Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

magajiya yace

"wallahi magajiya sai da wannan mutanan suka tafi hankalina ya kwanta gaskiya ban yarda da su ba....,


hhhhh ko kayi wani laifin ne da kake tunanin za a kamaka....,

cewar rabi

Rabi'u ba haka bane baka kallo takalmin dayan ba me tsadane fa

Harara rabi ya watsa mai yace

"ai kasan bani da ido ina jinsin mace kana sakani a jinsin ku....,

kai wallahi baka da hankali ni gani nake anya kuwa bakai suka biyo ba

saidai in lami suka biyo

da sauri yayo kansa iccen dafaɗikar uwani dinana ya zaro yace

"Wallahi yau in bakai wasa ba sai na kona maka jiki da fuska....,

bayan kahu ya laɓe yace


"Kahu kana ji kana gani za'a mai dani ƙawaro....,

hankaɗe shi kahu yayi yace

"In kuna abin ku ke dena sawa dani wallahi....,
wata uwar buɗe aka saki da sauri kowa ya jiyo a kuje rabi ya rungume rufa'i yace

"Ta Masar yau she kika dawo bani da labari...?,

wanda aka kira da ta Masar yaci uban eyelash ga jambaki yace

"Wallahi sau kar yanzu ina dan a shararle...?,

gashi can da sauri ta Masar ya zura a guje ya je gun Dan a shararle yace


"Sannu gidan yari ba dadi wallahi ranar da naji ance an kama Ka har sadakar gurasa nayi maka Allah ya saukaka maƙa hukunci....,


kallon ta Masar yake sama da ƙasa yace

"Rufa'i haka kazama bayan tafiya ta umara....?,

juyawa yayi yana juya ɗuwawu yace

"me ka gani nice dai wallahi...,

Magajiya wallahi Allah wannan abin ba dani ba kai haka kika zama ko wanne kwashe kwashe gidan nan ina magajiya ki canza hali wallahi ke ba sata ba ke ba yar iska ba amma kina tara yan isaka ai sana'a ba hauka bace ina jiye miki ranar da zasu goga miki kashin kaji

Kahu ya fada ransa a ɓace

Arziƙin kenan kahu bulama namu maganin kukan mu dinana ya fada yana shafa ƙeyar'sa

lallai kahu wallahi sun raina ka wallahi sun mai dakai yawa kakan su tofa dole ka tashi tsaye wallahi sumayya ya fada tana gyara riƙon katin karta na hannun'ta

Insah Allahu bazaki ci ba Shegiya me kan jimina ke dai anyi sheɗaniya muna da uba sama da kahu ne dan a shararle ya fada yana nunota da huƙa.....

tashi tayi tana tan gaɗi tace...

"Kai ƙaramin kwaro wallahi sanin kan kane yau na ga dama sai ka koma inda ka fito ni nake tare uban gayya....,


da hallacan rufen baki dan uwar....ki har Ni zaki faɗawa manya nine yaron dan siyasa me fada a ji a ƙasar nan wallahi

ai shi ya saka ya barka Kai wata shidda a gidan gyaran hali bata ƙarasa ba taji saukar mari be ajiye hannunsa ba ta dauki botikin karfe ta loda mai a gadon baya botikin rabi ya ɗauka yana waƙa kamar yadda ya saba yana kutaso babban kutaso ku taso ba me raba ku wannan fadan manya ne

zaro huƙar nan yayi da sauri.....✍️

*Ɗomin samun ci gaba da zarar na ɗora kuyi following ɗina*
*GIDAN MAGAJIYA*

OUMYASMEEN

Episode 18


Da sauri kahu ya riƙe mai hannu yace

"Sani sani karufawa kanka asiri wallahi kar kazo kana dana sani....ka kashe gawar da ba taka ba....ka kyale ta da halinta...,

