Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels


AISHAH-SIDDIQAH



1






SUMAYYAH ABDULKADIR
[email protected]
[email protected]
TUNASARWA/JAN HANKALI
Ba’a rubuta littafin AISHAH-SIDDIQAH don cin zarafin kowacce kabila ba, ko don nuna wata kabila ta fi wata daraja a tsakanin kabilun Najeriya ba.
Kyakkyawar manufar dake kasan labarin itace dabbaqa kalmar WA-ZO-BIA da fadakarwa cikin nishadi akan kabilancin da ake nunawa ita wannan kebantacciyar kabila dana dauka, da kuma wanda suma suke nunawa ga kabilar hausawa.
Labarin AISHA-SIDDIQAH labari ne da aka gina shi kacokam akan manyan kabilun Najeriya guda uku, don son samar da fahimtar juna da rage tasirin kabilancin da yayi katutu a zukatanmu ga junanmu.
Asali mun san cewa Najeriya kasa ce bata kabila guda ba, bata yare ko harshe guda ba. Bincike ya nuna kusan kabilu 371 da yarurruka sama da 500 suka hadu suka mallaketa, wadanda suka fi yawa sune Hausa, sannan Yoruba, Igbo da kuma Fufulde.
In haka ne kenan babu wadda ya kamata ace tana faharin tafi wata, ko tata itace kan gaba ko mafi daraja, in dai Allah daya muke bautawa sai mu rike ayar “Inna akramakum Indallahi Atqaakum”.
Idan kuma ba addini daya ya hadamu ba, sai mu dauki ayar “Lakum Deenukum Wa liya Deen” nan ma sai kaga an zauna lafiya da juna.
Fatan marubuciyar shine Hausawa mu daina kabilanci, in bazamu iya dainawa ba mu rage shi, sauran kabilun suma su rage nasu kabilancin ga hausawa, ta hakane kadai za’a samu hadin kai da fahimtar juna a tsakanin WA-ZO-BIA wadda zata iya zama jagora wajen cigaba da haifar da auratayya da kyakkyawar mu’amala tsakanin kabilun musulmai a duk inda suke a kasar nan. Don haka kada kayi tsalle ga tafiya karshen labarin ko ka dauki wani abu ya zama cin zarafi ga yarenka ko kabilarka ba tareda ka ga karshen littafin ba. Taku har abada.
–Takori Sumayyah AbdulQadir.
SADAUKARWA
Aisha-Siddiqah ta sadaukar da labarinta ga daukacin mambobin whatsapp group na TAKORI’S LOUNGE bakidayanku. Allah ya bar zumunci da kauna har ‘ya’ya da jikoki.
KIYAYEWA
Hakkin mallaka abin kiyayewa ne ga marubiciyar littafin, ban yarda a karanta shi a kowacce kafa ta sadarwa ba tare da rubutaccen iznina ba. Yin hakan ya sabawa doka ta shari’ah kuma abin tuhuma ne daga lauyana Barr. Sadiq Rufa’I Wali.
GODIYA DA JINJINA
Godiya da jinjina ga aminan kwarai wadanda suka taimaka matuka gaya wajen shawarwari, tacewa da gyarawa (editing) Dr. Amina Jafaru Musa, Barr. Azima Musa Abdullahi, Aisha Muhammad, Maryam Yusuf Abubakar, Haj. Zainab M. Ahmed da Bilkisu Askira.
In tsaya ina ce muku na gode kuma kunsan yayi kadan, saidai kawai in jinjina muku bisa namijin kokarinku akan ingantuwar littafin AISHATU SIDDIQAH.

KAFIN MU FARA INA TALLATA MUKU AISHA LAME (ORIGINAL ORIFLAME AMBASSADOR)
Kina neman jakadiyar oriflame ta kwarai? Kinason mayuka da zasu dace da launin fatarki a wannan lokacin na zafi kona sanyi? Kinason kamshi na alfarma? Kinason supplements ingantattu na wellness and meal replacement ga masu bukatar weight loss and weight control? Kayan kwalliya na kerewa sa’a? Kina bukatar zama Dawisu sarkin ado? Kawai tuntubi AISHA LAME a lambar waya 07036662633 zaki samu duka wadannan cikin farashi mai inganci da kyakkyawar mu’amala. Aisha Lame karshe ce wajen baiwa fata hakkinta ku tuntubi Aisha ku zo ku bani labari.
