Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

k'arasowa bakin
titi, sai dai yau babu yayanta a wajen, kamar
yadda kullum safiya shine mutum na 3 da ke
faranta mata rai, daga iyayenta, sai shi.
Don haka ta tsaya shiru cike da mamakin me ya
hana yayanta zuwa yau? Ta kusan minti 5r a
tsaye, sannan ta wuce jikinta duk ya mutu.
Kuma ko alama zuciyarta bata cikin sukuni har
na rashin ganin Salis jiya da daddare, kamar
yadda yayi mata alk'awari.
Ta fe take tana zancan zucci fad'i take,"Ina ka
ke yayana?" Zarah." Ta ji an k'wala mata kira.
Ta waiga gefen da aka kirata, firgici. Bak'in get
din ofishin "Yan sanda ta hango Sageer tsaye da
kayan makaranta.
Da sauri ta tsallako. Hankali tashe, ta
tambaya,"Ina yayana ne?" Ban gan shi ba yau."
Cike da damuwa ya amsa,"Ai yayan nan naki,
sai a hankali.
Yana nan ciki."
Ta k'ara ware ido ta-ce,"Ban gane yana nan
ba?"
(Police Station)Na ga ka nuna!
Ya ce,"Eh mana.." Hankalinta ya k'ara tashi,"Wa
ya kawomin shi?" Bata jira ya bata amsa ba, ta
wuce, ya biyo ta, yana fad'in,"Wallahi tsautsayi
kawai, jiya ya je wajen wani wai shi Salis, suka
fara gardama akan ki, sai fad'a. Kin san halin
yayan naki, k'ashi daya ke gare shi, yana dukan
sa, ya fad'i a sume."
Tun da yake magana, ta rage sauri. Yana sa
aya, ta juyo ido cike da kwalla ta ce,"Shi da Salis
suka yi dambe? To saboda me?"
"Oho!
Amma a kan ki ne Zarah. Naseer bai son Salis
na zuwa gun ki, gargad'in da na ji yana masa
kenan.
Abin ya kai su ga dambe."
Ta tsura masa idanuwanta da suka cika tam!
Da hawaye, ta ce," Za'a bar ni in gan shi?"
Ya amsa,"Ban sani ba. Ni ma yanzu na kawo
masa abinci, mu je mu gani.
Suka shige cike, da k'yar aka sake yarda su gan
shi,don bai jima da komawa ba. Ana fito da shi,
suka yi ido 4 da Zarah, sai ya juya, ya koma ciki
da saurinsa. Kamar za ta burma ciki, ta bi shi,
kira take,"Yayana! Yayana ka zo mana, in gan
ka!" Dan sanda ya ce,"Yan mata, ihunki fa yayi
yawa wajen nan. Hala saboda ke aka yi fad'an?"
Bata iya cewa da shi komai ba. Sageer ke jawo
ta waje. Zarah, ki yi hak'uri ki tafi makaranta, ni
ma yanzu zan wuce."Insha Allahu na san zuwa
anjima, za'a bada belinsa.
Yi hak'uri."
Tayi tsaye tana share k'walla." Zo mu je." Suka
fito bakin titi. Sageer ya tare mai mashin, ya
yana fad'in,"Ki wuce Zarah, kin ga lokaci yana
kurewa." Ta ce,"Zan ta fi." Mai mashin ya ja,
suka tafi. Yana waigen ta, yana nuna mata
alama da hannu ta wuce, har suka yi nisa.
Tsaye kawai take kikam! Ta rasa na yi.
Tunanin ta, me ya kai Naseer fad'a da Salis?Nan
take ta samo amsar. Wani ni'imamman farin ciki
ya lallube ta.
In banda abin yayana, ai sai ya gaya min kai
tsaye, menene na fad'a da Salis? K'walla suka
cika idanuwanta, tana kallon ofinshin "Yan
sanda,"Ba zan iya zama cikin aji ba, kai kuma ka
na tsare a nan yayana. Ta goge kwalla ta
kwashe sauri sauri sai gida.
Babu ko sallama, ta fito dakin. "Ke! Lafiya?"
Innar ta, ta tambaya, kuka ta fasa,"Inna 'Yan
sanda sun kama yayana! Ta dafe kirji a firgice ta
ce,"Me yayi?" Bakinta na rawa, ta mayar da
abinda ya faru. Inna ta d'auki salati, kan ta ya
d'aure"To ki yi shiru, bari Baban ki ya fito
wanka. Kai yara babu hankali, koma dai menene
cikin zuciyarsa, ai sai yayi hakuri, menene abin
fad'a?."
