Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

☆☆☆☆☆☆☆☆
🎾 NAWAFF 🎾
☆☆☆☆☆☆☆☆


NA BILKISA IBRAHIM💞




DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JINK'AI, ya ALLAH kabani ikon fad'ar abinda zai amfani al'ummarka, ka tsare harshena daga fad'ar abinda zai cutar da al'ummarka.


Assalamu alaikum,
gaisuwa da fatan alkairi, inamai farin cikin sake had'uwa daku asabon littafina mai suna NAWAFF, ALLAH yasa ya amfanar damu baki d'aya. Amin
🙏🏻.



Page👉🏻1&2

Yau antashi da tsananin zafi, saka makon ranar data kwalle🌞, mutane kowa yana neman mafaka, a karkashin rumfa ko bishiya.
Ga k'arar ababen hawa data cika birnin na kano, dukda katafaren gosulo d'in daya cinkushe titin, dayawa mutanen dake cikin moto cin sun gala baita, da tsananin zafin ranar.
Amma wannan bai hana 'yan tallah daf dalaba suna yayata tallar ababen sana'ar su, musamman masu tallar ruwa, saboda yanayin zafin mutane suna buk'atar ruwa mai sanyi.
Nakai dubana bisa wata farar mota mai k'yawun gsk, wadda daka mata kallo d'aya kasan mai ita yagama wada tuwa.
Wata k'yak'yk'yawar yarinya nagani kwance a bayan motar, farace saidai farinta bamai haskeba sosai, tanada kala irinna 'yan itopia, tanada dogon hanci da manyan idanuwa, kwance take abayan motar tana nazarin littafi.
Agaba kuma direbane, tad'ago kai tareda fad'in balarabe kaga abinda nake jiye mana ko?, shiyyasa nace kar mu biyo ta nan, gashi har ina neman makara, kuma inada lectures yanzu wlhy.
Balarabe ya ce, "kiyi hak'uri hajiya, wlhy banyi zaton zamu sami wannan cinkoson ba.
Ta d'anyi k'aramin tsaki tana fad'i ni wlhy saima karasa abinda yake haddasa irin wannan cinkoson a garin kano?, batareda ta saurari sharhin da balarabe yake mataba ta bud'e motar ta fice.
Tafito dai2 sanda wata jar mota 'yar k'arama ta tsaya saitin ta, ahankali aka zage gilashin motar zuwa k'asa, wani had'ad'd'en saurayi ya bayyana, saikuma wani danake tunanin abokinsane.
K'yak'yk'yawan saurayinnan ne matuk'in motar, kallo d'aya zaka masa ka gano yana cikin farin ciki, dan sai kad'a kai yake da alama wak'a yakeji, kuma wak'ar tana masa dad'i.
Ya d'akko kwalin hollanddia yana sha ahankali yana cigaba da kad'a kai, harda had'e yatsun hannunsa biyu yana bugawa.
Karku d'auka wannan k'yak'yk'yawar yarinyar shitake kallo, A'a ko kad'an hankalinta baya kansa.
Jitai wani abu yadaki k'irjinta, da sauri ta kalli jikinta.
Hummm kunsan miye kuwa??.
Ba wani abu bane illa kwalin hollanddia da gay d'innan yake sha, takuma bin jikinta da kallo, dan ganin yanda yogot d'in yay mata kaca2 da bak'ar jallabiyar dake jikinta, ta maida kallonta ga motar dan ganin wane wawane yay mata wannan aikin??.
Saitaga mutum yana kallonta yana tuntsirar dariya harda dukan sitiyari, d'ayan saurayin dake gefensa ya d'ago yana kallonsa, ya ce, "kai malam lafiyarka kuwa?, kanata dariya kai kad'ai kamar wani shafar aljanu.
Cikin dariya ya nuna masa yasmeen dake tsaye tamkar gunki tana kallon ikon ALLAH, tana mamakin wannan wane irin shashashan mutum ne, yayi mata abu amma yana nunata yana dariya.
Mas'ud ya ce, "amma kaidai d'an iskane NAWAFF, yazaka b'atama yarinya jiki, kakuma rink'a yimata dariya??.
Kasan kuwa wacece wannan kalli nomber motar data fito fa.
NAWAFF ya gallama Mas'ud harara yana fad'in aii bani nace tazo ta tsaya anan ba tana yima muta ne iyayi ko?, dazakace nawani kalli nomber mota, to saimi idan na kalla.