-Takorinku


SHIMFIDAR LABARIN
WAIWAYE ADON TAFIYA (1)
Dr. Murjanatu, wadda kowa a gidansu da danginsu bakidaya da “Taiwo” yafi kiranta, kannenta kuma suce mata “Aunty Taiwo”, abokan karatu su ce Murjanatu Akanni. Murjanatu baka ce ba sidik ba, bakin da akewa lakabi da (chocolate beauty) sabida sanyin kyawunsa da haskensa, doguwar mace mai ‘yar kyakkyawar kiba ta jikin hutu, irin kibar da batayi munin da za’a ce mata lukuta ba.
Saboda duk da kasancewar ingarman jiki keda Dr. Murjanatu to suffar jikinta mai tsari ce duk da kibarta, gata da doguwar fuska irinta fulani da dara-daran idanun yarbawa masu haske, Taiwo-Murjanatu, nada dogon hanci sambal irin na Kakarta ta wajen Uwa wadda ta kasance bafullatanar jihar Gombe da suke kira “NANI OUMMANA”.
Sannan tsayin ta masha Allah shima bai wuce misali ba. Komai na Dr. Taiwo kamar ita ta aunawa kanta ta kuma zaba. Domin dai a fasalce baza’a kira Aunty Taiwo doguwa irin sambal ba, saidai ace kamar kwalbar nan ta coca-cola ga kauri ga tsayi da dirin jiki mai zati, tana a ma’aunin daidai na tsayin da akeso a tareda mace.
Shekarun Murjanatu na haihuwa a wancan lokacin da muka waiwaya talatin cif. Murjanatu-Taiwo Akanni ga tsayi ga zati irin na mace mai aji da kasaitar nasaba, girman jikinta mai ban sha’awa ne don bai sa mata muni ba. A takaice komai na jikin Taiwo irin na matasan matan kabilar Yoruba ne, wato daga kabilar Yarbawa ta fito.
Tafiyar Taiwo mai daukar hankalin mai kallonta ce, domin tana tafiya ne cas-cas akan tsinin dugaduganta, cikin rangaji na jan aji da kasaita sanna ga iya ado mara misaltuwa, kullum haka take cikin tsantsar gayu da yawan ado, duk yadda ta motsa ko tayi magana ko murmushi sai kaga wannan ajin na musamman irin na jinin sarautar gidansu ya nuna kansa a tareda ita.
Kallo daya zaka yiwa Taiwo da dabi’unta da iya kasaitarta kasan ta hada jini da sarautar Yarbawa mai tushe, ko daga yanayin takun tafiyarta dinnan mai kayatar da idon mai kallonta kamar Dawisun da ya baza adon jikinsa yake tafiya.
Tafiyar Murjanatu cikin kasaita da iya sarrafa jikinta da yake mul-mul irin na kosassun ‘ya’yan kabilar Yoruba da suka ci suka tada kai.
A daidai wannan lokacin da Murjanatu ta shigo gidanta, yamma ce lis, hadari ya gangamo, sararin samaniya yayi duhu, sai cida da iska ke kadawa, gab ake da kecewa da ruwan sama mai karfi.
Wannan na faruwa ne a cikin daya daga manyan biranen Najeriya mafi yawan al’umma da kabilu daban-daban, wato birnin Legas ko Ikko da aka fi sani da jihar Lagos.
Gidan nata matsakaicin gidane kyakkyawan (Duplex Mansion) wanda anan Dr. Taiwo da iyalinta ke zaune tun dawowarsu Jihar Lagos da zama daga Ilorin, gidan yana nan a shiyyar babbar unguwa mai tsari ta masu hannu da shuni ‘Eko Atlantic’, gidan Murjanatu nada farin fenti mai dan duhu da ratsin ruwan madara-madara (off-white/milk), kuma gida ne da in ka gani ko daga nesa kasan masu shi sun jima da kama kasa.
Zamu iya kimanta lokacin da misalin karfe shidda na yamma, daidai lokacin da Taiwo-Murjanatu, ta shigo da kan motarta kirar ‘Hyundai Creta’ harabar gidannata, bayan tasowarta daga asibitin da take (housemanship) acan, wato asibitin koyarwa na jihar Lagos.
