Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wani garari, har yana tambayar kansa, "Da
ya motar nn tawa cefa." Ya kada kai kadan yace,
"Allah ya sanya alkhairi." yace, Amin. Ni zan tafi
sai yaushe zaka bullo ne?"Da kyar ya amsa, "zan
kira ka idan zanzo." Kukan wayarsa ya juyo daga
daki, don haka ya juya da sauri ya koma dakin,
yabar naseer tsaye ba tareda sunyi sallama ba.
Yana shigewa yaga ya turo kofarsa. Sam-sam
ran Naseer baiji dadin abinda takwarar sa yayi
masa ba. Shiyasa har ya bar wajen, yana
tunanin me ya faru tsakanin su? Don bai taba
ganin irin wannan fuskar ba awajen takwaran
na sa balle yayi masa irin abinda yayi masa yau.
Da wannan tunannin fal, ransa ya gama raba
tsarabar sa gidansu zahra da gidansu sageer.
Kowa nata murna, yanasa albarka. Ya dawo gida
karfe 12 dai dai na rana. Malam balarabe na
zaman jiransa. Yana shiga ya hau fada, "ina ka
shige saboda Allah? Bayan tun jiya na gayama
sammako zamuyi zuwa kaduna nan! Karfe 12
yanzu, yaushe kakeso muje mu dawo?" Yace "yi
hakuri Abba, ban san rana tayi haka ba. Ka
gama shirin ne?" Yace "tun yaushe nake zaman
jira? Tuwon girma, ai miyarsa nama. Wallahi
sammako naso muyi wa Alhj, don nuna masa
farin ciki na." Umma tace, "mallam ai gara ku
tashi da wannan maida zancan da kukeyi."
Gaban umman ya zube ledoji guda hudu,duk
kayayya ki ne. Umma ta zazzage su. Wai!
Haihuwa me rana, Kamar tayi kwalla saboda
murna. Haka Abba yayi zugum, yna alajabi. Da
ya tuna irin wuyar da naseer ya basu a can
baya, sai ya nisa yace,"Allah abin godia ne mai
shiryar da wanda yaso a duk lokacin daya so
din. Allah ka kara shirya mana ." Murmushi
naseer yayi, kwarai ya gane dalilin adduar Abba.
Ya dubi umma itama shi din take kallo, fara'ar
sa ta karu. Umma tace "me akayi?" Yace ba ayi
komai ba umma. Baki gama abinci bane." Abba
yace, "ba wani abincin da za'aci, tashi mu tafi,
ko kuma inbi ta haya." Ya mike, ya kwaso
takalma yayi waje ya cigaba da fadin. "Ai gidan
Alhj Basheer ba bako na bane." Umma tace,
"kaga, tashi ku tafi. Allah ya kiyaye hanya." Da
sauri ya tashi, yabi shi suka damki hanya.
Alhj na ofis lkcn da Naseer ya kira shi a waya.
Ya shaida masa zuwansu, don haka kai tsaye
can suka wuce. Malam Balarabe ya zuba godiya
kwarai da gaske. Abin yayi wa Alhj basher dadi,
shi yasa ya ce ba za su tafi ba, dole sai sun
wuce gidan sa sun ci abincin rana ko dama cin
abincin yake shirin tafiya. Lokacin da Naseer ya
yo masa waya, ya ce suna tafe.
Tare suka rankaya gidan na su.
Suna falon baki, akai ta shigowa da abubuwan ci
da sha iri-iri.
Tare suka ci, suka sha suna hirar duniya.
Sai misalin uku da rabi, suka baro kaduna.
************
Cikin wata guda, ginin da Naseer ke yi a cikin
gidan su ya kammalu tsaf! Gwanin ban
sha'awa, kowa ya ga tsarin da aka yi wa ginin
nan, dole ya ba shi sha'awa.
Bayan haka kuma sun yi shawara da Sageer
akan bude shagon dinki, don haka Naseer yasa
Sageer ya nemo shagon haya, ya biya kudin
shekaru 2.
Babu 6ata lokaci aka gyare shi, aka zuba
kekunan dinki guda 2 da na aiki (Design) tare da
na yin zig-zig. Sageer ya koma can ya samu
mataimaka, kafin ya kammala karatun sa,
wanda bai wuce wata 3 su fara jarabawar
karshen ba, ta kammala Diploma.
