Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

suka rabu gida uku kowanne layi da aikin da zasu aiwatar ,wani rukuni ne suka shiga bandaki ,kafin suka fito ,domin sanar da ita cewar ita suke jira domin fara wankan sarauta ,tashi tayi cikin sanyin jiki ,yayinda wasu acikinsu suka matso domin tayata cire kayan dake jikinta ,saida yazamo daga ita sai farin mayafi iya girjinta ,shiga tayi cikin ruwan da aka tanada domin wankan ,turarene kala kala acikin ruwan wankan banda wanda ake shafeta dashi dakuma wasu fulawoyi da ake mulkawa a jikinta ,sai da wanka ya kammala kafin masu kula da kayan shafe shafe suka fara nasu aikin ,bayan suma sun gama tasu fasahar sai kuma masu kula da ado dakuma sutura ,cikin kan kanin lokaci aka shirya gimbiya safeenah cikin kaya mai matukar kayatuwa ,sannan suka ja dabaya tare da rusunawa suka bar dakin ,sameerah ce tashigo bakinta asake domin ganin irn haduwar data yi ,dama kuma ga ga kyau ba karya ,bayan fitarsu da dan lokaci kadan kuma ,sai ga wasu rukunin bayin suma sun shigo ,saidai su sun fi na baya dan manyanta sannan masu da adon kaya kaman na farkon ,suma gaishe da ita suka yi kafin suka nemi izinin ta wajen fita ,domin ganawa da mutanen gidan sarautar.
Bangaren mahaifiyar sarki aka fara kaita wanda ta manyanta sosai ,kasancewar ta dade kafin ta haifi huruddeen ,basuyi wani dogon surutu ba kasancewsrsu dukka basuda wani surutu ,fatan alkairi tayi mata kafin sukayi sallama ,sashen sarauniya zulaikah suka wuce kasancewar matar sarki shamam ta biyu ta rasu bayan auro zulaikah da lokaci kadan ,tun daga hanya gimbiya safeenah ta jinjina karfin mulki na sashen sarauniya zulaikah ,domin to ko ina dakarune majiya karfi suke aikin tsaro ,kana kuma da bayi kala kala cikin kaya daban daban kowane da aikin da suke aiwatarwa ,bayan isarsu bakin kofa saida aka nemo izini daga wajen hakimar kafin suka samu damar shiga falonta na farko wanda shima tsaruwarsa tafi gaban kwatance ,zama tayi akan kujera yayinda sauran bayi kuma suka zauna a akan shimfida ,domin sauraron isowar babbar sarauniyar .
Can bayan wani lokacine suka ji takunta daga babban falonta tana fitowa ,wanda saboda shanya su datayi ,duk hakurin gimbiya safeenah saida taji ranta yabaci da abinda yayar tata tayi musu ,takowa tayi cikin takama gamida kasaita,tana tafiya bayi na tare mata rigarta saboda kar ta fadi ,saida ta iso har kujerar dake kallon gimbiya safeenah kafin ta zauna ,duk wannan abinda ake sarauniya zulaikah bata kalli inda sarauniya safeenah take ba ,saida tagama gyara zama tare da dora kafa daya kan daya ,kafin ta dago da idonta ta kalli inda sarauniya safeenah take ,zare ido tayi game da razana saboda .............

SADI -SAKHNA ce 😊😊😊

(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)

💎💎💐💐WATA RAYUWA 💎💎💐💐

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

(The legendary novelist),🌄🌄

(The legendary story)
📒💎↗↗🎿👿👽
written by💟 SADY-SAKHNA💟

💎💐 ..... WATA RAYUWA....💎💐

phone number:09035784150

telegram :https://t.me/joinchat/-_Qs5O8XH6cwYjQ0

whatpad :@SAKHNA03

......Dedicated to proficient writer association........