(Murjanatu-Taiwo Akanni, dalibar likitanci ce a Lagos State Teaching Hospital).
A wannan lokacin duk tunaninta da hankalinta na kan karamar diyarta (Kiki) wadda ta baro a gida hannun sabuwar mai rainonta Bunmi, tun bayan data fara housemanship ta samo Bunmi ‘yar kabilar Ibira suke zaune tare.
Kiki ‘yar kimanin shekaru uku wadda saboda son da dan uwanta yake mata, yasa a yawancin lokuta bata dauka cewa ita ta haifeta, tafi dangantata da ‘yarsa shi kadai, ko cewa zata yi Kiki sai ta hada da inkiyarshi, tace “Kikinshi” ko “Kikinsa”.
A lokuta da yawa idan ana hirarsa, kasancewarsa ‘Polo Celebrity’ ne, ‘yar uwarsa Murjanatu data fi kowa kusanci dashi ta kan gayawa kawayenta daliban LUTH, musamman wadanda ke bibiyar kallon wasan shi a kafar talbijin ta “Global POLO TV, suke kuma mayatar son jin wani abu da ya shafeshi personally, Taiwo kan basu labarin irin son yaransa ne, ta kan ce da dai ace maza na haihuwa da kansu, ba mata ke haifa musu ba, da tasan shi zai yi nakudar Kiki ya haifeta, wato da bazai bar mata ta haifota ba, saidai shi da kansa, saboda sonda yake mata a matsayin karamar diyar ‘yar uwarsa, wadda duk duniya bashi da makusanci, amini, amar ita ‘yar uwarsa Taiwo. Ya sha gaya mata cewa ya raina adadin kulawar da take baiwa Kiki, tunda har ta zabi karatun likitanci akan zaman gida ta kula da kyautar ‘ya’ya biyun da Allah ya bata.
Tana basu labarin irin yadda yake bata lokacinsa in yana gaban Kiki, don mayar da shekarunsa yake daidai da nata, su taru suyi ta zuba shirme na (Daddy and Daughters’ love).
Wani lokacin Taiwo har addu’a take yi tace Allah ya bashi nashi ‘ya’yan shima. Saboda son yaran shi har yaso yayi yawa.
Tana matukar marmarin ganin yaranshi, ko ba don komai ba don ta taya shi son su, irin dai yadda yake tayata son Kikin data haifa.
Murjanatu kullum addu’arta kada Allah ya baiwa dan uwanta matar da zata raba soyayyar shinnan da ‘yarsa Kiki. Don ko ubanta Toafeeq albarka.
“Kiki rigimammiya amanar Uncle dinta “Prince!”.
Wakar da Aunty Taiwo ke yawan yi mata kenan, wadda ainahin sunan Kikin na yanka (Ruqayyat). To amma tana ji tana gani ala dole Prince ya mayar mata da sunan diya “Kiki”, wai a cewarsa saboda kibar ta, da kazarniyarta, da rikicinta irin dai na yara lukutaye ‘yan shekaru uku, yace Kiki ne ya dace da ita ba sunan Nanin Gombe ba. don kam ita Kakarsu Nani Oummana bata da rikici kona tsufa, balle irin na Kiki.
Murjanatu na tafe ne tana tuki take wannan tunanin na dan uwan haihuwar nata, mafi soyuwa a ranta a duk cikin ‘yan uwanta da suke iyaye guda, kuma namiji daya tal a cikinsu. Gabadaya gidansu tafi shiri dashi watau shi Hussaininta, wanda suka zo duniya a tare, ta tuna ya hanata barin Kiki a gun masu raino, ba sau daya ba ba sau biyu ba, to amma yaya zata yi tunda ta saka ma ranta son zama likitar mata kota halin kaka?
Shi, a matsayinsa na (lifetime) dan “Polo” ba zai taba gane hidimar aikin asibiti bata haduwa data kananan yara ba, dole sai da taimakon mai raino da raba hankali gida biyu, da kuma taimakon makarantar nursery ne kadai kowannensu zai samu isashshen lokacinta. Kuma dai tayi sa’ar samun Bunmi wato mai rainon Kiki yarinyar kirki ce, bata da matsalar komai sannan gata musulma don kuwa daga Ilorin ta taho da ita, tana kula mata da Kiki sosai.
