Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nemi sanin mahaifin Naseer kuma ba 6ata
lkc, ya kulla zumunci da shi mai karfi gaske.
Sanin mahaifin Naseer Malam Balarabe, ba mai
karfi bane, shi yasa Alhj ke yawan yi masa
alkhairi akai-akai. Kwarai a halin da ake ciki
yanzu Malam Balarabe yana alfhari da Naseer
kuma yayi imani a polo abincin Naseer yake. Shi
yasa Allah ya shimfida masa so da kaunar
sukuwawan da shi a da yake ganin ba karamin
saba masa yake yi ba.
Sai dai duk da haka yana yi wa dan sa huduba
da kar ya mance da ci gaban karatunsa, kamar
yadda kullum Sageer da Zarah tare da iyayen ta
ke masa matashiya akan gyara jarabawar sa,
don ci gaba da karatunsa na gaba. Amma shi
dan gogan ya riga ya raja'a akan abin da ya sa
gaba, Kuma yake da buri a kan sa. Ko alama
baya waiwaye, wanda hausawa ke wa kirari da
adon tafiya.
Inda ya sa gaban sa, kawai can yadosa bil hakki
da gaskiya.
A yan tsakanin ne kuma Sageer yayi nasara
samun gurbin karatu a (poly) da ke Gaskiya,
Tudun-Jakun Zariya, a fannun kasuwanci
(Businees Admin).
Baba 6ata lkc, ya kama karatun zango-zango,
kuma abn mmk duk tare da gudumuwar aljihun
Naseer karatun na Sageer ke tafiya.
Bayan haka bai daina zuwa wajeb dinkinsa ba, a
halin yanzu ma ya kware babu irin dinkin da ke
gagaran sa, ta nan ma baya rasa taro sisi, duk
da dai ogan sa, bai yaye shi ba. Yana nan tare
da shi.
Haka al'amuran suka rinka tafiya dai-dai da
yadda Allah ya shirya wa kowa rayuwar sa.
Soyayya tsakanin Alhj Basheer da Naseer kuwa
kara shiga ran Alhj take yi tamkar yadda Naseer
ke kara fito da (DABAI RIDERS) a duniyar Polo
ciki da Wajen Najeriya, watau kasashe
makwantan mu.
Tuni Yakubu ya sakar wa Naseer kambunsa
gaba 1, yana mai alfaharin shi ya kawo wa Alhj
gwarzon Da, wanda yake ganin ma ya na taka
rawar da shi bai taka rinta ba.
Shi yasa kullum kirarinsa da babbar murya yake
masa,
"NaseerJah-Jah!"
*****************
. BAYAN SHEKARu BIYU.
A cikin shekarun biyun nan, ba sai mun tsaya
dogon surutun irin tambarin da sunan Naseer
Jah-Jah yayi a duniyar Polo ba.Musamman a
cikin garin su da unguwar su, idan aka yi
la'akarin da irin kwarjinin sa tun farko, balle
yanzu daya kasance duk wanda ya dube shi, ya
san yana hutawa,kuma yana kan lokacinsa,yayi
fad'i, ya yi zabgege, ya k'ara fari da ka ganshi,
ka ga d'an wasan motsa jiki. Maganar kyau da
iya shiga irin ta sutura, abin ba dama, domin
Naseer ya dad'e da gogewa wajen iya tsafta.
Don haka ya zarce wa tsara.
Ya zama abinda bature ke kira (TALK OF THE
TOWN), wato abin hira a gari.
Ta yadda ya tsara rayuwar sa. Abin ya na da
ban sha'awa, saboda babu girman kai, babu
wulakanci kuma abin hannu sa bai tsokane
masa ido ba. A duk lokacin da yake gari, za ka
ga samari na yawan sintiri gidansu.
Can kuma 6angaren tauraruwar sa, komai tafiya
yake dai-dai da ci gaban da aka samu, domin
kusan a yanzu Naseer shine ragamar karatun ta.
Bai kyashin kashe ko nawa ne a dangane da
hidimar Zaran sa.
Wani abin sha'awa da ya fi kowa, a cikin
gidansu yake shirin fitar da wani gini mai bn
mmk. Kasancewar gidan k'aton gaske ne, ko
dama rashin kud'i ne yasa yake a wulak'ance.