(08)

Gyara zamanta tayi saboda kar razanar da tayi ya fito fili ,saboda kar bayinta su rainata ,tunani tafara yi ranta cewa "tabbb gaskiya kyawun halitta ya bayyana a jikin baiwar allah nan ,don duk da izzar mulkina da kuma launin fata irin namu na kasar saraham ,tabbas bazan nuna wa wannan fatar kyau ba ,sannan .............tunanin da takeyi ta katse sakamakon muryar gimbiya safeenah da taji a cikin kunnenta ,
"barka da safiya sarauniya zulaikah dafatan nasameki lafiya ?"
yatsine fuska tayi kafin tace "zancen lafiyata ,kalau nake nida magajin masarautar nan dayake cikin cikina ,zuwanki bazai sa nakamu da cuta ba ,sannan ina miki barka da zuwa wannan masarauta wadda take karkashin ikon wata ,saidai mutum ya biyo a baya"
sarauniya zulaikah ce ta karisa maganar ta ,fuskarta dauke da wani mugun murmushi mai dauke da ma'anoni daban daban ,hannunta kuma akan cikinta tana shafawa cike da gadara ,sarauniya safeenah ce ta sunkuyar da kanta kafin tace,
"shikenan nizan wuce nabarki lafiya"
tana gama fada ta tashi kana tayi hanyar fita daga falon ,muryar zulaikah taji a bayanta tana cewa ,
"dama kuma inaso namiki dan tuni akan wani abu ,karki manta da kofar da kika shigo "
zuyowa tayi ,ta kalli zulaikah fuskarta dauke da alamar kanta ya daure da maganar ,ganin halin da ta shiga ne yasa zulaikah yin murmushi kafin ta juya zuwa babban falonta cikin takama.
Sarauniya safeenah ce zaune a gaban wani katon madubi dauke da kayan ado iri iri ,hankalinta ba akan abinda yake gabanta bane ,tunanin maganar da sarauniya zulaikah ta fada mata take ,sai can kuma ta watsar da komai ,ta tashi tana gyara alkyabbarta domin shiga turakar sarki ,jakadiya ce ta rakata inda aka sake shiryata domin jiran isowarsa.
Koda jakadiya ta ji alamun fitowarsa sai tabasu waje domin ganawa,zaune take fuskarta a sunkuye har yazauna a gabanta ,
"to ina miki barka da zuwa sabon waje sannan kuma sabuwar rayuwa "
"ina amsawa ya shugabana"
"hmm shikenan dafatan babu wata matsala da kike fuskanta ?"
"babu komai saidai rashin sabo"
"karki damu sannu zaki saba da hakan ,fatanmu shine allah yasa albarka a zamanmu "
"ameen ya allah ".
Daga haka labarinsu dakuma hirar su ta sanja salo ,nabasu waje domin su gana.
Haka rayuwar cikin masarautar ta cigaba da tafiya a tsakanin matan ,yazamana yanzu sarauniya safeenah tasaba da sabuwar rayuwarta ,wanda sanadin halinta na kwarai yasa da kadan kadan mutanen gidan da kuma bayi suka fara komawa karkashinta.
rayuwa suke ta kowa yayi harkarsa ,domin babu wanda yake shiga harkar wani ,saidai a bangaren zulaikah burinta da kuma tsarin da ta shirya yana nan a cikin ranta .
Abubuwa da dama sun faru a masarautar saraham ciki harda haihuwar sarauniya zulaikah da kuma barin ciki da da sarauniya safeenah tayi ,saidai abu yazo ba yanda aka zata ba .
