Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ita zai takurawa ta bashi ya siya kwafa tayi dole ta gyarawa kahun nata zama wallahi dinana ne ya shigo a guje yace


"Magajiya albishirin ki...,

kallon'sa tayi tace..

"Kaga faɗa min in zaka faɗamin basai ka tsaya jamin rai ba...,

lahi na siya a gun kaska to wallahi tun jiya nake waya kuɗin sunƙi karewa ga data sai tiktok nake gani haka ma rabi tare da shi muka siya yace akwai waya clean me kyau in zaki siya tunani ya shiga yi can ya tambayi rabi yace

"rabi yama sunan wayar da yan Film yanzu suke yayi...,

rabi da ya ɗuƙufa kallon tiktok yace

"iPhone 16...,

yauwa kinji dai sunan'ta gwara kema ki faso gari ace kamar ke kina yawo da rakani masai

zaro ido tayi tace

"kai dinana bana son iskanci wato Ni zaka mayar wata bi tacan ko ka kawo min maganar banza yau she taska yayi kuɗin da har zai dinga kasa irin wannan wayoyi masu tsada...?,

Kahu da yake kwance ya tashi yace

"Dinana nima ina son layin nan zan siya...,

zama yayi akan farin botiki yace

"wato kahu baza ka gane amfanin lahiin nan ba sai kira ya kama ka zakai ta magana da shi ba iya ka wallahi ɗazu ba muna waya da abokina nace ya jirani wallahi na gama uzurin gabana sannan na dawo muka ci gaba da waya amma ko girgiza kuɗin nan ba suyi ba...,

tsaki magajiya ta ja ya ci gaba da suyar'ta domin maganar da dinana yake yi bata ɗauke ta a hankali ba tuni wa yanda suke ca'ca suka tsaya da yin ca'ca suna shan labari abin takaici kahu da girman'sa ya tsaya ana zuga mai karya

tashi rabi yayi ya saita zanin da ya ɗaura ya sauke shi karaf suka haɗa ido da kahu da kullum al'ajabin halin Rabi'u yake kiri kiri ya maida kansa mace yau harda jagira da jam baki

da sauri rabi ya juya baya yace


"haba kahu kana kwanci kana kare mana kallo tsofe tsofe dakai kai da zakai wa su fada har wani karkata kai kake kana kallona ni wallahi kunya nake ji....,

sakar baki kahu bulama yayi ya tashi yace

"sannu dan kwal'uba wallahi ina jiye maka ranar da Allah zai maka babbakar tsire...,

juyowa rabi yayi ya saki kwai yayi wani fari buga hannu yayi a cinya yace

"ban sa baki da me dattin hula ba...,

yowa kan'sa kahu yayi da sauri ya dauki hijabin uwani ya saka wani chabka kahu ya kai mai yace

"dan uwarka cire min yau nake jij sabuwar shegan'ta ka hijabin matar tawa zaka saka.....,

shikke nan karshan duniya yazo ba'a kunyar cin zarafin ya'ya mata wallahi daga nan hum right (human right) zan kai ka ko hisba dole suyi min tsakani na dakai yana fada yana matsar kwallah

wallahi kana zuwa kama ka za suyi kama saukaka musu aiki ai daman irin ku zuke nema kwaton banza wallahi magajiya ki rufawa kanki asiri ki dena tara masu laifi a gidan nan wata ran da zasu jajamiki ko su kawo miki kayan sata ki siya....✍️


Kuyi following ɗina domin samin ci gaba da zarar na ɗora

*GIDAN MAGAJIYA*


https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k




*`EPISODE 12`*

Dasauri dinana ya kalle'sa ya bude baki zai magana rabi yace

"Wallahi kana magana sai na dauke ka na bugaka da kasa da wani shegen kugunsa yawa an tada akuya tsaye....,

magajiya da abin su ya ishe ta tace

"wallahi Allah zan kirawo yan sanda su kwashe ku ni zaku tozarta ɗazu nan sai da masu gidan nan su kazo wai ina tara mutanan banza..,

da hallacan sake ni shaƙe huyan'sa yayi a cikin hijabi sannan ya cire da yake a yanzu ba shi bane a gabansa ba ya kyalesa kallon magajiya yayi ya kama haɓa yace