Shigowar Malam Umar yasa tayi shiru,."Me ya
faru? Inna ta amsa,"Naseer ke hannu 'Yan
sanda. Wai jiya sun yi fad'a da yaron nan daya
zo gun Zarah jiya, har sumar da shi." Ya ce,"To
saboda me?"
"Oho!"
Yayi dan tsaki ya ce,"Yara ba sa jin magana,
menene abin fada anan? Ko shi ma sonki yake
yi?"
Ta sunkuyar da kai ta ce,"Nima ban sani ba."ya
ja tsaki. Inna ta ce,"Idan ma sonta yake, me zai
kai shi, fada in banda abin Naseer. Shi ma ya
san babu yadda za'ayi mu hana shi, mu ba Salis
in har ya furta.
Allah shi kyauta.
Yanzu yaya za'ayi Malam?" Ya ce,"Bari in shirya,
in je in ga Baban na sa, sai a san abin yi.
Ke kuma ga shi kin makara.
Ki bata sauran 20 din nan, maza ta je ta hau
mashin ya kai ta.
Ya fice daga dakin. Inna ta dauko 20 din ta
bata,"Tana bayan mashin hankalin ta na ofishin
'Yan sanda.
Haka suka wuce tana kallon wajen har suka
k'ule.
Malam Umar ke wa su Malam Balarabe sallama
a k'ofar gida. Tare da Mallam Lawal mahaifin
Sageer.
Bayan sun yi Musabaha, sun gaisa sai ya
ce,"Magana na ji babu dadi, shine bari in zo in ji
yadda aka yi?"
Malam Lawal ya ce,"Zaman nan da ka ganmu
nan, rarrashi kawai na ke yi.
Malam Balarabe ya ce babu ruwan sa a ciki.
Sannan baban tashin hankali, na je ofishin, don
in yi belin sa." Yan sandan, suke gaya min
iyayen wancan yaron, sun ce kara za su kai
kotu, wai da wuk'a ya zo, yana neman kashe
shi."
Da wuk'a?
Ya ce,"Sharri ne kawai, don Sageer ya gaya min
tare suka je, kuma babu komai a hannu Naseer.
Dukan sa kawai yayi, ya suma. Shi kuwa Naseer
tun yana yaro haka Allah yayi shi da karfin
tsiya.
Malam Umar ya kada kai cike da damuwa,
"Wannan al'amarin bai yi dadi ba. Su kuma bai
kamata su yi haka ba. Menene amfanin yin
sharrin?" Malam Balarabe ya amshe,"Laifin su
ku ka gani? Karan banin da ya kai shi,ya ta6a
masu yaro. Shi zai fidda shi. Saboda haka kar ku
wahalar da kan ku, ku kyale shi, su koya masa
hankali."
Malam Umar ya ce,"Ba kuwa za'a kyale shi ba."
To wallahi babu hannuna acikin, kun ji kuma na
rantse.." Ya ce,"Shi kenan Malam Balabare,
amma ina tabbatar maka, bai kamata ka yi
saurin rantsuwa ba. Tunda abin ya zama haka,
mu sai mu je ko?
Ya fad'i yana kallon Malam Lawal, duk dacewar
ba su taba sanin juna ba, sai yau.
Ya ce,"Taso kawai mu tafi." Rai 6ace suka bar
wajen, tamkar yadda ran Malam Balarabe ke
bace.
Ya jima a zaune, yana tunani da tambayar kan
san "Yaushe Naseer zai daina bata min rai?"Ya
ce,"Taso kawai mu tafi." Rai bace suka bar
wajen tamkar yadda ran Malam Balarabe ke
bace. Ya jima a zaune, yana tunani da tambayar
kan san."Yaushe Naseer zai daina bata min rai?"
Ya kada kai ya ce,"Allah ka shirya min." Ya
mike, ya shiga gida, ya mayar wa Umma zancan
kai Naseer kotu inji iyayen Salis.
Idanuwanta suka kada, cike da tashin hankali ta
ce,"Wannan sharri ne, na san Naseer bai jin
magana, amma bai ta6a daukan makami ya hari
wani da shi ba.
Gaskiya Malam bai kamata ka tsame hannunka
daga maganar ba."
A fusace ya ce,"To ai sai ki dauka ki maida min.
