Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da kishi, ga mari ga
tsinka jaka. Kin fa san mu maza mun fi ku zafin
kishi, illa iyaka na mata ne ya fi bayyana. Dole
Salis ya rasa na yi, tunda kin ce ba ki tare da shi.
Yayan ki, ki ka fi so ko?"
Ta saci kallon sa tana d'an murmushi ta ce,"Kai
wanne ka ke ra'ayi?" Yayin da wata bus ta tsaya
gaban su. Ya ce,"fad'a 6ata baki. Shiga mota
kawai mu isa gida." Suka shige cikin mota, ta
sauke su inda suke son sauka. Sageer ya biya
kudi.
***************
Washe gari Sageer na tare da Naseer a gidan
yari, kuma ya samu nasarar ganin sa. Zaune suke
suna nemar wa juna mafita.Gaba d'aya hankalin
Naseer a tashe yake kuma ya fi karkata ga
k'aunar jefa Sageer cikin maganar da babu
hannun sa a ciki. Saboda haka ya dage yana
fad'in,"Koda wasa Sageer kar ka kuskuara ka
amince da laifin da ake so a k'aga ma. Don na
lura Lauyan nan, shegen kan sa ne. Saboda haka
ka lura da laffuzan da za su fito bakin sa. Sannan
ka ba shi amsa."
Ya ce,"Ni ma d'in kai na fi ji Naseer, na san ka
ba ka da tsoro, don girman Allah kar ka fad'i
abinda zai 6ata ran Alkali, a zo kuma abubuwan
su k'ara rikicewa."D'an murmushi yayi." Ai taka
tsan-tsan na ke yi, sbd ba na son Zarah ta
dauwama a kuka, ba don haka ba, da tun
shekaranjiya na amsa da wukar na je, ka ga Alkali
ya huta, take a nan zai yanke hukunci."
Naseer kenan, to Allah dai ya fida mu lafiya. Bari
in lalla6a gida, me zan cewa mutuniyar?" Ya
ce,"Ka gaya mata idan har ta san tana sona, to ta
daina min kuka, lafiya lau na ke, damuwa ta 1
ce, yanayin da take na rashin kwanciyar hankali.
Muddin kuwa ta natsu, ta maida hankalin ta a
makaranta, shakka babu, ni ma zan sami
nutsuwa.."
Suka mike yana fad'in,"Zan isar da sak'on insha-
Allahu.
Sai mun had'u a kotu." Ya wuce Sageer na tsaye
na kallon sa. Gandiroba ya bi bayan sa. Kafin ya
fice, ya juyo suka had'a ido,"Ka gaya mata ta ci
gaba da lissafin kud'in (Break) d'in ta Insha
Allahu da na fito, zan biya su."
Murmushi Sageer yayi ya ce,"Zan fad'i." Yasa kai
ya fice, tare da ,mai tsaron sa. Sageer ya sauke
numfashi cike da tausayin abokinsa, sannan ya
fito yana fad'in cikin ran sa, "Da yardar Allah sai
ka bar gidan nan."
27 ga wata kotu ta cika mak'il!
Kasancewar litinin ce masomar aiki, ko nasara na
tsoronki. Ci gaba da shari'ar su Naseer aka fara
saurara. Gaba d'aya kowa ya hallara har da
shedun da lauyan Salis ya ce zai gabatar.
Ba wasu bane, illa abokan Salis da aka yi abin
akan idanuwan su, amma maimakon su fad'in
gaskiyar lamarin, sai suka goya wa k'arya baya,
suka tabbatar wa Alkali tabbas Naseer ya sumar
da Salis, sannan yayi k'ok'arin da6a masa
shar6e6iyar wuk'a.
Bayan Alkali ya gama sauraron shedun lauya, kai
tsaye yasa aka shigo masa da Sageer cikin akurkin
kotu.
Bayan yayi rantsuwar zai fad'i gaskiyar abinda ya
sani. Alkali ya tambaye shi, Me ka sani a game
da fad'an Naseer da Salis?"
Ya gyara tsayuwa, ya fed'e bayani kamar yadda
ya faru. Alkali ya ce,"To ina wukar da ka tsare da
ita?" Ya kad'a kai, fuska yamutse ya
amsa,"Naseer bai je da wuk'a wajen ba, balle har
in gudu da ita. Hasali ma, Naseer bai ta6a yawo
da makami ba." Yana sa aya. Lauya ya mik'e,
"My Lord!