Tuni aka fitar wa iyayensa 6angarn su. Shi kuma
na sa 6angaran aka shimfida filat mai d'akuna
3. Ba shi da buri daya wuce ya tsara wa Zarah
abubuwan da zai fiddo ta daga cikin tsara,
tunda ga shi Allah ya ce su huta."
Kwatsam!
Allah da ikonsa sai ga takarda daga k'asar
Ghana zuwa (DABAI RIDERS), suna neman izinin
d'aukar Naseer haya na wata 1, don gudanar da
wasa a wata kungiyar wasan Polo da ke can
Ghana.
"Al'amarin yayi wa kowa dad'i.
Musamman Alhj Basheer da Yakubu kuma babu
6ata lkc.
Alhj ya amince masa da tafiyar, babu wani
sharad'i ko wata tsatstsaurar doka.
Ranar tafiyar sa, yayi sallama da kowa, sannan
ya nufi gidan su Zarah. Tana zaman jiran sa,
kamar yadda ta san yana tafe. Kallo daya yayi
mata, ya gane hankalin ta a tashe yake, ya
karkade kai ya ce,
"Wai ke ba za ki daina wannan kuncin ba?
"To ko in fasa ne?"
Ta ce,"Kasan ban isa in hana ba."
Da sauri ya tari numfashin ta."
Kina ganin ba ki isa ki hana tafiyar nan ba?
Lallai za ki sha mamaki, idan aka wayi gari gobe
ki ganni a garin nan.Me zan samo a Ghana,
wanda ya wuce farin cikin ki?
Look Zarah!
Ina ganin ke har yanzu ki na daukata a
matsayin yayanki ne, ba ki san cewa akwai
banbnci ba.
Wallahi, kin ji na yi miki rantsuwa ko? Muddin
ba ki saki jikin ki akan tafiyar nan ba, zan fasa
ta, kuma babu wanda zai sani dole. To kila ko
su Abba su cika min ido.
Ta numfasa ta ce,
"Wai!
Ai kuwa na gode Allah, tunda akwai su Abba,
don na san zai wuya inji sanyi a raina, bayan na
san yaya na zai bar ni tsawon wata 1, "Alhali
ban saba ba."
"Dan murmushi yayi, kafin ya ce,"To ai ba zan
bar ki haka kawai ba, kin ga wannan?
Sabuwar wayar ki ce dalilin siyan kawai don
murinka sanin halin da muke ciki ne,
kodayaushe. Amshi nan."Ta saki baki tana kallon
kwalin rantsatstsiyar wayar da aka ce tata ce a
lkcn 1, kuma tana tambayar kanta yaushe
yayana ya siyo min NOKIA ta hannu na?"
"Kin amsa na ce, ki ka baje min ido, ki na kallo
na." Tasa hannu ta k'arba,"Amma dai yayana ka
na son kashe kudi, ita wannan Sabis d'in bai
zuwa Ghana ne?"
Dariya ta sake ba shi, ya ce,"Ina jin hakan a jiki
na, zuciya ta na gaya min tana gargadina da
cewa kai Naseer kar ka bar Nijeriya, ba tare da
ka sakewa k'anwar ka sabuwar waya ba, don ka
san ta hannunta ta shekara."
Zai iya kasancewa ta fara bada matsala. To kin ji
dalili,
da a sami matsala,
gara ayi wa tufka hanci.
Ko me ki ka ce?"
Ta d'an rausaya kai cike da mamakin yayanta,
ta ce,
"Godiya kwando-kwando yayana.
Allah ya k'ara bud'i."
Bai amsa ba.
Wayar sa ta hau ruri, ya jawo ta cikin alhu ya
duba lambar. Alhj Basheer ne, kamar yadda
yake a rubuce cikin wayar (Alhaji). Ya dube ta ya
ce"Mintu 2, "Sannan ya danna Ok."
Suna magana da Alhj.
Amma ita Zarah kallon sa take yi, kasancewar
hankalin sa ba ya gunta. Sai ta sami damar kare
masa kallon da ta jima da mancewa da ranar da
ta yi masa irin wannan kallon.
Nan take zuciyar ta, ka karan ta mata ba
k'aramar sa'a ta yi ba, da samun Naseer.
Kwarai ta tantance Naseer watanne, tamkar
yadda take Zarah.