"wanne dan durin uwarne yake mana kallon hadarin kaji har yake ce mana mutanan banza billahillazi magajiya sai kin tashi tsaye akan ya bani na iya...,

yana faɗa yana buga cinya hadi da rausaya da fari


kyale su rabi wallahi zan iya da ko wannen shege zama daram ya na me na ƙuda a nan gidan sannan gobe dole muci uwar sabada sheɗan ma ɗan kallone

shoki ya kwaso yace

"Wa bikin dawowar ɗan ashararle ai dole sheɗab ya zama dan kallo Alkur'an dole mu bawa maraɗa kunya...,

kai kahi ya girgiza ya koma ya zauna yana kallon kuɗurar Allah daman ba faɗimatu ce ta ɓata ba falmata ce ta ɓaɗa wannan abu da me yayi kama haka kurum ta barsa da jaraba dinana ne ya katsai shi daga tunanin'sa jin yana cewa

kinaga yan daba yan daudo karuwai masu dan malele yan balaja'u impart ma ba wanda baza mu gayyato ba indai shima irin mune gobe iwar haka unguwar nan ta cika da ƙamshin wiiwiii


gyara ɗaurin ɗan kwalinta tayi ta daɗa kar kace shi tace


"ashe naka wasa ne har kamru...uwar laifi sai ansha ta yarda za'aji dadin harka...,

Ke magajiya

ɗago kai tayi tace

"Yees kahu what happend to you....?,


Eh Lallai iskanci ya ci uwar nada to wallahi buɗe kunnanki ki auro fahimta baliga ki sawa ƙwaƙwalwar ki yasin ba a gidan nan ba ni zaku jawo ayi sama damu sai anje can a tantance uban laifi to banyar da ba ban laminta ba


wani kallo tayi mai ta koma ta zauna shewa saudat me idon cin naira tayi tace


"Allah ya bar mu dakai tsoho ka fiye shiga sabgar da ba ruwanka dole muyi bikin dawowar dan ashararle daga gidan dan kande...,

to mara kunya fitsararriya ke kikiyaye ni wallahi na kusan kawo muku yan hisba wannan wanne irin sheɗanci ne


Uwani ce ta fito tace

"Haba alanguburo kadena biye musu kai ma sai kaza su....tunda dai gaskiya ce basa so ka barsu ai ita duniya tafi bagaruwa iya jima...,

Allahu akbar duk kansu suka hada baki suka faɗa magajiya ta cafe zancan tace


"Ina uwani take to wallahi kar kiga ina raga miki ban ƙiba in cire zani inyi zigidir mubawa hambata iska aga sabon jini ke burin ki kullum ki haɗamu da kawo bayan iya biyayya muna yi mai....,

rasa bakin magana kahu da uwani sukai anya Magajiya kanta be taɓoba tab in iskanci yayi iskanci mutum zama yake mahaukaci rabi ne yace


"Fada dai mata Allah ya barmu da kahu kaga aurena...,

sai ya janyo zaninsa da yayi ɗaurin kirji ya rufe fuskar'sa wai yaji kunya gabaran ku dai masu gida da sauri ko wannan su ya jiyo ashone yake wata irin tafiya riƙe da akuya a hannun'sa cikin muryar wanda ya sha yayi manƙas yace

"yau magajiya ya kanwar uwata da nace miki zan kawo miki ya kunbo yar liti....,

me zasu yi in ba dariya ba magajiya tace


"Ehhhhh bashakka ka sha wacce tafi ƙarfin'ka akuyace fa a hannunka...,

da sauri ya kalle hannun'sa fuskar kanwar mahaifiyar'sa ya gani yace


"Wallahi zanci mutuncin ki magajiya yakunbon nawa kike cewa akuya....,

tashi tayi ta fara mici mici da ido ta kankan CE shi tace


"Kul kul asho faɗa da aljani ba riba ban shiga dawa ba sai da na shirya ta faɗa tana dunamai dantsan hannun'ta ta ci gaba da cewa Wallahi ina naushin ka sai ka dawo cikin hayyacinka mutuncina yayi yawa ka cishi....,

zama yayi ya janyo kan akuyar cinyar'sa wani kuka ta saƙa na wahala rarrashin'ta ya soma yi yace