Duk abunda suke fad'i Yasmeen tana jinsu, dan haka sai zuciyarta tak'ara tunzura, cikin fasifa ta k'arasa gurin motarsu.
Ta ce, "kai wawa wanda baisan darajar mutaneba, shin kobaka ga b'arnar dakayi bane??.
Cikin fushi NAWAFF ya kalleta ya ce, "waye wawan??.
Itama cikin tsiwa ta ce, "masa kai mana!!!, ko wawan yayi maka kad'an saina had'a da mahaukaci, dan naga kanada k'aramar kwakwalwa.
Afusace yabud'e mota yafito, ya wanka mata mari, jikake wani tasss.
Dayawan hankalin mutane yadawo gurin musamman 'yan tallah.
Ta dafe kunci tana kallonsa, sai kuma ta d'aga hannu itama zata wanka masa mari.
Da sauri ya rik'e hannun ya murd'e, ta ce, "kai karamin d'an iska ka sakar mini hannu, hannu yad'aga zai k'ara marinta mas'ud yay saurin shiga tsakkiyarsu, ya ce, "haba NAWAFF yazaka mata laifi sannan ka daketa??.
Cikin masifa ya ce, "dalla malam nibakaga raahin kunyar datake minbane?, ko kai kurmane?.
Mutane sai kallonsu sukeyi.
Mas'ud ya ce, "haba NAWAFF kasan dai fuskarka sananniyace dammi zaka aikata haka?, yanzu sakaji 'yan jarida suna yayataka aduniya kadai sani sarai.
NAWAFF yaja tsaki, karsu fasa gayawa duniya abinda nayi kajiko, kodan kar afad'ama duniya saina zauna yarinya k'arama tayimin rashin kunya.
Ya juyo gareta 👉🏻ke kuma ki rubuta ki ajiye saina nuna miki ni👈🏻 nafi mahaukaci hauka.
Yasmeen taja tsaki ta ce, "wlhy nikuma saina nuna maka nike maganin dukkan wani mahaukaci komai haukansa.
Aifa yasake harzuk'owa zai mareta, mas'ud dake tsakkiyarsu ya kare, wai ku miye hakane? dan ALLAH, waishin bakwa ganin kallon da'ake mukune??, gashi kun tarema mutane hanya.
Sai asannan NAWAFF ya lura gabansu babu kowa, duk tarin gosulo d'innan ya b'ace, saidai mutanen dake bayansu, sunata danna musu hon.
Balarabe da tund'azu yake bama Yasmeen hak'uri, amma tak'i saurarensa, ya ce, "kiyi hak'uri Hajiya kizo mutafi kinga kin makara.
Harara ta watsa masa sannan taja tsaki, mas'ud ya ce, "plz kiyi hak'uri dan ALLAH kinga a titi muke.
Juyawa tayi ga motarsu dan ganin kawai kallon da'ake musu, amma tad'auki alk'awarin duk ranar data sake had'uwa da gay d'innan saita nuna masa shi k'aramin d'an iskane wlhy.......................✍🏻

Tusk'ashi masu karatu, komi zai faru?, shin waye NAWAFF??? Miyasa 'yan jarida zasu iya yayatashi???? Wacece Yasmeen?? Kuma 'yar wacece??, kubiyoni danjin amsoshi tambayoyinku....

Taku har kullum BILKISA IBRAHIM (Bily)
( Mrs Abdus'salam)
Ku kasance dani!!!!!!👈🏻

Zaizo gareku nanbada dad'ewaba......😘😘luv u oll

©2016
💞Bilyn Abdul💞

[1/12, 8:53 PM] mrs bilkisu: ☆☆☆☆☆☆☆
🎾NAWAFF🎾
☆☆☆☆☆☆☆




NA BILKISA IBRAHIM💞




page👉🏻3


Ta ce, "da direba maidani gida.
Cikin tsoro ya ce, "to hajiya makarantar fa??.
Cikin masifa ta ce, "gida nace ka maidani ba dogon bayani na tambayeka ba, kajiko.
Ya ce, "yi hak'uri hajiya ALLAH ya huci zuciyarki.
Bata tanka masaba domin zuciyarta sai tafarfasa take, babu abinda take tunowa sai abinda gay d'innan yay mata.
Tun kafin yayi fakin tayi waje, da gudu tashiga gida.