Anya kuwa 'yan mata za su kyale mata Naseer
d'in ta ita kad'ai, yadda ya shiga yana fita gari
da kashashen duniya da irin wannan baiwa da
Allah yayi masa???"Nan da nan kishi ya rufe ta,
idanuwanta suka fara kad'awa, sannan kafe
suke tana kallon sa, ba tare da ta san tana yi
ba.
Kusan minti 2 da kammala wayarsa. Shi ma yayi
zurun yana maida martani.
Ganin idanuwan ta sun fara ja, shi yasa ya
murza yatsunsa biyu, suka yi k'ara bisa fuskar
ta. Cikin kunya ta sunkuyar da kai. Sai kuwa
tambaye yake,
"Menene?"
Ta ce, "Ba komai."
Kin san Allah, ban yarda ba, kuma ba zan bar
wajen nan ba, sai kin gaya min ko menene ki ke
tunani." Ta riga tasan halin yayan na ta, don
haka ta d'an dube shi, ta ce,
"Mata na zuwa kallon polo a Ghana?"
Tambayarta ta d'aure masa kai, kuma take ya
gane me take nufi. Amma sai ya nemi sanin
dalilin tambayar ta,
"Me ya sa ki ka ce haka?"
Sannan ba ki ta6a tambaya ta hakan ba, sai
yau?
Shiru tayi, ta rasa bayanin da za ta yi, don ita
ma ba'a son ranta tayi masa tambayar ba.
Jin tayi shiru tsawon 'yan dakikai, shi ya sa ya
ce,
"Zarah, dube ni nan."
A karkace ta dube shi, jim ta sauko ido.
"Zarah, son ki ba karya bane a ciki rai na.
Kar ki mance, tun bn san me zuciya ta ke nufi a
game da ke ba, har na gane so da kaunar ki na
ke yi.
Ma"anar tun yarinta, har zuwa sanin ciwon kai
na, ban jin akwai abinda zai cire min soyayyar ki
Zarah. Don kin jima cikin raina shekaru masu
yawa.Saboda haka ki kwantar da hankalinki, ni
yayanki nai miki alkawarin har abada ke kadai
ce, ba kari balle maganar canji. Kin ga zancen
mata na zuwa kallon Polo ko ba sa zuwa, duk
ba matsala da ta shafe mu bace.
Kin amince?"
Kad'a kai tayi, ta d'an nisa kafin ta ce,"Na gode
yayana, amma maganar k'ari, ka na nufin babu
zancen kishiya?" Da sauri ya amsa,
"Nufe na kenan Zarah.
Kin isheni rayuwar dauniya, domin komai na ki
yayi min yadda ra'ayina ke buk'ata."
Wannan karon ta kalle shi ido ciki ido, sannan ta
ce,
"Ban ji dad'in wannan maganar ba yayana, don
ka shigo hurumin da ba na ka ba.
Wannan hukunci ne na Ubangiji, wanda bai
kamata ko ma ince bai halasta ko wane D'an-
adam yayi shishshigi a cikin sa ba.
Ka ga dai........."ya katse fuska daure,
"Me ki ke nufi?
Na yi miki k'arya kenan?"
Ta ce,"Ban ce ka min karya ba,
amma magana ta gaskiya, duk macen da aka yi
mata alkawarin ba za'a yi ma ta kishiya ba, ta
yarda ta amince.
A hakikanin gaskiya ta yaudare zuciyar ta.
Don shi aure al'amari ne na Allah, tamkar
haihuwa da mutuwa.
Ubangije ne kadai ya san yadda ya shirowa
bawan sa rayuwa.
Shi yasa na ke ganin bai halasta masoya su
rinka yi wa junansu ko wane irin alkawari a
hurumin da ba na su ba.
Ina fatan yayana ya fahimce ni....?
Tun da take mgn, yake kallon ta, sai dai laffuzan
ta kawai ke sosa masa rai.
Bai kamata ta ki amincewa da shi ba,
don shi hakikanin gaskiyar sa ya fad'i.
Kenan duk son da yake nuna mata karya ne.
Nan da nan ya hassala.
Mikewa yayi ya sungumi jakar sa da ke gefe ya
ce,
"Allah ya sa mugana."Ita ma ta mike,"Yayana
fushi ka yi?" Tuni ya kai kan sa tsakar gida.
Inna na zaune kofar dakin Malam Umar can ya
nufa. "Inna na fito."
To dan Inna.
Allah ya kiyaye, ya tsare mana kai duk inda ka
ke." Sai ga M.Umar ya fito wanka, yayin da
Naseer ke amsawa da "Amin Inna."