Ya ja tsaki, ya bar gidan, ya wuce kasuwa. Ya
bar Mairon, kamar ta aza hannu bisa kai tayi
kuka.
Duk iya kokarin da su Malam Umar suka yi, don
ganin su kwantar wa iyayen Salis hankali, don
su janye kudirin su, sam sun ki sauraron su, shi
mahaifin sa ma ya ki yarda su gan shi ido da
ido.
Abokan Salis din ke gaya masu, an ma riga an
shigar da kara.
Takarda kawai suke jira a aiko ofishin 'Yan
sanda...........


Zaharaddeen Shomar
Whatsapp

08168575100



Ajininsa yake 1-03
Posted by ANaM Dorayi on 11:44 AM, 04-Nov-15
Under: Ajininsa yake
___ NA ZULAIHAT SANI KAGARA___________
Al'amarin bai masu dadi ba ko alama.
Karfe 11:30 duk suka koma gida. Inna na zaune,
duk tunani ya addabe ta.
Malam Umar ya shigo. Yadda ta lura ran sa a
6ace yake, yasa nan da nan ta gane ba ayi
nasara ba.
Hannu ta a kunci, ta ce,"Ya dai Malam?"
Ya jinjina kai ya ce,"Ai komai ya kwa6e A'i.
Iyayen Salis sun kai shi kotu."
Kotu?"
Me yayi zafi? Shi Salis din rauni yayi sosai?"
Ya ce,"Ko alama, duk da dai ban gan shi ba,
amma an ce ya bar asibitin.
Abin ma dasharri ya zama, wai dawuka ya je
kashe shi......."
Da sauri ta katse shi,"Wannan karya ne. Naseer
bai daukan makami, bar shi dai da saurin duka
ga karfi." Ya ce,"Babban abin tashin hankali ma,
shi Malam Balarabe ya ce, ba ruwan sa ciki.
Saboda haka al'amarin sai addu'a
. Mu jirar ranar da za'a shiga kotu.
Ni takaici na yaron nan jarabawa suke yi.
Mts!"
Yayi tsaki, ya kardada kai.Ta ce,"To yaya zai yi?
Ba dole yayi hkr ba. An san abin akwai 6acin rai.
Allah shi kyauta."
2:15 Zarah ta shigo gida a dokan ce, duk a zaton
za ta ji an ce yayanta ya baro ofishin 'Yan sanda,
sai ma ta ji wani labari sabo. Ta ha de kai da
guiwa, hawaye na ambaliya.Inna ta ce,"Hak'uri
za ki yi Zarah, haka Allah yaso, fatan mu kawai
Allah ya takaita abin. Tashi ki zubo abinci ki ci."
Ta girgiza kai,"Ba zan iya ba Inna. Ya za'ayi wa
yayana sharri, wanna ai zalunci ne."
To ya za'ayi? Tun da ya riga ya bi shi, har gidan
su ya ta6a shi, ai bai da mafita, sai dai Allah.
Allah ya isa.
Wallahi!
Kuma Salis din zai zo ya same ni!"
Ta tashi fu......... ta wuce.
Daki ta nufa ta kifa bisa gado, tana murzar ido
hawayenta bai yanke ba.
***************
Bayan sallar La'asar. Inna ta gama shirinta tsaf!
Ta tsaya kan Zarah da ke zaune bisa sallaya,
tunda ta idar da sallar, "Tunda nayi-nayi da ki
tashi ki tafi Islamiyya, kin ki motsi, ni zan tafi
layin Labadiya in yi wa Umman Naseer jaje. Sai ki
kula da gidan, ga miya can na dora, idan kuma
kin ga dama abincin na ki yana nan a kicin din."
Ta sa kai ta fice, ba tare da Zarah ta ce, wani
abu ba. Minti 10 bayan tafiyar Inna sai yaro yayi
sallama, ya shigo ya ce ana kiran Zarah inji Salis.
Da ita yaron ke magana, don haka ta ce,"Ka ce
tana zuwa."
Ta mike da hijabin da tayi sallah ta fito.
Salis na cikin zaure ya sha wankan la'asar, yayi
adon shadda bulu.
Fara'a kawai yake yi, ita kuwa jikin bango ta ra6e,
fuska daure. Ya dan matso yana fadin "Yan
matan da ta dace da sunanta, ya sanyin
la'asar????Ta dirka masa harara. Ya ce,"Wai!