Humm kunsan abinda yaba ni mamaki??, gidan da yarinyar tashiga daka gani gidan talakawane, bazaka tab'a tunanin yarinyar da motar 'yan gidan bane,, tokomadai miye agaba zamu sani.

Tashige falon tana kuka.
Wata dattiyuwar mace tana zaune a matsakaicin falon, farace tas maik'yau, suna kama da yarinyar, daka ganta kasan ma haifiyarta ce.
Tafad'a jikinta tana kuka, cikin hanzari dattijuwar ta rungume d'iyar tata tana fad'in yasmeen injidai lafiya?, bakije makarantar bane??.
Cikin kuka ta ce, "umma bamun tafiba shine gosulo ya rik'emu.
Umma ta ce, "to mikikema kuka? Ko gosulo d'in?, ta girgiza kai alamar A'a.
To minene?, umma ta tambaya.
Ta share hawaye bawani ne ya mareniba, mari kuma? Miki kai masa?, tana kuka tana bama umma labarin abinda yafaru.
Umma tashiga lallashinta tana bata hakuri, babanta yashigo da sallama, dan tunda suka shingo yagansu, yatsaya tambayar balarabene abinda yafaru.
Yashafa kan yesmeen ya ce, "karki damu mamana ALLAH yana tareda masu hak'uri, dan haka kiyi hakuri watarana sai labari.
Ahankali tad'ago manyan idanunta wad'anda sukayi jajur saboda kuka, ta ce, "karka damu abba kabarni dashi dakaina zan rama, wlhy abba saiya raina kansa, dan na daina zama ana rainamu, dan kawai muna talakawa saikowa ya ce, zai rainamu, abba aii babu maraya sai rago.
A'a mamana kibarsa kawai kinji, abbanta yafad'a yana shafa kanta.
Shuru tayi batace komai ba, dan tasan bazata iya hak'ura ba.
Umma ta ce, "mudai idan tamune ki hak'ura, yasmeen bana son tsiwar nan taki, idan kikayi hak'uri sai ALLAH ya saka miki, ki barmu muji da damuwarmu.
Shuru tayi batace komai ba, sai hawaye da idanunta ke zubarwa, cikin raunin murya ta ce, "kuyi hak'uri iyayena shima ALLAH zaimana maganin sa, ina ji ajikina bazai tab'a nasara akanmuba insha ALLAH.
Abba ya share hawaye yana fad'in to ALLAH ya amsa addu'ar ki mamana.
Sukace amin itada umma.

D'akinta ta shige, iyayenta suka bita da kallon tausayi, umma taja ajiyar zuciya mai k'arfi, ta ce, "lallai yasmeen kina ganin taskun rayuwa iri2, ALLAH dai yakawo mana k'arshen abunnan.
Abba ya ce, "amin.

Yasmeen tana shiga d'aki wayarta tahau wringing jiki a sanyaye ta d'auka, saidai fuskarta ta nuna alamun tsoro, murya na rawa ta ce, "Assalamu alaika.
Bansan mi akace a d'ayan b'angaren ba, amma naga idanun yasmeen suna zubar da hawaye, saikuma ta ajiye wayar tafad'a saman gado tana kuka, duk da bansan ainahin damuwar yasmeen ba amma tabani tausayi kwarai da gsk, cikin sanyin jiki nabaro gidan nima.