Shi kuma dan gogan fafitukan shirye-shiryen
auren sa ya ci gaba da yi, don ita ma Zarah,
wata 5 suka rage mata ta gama sakandire.
Manyan akwatunan sa (Set) guda ya kusan
shake su da kaya na gani na fada, na burgewa
gaba dayan su, sai sharholiyar su suke yi, ba su
da matsala, duk da cewar kusan kullun sai
Zarah, ta amshi bakin 'yan mata a makaranta
masu zuwa ganin ta, wanda akasarin su, su
Lubabatu suke yi masu jagora.
Abin ya daina tada mata hankali, ta daina wasi-
wasi. Zuciyar ta ta sami sukuni.
Domin ta hakikance Naseer na ta ne ita kadai,
don bata ta6a gani ko jin yana neman wata ba,
Masu karyar su 'yan matan sa ne, sun gaji sun
daina, saboda rashin ganin fuska. Kirsa iri iri
naseer na gani a wajen wasu yam matan
marasa kamun kai da hakuri. Su kan mance
mijinka, idan Allah ya kawo shi, kana
kyakkyawan zaman ka zaizo ya sameka.
"(Karshen zubar da aji kenan a waje na, kuma
ina ganin ko a al'adar bahaushe. Saurayi shi ke
zuwa tad'i, koda kuma had'in iyaye ne.
"Ma'ana iyayenki suka ba shi ke, su kan ce ne
ya zo ya ganki, ba wai ke za'a ce ki je ki gan shi
ba. Mata kuna da kima da martaba mai yawa.
Don Allah ku rika zama kamammu a
kodayaushe, domin komai yawan da ake cewa
kun yi, har ana muku kirarin kamar Janpa a jos.
Wallahi babu wanda ya isa ya je gidan ku ya
d'auko ki, dole sai ya bi ta yadda shari'a ta
tsara."
Ba wai da ganin saurayi, kina son sa ba, kita
binsa kamar yadda wasu yam matan sukeyi a
wannan zamani. Watanni uku bayan dawowar
naseer daga Ghana, ranar litinin da safe yana
office din Alhj Basheer kamar yadda ya bukaci
ganinsa a wannan lokaci. Alhj ya dube shi irin
wanda ya saba yi masa irin na kauna yace
"Naseer ya maganar karatun ka ne? Diploma
gareka ko degree?" Naseer ji yaji tambayar Alhj
tadan sa shi al'ajabi, sai dai zuciyarsa bata raya
masa komai ba, don haka yayi dan murmushi
yace, "Alhj sakandire kawai na gama". Shima
Alhj mamaki ne ya kama shi, fuska a yamutse
yace, "why? Kuma shine tuntuni baka koma ka
ci gaba ba?" Shiru Naseer yayi a dalilin bashida
wata hujjar badawa. Shi yasa Alhj yaci gaba da
cewa, "gaskia banji dadi ba, amma ba matsala,
ka kawo min takardunka, ka zabi ko wacce
makaranta kake son zuwa." Naseer ya shafa
keya, shi kan sa nauyin ya fadin abinda yasa
yake ji. "Ai ban....ban ma samu yin jarabawar
ba. Take nan tausayi ne ya lullube Alhj Basheer,
don babu abinda yazo zuciyar sa, illa matsalar
rashin kudi, saboda haka bai nemi sanin dalili
ba. Kai tsaye yace, "Anyway, tunda abin ya
zama haka, sai kaje ka binciko lokacin da zaa
fara biyan kudin jarabawar. Zan baka ka biya,
ka rubuta. Idan (result) ya fito zaa san abinyi.
Gaskia ban taba zaton haka ba, da tuni na
tilasta maka ka koma school. Shi ilimi ai baa
wasa dashi, domin wata fitila ce, wanda hasken
ta bai taba dushewa har abada. A kowane lokaci
zai yi maka amfani." Naseer ya kara sunkuyar
da ido yace "Na gode Alhj. Ina ganin ma an
kusan fara biyan external insha Allah zan biya."
Yace "bance ka biya ba, ka kawo min yawan
kudin nace, ni zan ba ka. Murmushi yayi kafin
yace , "to Alhj nagode. Bari in karasa wajen
Yakubu." Ya amsa, "To, shike nan. Yauwa, gobe
in Allah ya kaimu zan tafi Abuja, 'yar waje na
zata dawo daga jordan, zan dauko ta a (Airport).