Me ya faru?"
Ta gyara tsayuwa cikin fada ta ce,"Salis kar ka
sake zuwa guna!
Ban da lokacinka, ban da lkcn mai lakacin ka!
Saboda haka ka fita harka ta kawai, idan ka na
son kanka da arziki!"
Ta juya za ta wuce, da sauri ya ce,"Me ya faru
Zarah? Ke da ake neman kashe ni, saboda son da
na ke miki? Labarin da na zo in ba ki kenan, ya
za ki min haka?" Ta juyo ta nuna shi,
"Sharrin da ku ka k'ulla masa a kanka zai kare!
Kuma da yardan Allah, sai ya fito, ba zai mutu a
hannun Alk'ali ba!"ta shige gida, ta bar shi sototo
cikin duhu,"Me yarinyar nan take nufi? Ta san
fadan da muka yi kenan?
O.K, shi ma take goya wa baya, ba ni ba.
Shi ta fi so kenan?" Ya huta, ya ce a fili,"Zan yi
maganin sa kuwa.
Kuma ba zan daina son ki ba."
Ya fita, ya bar gidan ran sa 6ace."
Haka Zarah ke cikin kunci, har zuwa dare babu
abinda ta iya kaiwa bakinta.
Sallamar Sageer, ita suke amsawa yanzu. Ya shigo
duk suna tsakar gida zaune, ya tsugunna, ya
gaida su Inna.
Sannan suka gaisa da Zarah." Sai na dawo na ji
sabon labari.
Wallahi-wallahi Baba karya suke yi. Naseer bai je
da komai ba a jikinsa."Ya ce,"To yau muke tare
da Naseer? Duk iya kiriniyar sa na sani. Kawai
sun san yana jarabawa ne, shi yasa suka ja
maganar, don ya rasa. Sun kuwa yi a kansu. Idan
kuma har son Zarah yake yi, ni na ba shi ita
duniya da lahira. Za ta jira shi har ya sami
madafa.
Ba shi kenan ba? Na ga wani dan kusun uwar da
zai sake zuwa min k'ofar gida."
Ba k'aramin farin ciki ya ratsa zuciyar Zarah ba.
Suka kalli juna da Sageer, yayi mata murmushi,
ta yi sauri ta rufe fuska.
Yayin da Inna ke fad'in,"Ka gama magana
Malam. Allah yasa rabon sa ce."
Sageer ya ce,"Amin.
Ni zan wuce (Police Station) din, in gan shi."
Zarah ta mike,"Baba ni ma in je?"
Me za ki yi a can Zarah? ki yi zaman ki kawai,
wurin nan ba wajen zuwanki ba ne."Ta
marairace,"Zan gaishe shi ne Baba,
kuma......kuma........"
Kuma me?"
Inna ta tambaya.
Ta kwanto jikinta, ta 6oye fuska. Babanta ya
ce,"Ba fa za ki ba. Ki ba Sageer sak'on ko
menene a kai ma sa." Haushi ya kama ta, ta
tashi ta shige daki. Sageer yayi masu sallama, ya
fita.
Yana tsaye gaban kanta aka fito da Naseer. Da ka
kalli fuskar sa, za ka san ya fad'a, saboda bai
saba da wajen ba, ga k'yamar k'azantar da ke
wajen, shi yasa bai iya cin abinci sosai. "Ya aka
yi?" Ya ce wa Sageer.
Ya amsa, "Lafiya lau. Daga gidan su Zarah na ke
duk suna gaishe ka.
Zarah ma ta so biyo ni.
Babanta ya hana.
Ni da abinda na ke son in gaya ma ka, ko an je
kotun nan, kar ka amsa laifin da ba ka yi ba."
Ko na amsa, menene?
Sun dade ba su min sharri ba." Ya ce,"To wai kai
son Zarah ka ke, ko menene dalilin yin haka?"
Ya juya lafiyayyun idanuwan sa, ya amsa,"Me ka
fahinta?" Ya dan kada kai,"Naseer manya.
In kasan haka ne, sai ka gaya mata kawai,
menene na 6oye-6oye?"
Ya ce,"Ai Zarah yarinya ce, bai kamata in kasa
mata hankali ba.
Ina sa uniforma, tana sa uniform, sai ince ina son
ta?
Da sunan me?
Don kowa ya san ban isa aure ba.
Da fa hankalina sarai. Su Baba ne suke ganin
banda shi."