Ab'an garen su NAWAFF kuwa, sai mas'ud ne ya tuk'a motar, dan NAWAFF ya kasa saboda b'acin rai, tunda ya zauna akujerar gefen direba ya lumshe idanunsa masu haske, bai sake cewa uffan ba.
Mas'ud yanufi hanyar gida dasu dan yasan ran 'yan maza ya b'aci, kosunje inda sukayi niyyar zuwa NAWAFF bazaya sakeba, saboda yana cikin b'acin rai.
K'ofar wani matsaikai cin gida mas'ud yay hon, da sauri mai gadi yabud'e get d'in, mas'ud ya danna hancin motar zuwa ciki.
Ba laifi gidan yanada d'an k'yau kuma daga ciki babbane, NAWAFF ya fito yanufi cikin gidan, kai tsaye gidan ya shiga, amma babu kowa a falon, fitowa yayi yanufi b'an garensa wanda baikai girman inda yafara shigaba.
Ya fad'a saman doguwar kujera ya lumshe idanu, mas'ud yashigo ya bishi da kallo kawai.
NAWAFF ya mik'e yashige bedroom d'insa, bayi yafad'a batareda ya cire kayan jikinsaba ya sakarma kansa shawa, yakai tsawon minti goma ahaka, sannan ya cire kayan jikinsa yay wanka yafito.
Jalla biya kawai ya zura ya dawo falon, mas'ud na kwance a kan kujera mai zaman mutum biyu, ida nunsa nasaman tv yana kallon.
NAWAFF yafito yazauna batare da yayima mas'ud maganaba.
Mas'ud yad'ago yana kallonsa, dan shima yasan bazai tanka masa d'inba, yako bushe da dariya yana kallon NAWAFF.
Nawaff ya d'ago yana hararar sa, yaja tsaki, tareda d'aga goran ruwa ya kwankwad'a, har sannan mas'ud yana kunshe dariya.
Cikin masifa Nawaff ya ce, "dallah malam wai miye hakane??, zaka wani tasa mutane gaba kana musu dariya.
Mas'ud ya ce, "kajimin mutum, ina ruwanka da dariyata, ko kaji na ambaci sunan kane??
Ammafa wlhy d'an uwa kun dace da yarinyar nan gsky.
Wata uwar harara ya yasakar masa, batareda ya tanka masaba ya mik'e ya fice.
Mas'ud yacigaba da dariyarsa, kamar wani mahaukaci................✍🏻


Ina godiya ga d'umbin masoya, dasuka turomin sakwannin taya murnan kammala book d'in NI DA AMINIYATA ngd ALLAH yabar k'auna😘❤❣👈🏻




Kuyi hak'ura daga nan zuwa wani lokaci, zaku cigaba da samun page 1 ne kullum arana, kawai, kafin komai ya daidaita ngd.



💞bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞LUV U OLL😘😘😘😘💞💞
©2016
[1/12, 8:53 PM] mrs bilkisu: ☆☆☆☆☆☆☆
🎾NAWAFF🎾
☆☆☆☆☆☆☆





NA BILKISA IBRAHIM💞




Page👉🏻4


Yasmeen tafito sanye cikin jan les, d'ikin riga da siket, ta nad'e kanta da d'auri mai k'yau sai zabga uban k'amshi take, ga farin mayafi da farin takalmi, abin sai wanda yagani.
Mahaifiyarta ta bita da kallo, ta ce, "kai yasmeen d'in abba kinyi k'yau, kamar kece amaryar.
Hannu tasaka ta rufe fuska🙈 ta ce, "kai umma.
Umma tayi dariya ta ce, "to nabari, yanzu ke dawa zaki tafi, koda yaseer zakuje.
Yasmeen ta turo baki gaba, ta ce, "ALLAH umma bazanje dashiba, kina ganin jiya abinda yay min aii.
Yaseer dake zaune yana cin abinci ya ce, "nima ba zuwa zanyiba, dan haka maida wuk'ar, ni nan dakike gani kallon kwallo zani.
Yasmeen ta harareshi, aii kallon kwallo kawai ka'iya, mara aikinyi.
Yaseer ya tab'e baki, ke kuma zuwa biki kawai kika iya, ni wlhy nak'agara abba ya aurar dake abar mini filin ma.
Yasmeen ta kai masa duka, ya kauce yana dariya, cikin shagwab'a ta ce, "umma kin gansa ko?, umma tayi dariya, ta ce, "nikam babu ruwana, tunda kekika zauna yaseer ya rainaki, wanima saiyace shine yayanki aii.
Yaseer ya ce, "to umma ba'ita ta tsaya shagwab'a ba, shiyyasa akecewa nine yayanta, yafad'a yana mata 😜.
Yasmeen tabishi zata daka, suka fara zagaye falon, umma te ce, "kinga mamana k'yaleshi, zokiyi tafiyarki, kinga karkije ki fad'i da wannan takalmin mai tsinin tsiya.
Yasmeen ta tsaya tana turo baki, yayinda yaseer yake tsaye bakin k'ofa yana dariya, ta harareshi, habawa yaro wlhy zan dawo nasameka, saika gayama aya zak'inta.
Yaseer ya ce, "saidai mu fad'ama ayar tare, yana gama fad'a ya fice.
Itama dai sallama tayima umma, ta ce, "zataje su tafi da ameena, umma ta ce, "to hakanma yayi, amma kudawo da wuri.
Yasmeen ta ce, "to umma za'a kiyaye.