Ina da 'yan tambayoyi ga Sageer."
Na take ya sami izini." Gaban Sageer ya tsaya
suka kare wa juna kallo, kafin ya ce,"Hujja 1 na
ke so ka gaya min, menene dalilin gudan ka, ka
bar k'ofar gidan su Salis?"
Sageer ya amsa,"Gidan iyayen Naseer na je, don
sanar masu halin da ake ciki." To da ka garzaya
ka sanar wa iyayen na sa, sun zo wajen?"
Yayi shiru, na 'yan dak'ik'ai, sannan ya kad'a
kai,"Ba su zo ba."
Me yasa?"
Lauyan ya tambaya cikin sauri.
Gaban Sageer ya ci gaba da fad'owa, kamar ma
ba zai ce komai ba, saboda tsawon shirun sa, ya
nisa a natse ya ce,"Cewa suka yi babu ruwan
su." Lauyan ya gyara tsayuwa ya ce,"Ah!
Naseer ba d'an su bane?
Don me za su ce ba ruwan su? Nan kam Sageer
ya kasa amsa wannan tambayar, ya aje kai k'asa,
idawuwan sa suka cika da k'walla.
Barista ya dai-daita zaman kot dinsa, ya dubi mai
shar'ia ya ce,
"My Lord!
Bayanan Sageer sun nuna a fili ko a gidan su
Naseer ya ishe su, sun kuma tabbatar da zai
aikata abinda ake tuhumar sa da gasganta min
binciken da na yi cewar har kwana 2 yau, babu
mahaifin Naseer a cikin kotun nan. Ya mai girma
shari'a.
Iyayen Naseer ma sun tabbar da d'an su zai
aikata laifin,My lord, banda wannan ya dade
yana dauko wa mahaifin sa magana, wanda shine
babban dalilin da yasa ya tsame hannunsa akan
d'an sa. Bincike ya nuna ko cikin makaranta
Naseer bai da biyayya, domin har makaranta ta
ta6a korar sa na sati 2.
My Lord!
Ga shedu na na ga hujjoji na na, ga kuma
k'wafin shedar koran Naseer daga makaranta na
sati 2.
A tunani na sun isa su tabbatar da cewa Naseer
shaharrare ne wajen aikata laifuka iri-iri.
Saboda haka ina rok'on wannan kotu mai adalci
da ta duba ta fidda wa Salis hakkinsa, na neman
kashe shi da Naseer yake shirin yi.
Na gode."Ya mik'a takarda. Aka mik'awa
Alkali.Sannan ya koma mazauninsa ya zauna.
Kotu ta yi tsit! Yayin da Alkali ke duba takarda.
Can 6angaran 'yan kallo inda su Malama Lawal
da M. Umar ke zaune, tuni ransu ya gama 6aci,
da ka dube su, ka san akwai tashin hankali a
tattare da su. Zaune kawai suke, amma
zukatansu babu abinda bata sak'awa.
Alkali ya dubi Naseer da ke tsaye cikin akurkin
tuhuma, cikin madubin idon sa fari sol ya ce da
shi,"Ina fatan duk ka ji bayanan da suka gabata.
Ya ce,"Ka ji Me za ka k'ara a kai?"
Ya amsa,
"Babu."
Ya ce,"Duk ka amince da abubuwan da aka fad'i
kenan?"
Kai tsaye Naseer ya amsa,"Dole duk abinda aka
fad'i, ya zama gaskiya, saboda ni ba ni da wani
sheda sai Allah, domin haka babu amfanin
wahalar da kotu, duk hukuncin daya dace sai ayi
min."
Na amince da kowane irin adalci da mai shari'a
zai min."
Alkali shi kan sa, sai da kalaman Naseer suka sa
shi ya jima yana yana kallon sa. Haka su M.Umar
ke kallon Naseer cike da tausayi. Sun sani dole
dama haka za ta kasance, sai dai kawai addu'ar
Allah yasa hukuncin ya zama mai sauki.
Bayan kammala rubucen-rubucen Alkali, sai ya
yanke hukunci. Bayan ya karanto dokokin kundin
shari'a, sai ya zarce da cewa,"Kotu ta yankewa
Naseer d'aurin wata 3 a gidan yari, ko tara ta
3000. Haka kuma shi zai biya kud'in asibitin da
Salis ya kwana, wanda a yanzu haka (Bill) yake a
hannun kotu, na naira dubu biyar da d'ari biyar
da hamsin 5,550.