"Har ka fito?"
Inji M.Umar.
Ya amsa,
"Eh,
"Baba."
"Madalla-madallah,
to Allah ya ba da sa'a.
Sai a kiyaye da ibada, ita ce gaba da komai, ka
ji?"
Ya ce,"To Baba na gode.
Na bar ku lafiya."
Ya wuce suna ta sa masa albarka, kafin Inna ta
ce,
"Ke ba za ki k'ar6ar masa jakar bane, ki raka
shi?"
Ta wuce da sauri ta bi shi, tana fad'in,"Kawo
jakar yayana."
Kamar ma bai ji ta ba, ya shige zaure abinsa.
Da gudu ta karaso zauren, haba yayana, bai
kamata ka yi saurin fushi haka ba." Ya juyo a
fusace, har ta ji tsoro a zaton ta duka zai ka
mata, ganin yadda ya nuna ta yana fad'in
"Ki koma!
Allah kar ki biyo ni, na gaya miki!
Kin ji ko?"
Ya juya ya fice daga zauran.
Tayi tsaye cikin zauren shiru, idanuwan ta suka
kawo kwalla.
Menene abin fushi a bayanin da ta yi?
Don dai ba'a son gaskiya?"
Ai kuwa wannan maganar haka ta ke yayana, ko
ka ki, ko ka so ba zan yaudari kai na ba.
Alhalin na sani kai mijin mace 4 ne."
Ta fad'a a ranta.
Wanda ya k'ara birkito mata da wani salon kishi,
har ya tilasta mata tsiyayar hawaye.Kusan minti
2 tayi a tsaye, sannan ta goge fuskarta da kyau
ta dawo cikin gida.
Daki kawai ta shige, ranta in yayi dubu, a 6ace
yake.
Shi ya sa ma ko sake kallon sabuwar wayar daya
kawo mata ma bata yi ba, illa iyaka, ta bar nan
tsakar daki, har Inna ta shigo ta gani.
*********************
Kwana 2 kenan da tafiyar Naseer Ghana, amma
babu motsin sa. Ko alama Zarah bata cikin
sukuni, kuma yayan na ta ya bata mamaki.
Wannan irin fushi haka, daga gaskiya?
Zaune kawai take cikin ajin su, duk sauran
dalibai na ta harkokin su a dalilin tashi (Break)
din da aka yi.
Amma ban da ita.
Tunani ya addabe ta, ko alama ta kasa tantance
me shirun Naseer yake nufi?
Shin yana son ya nuna mata cewa dole sai ta
yarda da ra'ayin sa ne?
Ko kuwa so yake ya tilasta ma ta sakin na ta
hangen?
Ta nisa tana mai tsananin kewar yayanta,
saboda ta tabbatar da shi ma yana cikin
yanayin da take a halin yanzu, kuma ta yarda ta
amince ko bayan sun yi aure, ya ce zai k'ara
wani, ba wai ya na nufin ya daina son ta bane.
Son ko wacce mace, na tasiri ne a zuciyar
mijinta dai-dai da yadda ta zauna da shi.
Duk da dai akan sami akasi ta ko wane 6angare,
a sami rashin jituwa tsakanin ma'auranta, idan
ba'a kai zuciya nesa ba, sai ka ji ana cewa a
rabu. Amma magana ta gaskiya, ita ce so yana
tafiya dai-dai da rikon amanar zaman tare.
Yarda da juna, kyautayawa ta kowace fuska,
hakuri da juriya.
Duk ma'auratan da suka mallaki wannan,
shakka babu za su ci ribar zamantakewar auren
su. Musamman mu mata da muke zama a
karkashin mazajen.
Sai ki ga ko mata nawa ya ajiye, ba zai ta6a
daina ganin kimar ki ba, a idaunsa.
Sai dai miji butulu maras tsoron Allah.
Zarah ta yarda ta amince da wannan, saboda
haka take ganin ba za ta iya sakar wa Naseer
jayayyar da suke yi ba.
Kan ta a kife yake bisa tebur yayin da take
rattafo wannan dogon tunanin.
Sallama kawai ta ji bisa kanta, ta dago da suri
ta dubi masu sallmar.Wasu kyawawan 'yan
mata su 3 ta gani a tsaye, suna mata murmushi.
Ta zauna sosai, ta ce,"Sannun ku."