Alkuran kahu da Ka barni na burburma mata huƙa a ciki na kanannaɗo hanjinta tace ba suna na Sani ba

karɓe huƙae kahu yayi yace

"Ke zo ki tafi maza ki bar gidan nan....,

kahu ba inda zani da ka kyalesa bilahillazi yaga ba dad'i Ni bakar fura ce dakan ibilisai har ni zai fadawa dabanci sai da nayi shekara hudu a lagos a ƙarƙashin gada mene ban gani ba ɗan iskan karya

fisgewa yayi daga hannun kahu da sauri kahu ya ruƙo shi a shar yake ta ɗurawa sumayya itama na mayar mai magajiya ce ta kashe hutar wainar ta da yake ta gama a kullum tana karar da fulawa kwano biyar tun daga safe har dare ban da kiras ɗin kwai ga abincin siyarwa tace

"Narantsai in baku dena abin da kuke yi ba zan tafi in kirawo yan vijilanti tun da yan sanda kun raina su haba wannan bala'in da me yayi kama a kullum in ba ai fada kadan ai yi gudu biyar na gaji ina fita ana nunani da Baki.....,

ai kema sai ki nuna su da bakin ba Ubangiji yayi miki shi ba rabi ya bata amsa jefomai ludayi tayi tace

"Innalillahi anya kuwa Rabi'u kasan abin da yake maka ciwo....,

Kallon mutanan gidan yayi yace

"Ku a cikin ku a kawai Rabi'u to dai koma mene Rabiu kacan za hali wallahi...haba wannan abu har ina...,

mayafin ta ta cira a kan igiya ta cire zanin da take sawa akan kayanta ta fita da sauri dinana ya riƙota yace


"Mun shiga uku haba uwar mu yanzu in kika fita kika kirawo mana wayan nan su kamayen ai kin cuce mu wallahi suna zuwa kwashe mu za su yi su ba a wannan ɗaki me uban sauro kin ga dawo kowa ya kama gaban sa dare yayi....,

rabi ne ya tawo yana gyara zani yace

"Wallahi mun dena ni yanzy wanna kashin na kaina sai sun aike min shi tas wallahi yar masa kuwa tab wannan direct hisba za su kai ta in ta dawo da fata jikin'ta sun mata me kyau...da imani...,


dafa kirji ta masar yayi yace

"Kut mele sin ubancan ni kaɗai ka raina kaf gun nan kana yi min mugun baki da alkaba'i....me kan sigari...,

ya faɗa yana cigaba da cin chingum tare da yarfa hannu awarwaron hannunsa suna bada sauti

Cika sani sani kahu yayi yace

"Allah yayi muku albarka ya gyara ku maza ka tafi... sai da safe...,

Ba tare da yaci komai ba ya fice sauran ma fita sukai aka bar wannan shabta sai kuma gobe ruwan wankan'ta ta juye ta zuba wani ta shiga bayi wanka tayi ta fito rataye sosonta tayi ta shiga daki sama'ila ne ya shigo ya rufe gidan ya shiga dakinsa

Osokoro..... Abuja

Laptop ɗin'sa ya buɗe ya kunna datar'sa wayar'sa ce tayi ringing da sauri ya ɗaga saboda issue ne me girma ne cikin girmamawa wanda ya kirashi yace sir muna kan online....

kashewa yayi ba tare da yayi magana ba shiga cikin inda suke meeting yayi kowa yana kai da alama shi kadai ake jira gyara zama a yana jiran me za su ce gai she shi sukai ya amsa jabir yace

"My colleague Habib M Jigirya and I have been investigating on the project from sending us now. Any time they can be caught, they will come out and find out where they got the stolen sim and phone....,

gamsuwa yayi da bayanan jabir yace

"Habib you confirmed that they kidnapped Nazeer....?,


There is someone who brought the phone to them and they bought it. We can investigate but when they come in, they will explain about it and they found it and we investigate

cewar habib

Kai Asif ya gyada cikin gamsuwa ya dubi chief of security yace


"So, in the morning, arrest them and we will investigate further, even though your information shows that you have arrested them for the crime...,

Chief of security yace

"Insha'Allah, we will intensify the investigation, as long as their blood is gone, we will end kidnapping in Nigeria...,