Bayan doguwar nakudar da zulaikah tayi a dakin karbar haihuwa ne ta haifo yar ta mace ,sak kamarsu daya da ita ,lokacin da zulaikah ta kula da abinda ta haifa sai duk duniyar ta sanja mata ,amma soyayyar d'a da uwa ,hakan bai hana ta daukar yar ta ta rungume ba ,amma abinda yake cikin ranta yafi gaban kwatance.
Bayan kwana bakwai ne yarinya taci suna MEELAH ,inda sunan ya tara manyan mutane dakuma gagarimin taro ,sarauniya safeenah ma ta yimata murna ,saidai bata ga fuskar amsawa daga wajen uwar gayyar ba.
Lokacin da sarauniya zulaikah ta fahimci cikin dake jikin safeenah bakaramin girgiza tayi ba ,saboda a tunaninta zata haifi da namiji kafin ita,hada baki sukayi da wata baiwarta inda sukayi nasarar saka mata maganin bari a cikin abinci.
Haka abin yacigaba da faruwa inda har saida takai safeenah tayi bari uku a jere cikin shekara guda ,abinne yabata mamaki inda har saida takai ga tace ,"shin meyake faruwa dani "
Bayan abinda yafaru sai shigar cikin ya tsaya mata ,har ta shafe shekara biyar batare da tasamu cikiba .
Zulaikha ce a zaune akan kujera gefe kuma babbar baiwarta ce RALEEYAH kuma amintacciyar ta ,wanda duk wani shiri da ita ake kullawa ,sarauniya zulaikah ce tafara magana ta hanyar cewa ,
"gaskiya inaga abinda nake hasashe ya tabbata ,dan kiduba ki gani tsawon shekara biyar kenan har yanzu bata samu cikiba ,kuma dama maganin idan ya zubar da ciki fiye da sau uku ,to da wuya mace takara samun ciki "
"hakane ya shugaba ta ,hakika aikin mu ya yaci yanda muke bukata ,kuma dama nasara tana tare dage sarauniyar sarauniyoyi "
kantane yakara fasuwa dan dama hakan yana mata dadi yanda baiwar tata take zuga ta.
Har sun bude baki zasu cigaba da magana sai ga meelah ta shigo tana wani tamke fuska ,yarinya ce yar shekara biyar amma kuma kasaitar ta da jin kanta yafi na yar shekara goma ,dan a wajen gado mahaifiyarta har ta wuceta ,wannan hali na meelah yana yiwa zulaikah dadi ,dan tafiso taga jininta suna taka kowa yanda suke so ,zama tayi a gefen uwar tata ,inda raleeyah ta fara gaisheta tare da kirari ,ko kallon inda take meelah batayi ba bare ta amsa gaisuwar ta ,babu cin fuska dakuma zarafi da bayin basu fuskanta ba a wajen meelah ,wai hakan ma batakai ga girmanta ba.
Kallon uwar tayi kafin tace ,
"ummah zanje na kwanta idan mai karatu yazo ace masa yajirani har sai na tashi ,kar a tasheni dan hakan yana samin ciwon kai "
"shikenan shalele ki fito lfy "
zuyawa tayi tana wani taku kamar isassun mata ,wanda suka san takan rayuwa har ta bacewa ganin uwar tata ,saida tabar gun tukunna zulaikah ta juya tana kallon raleeyah gami da cewa ,
"kinji dai mai gimbiya meelah tace ,dan haka karki bar kowa ta shiga sashenta har sai ta bukaci hakan "
"angama mai girma sarauniyar saraham "
Acan bangaren sarauniya safeenah kuwa ,zaune take suna magana itada sameerah tana bare mata ayaba suna yar hira ,can bayan wani lokacine safeenah ta ajiye ayabar da sauri tare da barin wajen da sauri tana ...........