Koda yake bka san ta ba. Nusaiba sunan ta, ta
kare digiri din ta bana. (Arabic and islamic
studies)." Naseer ya numfasa yace "tayi kokari,
nayi mata murna. Allah ya kai mu lafiya."
"Amin, amin. Kana iya tafiya, shike nan."



Zaharaddeen shomar

Whatsapp 08168575100



Ajininsa yake 1-07
Posted by ANaM Dorayi on 08:04 AM, 09-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
.Ya mike ya sallame shi, ya fito Alhj ya raka shi
da kallo.
Yana rufe ofis din, ya dan kada kai.
Haka kawai Allah ya sanya masa kaunar Naseer.
Bai ki kodayaushe su kasance tare ba, sosai yake
jin sa cikin zuciyar sa, tamkar dan daya
haifa.Wani lokaci har ya kan tambayi kan sa ko
don ba shi Da namiji ne? To ai kuma yana da
yara masu yi masa hidima a ko'ina, tun kafin
zuwan Naseer,amma bai ta6a jin wanin su a cikin
ran sa, kamar yadda Naseer ya kama zuciyarsa
ba.
Komai zai iya wa Naseer dai-dai yadda zai yi wa
Nusaiba 'yar cikin sa.
Kawai ya kan danne wasu abubuwa ne, saboda
kar sauran yaran sa su ce ana nuna masu
bambanci ko su fa zargin wani abu.
Washe gari k'arfe 2 na yamma Alhj Basheer ke
tsaye wajen tarbar fasinjojin a filin jirgin sama na
tarayya Abuja.
Bayan wasu 'yan mintocin jirgin da ya taso daga
Jordan ya sauka.
Daya bayan daya fasinjojin da ke ciki suke fitowa.
Jimawa kadan wata tsaleliyar budurwa ta fito
saye da doguwar riga da dan karamin farin hijabi,
wanda gaba daya tsayinsa bai zarce kafadunta
ba.
Wankan tarwada ce sosai, fatar ta ke ta walwali
ga kyakykyawar fuska mai dan fadi.
Hakan ya dai-daita zaman siririn hancinta da
tsarraren baki.
Tana da wadatar idanuwa fa gashin ido da gira.
Dan matsakaicin tsayi gare ta, sai dai za ta dan
d'ara Zarah kadan,
tofa! Mekuma yakawo wannan zancen? Maji ma
gani...
jaye take da wata jaka ruwan toka mai
matsaikacin girma ga kuma karama rataye a
kafadarta.Tun da suka hango juna. Su kai
musayar murmushi har ta karaso fara'ar ta ta
kara karuwa take yi, tana isowa ta saki jaka ta
rungume mahaifinta,
"Abba na!"haka lallausar muryar ta ke fadi,
tamkar Zarah ce ke magana.
.*****Tinani**** kodai..........uhm banda
shishshigi ANaM...
saboda kwarai yanayin sautin muryar su, yayi iri
daya.Alhj ya dago ta bakin sa har kunne ya
dube ta,"Yar gidan Abba kenan,
"To ya hanya?"
Ya su Antinki?"
Ta ce,"Lafiya lau Abba na.
Ina Ummi?"
"Bata zo ba?"
Umminki na gida, ta so zuwa, amma kin san ta
so lazy,
you know?"
Wai kuma ta fasa saboda tafiyar mota'¿
Ta kayata fuskarta da lafiyayyen murmushi,
"Lallai Ummi, ko kewa ta ma bata yi ko?"
Ai shi ke nan."
Ya ce,"Ba ga Abbanki ba? Duk na kosa ki dawo
my baby, kullum na dubi kofar ki a kulle, sai inji
raina sam ba dadi."
Ta kara kwantar da kanta bisa kafadar sa,"Ni
ma haka, na yi Missing din ka Abbana."Cikin jin
dadi ya rungumo kafadarta, ya ce,
"To mu je mota,
direba na jira."
Dai-dai lkcn da aka kwarara sallama, duk suka
duba suna amsawa."
Wani kosashshen matashi ne, cikim adon
bakaken (Suit).
Yana da tsayi sosai, don ya kare Alhj Basheer."
Ga fadi da alamar hutu,
shi ba fari ba, fara'a sosai bisa fuskar sa, yayin
da ya dan duka yana fadin
"Ina yini Baba?"
Tuni Nusaiba ke kame da baki, tana masa kallon
mamaki, ido waje.