Dukkansu suka amsa, kafin guda ta ce,"Don
Allah tambaya muke?
Ta ce Allah yasa na sani.."
Ta ce,
"Ke ce Zarah?"
"Eh
ni ce."
Mai magana ta ci gaba,"To ni sunana Lubabatu,
sai kawaye na.
Wannan Hauwa'u, waccen Maryan, dukkan mu
muna S.S.3.
Muke,......



Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100





Ajininsa yake 1-06
Posted by ANaM Dorayi on 02:00 PM, 07-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
.may be ko ki na ganin mu anan."
Ta karkada kai.Bisa teburin Lubabatu ta haye,
kafin ta ce,"Dama abinda ya kawo mu, kin gane?
Kawai ance yarinyar da Naseer Jah-Jah zai aura
tana cikin school din nan.Shi yasa muka ce ya
zama dole mu ganki, sbd mu Fans d'in sa ne.
Ina fatan kin gane.?
Zarah ta dube su dai-dai ta ce,"Na gane kuma na
gode."Maryam ta ce,"Kuma wallahi kun dace, dan
ke ma kin mana."
Hauwa'u ta amshe,"Gaskiya ne, amma duk da
haka kin yi da ce, so handle him with care, kin
san yaron yana kan lkcnsa."kan Zarah ya d'aure,
ta rasa ta cewa ko dama ita ba mai yawan
magana bace ko cikin ajin su, ba da kowa take
magana ba.
Shi yasa 'yan ajin suke ganin kamar tana da
girman kai.
Saboda kyan da take da shi.
Alhali ba haka bane, haka Allah ya halicce ta.
Jin tayi shiru, yasa Lubabatu ta diro daga tebur
ta ce,"To mun gaishe ki, mu za mu ari na kare.
Muna S.S.3, in case ko za'a gaisa."Maryam ta
amshe,"Ai ko bata zo ba, mu ya zama dole mu
rinka zuwa muna duba ta, a madadin sa, kin san
an ce ya fasa
"Ghana.
" Haka."
Inji Lubabatu,
"To sai kin sake ganin mu."
Ta ce,
"Shi kenan,
na gode,"
Suka wuce ta bi bayan su da kallo har suka bar
ajin.
Tagumi ta zabga, tunanin ta ya dawo sabo, don
'yan matan sun firgita ta kwarai.
Ashe ma anan kusa da ita tana da abokan
hamayya bata sani ba?Shine Naseer yake son ya
cusa mata wani ra'ayin da ba shi yuwuwu ?
Bayan bata ma san meke faruwa a wasu wurare
ba.
Tsoro ya kama zuciyar ta, ba na wasa ba.
Shi yasa ta aje a ranta, zai yi wuya Naseer ya
kasance na ita kad'ai har abada, kamar yadda shi
yake hasashe.
A susuce ta kasance zuwa tashi gida.
Ko a gidan ma tunanin ta bai sauyawa ba.
Saboda ya kamata ace ta san halin da yayanta
yake ciki a k'asar Ghana.Kwanan sa 5, babu
bayani.Abin ya gagari zuciyar ta, ga shi har su
Inna sun fara tambayarta labarin yayan na ta.
Cikin shagon d'inki ta iske Sageer da safiyar yau
lahadi.abin ya ba Sageer mmk kwarai, jin cewa
wai Naseer bai kira Zarah sa ba, tun tafiyar sa.
Alhalin shi kusan kullum sai sun gaisa da shi.
Don haka ya tsare ta da tambaya," Kin masa laifi
ne kafin ya tafi?"ta ce,
"Eh
toh,
k'ila a wajen sa zai iya zama laifin
, domin ko a ranar ransa 6ace ya tafi."
Nan take ta warware wa Sageer komai.
Dariya Sageer yayi, sannan ya karkada kai, cike
da mmkin abokinsa.
Sanin hali, yafi sanin kama.
Sageer ya dade da sanin halin abokin sa, wani
fandararran mu2m ne, mai tafiya akan ra'ayin
sa.
Wannan AJININ SA YAKE.
Saboda haka ya ce mata,
"To ai ke Zarah yakamata ki yarda da aboki na,
don kin san yana son ki sosai, kuma na san babu
yadda za'ayi yayi miki alkawarin da ba zai iya
cikawa ba."Ta ce,"Saboda Allah Sageeer da
mutuwa, da haihuwa, da aure duk na wanene?"