Shi kuwa Sageer taimakawar da yayi wajen
ta'addancin, kotu ta ba shi tarar 1500, ko sati 2
gidan yari, tare da gargadin mai tsauri, idan har
aka sake kamasu da laifin irin wannan. Kwarai za
su had'u fushin hukuma.
A karshe ina jan kunnunwan Naseer da Sageer da
cewa kar wanda ya sake nemaan wani da fad'a.
Tare da fatan dokar kasa za ta zama abar biyayya
ga kowa.
Nan take ya sallami wannan shari'a ya kama
wata.Waje aka fito da su Naseer, duk jama'ar su
suka biyo su, yayin da gayyar su Salis da Lauyan
su suka wuce cike da farin cikin samun nasara. A
nan take su M.Lawal da M. Umar suka had'a
kud'i 1500, don biyan kud'in tarar Sageer, shi
kuwa Naseer suna ji, suna gani aka wuce da shi
gidan yari, don babu yadda za su yi.
Gaba d'ayan su babu mai adadin kud'in tarar sa
da na asibitin Salis, jimliar dubu takwas da dari
biyar da hamsin, kamar su zubda hawaye,
saboda 6acin rai. Shi kam Sageer sai da ya zubda
hawayensa, a haka suka nufi kasuwa, runfar M.
Balarabe suka sheda masa yadda shari'a ta kaya.
Kawai kad'a kai yayi, ya ce,"Allah yasa ya zama
darasi a gare shi."
Malam Lawal ya ce,"Yanzu matsalar kud'in
asibitin nan da aka ce sai an biya. 8,550." Mala,
Balarabe ya ce,"Ai da ma Alkali ya maida su
dauri. Wa zai biya?
Ni dai bn da wannan adadin kudin.
Dukkan su shiru suka yi na 'yan dak'ik'ai, kafin
M. Umar ya ce,"Allah ya rufa asirin, ni zan
k'arasa gida."Balarabe ya mika masa hannu,"To
ka gaida gida, Allah ya saka da alkhairi.."
Amin."
Yake fad'i, yana mik'ewa tsaye. Suka yi sallama
da Malam Lawal, ya fito ya bar su tare da Malam
Balarabe.
Gida ya nufa, lkcn 10:15 na safiya. Inna na
zaune tsakar d'aki cike da tunani, har wani
gyangyad'i takaici ke son d'ibar ta. Sallamar M.
Umar ta sa ta, ta wartsake."
Ka dawo?"
Ya k'araso cikin d'akin yana fad'in,"Na dawo."
Ya zauna rai 6ace, yayin da take masa sannu da
zuwa, ya amsa,"To yaya, me ake ciki?"
Ya ce,"Anyake hukunci. Wata 3 zai yi gidan yari
ko tarar 3000.
Sai kuma kudaden asibitin da suka ce sun kashe,
5550. Kin ji yadda aka yi. Shi kuma Sageer da
yake na sa babu yawa, mun had'a kud'in mun
biya tarar.
Inna ta aje numfashi, ta ce,"Yanzu shi Naseer din
gidan yarin zai yi?
Ya amsa,"To yaya ki ke so a yi?
Ba mu da adadin kudin nan A'i.
Dama ace 3000 ne kawai, da sai ayi 'yan buge-
buge a samu. Amma babu komai. Allah zai rufa
asiri, zan yi iya kokari na mu gani."
Ta ce,"Sati mai zuwa zan amshi adashina 3500
ne, sai in hakura da tafiyan kauyen, zan ba ka a
harhada mu ga abinda za'a samu." Ya nisa kafin
ya ce,"Allah ya kai mu lkcn. Ni bari in koma
kasuwa."
Ya mike ya fice Inna na fadin,"Idan Zarah ta
dawo zan leka wajen gidan su Naseer din in yi wa
Umman ta sa jaje.Ya ce,"Sai kin dawo." Ya fice ya
bar ta da jimami. Tamkar d'an cikin ta take jin
Naseer a zuciyar ta, sbd yadda ya kular mata da
Zarah lokcn da take buk'atar kulawar. Watau
sa'ilin yarintar ta.


Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100


Ajininsa yake 1-04
Posted by ANaM Dorayi on 10:59 AM, 06-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_____________
Karfe 3 ta gota, awa 1 bayan dawowar Zarah
daga makaranta, amma har yanzu tsiyayar
hawaye take yi. Tunanin ta me take da shi
wanda za ta siyar, don taimakawa iyayen ta
wajen fiddo Naseer daga gidan yari! Tsaf!
Ta mike ta nufi d'an akwatin kayanta ta bud'e, ta
za6o tsala-tsalan ciki, watau k'arshen adakar.
Kala 6 ta aje su bisa gado, ita ma ta nemi wajen
ta zauna ta ci gaba da tunanin adadin kudin da
kayan za su bayar. Can cikin zuciyar ta kuwa,
tsabar kewar yayanta ke addabar ta. Ji take
tamkar sun shekara goma rabon su da juna.
********************
Cikin kwanaki 3 bayan yanke shari'a Umman
Naseer tare da taimakon su Malam Lawal da M.
Umar da Inna suka had'a kud'ad'en da kotu ta
buk'ata, watau Naira 8,550. Suna biyan kud'in
kai tsaye kotu ta aika da takardar umurnin sakin
Naseer.
Yana fitowa yayi arba da su M. Umar da abokinsa
Sageer. Da sauri suka nufo juna Sageer, ya
rungume shi suna yi wa juna barka tare da nuna
tsananin godiya ga Ubangiji, sannan ya juya
wajen su M.Umar ya gaida su. Su ma cike da
farin ciki su ke, fuskokinsu tsaf, suke d'auke da
fara'a suka amsa gaisuwar sa. Daga nan gida
suka wuce da shi.
Umman sa na jin sallamar su, ta mik'i da
hanzarin ta, amma kuma sai ta kasa aiwatar da
komai, haka ta tsaya kame da ha6a tana kallon
Naseer. Kwarai ta tausaya masa ganin ya sauya
ba kad'an ba.
"Malam!"
Ta kwala wa Malam Balarabe kira, yayin da su
Naseer ke karasowa daf, da ita.
Ta koma bisa tabarma ta zauna suka zauna suna
fad'in,"Sannu Umma."
Ta ce,"Kai ne abin sannu, manya d'ibar fari. Allah
ya shirye ka." Ya sunkuyar da kai, dai-dai lkcn
Malam Balarabe ya fito daga d'aki. Sageer ya
gaishe shi, sannan ya ce,"Su Baba na nan zaure."
Bai saurari gaisuwar Naseer ba, yayi gaba abin
sa, ya nufi zaure.""Ku shigo mana M.Umar! Kun
tsaya daga nan kamar bak'i?"
Ya koma ciki suka biyo bayan sa. Umma ta k'ara
baza tabarma kowa ya zauna suna 'yar raha.
Bayan gaisuwa. M.Lawal ya ce,"Malam Balarabe
babu wato doguwar magana tsakanin ka da
Naseer, face ka sanya wa ranka ruwan sanyi,ka
yafe masa laifin da yayi maka, tunda Allah ya
tak'aita wannan wahalar. Shi kuma tun a hanya
mun jajja masa kunne, yayi alkawarin ba zai sake
maimaita laifin makamacin wannan ba. Ina fatan
za ka karbi tuban sa ka sanya masa albarka?
Malam Balarabe yayi d'an jim, sannan ya dubi
abokan sa ya ce,"Hakika kun nuna min kauna
tsakani da Allah, kuma wanda na yi imani ko
banda rai za ku iya rike min iyali na. Saboda haka
ba ni da wata kalmar godiyar da zan muku, illa in
ce Allah ya saka maku da mafificin alkhairi, ya
bar mana zumuncin da ke tsakanin mu, har zuwa
gidan aljanna. A game da Naseer kuwa, ni na
yafe. Ubangiji ya shirya mana dukkan zuri'a baki
d'aya.
Kowa ya ce,"Amin.
Kan Naseer na sunkuye, kuma har cikin ran sa
yana jin tausayin iyayen sa, sai yanzu yake
nadamar ta6a Salis da yayi. Sai dai ba laifin sa
bane, kaunar da yake wa Zarah, ita ta kai shi ga
aikata abinda zuciyar sa ta sak'a masa. Amma in
kwana dubu yana wannan bayanin, iyayensa ba
za su ta6a daina ganin laifin sa ba, Musamman
Abban sa. Ya sauke numfashi, na jin dadin
furucin Baban sa.