Alhj Basheer ya amsa."
Lafiya.
Da ga ina?
Ban shaida ka ba._?
Ya ce,
"Dama.............."
"A jirgi mu ka hadu Abba.
Wai sunan Sa Ibrahim."
Nusaina tayi saurin taran numfashin sa.
Alhj Basheer ya dan tsuke fuska yana dubn ta,
"I see,
ina mota ki same ni can."
Ya juya kan Ibrahim ya ci gaba,"Ka gaida gida."
Ya kara rankwafa ya amsa,
"To
Abba na gode."
Ya wuce ran sa bai masa dadi ba."
Yana bada baya.
Ibrahim ya dan runtse ido ya fada a hankali
"Yes!"
Ta ce,
"Don me za kai min haka?"
Ya ce,"Shi yasa ki ka fito da sauri kenan."
Bai kamata ka zo kai tsaye wajen Abba na ba,
haka kawai daga gani na a jirgi.
Ya ce,
"Oh,
duk bayanin da muka yi, fita suka rika yi suna
bin iskar jirgi?"
Haka bai dace da ke ba, yakamata ki amince da
cewar da gaske nake yi."
Cikin damuwa ta ce,"Ina cewa na gaya ma
sunana, na ba ka (Address) da lambar waya,
sai me?
Karshen amince kenan a zato na."
Tsararren bakin ta kawai yake kallo, sansanyar
muryar ta na sa shi dogon tunani.
Ya shafa kai, ya numfasa ya ce,
Fakat!
Kin kare magana.
Mu je in raka ki,
kar Abba ya ga kin dade."
Ta ce,"
Na gode."
Ba sai ka raka ni ba, ina jin kunyar Abba."
Amma yakamata in ce da shi Allah kiyaye hanya.
Ko kuwa?????""Ta juya, ta ja jakar ta, ba tare da
ta amsa ba.
Biyo ta yayi da sauri, yana fad'in
"Please, da zarar kin sanya layin ki, ki yo min
(Flashing)
don in san kin maida layin, ina fatan za ki
taimaka?
Ta tsaya cak!
Ta ce,
"Ni ma ka taimake ni ka koma, zan kira din."
Ya kare mata kallo, kafin ya ce,
"Promise?"
"Na yi."
"TO Allah ya kiyaye hanya, ki ce wa Abba a
sauka lafiya, kin kankane min shi."
"Dan murmushi ta yi ta wuce abin ta.
Shi kuwa nan yayi tasye yana kallon yadda take
takawa har ta fice daga wajen."
Yayi zazzafan ajiyar zuciya, ya so ace ta dan
sake waigowa ya kara ganin kyakkyawan fuskar
ta, amma ina,
hakan bai samu ba.
Shi yasa ya jima ya na wasi-wasi, yana ganin
kamar bai sami kar6uwa ba.
Alhj Basheer ke zaune a cikin lafiyayyar motar
sa (KIA).
Ko alama fuskar sa babu walwala.
Isowar Nusaiba ma yasa ya kara tsuke fuskar.
Tana karasowa jikin but, ya dago mata shi ta
bude, ta jefa jakar ta ciki, ta rufe.
Sannan ta iske shi a ciki.
"Mu je ko Abba."
Bai amsa ba, yayi wa mota key, ya fito harabar
aje motoci.
Ya dauki hanya.
Shiru suka yi na 'yan dakikan, ran Alh.
Basheer na sosawa akan al'amarin daya gani
wanda yake ganin yakamta yayi wa tufkar hanci
da gaggawa, don cimma burinsa.
Buri kuma!!!! Baridai inyi tanbaya a nan, friends
kunsan burinsa? Inna jiran amsarku wadda ita
zatazama matakin dorawa daga wannan page,
idankuka Marubuciyar tabamu baki daya ta
hutashshemu kenan!! ANaM Dorayi ***Smile***
Haka zalika ran Nusaiba yake kuntace....domin
ba'a son ranta Abban ta ya ga Ibrahim ba,
saboda bata gama tantance shi cikin ranta ba.
Musamman jin cewar yanada mata daya da yaro
daya. Shirunsu yayi yawa kuma, abinda Nusaiba
ta lura kamar ran Abbanta a bace yake, ba
yadda ta fara ganin shi ba, don haka ta nemo
abin cewa. "Abba na". Ta kira shi. "Uhmm!"