Ya ce,
"NaAllah."
Ta ce,
"Don me mu2m zai yi katsalandan a ciki?
Sai kuma an sami akasi, sannan a fara "Wallahi-
tallahi, ita ta lik'e min?"
Don haka ku ke yi ku maza, da zarar za ku k'ara
aure, sai ace wa uwar gida "Wallahi ta nace sai ni
ne.
To ba za'ayi haka da ni ba Gaskiya.Sageer ya
kama ha6a ya ce,"Zarah kenan, shi yasa
mutumin naki ke cewa sbd lafuzan ki yake k'ara
son ki.
Yanzu tunda abin ya zama haka, ga lambar da
yake kirana da ita, sai ki kira shi."
Tuni take kallon sa, baki sake, yana yin, shiru ta
ce,"Wai ka na nufin yana kiran ka?""Kwarai kuwa
kodayaushe sai yayi min tsiya, idan na ce masa
ban sami zuwa na duba masa ke ba.
Kin san sha'anin School, ba time.amma ki yi hkr,
ga lambar."
Ta ce,"Kyale kawai Sageer, ai dai har ga Allah
gaskiya na fad'i.
Da kan sa zai neme ni."
Ta juya ta fito daga shagon, Sageer ya biyo ta,
yana magiya.Sannan ta tsaya ta amshi lambar,
suka yi sallama ta koma gida da mmkn
Naseerrrrrrrr......!!!watau shi a dole da gaske
yake yi ko?"
"Eh
mana."
Inji wani 6angare na zuciyar ta.
Su Lubabatu suka fad'o
mata, take nan wata kwakwalwar ta mai kaifin
hankali, ta gaya mata,"Kin san Allah, kar ki
amince, gara ki tsaya tsaka-tsaka, idan tayi ruwa
rijiya, idan bata yi ba masai!"Da daddare ta
kasance ita kad'ai ta rage, bata yi barci ba,
wannan kad'ai ya tabbar mata da lallai son
yayanta.Wasi-wasi kawai take yi, ta kira shi?
Ko ta share kawai?
Ina ta kasa daurewa.
Laluba wayar ta tayi, ta loda lambobin a ciki ta
hau kira.
Amma har ta kaste, bai dauka ba.Nan fa abin ya
kara damunta.
Fushi masoyi, akwai dalili.
Ko dai kishi, ko kuma anyi masa kwakkwaran laifi.
Kafin safiya ta amsa laifin ta, na kin amincewa
da furucin Naseer.Kwarai yana son ta, kuma
watakila alkawarin da yayi mata, ya kasance
tabbatacce.Ko karin safe bata yi ba, ta nufi
shagon masu kayan waya.Sabon layin Etisalat ta
siyo, hada da katin 200, ta dawo gida ta dannan
sabon layin cikin wayar ta.
Sannan ta loda katin da ta siyo suka shige.Sai ga
ta da bonus na naira 100, take nan kudi suka
zama 300,. Bata jira komai ba ta nemo lambobin
da take son dauka tun jiya.
Bugu daya, ta juyo muryar da take ta kewa
kwanaki 6 kenan. Sai dai tayi matukar mamaki jin
ya ce,"Kanwata kenan."Jikinta yayi mugun sanyi,
a lkcn guda kunya ta mamaye idanuwanta, don
haka ta kasa cewa komai, ta bar shi da kiran,
"Hello!
Ba za ki magana ba?
Yi hakuri ki ce wani abu,
inji."
Hawaye suka cika fal!
A idonta kafin ta ce,"Ai ka nuna min iyakata,
me ka ke so ince?"
Tana jin hucin murmushin sa kafin ya ce,
"Ina zaton kin daina so na ne,
shi yasa na hkr.
Amma na amsa laifin,
tunda Sageer ya min fad'a.
Yanzu kashe in kira, kar kudin su k'are.
Kafin ma ta kashe.
Shi ya kashe.
Jimawa kadan wayar ta, ta dauki ruri, ba 6ata
lkc.
Ta danna
O.K,
"Ban ta6a tunanin za kai min haka ba yayana,
amma ba komai rayuwa ce."
Ya ce,"Zancen dai ki ke so aci gaba da yin sa, ni
kuwa tuni na watsar dashi, tunda ba ki yarda
ba.Ni Naseerr na sharo ta ko?