A yadda Prince yake son niece din nashi Kiki, wadda ainahi soyayyarsa da yarinyar ta samo asali ne daga sunan Kakarsu da taci wato Nanin Gombe Hajiya Ruqayya da suke kira (Nani Ummana), Taiwo ta tabbata da ace zata bashi ita ya rike a inda yake zaune, ta san tsaf zai karba babu musu, zai iya aje hidimomin Polo dinsa na wasu lokutan, ya zauna ya kula da Kiki da kansa sabanin ita, tunda gidansa babu mace har yau har gobe, amma kuma hakan bai hana shi kwadayin ta bashi rikon Ruqayyatu-Kiki ba.
Fatanta dai yanzu shine Allah ya taimakesu iyayensu wato “Nenne” da “Dade” su amince da maganar marainiya Haseenah, dan uwanta ya samu abokiyar rayuwa, yayi settling rayuwar iyali hakanan (at the age of 30) kamar kowanne lafiyayyen matashi.
Ita tasan ba wani uzuri da zata baima dan uwanta ya karba akan cewa kulawar da take yima Kiki tayi kadan, a wurinsa Kiki tafi karatun nata muhimmanci dari bisa dari don shi bai ga dalilin da Murjanatu zata ce sai tayi aikin likita ba.
Watakila ko don yana ‘life-time’ dan Polo ne yasa yake ganin kowanne Profession na duniya wahala ne, sannan takurawa kai ne, kuma babu riba a cikinsa banda Polo Sport, don ko tabbataccen aikinsa na man fetur an shaida, baya baiwa muhimmancin da ya baima wasan Polo dinsa.
A cewar Murjanatu ita kuma, karatun data zaba take yi na kishin kasa ne, bashi da alaqa da matsayin gidansu, reputation na gidansu ko na mijinta Toufeeq Adebayo. Sarauta bazata hanata yunkurin kokarin amfanar da al’umma ba ko neman abinci ta hanyar ilminta, don kuwa sun kere ma hakan. Taimakon kasarta takeso ta yi da nata dan effort din (with full patriotism) sabida karancin likitoci mata da ake dasu a kasarta, tunda kuwa gwamnati take da burin yiwa aiki da mata ‘yan uwanta ba private ba a ganinta aikinta mai hujja ne babba ba karama ba ko a cikin addini. Har ila yau, bazai hanata hidimar iyali ba.
Bayan kasancewarsu ‘ya’yan sarauta mai suna sarauta data amsa sunanta, sarauta irin ta gado bata taka-haye ba, kuma jikokin manyan sarakuna gaba da baya, maigidanta Toufeeq Adebayo, har ila yau, ma’aikacin majalisar hadin kan turai ne (European Union) kuma yanada matsayi mai girma a cikinta.
Don haka Toufeeq ba mazaunin gida Nigeria bane sosai. Karin dalilin da yasa Taiwo tayi amfani da damar wajen yin karatunta cikin nutsuwa a Ilorin, wanda ta tabbatar zai amfanar da al’ummar kasarta musamman mata ‘yan uwanta (Obstetrics & Gynaecology).
Babban burinta mata su amfana daga ilmin likitancin data wahala tayi, a Public University ta Ilorin.
Ta fara karatun ne da farko saboda rashin Taofeeq a kusa, madadin tayi ta zaman gida miji baya kusa, don a kalla Toufeeq sai yayi watanni uku ba tare da ya leko su ba ko meyasa? Nenne kance ita bazata iya zaman da Murjanatu ke yi ba na bin miji agindi-agindi akai-akai. Don itace tafi zuwa masa da yaran lokaci-lokaci inda yake, in ta samu hutu, wanda shi bai cika son haka ba. Toufeeq yafi son su zauna a gida inyaso duk sanda ya samu sarari shi ya zo, amma Aunty Murja bata yarda sai taje.
Kenan zamu iya cewa Dr. Murjanatu da aka fi sani da (Taiwo), tana karatun aikin likita ne ba don albashin da zata samu ba, sai don dalilai guda biyu; debe kewar mijinta tun na auren saurayi da budurwa hutsun bature Dr. Toufeeq Adam Adebayo, da kuma burinta na amfanar da al’ummar kasar ta, musamman mata.