Yayi d'an murmushi, ya ce,"To ai duk ta kare,
tunda sun gano ka.
Har Babanta ya ce,"In har son ta ka ke. Wallahi
ya baka ita."
Yayi jim!
Yana masa duban mamaki, Ni zaka zolaya?" Nace
wallahi, ka ce zolaya? Maganar da aka yi ta yanzu
a gaba na.
Zarah ma na zaune.
Yayi 'yar dariya, kafin,"Yaya Zarah ta yi?" Tsaf!
Fuskar ta, ta nuna min kai take so.
Ai kun shak'u da Zarah Naseer, dole mata so ka.
Ba ka ga yadda take rawar jiki, ta zo nan ba, aka
hana ta.
Tun jiya hankalin ta yake tashe."Ya lumshe ido,
shiru yana tunanin zucci, kafin ya bude. Dan
sandan da ke tsaye ya ce,"Lokaci yayi." Ya bude
ido sosai,"Ka ce mata, kar ta damu, lafiyar ta
lau, komai zai wuce Insha-Allahu." Dan sandan ya
ce,"Mu je ciki Yalla6ai."Naseer ya dube shi a
dage, ya ce,"Kai ne yalla6ai, ranka ya dad'e yace
Sageer.
Sai da Safe."
Can a mak'oshin ya amsa, don har cikin ran sa
yana bakin cikin ganin Naseer a wannan wurin.
Ya fito ya nufi ciki da tunani. Karatu kawai yake
yi, amma zuciyarsa na cike da tausayi Naseer,
ganin har za'ayi jarabawa 4.
Shi Naseer bai sami ko daya ba, abin ya dame shi
kwarai, don bai da abin yi ne kawai.
******************
Abin kamar wasa, sai da Naseer ya kwashe
kwanaki 3 ofinshin "Yan sanda, sannan takardar
sammacinsa ta zo. Ranar juma'a aka fara
sauraron shari'ar. Malam Balarabe dai babu
ruwan sa, don haka bai ma je kotun ba, su M.
Umar ne da mahaifin Sageer su ka je.
Sageer kuwa yana makaranta, amma gaba daya
hankali sa bai jikinsa. Balle kuma Zarah, wacce ta
fi kowa kunci na ta na tsare.
Tayi iya kar k'ok'arin ta, don ganin ta jure zaman
ta cikin makaranta kamar yadda Babanta ya
tilasta mata tafiya.
Amma sam ta kasa.
Bata fahimtar komai, kwance take kawai bisa
tebur, zuciyar ta na zugin tunanin wane hukunci
za'a yanke wa yayanta?
Saboda Salis ya sha alwashin sai ya sa an d'aure
Naseer, dalilin juya masa baya da Zarah tayi tashi
guda.
Naseer tsaye gaban Alkali, babu fargaba ko
shakkar wani abu, yana saurare aka gabatar da
k'arar sa, tare da laifin da ake tuhumar sa. Alkali
ya tambaye shi,"Ka ji laifin da ake tuhumar ka?"
Ya ce,"Ran ka ya dade, na ji."
Ya ce,"To ka amince da hakan, ko ka na da abin
cewa?"
Naseer ya amsa."
Ban amince ba, ni ban ta6a fad'a da makami ba.
Kawai dukan sa na yi, ya suma."Wani Lauya da
ke zaune tuntuni, cikin rukunin lauyoyin da ke
zaune, yayi fit!
Ya mik'e tsaye ya ce,
"My Lord,
Sunana Barista Usman, ni ne Lauyan mai kare
wanda yake k'ara, watau Salis.
Ina da 'yan tambayoyin da na ke son yi wa
Naseer."
Alkali ya ba shi umurni.
Nan take, yayin da su Malam Umar da M.Lawal
suke cike da fargabar wannan shari'a, gain har
lauya su Salis suka d'auka.
Lauya ya matsa kusa da Naseer, suka k'arewa
juna kallo, sannan ya ce,
"Ranar lahadi daya ga watan nan da muke ciki,
da daddare ka je k'ofar gidan su Salis, ko zan san
abinda ya kai ka can?"
Naseer ya amsa,"Gargad'i na je yi masa, akan
k'anwata Zarah, don ba na son ya rinka zuwa
gunta." Ya ce,"Wane irin gargadi ne da za ka bi
mu2m har k'ofar gidan sa, ka rufe shi da duka.