Ko kuma yaudarar samarin zamani ta zo gare ki
kenan."
Muryar sanyaye ta amsa,
"Ban fad'i haka ba, ranka ya dade."
Ai inda kasa nan ake gardamar kokowa.
Ga fili,
ga mai doki."
Ya ce,"
"Ni
Jah-Jah
zan gwada sukuwa ta,
wacce ta sha ban-ban da ta kowa.
Insha-Allah sai na ba ki kunya."Ta ce,"Ni kuma?
Sai dai 'yan matanka a sake masu kiran kan su,
wai fans din ka."
Kan sa tsaye bata amsa,
"Ke ki ka san wannan, amma ina gargadin ki da
ki kiyayi zargi da surutan 'yan karan kad'a miya.
Masu ara su yafa. Alhalin ni bn ji ba, balle in
gani.
Muddin kika cigaba da sawa ranki cewa fans
dina 'yan mata na ne, ina me tabbatar miki
zuciyar ki za ta buga akan aikin banza."
Aikin banza yayana?"
"Eh mana.......
"Wai kai a'a, ashe fa kishi ne ko?
Ki na son yayanki kena. To na gode, sai dai don
Allah ki rinka daurewa.
Naseer na ki ne.
Jah-Jah kuwa na fans ne a filin sukuwa.
Kin amince da ni?" Ta ce,"Uhm...."
Ya ce,"Ban amsa sosai inji, ba uhm...... Ba."
Ta yi dan murmushi ta ce,"Na amince."
To ya su Inna da Baba?"
"Suna gaishe ka. Ni ba zan tambayi Ghana ba,
don tai min ba dai-dai ba."
Dariya ta ba shi, shi yasa ya ci gaba da tsokanar
ta, suna hawa suna sauka."
*******************
Wata guda da kwana 2,"Naseer ya dawo gida
Najeriya, bayan ya kammala aikin da aka dauke
shi haya a k'asar Ghana.Kamar kar su bar shi
ya dawo, sbd iya aikin sa da kwarewar sa
wanda yasa ba k'aramin masoya yayi ba a can
maza da mata.Kaduna ya sauka daga Abuja,
inda Alhaji da kan sa tare da Yakubu suka
dauko shi a filin jirgi.
Bargar dawakin Alhj suka wuce.
Naseer ya warware gajiya, sannan aka maida
bayanai akan kudaden sa da suka shigo ta banki
Naira dubu dari shida, sun jima da shiga akaunt
din sa.Alhj Basheer bai bukatar ko sisi daga
hannun Naseer, maimakon haka ma take nan ya
mika masa kyautar makullin mota, don nuna
farin cikin sa ga manya-manyan lambobin yabon
da Naseer din ya dawo da su, wadanda za'a aje
tarihi a ofishin Alhj.Naseer kuka ne kawai bai yi
ba, sbd murna da farin ciki.
Bayan sallar azahar suka koma (Dabai Motors),
inda Alhj ya nuna wa Naseer motar sa. (Honda
civic) ce mai kofa 1, kowa sai taya Naseer murna
yake yi.Shi kuma Naseer Yakubu ne kawai cikin
ran sa,
don komai Allah yayi Yakubu ne sila.
Tankinsa cike da mai, yana gaba Yakubun na bin
sa a baya akan hanyar su ta dawo wa
Zariya.Allah ya kawo su lafiya, kowa ya nufi
unguwar su.
Arziki kashi, abin har daure wasu Umma kai
yayi, wai yau Naseer din su ke jan motar kan
sa.
Ba abin mamaki a al'amarin Ubangiji,
Don shi yake fitar da mai arziki daga talaka.
Idan kuma ya ga dama ya fitar da talaka a jikin
mai kudi.
Shine kuma mai bada baiwa da hikima, mai
daukaka mu2m duniya ta sanshi har yayi sunan
da wani mai mulkin bai yi ba.Shine mai rufawa
bawa asiri ta yadda ba wanda ya isa ya tona
masa, har jama'a su rinka ganin shi wani abu
ne.Ubangiji gare ka muke neman rufin asiri.
Ya Allah ka amsa!...Amin ya Allah (ANaM)
Allah ya kam ya rufa wa Naseer asiri, yayi masa
baiwa, ya kuma daukaka shi ta yadda jama'a
suke masa kallon mai kudi a halin yanzu.