Tsam!
Ya taso ya tsungunna gaban sa, ya ce,"Abba na
gode." Ya dube shi a raunane ya ce,"In kunne ya
ji, gangar jiki ta tsira Naseer. Ka sani kullum
shekaru na tafiya suke yi, za'a wayi gari wata
rana ace babu ni, shi yasa kodayaushe kokarina
ka dan sami ilimi dai-dai gwargwadon k'arfi na,
amma kai hankalinka ba shi a nan.
B'acin rai na kodayaushe, idan na tuna cewa ba
ka sami rubuta jarabawar ka ba, ga shi ance
saura guda 3 a kammala ta.
Wannan babban rashi ne, don ko banza sai wata
shekarar za ka sake wanda ya kamata ace katafi
wani mataki na gaba. Haka Allah ya so."
Wannan dogon jawabi ya sanyaya jikin kowa, duk
sukai shiru na 'yan dak'ik'ai kafin M. Lawal ya
ce,"Lokaci kam an 6ata shi.Amma babu wuya a
wurin Ubangiji, wata shekarar za ta zo ne, sai ya
sake. Allah dai ya kai mu dai rai lafiya."
Suka ce,"Amin."
Malam Umar ya muskuta, ya ci gaba,"Akwai wata
magana da na ke ganin zai yi kyau in fade ta
wannan zaman, don kowa ya zama shaida. Allah
ya sani, ba ni da abinda zan yi wa Naseer in iya
saka masa akan hidimar kuluwar da yayi wa
Zarah, wanda shine silar kullawar zumuncin mu,
face in ba shi auran Zarah.
Don samun d'oruwar zumuncin mu. Ina fatan
kowa zai amshi wannan kyauta tawa da hannu
biyu. Saboda haka Naseer, ga Zarah nan matar
ka ce insha Allahu.
Za ta ci gaba da karatu har zuwa lkcn da Allah ya
hore mana d'an abin yi. Haka kuma ina son kowa
ya shaida ko bayan raina, ban ce a tada wannan
magana ba, koda za'a sami wani akasi ta
6angaran Zarah, wanda ba na fatan faruwar
hakan, ban jin Zarah za ta iya juya wa yayanta
baya. Ko akwai kuskure a zan ce na?
Gaba dayan su farin ciki ke bayyane bisa fuskokin
su, musamman uban gayyar wanda yake jin
tamkar an tsunduma shi a al-janna.
Kiris ya rage ya riga iyayen sa magana. Sageer
yayi sauri ya toshe bakin sa. Umma ta ce,"Kyale
shi mana mu ji abinda zai ce maras kunya, dama
tunda aka fara maganar bakinsa ya k'i rufuwa.
Ai sai mu kyale shi, ya amshi auran da kan sa."
Da sauri ya mik'e, yana dariya yayi zaure. Sageer
na bin sa, yayin da iyayen ke masa dariya.
Malam Lawal ke fad'in,"Yaya za ki maida shi
kamar mace? Ai mata aka sani da wannan
kunyar.
Gaskiya abu yayi dadi, kuma mun amshi wannan
babbar kyauta taka.
Allah ya sanya duban albarkun tare da fatan ran
mu ya kai had'e da koshin lafiya."
"Amin."
Duk suka amsa Malam Balarabe ya mik'awa M.
Lawal hannu su kai Musabaha,
"Mun gode!
Mun gode!!
Allah ya bar zumunci.
Malam Umar ya ce,"Naseer d'a na ne, ni kad'ai
na san irin gudumuwar daya bai wa rayuwar
Zarah, na kuma fahinci dalilin fadawar sa
wannan fitinar.
Zarah yake so, ni kuma naba shi. Allah ya
tabbatar mana."
Umma kan ta farin ciki ya hana ta cewa k'ala, illa
ta amsa da amin, ta zarce ta sawa abin albarka
cikin zuciyar ta, sun dan jima suna hirararrakin
raha, kafin suka yi sallama suka fito.Naseer da
Sageer na cikin dakinsa su ma suka fito suka yi
rakiya tare da k'ara godiya, sannan suka dawo
d'aki. Bisa katifa Naseer ya zube a ringine.