Tana fita gidan su Ameena ta shiga, gsky gidansu ameena yafi nasu yasmeen k'yau sosai, a get suka had'u, ameena ta ce, "yauwa garama haka, dama bana son nashiga mu b'ata lokaci.
Yasmeen batace komaiba taja hannun ameena suka shiga mota balarabe yaja.
Wani had'ad'en guri aka kaisu, bazan fad'i gurinba dan karsu teema suce zasu itada deexerh😜, wajen yayi matuk'ar had'uwa, anshirya komai, yanda yakamata, yasmeen ta ciro waya a jakarta takira wata no.
Ana d'auka ta ce, "Asmy ALLAH ke 'yar is... ce, kince babu African time amma gashi waje babu kowa.
Daga can akace sorry my dear gamunan, wlhy laifin Safwan ne shida abokansa, wai sun tsaya jiran babban aboki, kuma har yanzu bai isoba, amma gamu nan zuwa.
Yasmeen tayi d'an tsaki ta ce, "inji dai ba d'an iskan jiya bane daya shanyamu.
Amaryar ta ce, "wlhy shine.
Yasmeen taja tsaki, tswww, sai kuma akace dole saidashi za'ayi komai, cikin haushi ta kashe wayar batare da tajira amsar Asmy ba.
Ameena ta ce, wai mitace miki??, yasmeen ta yatsine fuska, wai d'an iskan jiya suka tsaya jira, saikace wani d'an gwal, kina ganin yanda ya shanyamu jiya, daga k'arshe dan rainin hankali saiya aiko mana direba.......
Yasmeen bata rufe bakiba motocin su Asmy suka fara shigowa.
Bayan tsayawar su mutane suka fara fitowa, kowa yana neman wajen zama, saida kowa ya zauna sannan yasmeen ta je tafito da Amarya, ango ma yafito, 'yammatan amarya da abokan ango suka take musu baya har inda aka tanadar musu.
Sai kujeru biyu a gefe wanda babbar k'awar amarya zata zauna, da babban abokin ango.
Yasmeen ta zauna kusada asmy amarya suna magana kus2, yayinda aka fara gabatar da abinda yatara mutane.
Zuwa can mai gabatarwa ya fara wasa babban abokin ango da aka dad'e ana jira, gaba d'aya hankalin mutane yakoma kan had'ad'd'iyar motar data tsaya kalar jaa da ratsin fari, gsky motar ta d'auki hankalin mutane, sai dai banda yasmeen, da waya ta d'auki hankalin ta.
Tunda yafito ake ihun fad'in sai modeebbo! Sai modeebbo!!. Shikam hannu kawai yake d'aga musu yana murmushi, har wajen zamansa aka rakashi wato kusada ango.
Bayan anyi shiru, akayima babban abokin ango barka da zuwa, ya k'ara d'agawa mutane hannu yana murmushi.
Ango ya ce, "mutumina ina ka mak'alene haka, tuni kai ake jira, cikin muryarsa mai dad'i ya ce, "ayimin afuwa my friend wlhy matsaya jiran mas'ud ne, baima dawoba hakanan na hak'ura na taho.
Ongo yay murmushi ya ce, "anyi maka modeebbo, sukai murmushi tareda yin musabaha.
Yasmeen koda tagama wayar bata damu kanta da son ganin waye babban abokin angonba, dan haushinsa takeji sabida b'ata musu lokacin dayayi jiya.