Shi yasa abin ya k'ara rikita Zarah, lkcn da ta
fito ta ga yayanta a mota, kwarjininsa ya zarce
misali.komai kyau yake wa Naseer, shi yasa ta
kwana addu'ar Allah ya sa zancen Naseer ya
tabbata gaskiya.
Don bata jin za ta yarda da duk wani kalubale
Naseer na ta ne, ita kadai.
Washe gari banki ya fara shiga, bai gushe ba.
Sai da ya turawa Yakubu Naira dubu hamsin
cikin
(Account)
din sa, sannan ya fitar da wasu Naira dubu
hamsin din.
Ya nufi shagon siyar da atamfofi, ya zo6o tsala-
tsala guda 6 'yan dubu bibbiyu.
Ya za6o Engilsh guda 2 ya had'o da shaddoji
kala 6, masu kyau.
Sannan ya koma 6angaren kayan sanyawa na
maza.
T.Shirt da wanduna Jeans da Shirt masu dogon
hannu, nan ma ya kwasa iya yadda yake so.
Yana barin nan gidam su Yakubu, ya wuce
sashin mahaifiyar sa, nan ya shiga da atamfofi
kala 2 cikin leda.
Bayan sun gaisa, tayi masa lale da dawowa daga
Ghana.
Ledar kaya ya mika mata ya ce ga tsarabar ta
nan.Kai tayi farin ciki ta kuma sa albarka kwarai
da gaske.Yana kokarin tashi, sai ga sallamar
Yakubu, ya shigo.
"Naseer!"
Yayi kiran sa ya ce,"
Na'am yayana. Ina kwana?"
Ya amsa, lafiya lau.
Ai yanzu na fita zan fito da mota a wanke, sai
naga taka motar a waje, kuma dama wajen ka
za ni.
Sako na gani an aiko min a waya, wai an
min tiransifar dubu
hamsin daga,
(Account)
dinka."
"Dubu hamsin?"
Hajiya ta sake maimaitawa.
Ya ce,
"Wallahi hajiya."
Naseer ya ce,"Haba yayanmu, kamar wasu
kudin kirki?"
Ka cancani haka ne shi yasa, kuma ni ba ni da
abinda zan saka maka da shi,
don komai na samu, kai ne sila."
Ya zauna hannu kujerar da yake kafin ya ce,
"Naseer kenan, to Allah ya bar kauna.
Hajiya sai a tayani godiya.
Ta ce,"Dole, ka ga ni ma ga tawa tsarabar.
Allah yasa a kare da iyaye lafiya.
Ya ce,
"Amin
, Hajiya."
Ina takwara na ne? Halan bai tashi barci ba?"
Yakubu ya ce,"Kamar kuwa ka sani, yana can
yana barci."mik'ewa yayi, suka yi sallama da
hajiya suka fito tare da Yakubu,
shi ya wuce sashinsu, don yin wanka.
Naseer kuwa waje ya fito,
ya bude mota ya dauko wasu kayan a wata
babbar leda, ya nufi dakin da ke kofar gidan,
yana kwankwasa.
Zuwa can aka bude cikin fara'a Naseer ke
fadin"Ka na huta wallahi."
Ya dan duba shi,
ba tare da ya ce komai ba, ya juya ciki.
Naseer ya biyo shi, "Watau ba ka ma tashi barci
ba?
Ya murtsuke fuska da hannayensa, sannan yayi
mika, kafin ya ce,"
Na gaji ne."
Ba aikin fari, balle na baki ka ke fadin ka gaji.
Jiya ma ina ta sa idon ganin ka, sai na ji shiru,
wayar ka kuma na kashe."
Ba wata walwala a fuskar sa,
"Ban da caji ne, jiyan nima na so zuwa, lkc ne
bn samu ba."
Ya ce,"
O.k,
to ga tsarabar ka.
Ya mika masa ya kar6a, sai kawai ya wurga bisa
katifa, yana fadin ,
,"Na gode."
Abin ya daure masa kai, har ya kasa cewa wani
abu.
Haka suka danyi jim shuru kafin Naseer ya
mike, "bari in karasa gida." "to sai anjima". yace
yana kwanciya a katifa.” bakaje kaga mota ta
ba, ko bakada labari ne?" ya dago fuska daure
yace "Oh, naji, mancewa nayi." ya mike suka
fito. Ya kare wa motar kallo, zuciyarsa ta kara
shiga

Please Login or Register in order to submit comment