Sageer ya zauna kusa da shi ya ce,"Yanzu ba
washe hak'ora ba, mice ce shawarar ka?" Ya juya
ya dube shi." Ta me? Ya ce,"An ba ka Zarah,
wane shiri za ka yi na dogaro da kanka, don ci
gaba da kulawa da ita?"
A natse ya taso, ya dube shi kafin ya nisa, ya
ce,"Akwai fa sauran aiki, amma ai Allah na nan,
shi yasan yadda za'ayi ko?
Haka ne,
sai dai yakamata kai ma daga (Next year) ka dai-
daita jarabawar ka, don na san ka da shiririta
akan karatu. Wani lkcn har da laifin ka."
Ya kwada masa harara, ya ce,"To zigziglar
baturan ilimi!
Cewa na yi ba zan sake (Exams) d'in ba ko yaya?"
Ya ce,"Ka ji tsiyar ka, sai ana maganar arziki, sa
ka fand'are. Ni bari in wuce gida, tun kafin mu
hau rimi mu fad'o karyayyu."
Ya mik'e zai fice, "Naseer ya janyo hannun
sa,"Kai banza ne Wallahi, duk ka 6aci da bakar
zuciya, yanzu kuma me na yi? Ya sanya masa ido
suna kallon juna. D'an murmushi Naseer yayi, ya
saki hannun sa cikin damuwa ya ce,"Je ka ma
kawaia anjima idan na yi wanka, zan fito mu je
gangare." Ka wuce kawai, kar ka biyo min."
"Me yasa?"
Ya ce,"Shi yayi saniya, d'an rainin wayau. Kasan
in yi maka rakiya, amma ba ka san in ba ka
shawara, ka ji ba.
Ka tafi kai kad'ai, ba Zarah bace? Kun
san.............."
Ya katse shi, saboda fizgo shin da yayi, ya zauna
dabas!
"Bani shawara Sageer, me ne zan yi?
Faskare ko dako?
Yasar masai ko kuwa in fara turin kura?"
Ya ce,"Ko wanne ka d'auka yayi, idan ma gatse
ka ke min, ina son ka sani duk sana'a ce, kuma
da su mutane da yawa suke ciyar da iyalan su.
Sana'ar hannu aba ce mai kyau, wanda duk me
yin ta, ya wuce raini.
Sai anjima."
Ya ce,"Tsaya mana,
ai ka fad'i gaskiya Malam Sageer. Ba gatse na ke
yi ba. Yanzu menene abin yi? Ya ce," Akwai
shagon da na yi magana zan rinka zuwa koyon
d'inki. Nan shagon Alh. Hassan, idan ka na so, ka
zo mu rink'a zuwa tare.
Me ka ce?"Kai tsaye ya amsa,"Dai-dai wallahi.
Yaushe za mu fara?" Ya ce,"Ka ga ranar
Wednesday za'a gama (Exams),zuwa alhamis ko
juma'a, sai mu fasa kawai." Ya ce,"Dole a fasa ko
a sami na auran Zarah. Komai zan iya yi, sbd ita,
don jin ta nake tamkar rai na. Anjima za ka raka
ni d'in ko?
Yayi d'an murmushi,"Shi yasa ka yi saurin amsa
min? To bn zuwa, ka je kai kad'ai, kafin laifin ka,
kai kad'ai.............."
Umma ce ta katse hirar da ta kwala wa Naseer
kira. Ya mik'e yana naushin kafad'ar Sageeer. Jim
kad'an ya dawo da kwanon abinci.
Sageer ya ce,"Umma har ta gama abinci k'arfe
11?" Ya ce,"A'a, waina ce Abba ya bada kud'i,
maimakon ta kira ni, mu siyo shine ta shiga nan
gidan wainar ta siyo da kan ta."
Sageer ya kad'a kai, ya ce,"Su Umma na son ka
Naseer, ka yi wa Allah ka rink'a gudun 6acin ran
su."
"To, na ji."
Haka ya fad'i yana bud'e wainar, komai yayi.
Suka fara ci, sai dai Sageer ya lura kamar Naseer
bai son yin magana, don haka ya tambaya,"Me ka
yi?"
"A'ina?"
Shi ma ya tambaye shi. Ya ce,"Kamar wani abu
ya dame ka?"