Jin daɗin abin da yace yayi sai ya ce

"May God seek us and cook for us...,

Amin suka amsa dashi sannan sukai sallama aiki ya ci gaba da yi ringing wayar'sa ta kara yi dauka yayi ganin aysha ce ta kira kukan ta ne ya ya doki kunnan'sa da sauri yace

"Sweet lafiya me ke damun ki...?,

cikin shagwaɓa tace

"Wallahi zaman asibitin nan ya ishe ni gashi kai baka samin time ɗin shigowa guna ko wannne lokaci baka da lokacin kan ka sai na al'umma in zaka zo kazo da masu tsaronka lokaci kalilan ka tafi.....Asif Kai na ke so ba kuɗin ka ba bana buƙatar kuɗi kullum Cikin turomin da kuɗi kake.....yau hajiya ta bugo min ba zagin da bata yi min ba...ta ƙara fashewa da kuka wai ni haihuwar nan ni naƙi bawa kai na ne...?,

dafa kansa yayi ya tashi daga inda yake komawa bedroom ɗin'sa ya zauna akan gado yace

"tun kafin ki aureni kinsan irin yadda aikin mu yake...sai kin ƙara hakuri in nayi ritaya za ki sameni kamar yadda kike so...kiyi shi ru kinsan bana son kukan ki...,

share hawayen'ta tayi tace

"daman nasan ba son laifin hajiya kake ba nayi maka maganar'ta kayi buruss dani....,

ajiyar zuciya ya sauki cikin kakkausar murya yace mata A'isha har yanzu kin kasa gane wace hajiya a guna duk wannan ni'imar da kike ciki ita ce sanadi domin duk wani karatu danayi ita ta ɗauki nauyina baki ga tsohuwa bace sai kinyi haƙuri da ita tsofa ne amma kin kasa yarda bana son wannan korafin

kashe wayar tayi ta jefar a da ita kallon'ta hidaya tayi tace

"ai gwara da kika kashe wallahi in baki tashi tsaye akan wayan nan banzayen yan uwan mijin naki wallahi son da yake miki sai ya dena ....,

Hidaya ya zanyi da su kina gani a gaban ki nayi wayar nan amma me yace min duk abin da kika kwatantamin nayi

ai wallahi tun farko ke kika bari yasan cewa kuɗin'sa kike so haba ga shinan ya sakar miki kuɗi amma ba farin ciki ko gaba zai iya yi miki gori kudin'sa kika gani kika manne masa


Hidaya nasan nayi kuskure ya zanyi da wannan result nifa ke da matsala bashi ba ko wanne lokaci ya gani zai iya karo aure saboda haihuwa yake so

ai shi yasaka nace miki za mu nemo mafita dole ki canza ki dinga yi mai biyayya fiye da da sannan dole mu bi malam mai su rufe mai baki duk wanda zai mai maganar haihuwa yaji ya tsane sa

nagode sosai kawata


Washe gari kano

da asuba kahu ya fito daga Masallaci bayan an idar da salla abin mamaki wasu mutane ya gani a cikin mota wasu kuma na dan zazzagawa rayawa yayi wata kila wani taron ya shige gida samin magajiya yayi a zaune ta idar da salla sai uwani da take tsakar gida tana wanki yace

"yau kuma da huri haka....,

Eh wallahi alanguburo ai gwara inyi da huri ya bushe da huri garin nan na damuna ko wanne lokaci ana iya yin ruwa

hakane wallahi kinyi da bara magajiya yau da huri haka

murmushi tayi tace

"kahu wallahi yau da huri na kwanta...,

ai gwara ki dinga haka ita sallah asuba kariya gareta

hakane kahu shiga ciki yayi haka kurum taji gaban'ta na waɗuwa amma sai ta ci gaba da addu'a gari ne yayi haske waje kuwa tuni ma'aikata suka zagaye gidan da bindigogi duk fuskarsu a rufe da baƙin yanki ga baƙin glass mutane suke liƙe ta sama domin ba damar zuwa ma'aikata ne guda hudu suka tiso keyar su dinana rabi sai kuka haka dinana har da majiya shiga cikin gidan sukai fitowar malam daga bayi kenan a guje ya koma yana cewa innalilahi yau na shiga uku ɗaya daga cikin su ne yace