Sai da ya daina numfashi, sannan ka yi k'ok'arin
da6a masa Wuk'ar da ke jikinka?"
Hankalin Naseer ya k'ara tashi, idanuwan sa suka
kad'a jajur!
A fusace yake magana,"Ba haka bane!
Tare da aboki na Sageer muka je, na yi masa
gargadi da baki, na ce kar ya sake zuwa wajen
Zarah.
Shi ya fara kai min duka, duka 1 na yi masa, ya
fad'i sumamme.
Abokan sa 2 na wajen, kuma suna gani!
Lauya yayi d'an murmushi ya ce,"Malam Naseer.
Lokacin da ka yi wa Salis lilis!
Har ya suma ka yi iya k'ok'arin ka, don ganin ka
dank'arawa Salis wuk'a.
Amma ba ka sami nasara ba, sbd abokan sa da
suka fi k'arfin ka.
An kira 'Yan sanda sun zo wajen, har suka tafi da
kai ofishin su.
Amma abin mmk, babu wuk'ar nan a tattare da
kai.
Ko za ka gayawa kotu inda ka 6oye ta?"
Ya k'ura Lauya ido, kamar shi ma ya sumar da
shi yake ji, ya jima kafin ya ce,"Had'iye ta na yi."
'Yan kallo na ta dariya.
Alkali ya ce kowa ya natsu.
Sannan ya ce,"Nan a kota ka ke Naseer, ka kula
da harshenka."
Barista Usman ya gyara zaman kot d'insa, ya
ce,"Kowa ya san wuk'a bata had'iyuwa gare ka,
amma kowa ya ji da bakin ka ka ce tare da
abokin ka Sageer ku ka je k'ofar gidan su Salis.
Bincike ya nuna Sageer ya gudu kafin 'Yan sanda
su zo.
Menene dalilin gudun sa?"Ya kad'a kai tare da
fad'in,"Ni ma ban sani ba." Lauya ya dubi Alkali
ya ce,"My Lord, dole Naseer ya ce, bai san dalilin
gudan abokin Sageer ba, domin shi ya mikawa
wukar ya gudu da ita kafin isowar 'Yan sanda.
My Lord, kudirin Naseer ya kashe Salis da ya sami
damar yin hakan, sbd haka na ke rokon wannan
kotu mai adalci, da ta daga sauraron wannan
k'ara zuwa 27 ga wannan wata da muke ciki, don
ba ni damar tattara shaidu na, wadanda za su
tabbatar wa kotu wannan tuhuma da ake wa
Naseer gaskiya ne.
Na gode."
Ya koma kujerar sa ya zauna.
Zuciya kamar ta kashe Naseer.,
Kiri-kiri an lauya magana, ta zama sharri har ana
neman jawo Sageer ciki Ba shi kad'ai ba, hatta
Malam Umar haka zukatan su ke tafasa, shiru
kawai suka yi suna sauraron jawabin Alkali.
"Kotu za ta ci gaba a wannan watan kamar yadda
lauya ya buk'ata.
Sannan kotu ta buk'aci a kawo mata Sageer a
wannan ranar.
Shi kuma Naseer za'a aje shi a ruman har zuwa
wannan ranar."
Al'amarin daya fari a kotu, ya daga hankalin
kowa, hatta Malam Balarane da ke ikirarin babu
ruwan sa cikin rigamar da Naseer ya jefa kan sa.
Sai dai bai fito fili ya bayyana damuwar sa ba.
K'ala bai ce wa su M.Umar ba, har suka k'are
bayanan su.
Shiru na tsawon sakwanni bai tanka ba.
M.Umar ya ce,"M. Balarabe ko ba za ka ce komai
ba, ai ko tofa 'yar addu'a, don samun al'amarin.
Ya dube shi tsakar ido ya amsa,"Naseer ba ya
buk'atar addu'a, sai hukunci.
Damuwa ta 1 ce, yaron nan da aka jawo shi cikin
fitinar da bai ci ba, bai sha ba.
Shi kad'ai ke buk'atar addu'a.
Ubangiji Allah ya ku6utar da shi."
M.Lawal ya ce,"Insha-Allahu baki dayan su za su
ku6uta, duk da dai mu ba mu da k'arfin d'aukan
lauya, ai Allah na nan, za mu gaya masa ya duba
mana.
Ni zan k'arasa gida M. Balarabe, kuma ina ba ka
shawara fushin farko ba na ka bane.