"wallahi dole ki kuka wacce kike ganin kin yi jika da ita ta zata kalleki ta ci miki a kuya...,


Dinana ne ya taso yace


"Gaskiya kam amma kasan me asho...?,
kai ya girgiza mai be damuba ganin halin da yake ciki yace mai


samu za kai ka siya mata wainar nan tunda kaga magajiya mu da muke mata aiki bata bamu ba balle kai da ba cas ba as ko ta dubu ce ko bakin cikin da take ciki zai yaye


kuɗi ya zaro dubu biyu yace


"Miƙawa yar hau ɗin nna ta bani ta naira ɗari ita naga zan iya siya mata....,

da sauri dinana ya amsa yace


"to ki bawa yakumbo yar liti akuyatun ta dari sauran kuma sai ki miƙo min in saka a bakin salati tun da banza ta samu....,

amsa magajiya tayi ta soƙe a kugun'ta soya mai tayi ta miƙo mai sakawa wannan akuyar yayi a gaba aikuwa akuya ta faraci

Buga kofar gidan akai da karfi da sauri magajiya ta ɗago yan sanda ne guda biyu sai babar dan asabe da shi dan asabe tana ta sababi wallahi bazan yarda ba in banda iskanci sata har da rana a kwace akuya a hannun yarona saboda shi bashi da ta ido har da cewa wai kanwar mahaifiyar'sa ce to wallahi yau zanci ubanka daga kai har be taraku...

wata dariya magajiya tayi tace


"Sweet sajan bala kana ji wannan tsohuwar kilakin na cewa za tayi magani na shin bata san wacce ni ba ko bata san wannan gidan ba me kayan aiki in da arziki kazo mu tareka inda tsiya ce mu tare aka zo dai-dai da kai....,


dariya yayi ya shafa fuskar'sa yace


"Beb ina zata sani saidai yau ta ganewa idon'ta ke hukuma ce sai rarrashi kinyi taki kinyi ta wasu....,

rausaya kai tayi tace

"Maza ɗauke wannan shagalallan kayi gaba dashi inban da iskancin asho ina shi ina satar a kuya memaƙon ya sato abu me kauri maza wartsake dan uwarka....,

ta faɗa tana saita shi da farantin silver saitawa akuyar nan ledar waina yayi dan shi beyi zaton ma dashi take ba


bazato na tsammani yaji anyi sama dashi da sauri ya saki wani ihu yana cewa wayyo yakumbona kina gani ana yi min rashin arziki

kama a kyar'ta babar dan asaba tayi ta fara tafiya da sauri sajan bala ya sake asho ya tare hannua yace


"bani kuɗin man mota....,

da sauri ta kalle'sa tace


"daga wambai ne i zuwa wannan sai na baka kuɗin mota ai naga a kafa muka zo....,


haɗe rai yayi yace


"kar ki raina min hankali ƙafafuwana ba mota bane har da kuɗin wankin takalmi kin jawo takalmina yayi darty......,

wallahi ko karfanfana bazan bayar ba ai gwamnati ita ta dauke ku dan haka ita zaka faɗawa ta baka kuɗin mai bani ba

ofisa gaskiya wannan matar ta raina ka kana faɗa tana faɗa dole ka saita mata kai ko a bayan kanta ne ka sata ta fahimci me ce duniyar.....cewar rabi.....✍️

Domin samin ci gaba da zarar na ɗora kuyi following ɗina na kusan dena posting a kowanne group sai channel ɗina Please yan aljanna a dinga sharing

*GIDAN MAGAJIYA*


https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k

*`EPISODE 13`*


Gaskiya kam yannan kuwa basai an jima ba zan koya mata darasi mafi girma sanin halin yan sanda badai sharri ba ta ciro kuɗi a kugun'ta ta bashi amsa yayi dubu uku ce ya sakar mata akuyar'ta tafiya tayi tana Allah ya isa a zuciyar'ta....