Tace, "Ummi taki zuwa dauko ni, abin yana ta
ban haushi." Da wutsiyar ido ya kalleta, "Ni ba
wannan matsalar ta dameni ba." "Meya dameka
Abba?" Yayi dan jim, kafin yace, "me kike tunani
gameda Ibrahim?" Kunya cike da idon ta, ta dan
sunku yar da kai, tace "Abba, Ibrahim a jirgi
kawai muka hadu." Yace, "wannan ba itace
amsa ba, zaka iya ganin mutum yanzu take nan
ya shiga ranka, shi yasa na tambaye ki menene
raayinki akansa." Tayi shiru, jin tayi shiru, yasa
ya c igaba. Kar kiji kunya, ki gaya min komai
Nusaiba, kin san ni mahaifinki ne, kuma ke
kadai ke gareni, kuma ina alfahari da ke.
Saboda haka ki warware min komai, menene
raayinki akan Ibrahim?" Tadan cire kai ta dube
shi, tace "banda wani raayi akan sa tukuna,
saboda kasan komai sai da shawara da tunani."
Yace "hakane, amma zanso ace kin gaya mun
wani abu." Tace, "bansan komai a gameda
Ibrahim ba, illa ya gaya min shi dan gidan Alhj
Abdul Mutallib Kazaure ne.Shahararren dan
kasuwan nan na kano. Garkuwan kazaure. Shi
maaiksaci ne a (Nigerian Embassy Jordan),
yanada mata daya da da daya." Alhj ya kada kai
yace, "Nusaiba." Ta amsa "Naam Abba." Yace,
"idan nace ki aje Ibrahim a filin jirgi, tunda a
jirgi kawai kuka hadu, zaki iya?" Kai tsaye ta
amsa, "me zai hana Abba? Kaban umurni, in
ketare, mecece hujjata a matsayinka? Biyayya a
gareka dolene Abba, muddin ban sabi sharia ba,
saboda haka na aje Ibrahim, ban san abinda ka
hango min ba." Ya kare mata kallo, sannan ya
aje numfashi. Shi yasa yake son Nusaiba kamar
ya hadiye ta. Yace "yar albarka mai kaifin
hankali da sanin matsayin na gaba." Musamman
iyayenta da take jin su sosai cikin ranta.
Abbanta ma yafi shiga ranta, ba kadan ba,
saboda yadda ya nuna mata kauna da soyayya,
tun tana yar mitsitsiyar ta. A lokacin data
mallaki hankali kuwa, sun kasan ce abokan
shawarar juna, babu abinda ya dami Alhj
Basher, zama yake da abar sa, ya war ware
mata duk abinda ke cikinsa. Walau farin ciki ko
akasin hakan. Balle ita da take a matsayin mai
karancin shekaru, bata zar tar da komai sai
abban ta yasani. Hakan ba kankanin tattalin
kaunan dake zukatan su yayi ba. Mika hannu
yayi, ya dauko nata, yadan matse shi, kafin yace
"Nusaiba na gode Allah daya bani ke daya tal!
Amma ki ka zama tamkar dubu. Kinsan dalilin
cewa ki aje Ibrahim?" Ta kada kai tana dubansa.
Yace, "miji na zaba miki.". ****Uhm*** anxo
gurin, amma banan gixo ke sakarba!!!!! Haka
kawai taji gabanta ya fadi, sai dai kuma ta rasa
dalilin bayyanar murmushi a fuskar ta har da
wata bazawarar kunya data sauka cikin
idanuwanta, masu kyau da haske. Aje kai tayi
kasa taci gaba da murmushin. Abinda ya kara
faranta ran Abbanta kenan. Ya Kara runtse
yatsunta, yaci gaba da cewa, "Naseer yaro ne
dan mutunci. Dan babban gida. Ba wai ina nufin
babban gida irin na wannan zamanin ba, kamar
yadda mutane suka maida rayuwa akan tarin
dukiya shine mutunci da babban gida. A'a ina
nufin kyan asali, addini,da dabiu na gari, wanda
yakan samo asali ne daga tarbiyar iyayen
babban gida.
Aunty Zulyma ta hutashsheku!! Ammafa......
Uhm! Muje zuwa wai Mahaukaci ya hau kura....