"Baba fito ba abin da za muyi maka...,

jikin kahu yana rawa ya fito sauran kaɗan ya saki gudawa ɗayan yace

"Ina magajiya....,

"Gani me za a siya da sassafen nan Ku ishi mutane...ta fada tana fito daga daki turuss tayi ta zaro ido kirjin'ta na yin sama yana ƙasa kallon dinana wani daga cikin su yayi yace

"Wannan ita ce....?,

aa yallaɓe sunana falmata lawan maina wallahi kai dinana ni zaka gogawa kashin kaji wallahi ban taba aikata wani laifi ba bata ƙarasa ba taji dayan ya saita ta da bindiga yace

"kina kara wata magana sai na fasa kanki ina wayar da kika sata....,

da sauri ta miƙo mai daman tana hannun'ta ankwa wata mace a cikin su ta shigo ta sa mata kuka take sosai takalli kahu tace

"Kahu....✍️

labari ya zo tsakiya na kusan dena posting a ko ina ku hanzarta following ɗina


*GIDAN MAGAJIYA*

Oum yasmeen

*End of book 1 mu haɗu a book 2 shima free ne kar wanda yace ku bada kudi ya baku document har yanzu ban fitar da document ɗin'sa ba typing nake*

EPISODE 19-20


Kina kara wata magana jikin ki zai fa gaya miki tsit tayi tana kuka kahu na sharar hawaye ba baƙin magana wa'yannan Mala'ikun duniya na gabansa ɗayan ne yace


"Baba wannan wayar da ka gani kidnapping ɗin matar director Janal Asif kabir sardauna akai to wayar nan ta tace mun ƙama sauran Sim ɗin a hannun wa'yannan....,

Wallahi Allah siya tayi bata san abin da akai ba ita ce katan mu ita ke ciyar da mu
ko sauraran sa basu tsaya yi ba sai kokarin fita da suke da su

uwani kuwa tana kuryar ɗaka jikin ta na zikiri Allah Allah take subar gidan tusa ƙiyar'su akai kahu har waje ya fita ko wannan su mota daban a ka sa shi kuma prevent car a guje suka fice daga lahin su ka hau kan titi kuka sosai magajiya ke yi ta haɗa kai da gwiwa tun da take a rayuwar'ta bata taɓa ganin tuzarci irin wannan ba roƙo take Allah ya ɗau ranta ta huta tasan yau mutanan unguwa suna nan suna murna wannan abu ya sameta


miƙar hanyar Abuja sukai dan ko a bangaran'su na nan ba a ajiye su ba kai tsaye can za a huce da su ganin suna ta waya ta gane bama anan aza a ajiye su ba shikkenan mutuwar'ta tazo domin ta san tun da abin na manya ne fasa kansu kawai za ai ba za a tsaya bincike ba

karfe biyu suka isa abuja babban headquarter su fito wa sukai ita ma ta zuro kakafuwanta da ko talmi babu balle mayafi sai yar hular da take kanta ba sosai ta rufe tulin sumar kanta ba duguwar riga ce a jikin'ta buba abin mamaki bata ga su dinana ba kai Allah ya tsinewa kaska wani ɗaki aka shiga da ita duhu diɗim sai wani table a tsakiya sai kujera biyu kallon ta wannan jami'ar tayi tace

"ga gu nan zauna....,

zama tayi yayin da wahaye ba bin fuskarta fita tayi kai tsaye office ɗin director ta nufa da yake yace musu in sun dawo su kirashi bata tarar da wani cinkoso ba ta kalli sakatariyar sa tace


"zan iya ganin oga...?,

kallon sama da kasa tayi mata ta ci gaba da danna laptop ɗin'ta tace


"you can't see him because you are not in the appointment with him today he has a lot of work...,


cikin ɗaga murya tace


"She told us that when we came back from the operation, one of us came and told him that he wanted to meet them first....,

da sauri ta tashi tace


"You are raising your voice about the work of the men you took with you, but you are going to come and tell him.....,


dai-dai fitowar sa daga office ɗin'sa domin har maganar da wowarsu ta zo mai be tsaya kallon su ba ya huce su ta kaici ne ya ishi surayya tace