da sauri rabi ya tashi yace

"Ofisa bani nawa kason...,

wata harara ya zabga mai yace

"Yar barno yimin zubin alfarma har da nama...,

fara zuba mai abinci tayi da naman kaji ta miƙa hannun'ta tace

"Inji dr Aliyu me barno....,

dubu ɗaya ya cilla mata yace

"a gabakin ki dai na sami kuɗi yau ni ba matsiyaci bane....,

Owo maka bana bada bashi daga bada bashi sai a karya mutum ta ɗauki kuɗin'ta

Kaga magajiya tundaga nesa nake gano hasken ki na haskaka gidan nan ɗago fararan idanuwanta yi ta kalli kaska tace

"gama banbaɗancin naka sai ka bani sannan zan baka....,


haɗa rai yayi ya riƙe giya yace

"Tabbas waya fada miki ni yanzu ina cikin talauci tun da na sami kaya a Abuja tofa kakata ta yanke saƙa akwai labulaye zannuwan gado zan kawo miki ki kasa sannan akwai waya kirar iPhone 16 wallahi....na sallama miki ita a dubu dari uku kema kyasan me duniya take ciki....,

kafito fili kace ta tashi daga magajiya ta koma dillaliya me ya mai dake nan an faɗa maka yan gumamane....?,

yauwa rabi faɗa mai aini na rasa baƙin magana wallahi

Wai kai me isaka baka da kirki ne duk wasu alamun taɓewa sun bayyana akanka amma saboda kai ɗamsil basiratu ne kakasa fahimta Allah wadaran naka ya lalace na tabbata kai ka hana ƙananan ka aure wazai yarda ya auri kanwar ɗan daudo gardo kawai


wata uwar buɗa ya saki yace

"Masha Allah Allah malam idi me gyaran hula to buɗe kunnuwanka ka jini da kyau wallahi kai wasa zan saka ai maka dukan tsiya wato ashe kai kake sheganta min ƙanne har suka kasa aurowa haka kakeso ka faɗa ko to yasin daidai nake da kugun idi da harira.....,

damƙar kirjin'sa yayi wayyo Allah magajiya kika kallo ana cin mutuncin ɗiya mace amma kinyi shiru saboda iskanci har taɓamin nonona yake dahallacan cika ni ni ba yar iska bace

Kai Yahaya ci kashi wannan da kake gani yayi nisa baya jin kira cewar kahu bulama

Cika shi yayi yace

"Kahu da ka kyale'sa nayi ƙasa ƙasa dashi ɗan iskan ƙarya....,

Owo dai ba'a taɓa kamani ba ina latsai yaran mutane ba

gyaran murya magajiya tayi tace

"ku dakata kaska muga wayar....,

cirota yayi fara da ita me kyau amsa tayi ta jijjoyata tace

"Faɗamin gaskiya bana son siyan kayan sata sannan ka bani receipt...ɗin'ta...,

haɗa rai yayi yace


"kedai bani kuɗi innaje kasuwa zan rubuto miki sai in bawa ko dinana ya kawo miki....,

sakar baki kahu yayi yace

"Magajiya me maƙon ki siya mana kayan abinci ki ajiye mana kin sani bani da karfin fita nema sai ki ƙuƙe ki siyi waya....,


Kahu zamaninka ya huce ko nayi maka explanation wallahi baza ka gane ba wallahi....,

Cewar magajiya


ta'ina zan gane tun da gani tsoho mara fahimta

Dariya dinana ya saki ya ɗago daga cacar da yake yace

"haka abin yake kariga kazama sorry...,

rubar dake kusa da shi ya cillowa dinana sai a fuskar zubeey da sauri ta tashi tace

