Da time wanne be san halinki ba kina sumi sumi sai kabiru da har yau be gane ki ba.....,

ya'yan albarka ku shige mu tafi ai ba adaji muka ɗauko ku ba munsan darajar ku...Ni ban taɓa ganin wannan baƙar jarabar ba a yiwa yarinya aure ko kirgar dangi bata fara ba Allah ya kawo rabo aka sani a tashin hankali kwana nake ina leƙa mutum ka haihuwa tazo ba ƙugun haihuwa.....


Cije lips ɗin'ta umma tayi har yau Hajiya ta kasa dene Mata wannan gorin ko da yake inteesar ce ta jaja mata juyawa tayi ta koma kitchen in da sabo ta saba cin mutuncin Hajiya ba wanda ya kyale

Kam take duk kuwa da tarin shekarunta ji tayi an rungume ta ace granny granny
da sauri ta banɓare hannun Faisal zaro ido tayi tace....✍️


*Comments and reacting my lovely fan's mu haɗu a shafi na gaba....*


*Sauran page 9 in dena sawa a ko wanne group kuyi maza kuyi following ɗina*


*GIDAN MAGAJIYA*

https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k

EPISODE 8


"To rasa kunya wato ga tsohuwar wotiwo ko wacce bata da gata bara ka karya ni...,

sakin'ta yayi yace

"Granny nayi missing ɗin ki ne....,

batare da ta tanka shi ba nayi gana abin'ta su inteesar da jidda na biye da ita har part ɗin'ta zama sukai jidda tace


"Hajiya yau she za mu abuja....?,

sai lokacin da Sardauna ya dawo kinsan yanzu me nake so da ke....

kai jidda ta girgiza alamar aa

nasan ke ce zaki iya wannan aiki zauna a kusa da ɓangaran izzatu kiyi kamat wasa kike tana fita ki faɗamin yau zan tabbatar wa da mijin'ta abin da take aikatawa amma baya gani

t inteesar tace

"Hajiya bani kuɗi na siyo alawa....,

Singa zaki siyo ta ci gaba da taunar goranta

tashi tayi ta fita a baƙin shashin izzatu ta zauna tana wasa da dutsuna fitowa izzatu tayi tana waya tace


"Allah ko ai kuwa gani nan kice yau raƙashewa ake ...?,

sai ta saurara dan jin wacce amsa za'a bata tace


"harda yan daudo kai kice abin nayi ne gani nan bani minti goma ta kawo ni unguwar ku...,

tana faɗar haka ta kashe wayar bata lura da jidda ba ta fara tafiya tana gyara mayafin'ta da gudo jidda ta shiga floor hajiya tace

"hajiya ta fito...inaga

Please Login or Register in order to submit comment