"burin ki ya cika sai ki huce ki ban guri....,


kallon inda take bata yi ba ta huce ta tare da jan karamin tsaki ta fita yana fita duk yawan ma'aikatan gurin sara mai su ja shiga yi kowa ya tsaya da aiki fuskarnan ba ɗigon annuri ya daga masu hannu domin ransa a ɓace yake da zuwan wannan rahoto mace mace har da mace me yiwa wani tarbiya ita ta saka kanta a cikin wannan hali koman daran da ɗewa zata zama uwa shiga yayi ya zauna har lokacin bata san ya shigo ba tana kuka ta kifa kan ta akan table hannayanta har yanzu na cikin ankwa lurar da tayi tana motsi tana ƙara dame hannun'ta dan haka ta tsayar da shi gu daya gyaran murya yayi hadi da buga table ɗin ɗago kan ta tayi idon'ta yayi ja tsoro ya bata tuni zuciyar'ta ta shiga harbawa zama ya gyara a ajiye wani abu akusa da shi yace


"ya sunan ki....,

buɗa baki tayi zata yi magana kuka ya ƙara kwace mata cikin tsawa yace


"Tambayar ki nayi da baki tanadi zuwan nan ranar nan ba mayanan ki ƙadai zasu fitar da ke daga gun nan inhar muka ƙara bincike muka ga baki da sa hannu a cikin wannan laifin amma in har sunan kiya fito nan gurin shine kabarin ki....,


jikin'ta ne yawa kakkarwa ta kasa koda motsi dan karin kumallon safe da tayi shi ta shiga amarwa iya tsorata ta tsorata daga nin wannan mutumin a gaban'ta saboda tsoro ta kasa tantance wane a agaban'ta harda yatsun'sa yayi ya ƙara cewa


"Tambayar ki nake ko sai nayi miki abin da zaki magana ba zaki faɗa mana ta dadi ba.....?,


kukan ta ne ya ƙara tsanan'ta tashi yayi ya fita cikin ɓacin rai ya kira wo wani shugowa yayi yace

"ga ta nan in har ba tayi magana ba ku mata duk kan wani horo har sai tayi magana masu cin amanar ƙasa kina mace kin banzatar da darajar da Allah yayi miki duk abin da za kiyi baza mu taɓa sassauta miki ba ko tausaya miki kone masu kona gidajan mutane kuna cin zarafin'su...,

muryar'ta a dashe tace

"ba sai kun min komai zan faɗa muku abin da na sani...,

fita yayi ba tare da ya tsa jin maganar'ta ba inda sabo ya saba da wannan rainin hankalin mutanan nan wasu ma sun gwammace a kashe su da su faɗi ubangidan su amma in suka sa musu na'ura dole suyi magana abin da basu shirya fitowar'sa ba dole su faɗa wani guri ya shiga inda rabi yake zaune zama yayi yace

"Ya sunan ka....,

kusan dai yadda yake magana haka yayi mai yace

"Rabi'u hamisu....,

tsawa ya daka mai yace

"daidaita muryar ka ko inci ubanka ba sunan ka rabi ba....to wallahi za ka dawo dai-dai ne..,

gaban rabi ne ya waɗi yace

"Eh amma wanda mahaifina ya saka min Rabiu.... saboda ta kaita dogon zance ake ce min rabi....,

wato kai da dan iska ko

shiru yayi jikinsa na rawa ko a mafarki be taɓa tunanin zai ga wannan tashin hankali ba

katsai masa tunanin yayi yace

"Wane uban gidan ku da yake saku wannan kidnapping...,

Narantsai da Allah ban san kowa me yin wannan harkar ba layi na siya agun kaska dina dinana bamu san cewa ga abin da akai da layin ba wallahi wannan ne kaɗai abin da na sani amma ban san wani masu kidnapping ba

haɗa rai ya ƙara yi yace

"taya akai wayar ta zo hannun ku in mun yadda cewa siya SIM kukai....?,

wallahi magajiya ce ta siya a hannun kaska duk tare muka siya yana zuwa gidan ta siyan abinci

tashi yayi ya zuba hannun a aljihu yace

"wato ba zaku faɗan gaskiya ba sai jinkin ku yayi tsami....,

rantsuwa ya fara yi amma ina har ya fita shiga dakin kusa da shi yayi inda dinana ke zaune zama yayi yace