Baki nan aka kawo min Naseer, yana min wasan
polo, a maganar nan yanzu da nake miki, ya
zama wani jigo a harkar wasan polo abin
alfahari. Allah ya sanya min so da kaunar Naser
fiye da tunaninki, wanda har ya kai ni ga son
hada zuria da shi. Sai dai bani da kowa sai ke
Nusaiba, shi yasa nake rokon ki da nuna min isa
da ke kuma biyayya ta karshe da zaki min, ki
amince da zabin da nayi miki" Wasu kwallane ke
cike fal! Cikin idanuwan ta, wadanda ita kanta
bata san dalilin taruwar su ba. Daga bisani ne ta
fahimci cewar kalaman Abbanta na karshe, su
suka tara mata hawayen da suke neman sauka
bisa kuncin ta. Jin yayi shiru, yasa ta dube shi,
duba na aminci da girmamawa, tace Abbana
kaban mamaki daka ce kana rokona, kenan kana
kokwanto akan ba zan maka biyayya ba. Ai...."
Hawaye shar shar! Bisa kuncinta. Shiya hana ta
karasa zancen ta. Tasa hannu tana sharewa
wasu na kara fitowa kamar ma kukan naso yaci
karfin ta. Hankalin Alhj Basheer ya tashi
matuka. Fuskar sa ta nuna karara, "ba haka
nake nufi ba bebina, kin ga dubeni. Ki dubeni
nace" Ta dago idanuwanta jajur! Ta kalle shi,
yayi sauri ya goge hawayen ta sannan ya dawo
da hankalin sa ga tukinsa, bakinsa na fadin,
"wannan maganar ta wuce. Yanzu gaya mun
yaya kikaji daga ambatar sunan Naseer?" Tace
"Abbana ai tun ina yar yarinya raayinmu daya
dakai, balle a yanz dana mallaki hankalina,
nasan cewar ba zaka taba kai ni inda zan cutu
ba. Dadin dadawa kuma a shariance, matsayin
dana ke yanz na wacce bata taba yin aure ba.
Hakkin Kane ka zabar min miji na gari wanda
kake min hangen farin ciki da kwanciyar hankali.
Don haka Abba ka daina roko na, kace mun
Nusaiba na baki umurni kawai, ni kuwa inbi."Bai
san lkcn daya fashe da dariya ba,yana fadin,
"Bebina gime a hug!" Ta matsa kusa da shi
sosai, tayi kwance bisa kafadar sa kunshe da
murmushi bisa fuskarta." Allah yayi miki
albarka."Insha Allahu yadda ki ka faranta min
rai, haka ke ma zaki kasance cikin farin ciki."
****Uhm! To Allah ya amsa?****
Ta k'ara makale masa ta ce,"Amin Abba
na........." Ta ja sunan Abban yayi tsawo, don jin
dadin sa. Haka suka kasance har isowar su
Kaduna." Labarin Naseer yake bata. Jaruntakar
sa da kwarewar sa akan wasan polo.Haka kuma
bai 6oye mata karancin karatun sa ba. Take nan
suka zakulo yadda za'a warware wannan 'yar
matsalar.
Ko alama Nusaiba bata yi kama da Hajiya
Zulaihat ba, watau duk kyanta a wajen Abban ta
ta samo shi.
Ita fara ce sol! Tana da manyan kyau, ma'ana
da ka dube ta, za ka gane kyakkyawa ce.
Sa6anin Nusaiba, ita kananan kyau gare ta,
kana kallon ta, tana qara kyau, ba za ka ta6a
ganin sauyi ba.
An riga anyi sallar magariba, lkcn da suka iso
gida. Tana rafka sallama. Ummin ta ta fito,
"Oyoyo, bebin Ummi!
Nusaiba ta cunno baki,"
Ba wani."
Ai wallahi Ummi......."
Rungume ta tayi, shi yasa ta kasa k'arasawa.
Ummin ke cewa,
"Yi hakuri, jiki na ne na ji yayi min nauyi, shi
yasa ban biyo Abban ki ba. To ya hanya?" Ta
ce,"Lafiya lau.
Su Anti na gaishe ki."Ta ce,"Kyale Antin nan ta
ki, wai a waya take min shegantakar da ta
saba." Tayi 'yar dariya ta ce,"Zan cen Anti bai
wuce na amarya. Na dai ce mata ta bari sai an
rangado mata, sannan ta sami bakin magana."
Yauwa, na gode da ki bata amsa, sannan
sallamar Alhaji." Kin ma tsaya ki na hira da ita
ne, bayan ta ki zuwa dauko ki."