Ka sani bakin mahaifi dafi ne ga 'ya'yansu, yayin
da suke cikin fushi da su.
Saboda haka ka sanya wa ranka ruwan sanyi, mu
rungumi k'addara.
Ya mik'e, ya na k'ara fad'in,"Malam Umar ni zan
wuce, sai yadda hali yayi kenan?"Ya ce,"To Allah
ya jishe mu alkhairi, ya kuma sauka mana
wahala."
Ya amsa da amin, duk suka yi Musabaha.
Ya wuce ba tare da M.Balarabe ya k'ara tofa
wani abu ba.
Bayan tafiyar M.Umar, ya dube shi, ya ce,"Malam
Balarabe ka yi wa girman Allah, ka sanya wa
ranka cewar wannan abu mukaddari ne daga
Allah, babu makawa sai ya faru." Ya ce,"Shi fa
Allah baya d'ora wa bawa abinda ya fi k'arfin sa,
sai abinda shi bawan ya d'ora wa kan sa.
Idan yayi taka tsan-tsan da rayuwar sa, yana
kiyayewa, sai Allah ya taya shi kiwo.
Shi yasa Ubangiji ya ce,"Idan kun ga sharri, to
daga gare ku ne, sai ku binciki kan ku.
Amma shi ya ce yana 1 daga cikin imani yarda da
k'addara mai kyau ko maras kyau.Na yarda cewa
Naseer shi ya jawo wa kan sa, sai dai kai ina son
ka yarda da cewa kaddara ce Allah ya dora
maka, babu makawa sai ka ga wannan 6acin ran,
amincewar kuwa shine ka daina fushi da Naseer,
ka taya mu addu'a Allah ya ku6utar da su."
Yayi shiru kamar ba zai tanka ba, tsawon lkc.
Sannan ya sauke numfashi ya ce,"Na ji Malam
Umar, na kuma gode. Allah ya bar zumunci,
amma kar ka manta, na yi rantsuwa ba zan yi
kaffara ba."
Malam Umar ya mik'e rai 6ace, ya fice daga
rumfar Malam Balarabe.
Babu Sallama.
Malam Balarabe ya bi shi da kallo, kawai na
tausayin su ya lullube shi, ya kad'a kai, ya ce a
ran sa,"Naseer na da gatan sa, amma shi bai san
hakan ba.
Allah ka shirya."
Haka hankali Sageer yake tashe, jin cewar shi ma
ana buk'atar sa a kotu da laifin shi ya gudu da
wuk'ar da ake zargin Naseer ya je kashe Salis da
ita.
Bai san lokacin da ya kawo kan sa gidan su Zarah
ba.tana kwance ruf da cikin, gefen tabarma da
suke tare da Innar ta,har ya gama gaisawa da
Inna Zarah bata iya dagowa ta dube shi ba, sbd
jin muryar sa ma k'ara dagula mata lissafi yayi,
wasu sabbabin hawaye suka cika idanuwan ta
tam!
Kayan makaranta ke jikinta, don bata iya cire su
ba, tunda ta dawo ta sami yadda shari'ar ta kaya
a kotu, ido jajur!
Sageer ya dubi Inna,"Yanzu mecece mafita
Inna?"
Gaba 1 tausayi yaran ya gama kashe mata jiki.
Ya nisa ta ce,"Mafita 1 ce Sageer, ita ce addu'a
wajen Allah.
Ka kwantar da hankalin ka.
Insha Allahu za ku ku6uta.
Kar ka damu ka ji?"Ya ce,"Shi kenan Inna. Allah
ya taimake mu." Ta ce,"Amin." Ya sauke
idanuwan sa, inda Zarah ke kwance, yayi kiran
ta,"Zarah! Bata amsa ba, ya ci gaba,"Kiyi hak'uri
Zarah." Dasauri ta mike cikin sassarfa, hawaye na
zuba ta nufi daki. Dai-dai k'ofa ta tsaya tana
fad'in,"Sai Allah ya tsinewa Salis!wannan sharri
yayi yawa.
Insha-Allahu sai ya ga k'arshen sa!"
Ta juya cikin d'aki da gudu.
Sageer ya ce,"Yaya za mu yi Zarah? Sai hak'uri
kawai."
Ya juya kan Inna,"Bari in koma Inna, ki gaida
Baban. Gobe asabar. Insha Allahi zan je in ga
Naseer d'in." Ta ce,"To Allah shi kare."
Ya amsa da
"Amin."