"Kahu yanzu fuskar'tawa zaka fasamin saboda ni ka fi tsana duk a bin da suke maka...,

yi hakuri zillaziya wallahi bake nayi niyar jefowa ba ga kima godewa Allah yarda fuskarnan taki ta zama yawa ɗanyan nama bata kwabkwaɓo ba dan wallahi gani nake zungura ka ɗan za a yiwa fuskarki in ga nama a ƙasa yana yawo wallahi zillaziya ki rufawa kanki a siri ki dena wannan shafe shafen....ga hannunki yawa anyi gobara ni wallahi
mutanan da suke ma'amalla daku suna ƙoƙari wallahi duk warin mai kuke ga rashin wankan tsarki....turaran ku da ban tsamin ku daban kisan duk abin da ake ce Allah ya hana tofa wallahi sai anga bada dai aka yi shi


haɗa rai tayi ta zauna ta ci gaba da ca'carta tana murguɗa baki tabarmai rabi ya hau ya zauna yace


"Hhhh wallahi ya riga ya ciki 1 -0 ke kuma kika yarda shifa kahu in ba faɗamai magana kake ba to wallahi baza ku daidai'ta ba....,

to munafiki ina jinki tanunamin da sauran tarbiyyar'ta wato ni ka mai dani sa'an wasan ka


Duk abin da suke magajiya na jin su amma tayi burus saboda tana duba wayar da kaska ya kawo mata ɗaukan karamar wayar'ta tayi ya faɗa mata account number din's a ta samai kuɗin yayi gaba yana cewa

"gobe insha Allahu zaki ga receipt....,

kai ya ɗaga mai ya sowa sukai suna tayata murna haɗi da ɗaukar photo


*Abuja...Maitama Avenue, P.M.B. 253, Abuja*
*Yellow House*


Sosai suka ɗuƙufa wajan neman inda wayar Aysha take ta wannan hanya ce ka ɗai za'a san suwa ye sukai kidnapping tunda har yay basu nemi kuɗin fan'sar security ɗin gidan' director general da suka ɗauka jabir ne ya ɗago kan'sa duk da Ac da yake cikin amma gumi yake yace

"Sir wayar da komai tana kano abin da tracking details ya nunamin komai yana wani gida house number 178 kofar mata...,

da sauri ya taso haka ma sauran wa'yanda gamaki ɗayan su sune masu kula da shashin bincike na gidan ƙarɓar laptop ɗin yayi ya shiga kan gidan zooming din'sa yayi ya kurawa gidan iso yace

"Jabir Habib tare zaku tafi yau Kano amma taking care ba za mu kama kowa ba sai munyi kwakkwaran bincike abin da kuka ga gidan ke ciki a sufar za kuje sannan a unguwar kuyi takatsan tsan sannan ku binciki me gidan yake ciki...,

to suka ce mai suna ƙara duba yadda yanayin unguwar yake tashi yayi ya ɗauki files ya zura a briefcase wan daga cikin su ne ya ɗaukar mai suka fita direct in ya ajiue motar'sa suka nufa buɗe mai yayi ya shiga ya mai da kofar ya rufe a seat ɗin baya a ajiye briefcase ɗin'sa fara driving yayi a hankali kasan cewar baya son comber a komawar'sa gida ko security tafiya yake cikin natsuwa wayar'sa ce ta shiga ringing banza yayi da kiran ganin sunan hajiya yanzu sai ta ɓata mai rai da lokaci gashi kuma yana driving shi mutunne me taka tsantsan sa doka wani irin murɗaddan haline da shi da huya ka gane inda ya dosa hajiya ita kuma kira take ba kakkautawa yawa wanda ya ci bashin'ta


dariya abin ya so ya bashi yanzu haka yasan taji ya dawo garine baya tsammanin ko a mafarki zai iya ƙara aure ko mece damuwar hajiya da rashin haihuwar'su shifa jika ne ba ɗa ba duk da ita ta riƙe shi isa gida yayi horn yayi da sauri me gadin ya buɗe haɗi da saramai ido ya kuramai kafin ya amsawa sojan dai-dai'ta parking ɗin'sa yayu ya buɗe ya fito briefcase ɗin'sa ya ɗauka sosai ta baƙin glass ɗin'sa yake ƙarewa sauran sojojin da suka rage mai tun da har yanzu ba akawo mai wasu ba ayar tambaya ya sa musu