"Wace ce Nuratu...?,

wallahi Allah ban santa ba ban taɓa ganin'ta ba

Cikin kakkausar murya yace

"tanan kuka bullo za ka faɗa gaskiya a cikin ku wace nuratu ko sai na fasa maka kai ya fito da yar ƙaramar bindiga yana saita kansa da ita fitsari dinana ya saki hakuran'sa har gwaruwa suke da juna saboda tsabar tashin hankali yace

"Wallahi Allah ban santa ba....,

cire bindigar yayi yace

"wacce aka kawo ku da ita ita wace ce....?mene alakar ku da ita....?,

magajiya sunan'ta

tsawa ya buga mai yace

"wato ka biyo tanan hanyar ne dan kar mu gane magajiya sunan gaskiya ne ...?,

sunan'ta falmata lawan maina yar garin Maiduguri ce sanadin haduwar mu ina zuwa gidan su siyan wainar'ta amma itama wallahi siyan wayar ta yi a hannun wanda muka siyi layin kaska..


wane kaska

a jalwala yake dan gaban mu ƙadan yana saida wayoyi da layi ka yayi mana talla layin unlimited credits card haka yace mana muka siya dubu biyu sannan yace muyiwa magajiya tallan wayar dan akaf cikin mu ita ce me sana'a kuma zata iya siya mukai mata talla ta siya yace zai kawo mata receipt jiya ya kawo min gidan mu yace tafiya ta kama shi na sashi a aljihun wannan kayan da niyar da safe in bata


kai ASIF ya jinjina ya kama hannunsa cire ankwar yayi yace

"fito min da receipt ɗin....?,

hannunsa yana rawa ya shiga laliban aljihun'sa cire wa yayi Asif ya amsa dubawa yayi washe garin anyi kidnapping ɗin su nazeer aka siyar da wayar kai ya jinjina ga sunan ta nan ma duk yadda akai me sai da wayar nan yana ɗaya daga cikin wa'yanda sukai kidnapping ɗin su nazeer wata kila ma yan uwansa basu san ya dauki wayar ba tashi yayi ya fita wani waje ya shiga kamar lap da sauri suka dena abin da suke kowa yayi mamakin ganin Ogan nasu saramai sukai ya miƙawa wani ma'aikaci yace

"kai min binciken wannan lambobin yanzu sannan ka dubu biometric hannun wa da hannu wa yaje sannan sai ka tura da sakon ma'aikatar kula da bvn wannan shatin hannu ya taɓa yin register da su....,

da sauri ya amsa yace

"to fita yayayi ya koma dakin da magajiya ke ciki iya wahala ta wahala domin shocking aka saka mata ko ɗaga kanta bata iya yi cikin ɓaci rai wata ma'aikaciya tace

"taƙi magana cewa dai take wallahi bani bani bace siya nayi....,

ku sata a dark room bata wahala bane ina tunanin sauran bakin su ɗaya amma su sunyi bayani ko wanne kareta yake suma ku kai su wani daki ku ajiye yana fadar haka ya fita dagata tayi ta daka mata tsawa dakyar take iya tafiya jikin'ta duk amai wani baƙin daki aka saka ta dakyar mutum zai iya tashi tsaye suka rufe kwanciya tayi idanuwanta na zubar da hawaye....✍️

*Allah ya raba mu da sharrin banji ban gani ba ya kare mu da taka sahun ɓarawo*

Alhamdullahi ayau na kawo karshen book 1 sai mu haɗu da ku a book two

An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you

Please Login or Register in order to submit comment