Ya dube shi da kyau, ya ce,"Har yanzu babu
wanda ya fahimce ko ni wanene, shi yasa aka
min kallon maras ji. Alhali ni ina son duk abinda
zan yi, ina da dalili na.
Kuma wallahi ina tausayin iyayena. Amma abinda
ke ba ni haushi, ku ba ku fahimtar halaye na A
JINI NA SUKE. Sannan shin wai ma, me na ke yi
na 6atanci, wanda ya taka shari'a?"
Sageer yayi shiru, yana kallon sa. Naseer ya kad'a
kai, manyan idanuwan sa suka fara kad'awa, ya
sanyaya murya,"Amma tunda kai ma ka na ganin
ina sa6awa su Abba, yanzun nan zan je in nemi
gafarar su, ni kuma zan nemawa kai na mafita,
duk da na san cewa ban aikata komai ba, don
ran su ya 6aci.
Sageer nisa ya ce,"To ka yi hak'uri, idan magana
ta bata yi maka bane."
"A'a,
ka fad'i dai-dai, abinda ka fahimta ne tsakanin
ka da Allah so ba matsala na gode, mu ci abinci
kawai." Suka ci gaba da cin abinci, suna hirarraki
har suka kammala. K'arfe 12 Sageer ya koma
gida, ya bar Naseer tare da su Abba yana sake
neman gafarar su.K'arfe 4 bayan sallar la'asar,
ya fito fes! Cikin k'anana kaya. Shagon aski ya
fara shiga, aka yi masa, gaba d'aya ya k'ara
tsaftacewa kamar wani ango. Daga nan gidan su
Sageer ya nufa, yana zaune bisa dakali ya na
karatu. Naseer ya jira shi, ya mayar da littafin ya
kulle k'ofa, suka wuce gangare. Cikin zaure ya
tsaya ya dubi Sageer ya ce,"Zan iya shiga gidan
nan kuwa?" Ya ce,"Me yasa?" Kunyar Inna na ke
ji............."Bai gama zancensa ba, sai ga Inna ta
kawo cikin zauren. Take nan Naseer ya daburce,
tsanananin kunya ta kama shi tamkar bai ta6a
sanin Inna ba. Shi kan sa ya rasa dalilin hakan.
Hannun sa a k'eya yana ta sosawa,"Sannu Inna.
"Dukkan su suka ce. Bakin ta har kunne ta amsa.
"Allahu Akbar Naseer, yanzun nan gidan ku na
nufa in duba ka.
Sannun ku!"Suka tsugunna suka gaida ta, ta
amsa, sannan ta zarce da fad'in,"To ku shiga.
Zarah tana nan a ciki, sai na dawo." Suka amsa,
"Adawo lafiya." Amin." Ta wuce tana fad'i.
Su kuwa ciki. Suka yi sallama, kamar su take jira,
domin kuwa ta zuba adonta da wani material
ruwan hoda da farin furanni. Ko ba'a tambaya
ba, adonta ya nuna tsaf, tana cikin farin ciki irin
na bege. Amma maimakon ta tarbi yayanta
kamar yadda ta saba, sai ta kasa, saboda wata
sabuwar kunyarsa da ta mamaye idanuwanta,
masu sa yayan nata neman zarewa.
Sallamar kawai ta iya amsawa, ta k'ara sunkuyar
da kai, ta d'ora idanuwanta bisa tiran da take
gyaran wake. Kujeran tsakar gida suka ja suka
zauna, sannan Sageer ya ce,"Zarah, yau kuma ba
za'a kalli yayan bane?"
Sageer ta duba fuska cike da murmushi,
"Ina ruwanka?"
Ya ce,
"Au,
haka ne?
Saboda na kawo miki shi ko?
Ba laifin ki bane.
To ya ki ke?"
Ta ce," Lafiya lau, ya mutan gida?" Ta amsa,"Su
ma k'alau suke. Yau dai kuka ya k'are ko? Ga
yayan ki nan. Allah ya taimake mu ya fito."Ta
ce,"Allah ya kare na gaba." Amin, sai ki yi masa
fad'a ya rink'a danne kishi." Ta karkad'e kai. Duk
suka fara dariya,"Kin goye bayan sa kenan?" To
babu ruwa na, kinfi kowa sanin halin yayan ki."Ta
ce,"Akwai k'arya k'ashin wuya ko? Ai ya bada
darasi, ka ga babu mai sake kwatantawa.