taya har sukai sakaki hakan ta faru me isaka su ba a kwashe su ba sai aka zaɓi wasu kau da kai yayi ya tsaya a gaban kofar da zata kai shi floorn sa tantance shi tayi sannan ta buɗe mai da yake a ɓangaran'sa ba'a binda aka taba mai kunna switch yayi tuni haske ya gauraye floor tamkameman photon'sa ne sanyi da kayan aiki da baƙin glass da suit baƙa ya saki wani murmushi har sai da hushiryar'sa ta fito

ashe daman annuri yana yiwa fuskar'sa kyau

Ajiye briefcase ɗin'sa yayi ya buɗe fridge ruwa me sanyi ya ɗauko ya buɗe'sa ya kafa a ɓakin'sa sai da ya shanye tas sannan ya saka robar a dustbin wayar'sa ce ta ƙara ringing da sauri ya dauka sallama yayi ba tare da ta amsa ba ta rufe shi da faɗa tana cewa


wato sardauna ka nunamin ban isa da kai na yau wa'aɗin da na ɗiba maka ya cika amma banga alamun zan samin yandagwai dagwai ba sai ma karyar an shiga gidan ka anyi kidnapping bata da lafiya ni za a mayar wotiwo har da bugawa a shafin jaridu kai da jaridun naci uban...ku to wallahi ko Kabir isa ba inshin fiɗa mai doka yaƙi bi ballana kai....


limshe idanuwan'sa yayi yace


"yi hakuri hajiya ina kan hanya kika kirani...,

rufemin baki ko in zubar maka da haƙora har ni zaka fadawa hanya ke duk wani karya da sokulle ba abin da zaka faɗamin wallahi tun huri in ganka a kano kafin ranka ya ɓaci tun da su basu dami da jika ba ni na damu da shi barin shashashar uwar ka baka gaban'ta ni nata ɓa ganin uwa irin mahaifiyar ka illar fulanin daji kenan in suka sa kansu a gabas to ba waiwayan yamma....✍️


*Kuyi following ɗina domin samun ci gaba da zarar na ɗora*


*GIDAN MAGAJIYA*


https://whatsapp.com/channel/0029VaLdFeg4SpkQ9xyW5c0k


EPISODE 14

Runtsai Ido yayi yace

"Hajiya zan duba in gani...,

ka duba uban..ka Asif wallahi ka fita a idona in rufe ni sa'ar wasan kace

kansa ya dafa da yake sara mai saboda ihun da take mai a ka yawa zata fasa dodon kunnan'sa yace

"Allah ya baki hakuri hajiya hakuri me tatda rabo insha Allah zaki ga wata ran kin sami abin da kikeso....,

salati ta fara tana cewa aww wato ni kaɗai nake son haihuwar ban da kai...to ka shekara dubu baka haihuwa ba damuwata bace daman nasani tuni aysha ta gama cin ye maka kurwa baka ganin kowa da gashi sai ita ke hauwa'u kashe min wayar nan zai sa hawan jini na ya tashi saboda shi imaninsa ragaggene ta miƙawa jidda wayar

jin abin da tace yadan murmusa ya kashe wayar tashi yayi ya shiga bedroom ɗin'sa iya kyau da tsarowa yayi komai na ɗakin farine tas a hankali fararan curtain ɗin ke motsawa sakamaƙon haɗari da ya gaggamo rufe windows ɗakin yayi ruwane ya tsuge yawa da bakin kwarya cire kayan'sa yayi daga shi sai boxer ya shiga toilet shower ta sakarwa kan'sa ba tare da ya cire boxer ɗin'sa ba limshe idanuwa yayi yana fatan ace a wannan karon yaci nasarar kama nuratu

ganin tunanin zai mai yawa ya cire boxer ɗin'sa ya zura a cikin washing machine ya fara wanka yana gamawa ya ɗauro toilet ya fito samu yayi wayar'sa na ringing da sauri ya ɗaga ganin AYMAN ne ke kiransa yaya wallahi mutanan gari sai zaginka suke yanzun nan yan kidnapping sun yiwa security ɗin gidan ka video a take anan suka kashe su....mujallu sun saka haka gidan radio da television sun ɗora