Dukan su dariya suka yi." Abba na ai rike ni
tayi."
To kwace ki gudu kawai, kar tayi miki wani dadin
baki."
Ta ce,
"Yanzu kuma Abba."
Ta suri jakar ta nufi dakin ta.
Ummi na fadin,
"Au, zuga ki yayi?"
Ta juyo dauke da murmushi, ta kada kai ta
wuce abin ta.
Hajiya Zulaihat tayi wa Alhj sannu da zuwa.
Ya amsa, tare suka haye sama."
Nusaiba na shiga dakinta, ta yar da jaka,
ba6ata lkc ba, bayi ta shige, jimawa kadan ta
fito da alwala, tayi sallolin ta.
Ta jima bisa sallaya tana lazimi har zuwa kiran
isha'i, ta mike ta ci gaba da sallah. Bayan ta
idar, sannan ta cire kayan jikin ta, tayiwanka ta
nufi.
Madubi da ke shirye tsaf!
Da kayan kwalliya iri-iri, ta ja kujera ta zauna."
Daddaga kayan da ke wajen tayi, duk sababbi
ne aka zuba mata.
Dan murmushi tayi, ta fada a ranta,"Ummi na
kenan."
Ta shafe jikin ta da (Lotion), sannan ta mike ta
nufi Wadirof, ta janye murfin gilas din, haka tayi
tsaye wangame da baki.
An cire wadirof din ta tsadaddun kayayyaki kala-
kala.
Wani farin ciki ya sake kama ta, a lkcn guda
zuciyar ta ta kara kamuwa da tsananin son
iyayenta.
Ta shiga dubawa, gaba daya ta rude ta ma rasa
wace riga za ta sanya."
Domin duk wacce ta d'aga, sai taga ta fi ta farko
kyau. Da kyar ta iya dai-daita zuciyar ta, ta
dauki wata 'yar kanti ruwan hoda, doguwa mai
karamin hannu ta sanya.
Gaban rigar akwai ado na furanni farare
kanana, su suka kara wa rigar kyau.
Da ta koma jikin madubi kuwa, ka rantse da
Allah sbd jikin ta kadai aka yi rigar, ita kanta ta
tantance hakan.
Gashin kanta da ke sake, shi ta kama tana
daurewa da wani dan karamin (Ribbon) da ke
makale jikin rigar.
Bata kammalaba Umminta ta budo kofa ta
shigo,
"Ke!
Wai ba za ki fito cin abinci bane,
iyayen gayu?"
Da sauri ta tarbi Umminta ta rungume,
"Allah sarki Ummina, na gode da kaya."
Ta dago ta,
"Gaskiya kuma kin yi kyau bebin Abba. To mu je
ki ci abinci. Abbanki ya ce idan kin gama, ki
same shi daki." Bakin ta har kunne ta
amsa,"Minti 2, Ummi gani nan." Ta wuce dauko
mayafin rigar. Ummi kuwa ta fice daga dakin."
Akan tebur, daga ita sai Umminta, domin shi
Alhj Basheer bai damu da ya ci abinci bisa tebur
ba, ya fi son akai masa cikin dakin sa ya ci.
Abinci kala-kala, kowa ya za6i abinda yake so
ya ci.
Nusaiba ta yayyafita, saboda kosawa tayi ta ji
kiran Abban ta.
Tana mikewa. Ummi ta ce,"Ke ba dai kin koshi
ba?
Ta nuna hanyar sama ta ce,
"Abba na kira can za ni."
"Cewa yayi ki ci ki, koshi kafin ki je."
Cikin doki, ta ce,"Na koshi ummi, idan ma zan
kara, na kara a wajen Abba na."Ta sumbaci
kuncinta ta haye sama da gudu. Ummin ta, ta
raka ta da ido har ta kule." Ta aje numfashi,
tana karkada kai. Tabbass tayi kewar 'yar diyar
ta, tilo tamkar dubu."
Sallamar Nusaiba Alhj Basheer ya amsa.
(Laptop) ce a gaban sa, yana ta 'yan dube-
duben ajiyar sa. Koda shigar ta, kwarai ta ga
dakin ya sauya mata.
Ga wasu bakin makamakan hotuna guda 4 da
suka kara kayata kafcecen dakin, daya kai
girman wani falo.