Mai gabatarwa yafara kwala kiran sunan yasmeen Abubakar habeeb, tazo ana gayyatarta.
Yasmeen ta dad'e zaune bata motsaba saida Asmy ta ce, "plz dear kitashi mana, yasmeen ta ce, "ALLAH kunya nakeji dear.
Asmy ta harareta lallai dear awajen aurena kike jin kunya.
Aka cigaba da yayata sunan yasmeen dole ta mik'e tsam tanufi inda aka tanada.
Ya mik'a mata abin magana🎤, tareda fad'in munaso ki gabatar mana da kanki, dakuma tarihin amarya.
Jiki a sanyaye ta karb'a, 🎤👩🏻duk ta takura saboda kallon da mutane suke mata, ta d'auki hankalin yawancin gays d'in wajen, ahankali tafara magana, cikin murya mai zak'i, aii wasu saida wutar kansu ta d'auke, harda babban abokin ango (modeebbo) yak'agara yaga fuskar mamallakiyar muryar nan.
ta fad'i sunanta da alak'arta da amarya, bayan tagama aka shiga yimata tafi.
mai gabatarwa ya ce, "itace zata gayyato babban abokin ango zuwa wannan waje.
Batare da musuba takarb'a takardar tafara kiran NAWAFF SA'ED MODEEBBO.
Takira yakai sau biyar amma bai ko motsaba daga inda yake, tajuyo dan ganin wai waye wannan d'an rainin wayon abokin angon.
Karaf idanunsu suka had'u a k'ar kashin inuwa d'aya, zumbur NAWAFF yamik'e tsaye.
Yasmeen ta ce, "taf tsuntsu daga sama gasashe, azuciyarta take maganar.
shima dai NAWAFF raya abinda zai faru yakeyi dan yasan dole sukwashi 'yan kallo, amma yasan maganin ta..........................✍🏻
Hahahha yauda budiri tsakanin YASMEEN DA NAWAFF.😂😂😂😂😜





💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞LUV U OLL😘😘😘😘💞💞

©2016
[1/12, 8:53 PM] mrs bilkisu: ☆☆☆☆☆☆☆
🎾 NAWAFF 🎾
☆☆☆☆☆☆☆





NA BILKISA IBRAHIM💞




Assalamu alaikum.
Alhmdllh 'yan uwana kamar yanda nafad'a muku natsaya da rubutu sabida wani dalili.
To Alhmdllh yanzu komai ya dai daita, in farincikin kasancewa daku😘😘😂.





Page👉🏻5


.....Nawaff ya tsuke fuska, itama yasmeen ta tsuke tata fuskar.
Yak'araso gareta cikin wani taku na isa da tak'ama, wajen yayi tsit ana kallonsu, yayinda masu hotuna suketa haskasu.
Yak'araso daf da ita, tamkar zai shige jikinta, tayi saurin ja baya, ya had'a yatsunsa biyu yana bugawa, yay k'asa da murya yanda ita kad'ai zata iya jinsa, ya ce, "wlhy kika yimini hauka awajennan saina aikata miki abunda 'yan jaridu da mujallu zasu buga a safiyar gobe juma'a.
Dukda tsoro mai tsanani yashigi yasmeen wannan bai hana ta hararar saba, ta rik'e k'ugi cikin tsiwa ta ce, "kai baka isa kasa 'yan jarida yad'aniba, kuma ALLAH shizaimin tsari da sharrinka.
Nawaff modeebbo yad'an d'ago yana kallon yanda hankalin mutane yadawo kansu, saiya saki murmushi na basarwa.
Gaba d'aya gurin yad'auki sowa da fad'in sun dace da juna.
Nawaff yaja tsaki tareda fad'in shashashu kawai, ta ina na dace da wannan mai kama da aljanar.
Yasmeen ce kawai taji furicinsa saikuma mai gabatarwa dayake kusada su tsaye.
Yasmeen tai murmushin takaici ta ce, "ai basu bane shashashun kaine babban shash............kafin tarufe baki ya damk'o hannunta ya murd'a da k'arfi, wani tsananin zafi yaratsata har kwakwalwa, ALLAH yasota fitilar gurun Blue ce tana kuma kunnawa ta kashe, dan haka ba kowa yaga muguntar da Nawaff yake mataba.
Zafin ya ratsata sosai, afusace ta watsa masa mari, da sauri yasaketa yana murza kumatu, itama takoma kusada amarya da sauri ta zauna tana haki.
Nawaff yad'ago da sauri danjin andafa shi, mas'ud yagani tsaye.
Mas'ud ya ce, "plz my bro's ka share kawai, karka bari wani yagane wani abu dake faruwa.
Nawaff ya kalli mas'ud da idanunsa dasukayi jaa, ya ce, "wlhy Mas'ud saina yima yarinyarnan abinda zatayi dana sani arayuwarta, kamar yanda ka buk'ata zan barta ammafa had'uwarmu tagaba batada k'yau ko kad'an, kuma ka rubuta ka ajiye.
Yana gama fad'a yakoma mazauninsa dake kusada ango, mas'ud ne ya wakilcesa, wajan fad'ar duk abinda ake buk'ata.

Asmy ta ce, "yasmeen wai miye had'inki da modeebbo??, yasmeen ta share hawayen fuskarta, ta ce, "karki

Please Login or Register in order to submit comment