Innalillahi wa'inna'ilaihir raji'un haka ya dinga na natawa idon'sa yayi ja yawa garwashi lips ɗin'sar har motsi suke saboda tashin hankali kashe wayar yayi ba tare da yace komai ba zama yayi ya rasa abin yi be fiye hawa media ba amma a yau aji sha'awar ya shiga yaga me ke gudana wayar'sa ya ɗauko ya shiga Twitter shafin Farko na labari BBC labarin suka wallafa duk da yaci karo da uban notification dayawa ga inbox ɗin'sa ya cika da messages besan ta ina zai faraba.....

ya kamata ace ya warewa social media wani dan lokaci da zai dinga sanin me ke tafiya dole ya ware wani fake account da Zai dinga sanin me ake ciki wanne temako zai iya bayarwa a matsayin'sa na shugaba kuma musulmi

Video ya shiga ya ga dan taddan yana cewa

"Iya Ak sardauna to ka saurare ni ko iyayen gidan ka karya suke su kama ni balle kai video ne ya datsai daga nan inda ake mahawara kan video wani dan jarida yana cewa


"Ina manyan arewa wannan abin mu ya shafa shin baka tunanin ha ɗuwarku da Allah wanne abin rainin hankali ne inhar yana da waya har ya Iya video tofa za'a iya kama shi ta wayar nan za kuma a iya sanin inda yake musamman ma Ak sardauna kana ji kana gani a matsayin ka na shugaban dss wanda saboda kai aka kama wayan nan bayin Allah suna da iyalai suna da yan uwa amma kayi burus baka bi ta kan su ba gashi har sun kashe su a Nijeriya gabaki ɗaya ba'a maganar adalci kana da dukiyar da zaka iya biyan kuɗin fansar su inba baka saka annemo inda suke ba
ada mun zata kai me kishin arewa ne ashe bahaka bene

Dayan dan jaridan ne yace

"Munyi kokarin jin ta bakin'sa lokacin da abin nan ya faru amma me magana ba da uban hadarin nan mutane sun fito sun fara zanga zanga-zanga dole ya sauka daga kan kujerar sa tunda ba zai iya ba .....,

Kashe wayar yayi ya ajiye karar shigowar message ya gani da sauri ya ɗauka dan a tunanin'sa Ayman ne ya turo mai wani abu zaro ido yayi ganin prevent number CE tayi mai messages ɗin kamar haka

*DILA SARKIN WAYO DA KAYI TUNANIN ZAKA GAMA BINCIKEN KA KA CIN MANA....KAYI KUSKURE*

mai maita saƙon ya shiga yi kamar ba hausa aka rubuta ba saboda wani sarkakiya dayake tunanin anyiwa saƙon akwai na kusa da shi da yake fitar da sirrin su ba tare da sun saniba.....

saka kaya yayi ya ɗauko Kur'ani yana karantawa har lokacin ba adena ruwan ba ganin lokacin magarib yayi ya tada akbarar sallah ya dade yana addu'a a sujjadar karshe Allah ya kawo mai ɗauki bayan ya idar ya ci gaba da karatun sa har aka kira sallar isha sai karfe biyun dare ruwa ya tsaya bayan ya gama lafila ya kwanta


***********Kano unguwar kofar mata


Da asubar fari magajiya ta fito riƙe da buta a hannunta tsayuwa tayi tana tunanin yadda zata zuba ruwan nan a jikin'ta dole ta nemi gas kodan wannan yanayi da suke ciki na damuna kahu ne ya dawo daga masallaci ya riƙe haɓa yace

"Falmata sai yanzu zaki salla anya kuwa...da ilimin ki amma kin mai da kanki tamkar wacce bata san me take ba kin raba dare kina charting....,


shiru tayi mai ta shiga bayi da sauri ta fito ko gama wanke fuska batayi ba

Please Login or Register in order to submit comment