Suna ta k'yalk'ya dariya. Naseer kamar ya lashe
ta, sai lkcn ya fara magana, "Kinyi min dai-dai
my sister, jarumta adon namiji, kuma ai kishi
halas ne, duk wanda ya shige maka hanci, ka
daddage ka fyato shi, har sai ya balle k'ashin
wuya. Idan ya suma, ya farfad'o ya gane
kuskuren sa ko tawan?" K'ara aje kai tayi k'asa
tana murmushi.
Sageer ya ce,
"Ok,
irin na ku tsarin kenan?
Lallai jiki magayi, gara shi da ke mai kukan tsiya."
Wasa na ke Sageer,ai yayana yayi min babban
laifi.
Shekaru nawa mu ke tare da shi? Koma dai
menene, sai ya gaya min, ba wai ya je ya jawo
mana tashin hankali ba. Babu wanda ran sa bai
6aci ba akan abinda ka aikata.........."
Ta d'an dube shi a raunane ta ci gaba,"Don
girman Allah yayana ka rink'a gudun abinda zai
rik'a 6ata wasu Abba rai."
Gaba d'ayan jikin Naseer yayi sanyi, ta jefa shi
cikin damuwa.
Yayi d'an shiru kafin ya numfasa."
Ya ce,"Na ji Zarah.
Insha Allahu ba za'a k'ara ba. Kuma na rok'i su
Abba sun ce komai ya wuce.
Ina fatan ke ma za ki min afuwa, ki d'auka cewa
kishin ki ne yayi min yawa har idanuwa na suka
rufe ruf!
Ba na ganin kowa a gaba na, balle ya gaya min in
ji. Ki yi hak'uri, kin ji?"
Ta d'an rausaya kai tana murmushi,"Ya wuce,"Sai
harkar soyayya ko?"
Kunya ya bata sosai, ta rasa madafa. Sageer ya
ce,"To in d'an jira daga zaure ne? Yadda ka so."
In ji Naseer ya sanya hannu cikin tiran da ke cike
da wake ya shiga taya ta. Ta ce,"Yimin
wulank'anci, don na rako ka."
Zarah ta amshe,"Kyale shi Sageer, yi zaman ka ai
kai yayana ne."Maigida na ke, komai sai da izini
na." Ta ce,"Haka ka ke gani, amma ni na san
sabon yayana ya fi power, don haka ka bi shi a
hankali.
Ya dubi Sageer ya ce,"Allah ko? To sannu yaya
ina yini?" Sageer dokar masa kafad'a, suka ci
gaba da hira cikin farin ciki.Daran wannan ranar
Naseer bai iya barci ba. Ba waai k'aunar Zarah
ke masa tuk'uk'i ba, don wannan ta dad'e masa
cikin zuciya. Ammamaganar da ta zame masa
sabuwa, ta kuma hana shi sukuni, ita ce maganar
da kowa yake masa, watau ya rink'a gudun
abinda zai rink'a 6ata wa iyayensa rai. Ko Inna
da ta dawo, ta same su a gidan. Sai da ta fad'i
wannan maganar sbd haka abin yayi matuk'ar
tsaya masa a rai.
Kuma ya rasa mafita, domin shi a ganinsa bai
aikata komai ba, don ran su Abba ya 6aci, akan
gaskiyar sa yake kuma ko a yanzu ba don kotu ta
shiga tsakanin sa da Salis ba, da Salis ya gane
shayi ruwa ne, madara ake zuba masa yayi kauri.
Duk da cewar Baban Zarah ya share masa
hawaye kuma ya hana Salis zuwa wajenta.
Wannan ba zai hana shi k'wato hak'k'in sa ba.
Amma magana ta kau, tunda kotu na tsakani.
Ya juya rigingine, ya numfasa,
"Mece ce mafita a waje na ni Naseer?
Na san ba ni da hak'uri, amma ai sai anyi min na
ke ramawa. Sai kuma a rink'a ganin laifi na." Ya
ja tsaki, ya kada kai mai cike da takaici. Har aka
kira assalatu idonsa 2, ya fito yayi alwala, suka
fita masallaci da Abba.
Bayan cin abincin safe, ya fito k'ofar gida yayi
shiru a tsaye, kusan layin yayi tsit! Saboda duk
wani yaro daya isa zuwa

Please Login or Register in order to submit comment