Hassana (Taiwo da harshen Yoruba) wadda ainahin sunan ta na yanka (Murjanatu) da Hussaininta Prince Abdulrasheed (Kehinde da harshen Yoruba) tagwaye ne masu abin mamaki. Su din ‘yan biyu ne da aka haifa tare amma ta girmeshi da awanni biyu, suka kuma taso tare bisa doron tarbiyyar islama cikin shakuwa da kaunar juna mara misaltuwa, duk da kasancewarsu mace da namiji, sai suka maida kansu sune aminan junansu daga kuruciyarsu har girma basu da abokan shawarar da suka fi junansu.
Taiwo (Morjanatou), da dan uwanta Abdulrasheed (Prince) wasu irin twins ne kebabbu a cikin kafatanin zuri’arsu saboda sune manyan jikoki kowa na girmamasu, amma a halayya da dabi’a basu da alaqa da juna don Taiwo mai wasu baudaddun halaye ce, wanda iyayenta ne kadai da shi dan uwanta kadai suke iya gane inda ta dosa, sune kuma kadai suke iya tafiyar da ita da baudadden halinta, amma ko Toufeeq wani lokacin haurawa suke su fado kasa saboda bashi da hakurin jurewa halin Mourja.
Hadin kansu itada Prince shine kan gaba wajen nuna cewa su ‘yan biyu ne masu fahimtar juna, da tolerating each others’ attitude. Prince ne kadai in Taiwo tayi ba daidai ba zai zare ido ya gaya mata tayi ba daidai ba ba tare da yayi la’akari da girman awannin data bashi ba da cika idon ta ga al’umma, nan kusa babu irinsu a family dinsu ta fuskar closeness da sincerity ga juna.
Su haka su rufe su binne sirrin juna ba wanda ya ji ba wanda ya gani, don haka wajen hadin kai da kaunar junansu basu da na biyu. Zumuncinsu ga juna mai burgewa ne, ban sha’awa da ban kaye, in kai mai nazarin ilmin mu’amala da zamantakewa ne har kaso yin rubutu a kansu, domin kuwa zumuncin su ya zarta normal irin wanda ke tsakanin ‘yan biyu na ciki daya, wadanda akasari kusan koyaushe zaka samu suna against junansu, ko yiwa juna cin diddige wato suke yin rivalry da junansu. Su kam nasu zumuncin na musamman ne, a kullum AbdulRasheed da Murja cigaban juna da farin cikin juna suke hangowa junansu. Abin hannunsa nata ne da ‘ya’yanta.
A wasu lokutan har feelings na zukatan junansu suna iya ji a jikinsu, na farin ciki ko akasinsa, idan ya samu dayansu.
A takaice tagwaitakarsu extraordinary tagwaitaka ce ta bada labari da bugawa a jarida. A wancan lokacin da na waiwaya na hasko muku su (flashback), Hassana Murjanatou da Hussaininta Prince, sun mallaki shekarun matasa ne talatin da haihuwa tana housemanship dinta a Lagos State Teaching Hospital.
Ta iso gida kenan tana kokarin sanya motarta a ma’adanarta, wayar ta dake aje gefe ta hau ruri kiran Hasinahn Prince ya shigo mata. Da far’a sosai Aunty Murjanatu ta daga kiran Hasinah, duk kuwa da gajiyar dake tare da ita, ta kwana biyu bata ji ta ba dama, don kusan kullum sai sunyi waya tun barinta gidanta da fara karatun Digirinta a kusa dashi a birnin Tokyo.
Taiwo ta daga wayar Hasinah (fiancée din Prince) tana tsokanarta da waka cikin yarbanci yadda ta saba koyaushe sukayi waya.
“Hasinah ta Prince, Hasinah kanwar Taiwo, Hasinan Taiwo & Kehinde, ta Abdulrasheed PRINCE bada kanki a sare kije gida kawai kice ya fadi!”.
A baya a duk lokacin da take mata irin wannan wakar mai kama da kirari kan Hasinah kumbura yake yi tayi ta blushing ita kadai kamar Aunty Taiwo na kallon ta, domin hakika tana jin dadin wakar gtana alfahari kwarai da son da Aunty Murja ke mata, amma a yau sabanin kullum sai tayi shiru tana kakarin magana amma maganar taki fita daga makogaronta tiryan-tiryan. Murjanatu ta fakamota ta kashe sai ta zauna a ciki ba tareda ta fito ba, ta ce.
“Yaya akayi ne kanwata nake jin muryar ki a shaqe kamar mai fama da mura? Kin fadar min da gaba. Kwana biyunnan ban jiki ba dama, Dear Haseenah in ce ko lafiya?”