Uku daga cikin hotunan Alhj Basheer ne tare da
Naseer rike da wasu kofuna tare da wasu
kyaututtuka.
Dayan kuwa Naseer din ne shi kadai, ya da wani
katon kofi sama, dariyar da yayi ta kara
kwarjinin fuskar sa. Kai tsaye gaban hotunan ta
tsaya ta zuba ido.
Domin ko alama bata tantama wannan shine
Naseeerrrrrr!!!!......."
Ba wai son sa bane take ya kamata, a'a
kwarjinin sa ne ya debi hankalin ta har ta ji
faduwar gaba, kuma ko alama bata ji tana kin
sa ba.
Tana kokarin kaucewa hotunan, ta ji hannun
Abbanta ya rungumo kafadar ta, ya lika ta
kuibinsa.
Ta dan sauke numfashi kadan, ta ce,"Hotunan
ko sun yi kyau."
Yayi dan murmushi ya ce,"Allah ko?
To ki canka waye a tare da ni? Cikin
zolaya t amsa,
" Bebin ka of course."
Ya ja hancin ta ya ce,
"Stop joking."
Ba ni ce a tare da kai ba Abba?"
A hoto na ce,
kin sani sarai,
come on,
gaya min."
Tayi 'yar dariya,
"Uhmm...........jarumun dan wasan polon nan da
aka kawo ma ka shi, lkcn da ba nan.
Ya ma sunan sa?"
Ta tambaya, tana duban sa.
Haka shi ma yake kallon ta kafin ya ce,
"Sunan sa ya 6ace miki kenan?
Maganar Abba bata da muhimmanci ko?"
Ta kada kai,
Wasa na ke,
ai da shigowa ta na gane Naseer ne."
"To yaya ki na son sa?????"""""
Da sauri ta bar wajen, ta koma bisa wasu
kujerun farin karfe na alfarma ta zauna.
Kunya ce mai karfi ta kamata.
Shi ma ya tako a natse ya zauna gefen ta."
Wannan shine zabin da na yi miki, ina son ki
gaya min yayi, ko bai yi ba?" Kan ta a kasa, ta
amsa, "Yayi Abba."
Ki na son sa?"
Tayi shiru jim.
Sannan ta kalle shi,"Ummi ta ce kana kira na."
Wannan shine kiran, ki ga mijin da na za6a miki,
sannan in tabbarar da ki na son sa.
Ki gaya min."
Abba na ce yayi."
Ba yayi ba,
ki na son sa?"
Alhj fa ya tasa ta gaba, ita kuma duk kunya ta
rufe ta, da kyar ta cije ta daure ta amsa,
"Eh!"
Ta mike a guje, ta bar dakin.
Alhj Basheer ya bi ta da kallo yana dariya,
sannan ya numfasa yayi hamdala ga Allah.
Kai tsaye Nusaiba dakin ta shige, ta fad'a bisa
gado, ta nutse cikin katifa.Ta jima a kife, kafin
ta birkito ta tsirawa fitlun da ke cunkushe suna
lilo a saman tsakiyar dakin ido.
A zahiri su take kallo, amma ko alama ba kyan
tsarin bane cikin ran ta.Zuciyar ta yamutse take
da tambayoyi masa yawan gaske a game da
za6in da Abban ta yayi mata."
Shin waye Naseer?
Wane irin sani Abban ta yayi masa?
Duka zahiri da badini?
Ya za kai kar6e ta, idan ya ganta?
Watakila shi ma hoton na ta ya gani, kamar
yadda ita ma ta gan shi...................
Ta sauke numfashi, ta fada a ranta,"Allah ka sa
aure na da Naseer alkhairi ne."
Ta yunkura ta tashi zaune,
"Yar jakar hannun ta da ta yasar bisa gadon tun
shigowan ta, ita ta jawo gaban ta, ta bude zif
din ta dauko wayar ta.
Ta mike ta koma jikin wata dirowa, wacce jerin
akwatuna ke bisa kanta." Ta jawo ta tsakiya, ta
binciko (Sim card) na ta, na gida Najeriya ta
dawo bakin gado ta zauna. Sannan tayi aikin
maida shi cikin waya. Jimawa kadan ta nemo
wata lamba mai dauke da sunan KAUTHAR. Ta
kira babu wani bata lokaci aka sada ta da
kauthar. Can ta tsinkayi ihunta, "ba dai kin iso
ba!

Please Login or Register in order to submit comment