Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

alama bai ji wani
matsugunni da zai aje Nusaiba ba.
Sallama tayi masu, tana dan murmushi, suka
amsa ta ce.
"Kuyi hakuri, ku na ta tsayuwa ko?
Sannun ku da zuwa."
Sageeer ya ce,
"No,
kar ki damu.
Ai ba mu wani dade ba.
To ya ki ke?
Ta ce,"Lafiya lau.
Ku k'araso ciki mana."
Ta fadi tana duban Naseer ido cikin ido. Kwarjinin
Naseer ya zarce na yadda ta ji, a ganin sa na
farko a hoto, shi yasa tayi saurin kauda idonta.
Bismillah!
Ta wuce suka biyo bayanta
zuwa babban falon gidan,
wanda ba kowa ke shigar sa ba.
Naseer da Sageer, sun ga launanin abubuwan
rayuwar duniya cikin falon nan, kai ka rantse ba
za'a ta6a barin duniyar ba.
Bayan sun zauna, ta gaishe su cikin kunya da
ladabi.
Abin ya burge Sageer, yanayin yadda ya ga
Nusaiba.
A na shi gannin, bai ga wani abin ki ba. Shi kuwa
Naseer ba dole bane ya so wannan yarinya, duk
da tana ingattatun abubuwan bukata. Shi abin
daya sani Zara yake so, ita ya za6a, ita kuma
yake son ya aura ya zauna da ita iya rayuwarsu."
Bayan sun kammala gaisawa, ta mike tana
fadin,"Minti 2,." Sageer ya ce,"Mun baki."
Ta fice tana fara'a.
Suka kalli juna jim.
Sageer ya fara murmushi.
Naseer ya kauda kai. Nan da nan ya hadiye
murmushinsa, ya gyara zama a kujera.
Ya fara lissafin zuci. Da sallama ta sake shigowa,
dauke da dogon tire fari, shake da kayan lashe-
lashe da shaye-shaye.ta aje masu.ta zuba
(Drinks)' kala-kala, ta koma ta aje gaban sa, "Ku
sha ruwa."
Sageer ya ja robar Swan, ya dauki kofi,"Mun gode
Malama Nusaiba." Ta koma gefe ta zauna.
Sageer ke ta magana." To, ga fa aboki na Naseer.
Ni kuma suna na Sageer.
Ya ki ka gan shi? Ya dan sadda kai kunshe da
murmushi ta ce,
"Dai-dai."
Yace kin tabbata, yadda ki ka yi mana dai-dai,
haka shi ma yayi miki? Ta gyada kai, tare da
fadin "Na'am."
A karkace Naseer ke kallon ta, tana amsawa, ya
numfasa, kamar wanda zai fadi wani abin kirki.
Duk da yana son yayi mata magana, amma
rashin sanin abinda zai fadin, yasa shi yayi shiru,
kamar ba shi ba.
Saboda haka ya bar Sageer , yana yi masa tad'in.
Ya ce,"Gaskiya mun gode da fatan Allah ya sanya
albarka a cikin abinda za'a kulla.
Sannan wani hanzari ba gudu ba.
Abba yayi miki bayanin akwai uwargida ko?
Ta ce,
"Eh."
Ya ce,"Ina fatan za ku hade kan ku kamar Ya da
Kanwa. Zarah babu ruwan ta, kuma tana da
hakuri da hankali. Koda aka gaya mata zai aureki,
addu'a kawai tayi, tare da fatan samun hadin
kan ku."
Hankali kwance ta ce,"Insha Allahu babu matsala,
domin shi shirin Ubangiji kullum alkhairi ne ga
bayin sa, idan ka ga akasin hakan to laifin daga
mu ne 'Yan-Adam.
Saboda haka ni ma ina mana fatan alkhairi tare
da fahintar juna."
Sageer ya jinjina kai, ya ce,"Amin.
Naseer ka ji, ko kuma in bari in ba ku wuri ku
gaisa."
Ya dan muskuta ya ce,"Ina jin ma idan ma za
kayi zaman ka, babu damuwa, ai ni da kai ba
bambanci.
Duk abinda ka fadi tamkar ni ne na fade shi."
Ya riga ya gano shi, don haka ya ce,"Haka ne,
amma waka a bakin mai ita, ta fi dadi, ko
Malama Nusaiba?
Ta ce,"To ni me zan ce?
Ya mike ya ce,"Bari dai na jira ka a mota.
Malama a fito lafiya."
Ta ce,"Kuwa ba ka zauna shiru kai kaidai a mota.
Ta mike, "Zo mu je." Ta fice ya bubbuga kafadar
Naseerr, sannan ya bi bayan ta.
Wata kofa ta bude, sai ga su a wani matsaikaicin
falo. Ta ce ya zauna ta kunna masa T.V. "Wane
( Channel) Ka ke so? Ya ce,"Bar min labarai, na
gode."
Ta fita, jimawa kadan suka dawo tare da Mariya,
dauke da kayan abinci da na sha, ta aje masa."
Duk ni kadai?
Tayi murmushi," Duk kuma na ke son ka cinye."
To na gode."
Ta sa kai ta fita.
Sageer yayi kishingide a kujera, ya cigaba da
kallon sa.
Tana sallama babban falon. Naseer na daukan
waya, "Yaya B, ya aka yi ne? Ka na wane gari ne
yanzu?
Ya ce,"Tafiyar nan bata yuwu ba B. Sai dai mun
hadu, ka ji labari. Ina ma Kaduna a halin
yanzu.......
Takaici yasa Naseer B, ya kashe wayar sa. Jin
shiru. Shi yasa shi ma ya cire ta a kunnan sa.
Ya gama 'yan latsen-latsen sa tsawon lokaci,
kafin ya dubi inda Nusaiba ke zaune. Kanta a
sunkuye yake, don haka ya ci gaba da hararar ta.
Jikinta ya bata ana kallon ta, saboda haka ta dan
dago ba zato suka hada ido.
Yayi sauri ya janye na sa...................
______________________________
Masu karatu, yaya za ta kaya ne? Wace badakala
za ta faru a wannan labari? Ga Naseer Ga
Nusaiba, cikinsu wa zai ci gari? Na yi gaba a
dangaraman jirginmu na (MAIZAR AIRLINE). Mue
je zuwa, wai mahaukaci ya hau Kura.


Zaharaddeen Shomar

Whatsapp 08168575100
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels


Please Login or Register in order to submit comment