Shiru Hasinah tayi bata ce komai ba ta daina kakarin maganar ma sai ciza lebe. Aunty Taiwo ta sake cewa “In ji dai lafiya kuke keda shi? I mean Prince din? Kuma yaya kuke coping da wheather din sanyinnan na winter da karatun naku ke da shi?”
Amma ga mamakinta sai taji kamar Hasinah sheshshekar kuka take yi. Kukan ma irin na fitar rai da ta kasa dannewa, irin mai cin zuciyar mai yinsa, da dugunzuma zuciyar wanda ake yimawa.
Murjanatu was shocked! Stunned daga zaunen da take a cikin mota, duk da ta kashe motar a ma’adaninta kukan Haseenah yasa ta kasa fitowa kuma.
Da kyar taji muryar Haseenah na fita zuwa cikin kunnenta, cikin sauti mai nuna matsananciyar nadama.
“Ki taimakeni ki bashi hakuri Aunty Taiwo, kaddara ce!!!”
Murjanatu ta zaro ido, kafin tace komai Haseenah ta sake cewa “kema kin san ba halina bane, kullum kina gargadina akan hakan, kuma na dade ina kiyayewa, kun sani lafiya kuka dauko ni a ‘virgin’ daga Ambursa, wallahi kafin na zo school ban taba yi ba, sau daya ne, sai wannan na biyu, shima kuma wallahi da kudi Tokumbo yake jan ra’ayi na, na dade ina kaucewa fitinarsa, wannnan din ma akasi aka samu, tsautsayi ne.
Nayi masa babban laifi Aunty Taiwo, kaddara ce ta fada mini.
Zina ba hali bace afkawar kaddara ce da karfin sha’awar da ya gagari dan adam.
Prince ya daina daga wayata yau kwana biyu kenan…. ya min iyaka da zuwa gidansa…. Ya ce kada in kara nuna masa mummunar fuskata ko a lahira!
Laifina bai kai haka ba. I didn’t deserve such a severe punishment, zan jure kowanne hukunci banda na rabuwa da Prince. Na shiga uku Aunty Taiwo, yau kwana biyu ban saka Prince a idanuna ba…
I am dying without him! Truly I am dying! Aunty Taiwo ki taimakeni! Ki cece ni ki ceci marainiya, ke kadai nake da yanzu, a duniya banda kamar ki, ki ceci soyayyar gaskiya da Prince yake yi mun, nasan Tokumbo ba aurena zai yi ba ya cuce ni ne kawai!”. (She screamed!!!). Irin ihunnan na girgiza zuciyar uwardaki. Har cikin kwakwalwar Murjanatu ihun nata ya ratsa ya kusa kurumta kunnuwan Murjanatu.
Ta shiga afi da hurwa, tana tumami a kasa cikin hawaye da majina, kamar Murjanatu na kallonta, kalamai take na tuba da nuna nadama, amsar kaicon kai, da kuma daukar alkawarin bazata sake ba. Begging for “one more last chance”.
Amma taki fadin hakikanin laifin nata, cikin matsanancin kuka na tashin hankali kawai take rokon Taiwo kamar itace Prince AbdulRasheed din da kansa.
Ta kwana da sanin idan Aunty Murjanatu ta yafe mata, tamkar Abdulrasheed da kansa ya yafe mata ne.
Kasancewar kowa dake tare dasu ya san Prince (AbdulRasheed) bai iya tsallake rarrashin Taiwo dinsa. Kamar yadda bai iya tsallake abinda ta umarceshi inta bullo masa da lallashi da banbaki ta bayan gida wanda ita kadai ta san lagonsa.
Amma itama Hasinah duk da wannan tabbacin data ke dashi, ita da kanta wannan karon tana shakka.
Ta yaya take da tabbacin laifin nata mai yafuwa ne ga Taiwo dinma? Since they sometimes share the same feelings itada kaninta Prince? Akan-karan kanta ta san laifinta ba mai yafuwa bane saboda girmansa. Musamman ga babban mutum, mai kishin kansa, dan babban gida da yasan ciwon kansa kamar PRINCE ABDULRASHEED.
Wannan shine babban tashin hankalin Hasinah Bello, idan ta tuna lokaci yazo da

Please Login or Register in order to submit comment