Ya mik'e ya bi Zarah d'aki. Can yayo ta
rarrashinta har suka shirya tafiya gidan yari gobe,
ganin Naseer, ba tare da sanin su Inna ba, don
kar su hanata.
Karfe 10 na safiyar asabar a k'ofar gidan yari tayi
masu. Sun jima suna neman yadda za su yi, a
bar su ga Naseer d'in, kafin suka sami
amincewar hukumar gidan mazan. Suna zaune
cikin wani d'an d'aki wanda za'a iya cewa ofishin
gandirebobin ne, aka fito da shi.
Bak'in k'ofar yayi tsaye ya sanya wa Zahar ido.
Kwanaki 5r kenan, amma ji take tamkar shekaru
5r ne.
Rabon da ta sanya shi a ido. Tausayinsa yasa
take ganin ya rame, ya dishe kamar ya shekara
yana ciwo. Hawaye kamar fanfo, suka tsunke
mata.
Naseer ya juya da sauri cikin 6acin rai ya ce wa
gandiroban,"Maida ni ciki!"
Ko kafin Sageer ya ce wani abu, har Naseer ya
kai bak'in k'aton gate d'in da ke k'argame a
bakin babbar k'ofar da za ta kai ka ciki.
Gandiroba na biye da shi,"Ba ka son ganin su
ne?"
"Eh!"
Ya amsa ba tare da ya waigo ba.
Gandiroba ya bud'e get, yayin da Sageer ke
k'arawa wajen,"
Naseer!
Naseer magana na ke so mu yi! Ya shige ciki, aka
rufe, sannan ya juyo ya ce,"Idan za ka zo, ka zo
kai kad'ai, ban da Zarah!
Ya wuce cikin sassarfa ya bar wajen.
Sageer yayi tsaye, yana kallon sa, har ya daina
ganin sa.
Ya tako a hankali inda Zarah ke durk'ushe, kanta
cikin guiwa.
Ya ce,"Zarah!
Taso mu tafi." Da kyar ta mik'e, gaba 1 Gandiroba
da ke wajen, babu wanda bai kalle ta ba, wasu
ma dariya ta ba su, ganin yadda Sageer ke jan
hijabinta, tana jefa k'afa kamar makauniya.Daya
daga cikin su da ke zaune gaban wani katon
tebur da alama yana daya daga cikin manyan
wajen.
Tsam!
Ya mik'e ya nufo su, abinka da yare kuma babu
musulunci, yana zuwa ya rungumo kafad'un
Zarah ya shiga rarrashin ta,"Kin kuwa san yadda
ki ke da kyau, ki ka zauna ki na kuka? Don
wannan tsohon mai laifin, ya ce bai son ganin
ku?"
Da sauri ta kwace kafad'un ta, ta balla masa
harara." Tsohon mai laifi?
Yayana ba tsohon mai laifi bane,sharri aka yi
masa, kuma Allah zai fitar da shi! Tuni ta bar
Gandiroba nan a tsaye. Sageer ya biyo ta. Dariya
suka ci gaba da yi, abinda ya k'ara hassala
zuciyar Sageer. Gudun mai zai faru, idan ya
tanka, shi yasa ya rufawa Zarah baya, suka bar
harabar wajen.
Tafe suke. Zarah na koken,"Kiri-kiri yayana ya ce
baya son gani na, me yasa?" Ya ce,"Ai ba zai so
ganin ki a yanayin da yake ciki ba. Ba zai so ki
rink'a kuka ba Zarah.."
Ta ce,"Ba wani Sageer, akwai abinda yayana ke
nufi." Bai nufin komai, yakamata ki gane, ba
kowane zai jure ganinsa a haka ba.
Kawai ki manta Zarah, addu'a kad'ai za ki taya
mu."
Ta sauke numfashi ta ce,"Yadda yayana ke so na,
haka na ke son shi Sageer, ya kuwa zama dole in
yi kuka, tunda yana cikin wani hali. Na san
yayana jarumi ne, komai zai iya jurewa, amma
zama cikin wannan shegen gidan rayuwar kunci
zalla cikin sa.
Salis ya bi son zuciya zai kuma ga 6acin ta yarda
Allah."
Dai-dai suna tsayuwa bakin titi. Sageer ke
fad'in,"Zarah yayenta kenan, soyayyar ta d'aure
min kai. Shi kuma Salis ai har

Please Login or Register in order to submit comment