alkalami ya gaji sosai 😊 ku tara dani a gaba.

SADI-SAKHNAce

(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)

💎💎💐💐WATA RAYUWA 💎💎💐💐

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

(The legendary novelist),🌄🌄

(The legendary story)
📒💎↗↗🎿👿👽
written by💟 SADY-SAKHNA💟

💎💐 ..... WATA RAYUWA....💎💐

phone number:09035784150

telegram :https://t.me/joinchat/-_Qs5O8XH6cwYjQ0

whatpad :@SAKHNA03

......Dedicated to proficient writer association........

chp(09)

Tana kokarin amar da yabar data shiga bakinta ,sameerah ce ta mika mata ruwa tare da yimata sannu ,saidai kuma abin yazarce saninsu ,domin kuwa bayan amar da ayabar sai yazamana tafara amayar da duk ruwan dake cikinta ,saida aman yalafa matane ,sameerah ta rikota suka dawo daki tana mata sannu ,ganin irin galabaitar datayi lokaci daya ,numfashi take sauke wa a hankali tareda amsa sannun da baiwar tata take mata ,kwanciya tayi domin tasamu ta dan huta kafin zuwa anjima .

Gimbiya meelah ce ta tashi daga barci ,lokacin maraice ,tana wani yacine fuska kamar ta hadiyi ashana ,takawa take cikin karairaya tana wani shan kamshi ,tafa hannunta tayi a bakin kofar ,wanda hakan yabawa bayin dasuke bakin kofar shigowa cikin sauri ,rabuwa sukayi kowacce tafa aikinta ,gyaran inda ta tashi dakuma gyaran bandaki da yimata wanka .
Bayan sun gama shiryata ne ta tafi zuwa turakar mahaifiyar tata ,wanda tana ganin yar tata ,ta bude mata hannu alamar ta taho ,
"laleh da gimbiyar daular saraham kuma farin cikin sarauniyar daular saraham ........."
haka tagama yimata kirari itakuma tana wani daga kai ,(nidai nace tohhh ).
Bayan sati guda ,amma har sannan jikin sarauniya safeenah babu dadi ,domin duk abinda taci sai ta amar shi ,ga zazzabi sosai ,sameerah ce takare mata kallo kafin tace ,
"ranki yadade inaga cikine dake domin alamun hakan sunnuna "
"ehh nima ina tunanin hakan ,inaga kije kikiramin ma'ikaciyar jinya ta dubani "
"ahah ranki yadade ,nifah banyadda da mutanannan ba ,dan wannan zubar da cikin da kikayi a baya ,AKWAI LAUJE CIKIN NADI akai ,inaga murufe zancen cikinnan har sai yayi kwari ya isa haihuwa "
"shikenan sameerah ,amma ni aganina bai kamata mu zargi wani ba ,akan hakan ,domin komai allah ne yake kaddarawa ,allah yazabamana mafi alkhairi "
Haka kuwa akayi babu wanda yasan da zancen cikin safeenah har saida yakai wata biyar kafin ta sanar da mai martaba shima dan ya kula da hakanne ,yayi farinciki sosai daya samu labarin hakan ,sai kuma abin yabashi mamaki akan mai yasa bata sanar dashi ba ,dabara tayimasa irin namu na mata akan cewa ,tana son yimasa bazata ne ,shida sarauniya zulaikah ,amma tunda shiyasani to yabari iya kar yafadawa kowa sai sanda ta haihu ,bai kawo komai a ransa ba ya amince da kudurin ta .
Bayan cikin sarauniya safeenah yayi wata bakwai ne ta tambayi mai martaba akan zataje garinsu ,dafarko yanuna kin amincewarsa ,saboda cikin dake jikinta ,saidai dayaga hankalinta ya tashi sai ya amince ,tayi farinciki sosai daya barta ,inda sukafara shiri itada sameerah ,basu dau lokaciba washagari suka kama hanyar maihaifar tata cikin farin ciki .
Saida sarauniya safeenah tashafe wata biyu kafin ta dawo saboda lokacin haihuwarta ya kusa kuma yazo mata da jinya mai matukar wahala ,inda mutanen fada suka fara samun labari cewar sarauniya safeenah bata da lafiya amma ,anhana kowa damar dubata daga gidan sarautar.
Hakan yajawo gulmace gulmace kowa da abinda yake fada ,(uhmm gidan sarauta )
A bangaren sarauniya zulaikah kuwa zaune take a turakar mijinnata suna hira ,kallonta yayi kafin yace ,
"zulaikah yakamata kije ki duba abokiyar zamanki domin tun sanda ta dawo daga garinsu bata lafiya ,sannan naji labari bakije kin duba dakinta ba tun sanda tazo gidannan "
"au gulmata aka kawo maka ko ?to ni zulaikah bata isa tasani abinda banyi niyya ba "
tana gama fada ta tashi fuuuu tabar turakar ,binta yayi da kallo kafin ya jijjiga kai .
Yau ta kama jumaa lokacin hantsi ,sarauta safeenah ta tashi da nakuda mai matukar wuya ,inda aka kira ungojama daga fada ,ita kanta tayi mamaki da taga uwar gijiyatata da ciki saidai bata nuna ba ,tafara bata taimako ,
sun sha wuya sosai kafin allah yabata iko ta haifo danta namiji ,saidai daya tashi fitowa tare yafito da mahaifarta ,wanda dama tasamu matsala sanadiyyar barin da tayi a baya ,gyara jaririn akayi wanda yafito sak jikin ubansa saidai kama dayayi da mahaifiyarsa ,itama taimako suka bata kafin kuma aka gyara mata jiki domin ta huta .
Labarin haihuwar sarauniya safeenah ne yafara zaga cikin masarautar inda kowa abin yabashi mamaki ,domin kowa bashida masaniyar samun cikinta bare kuma ace ta haihu .
A bangaren sarauniya zulaikah kuwa zaune take itada babbar baiwarta suna hira ,sai ganin baiwa sukayi ta zube a gabansu tana haki ,
"ranki yadade kiyimin rai ,amma hakika naji wani labari yana yawo a cikin masarautar nan "
"to menene ya faru ki fada mana "
cewar raleeyah ,
"uhmm dama labarine ya riski wannan fadar na haihuwar da sarauniya safeenah tayi a yau "
"ehhhhh me kikace haihuwa kuma tabbb "
sarauniya zulaikah batace komai ba ,sai yanzu tace ,
"me ta haifa ?"
"uhmm da namiji "
"iyeee ,namiji 😠😠,saboda bakin sakonki kije ki karbi bulala shabiyar a wajen sarkin horo ,(nace maganin munafiki )"
fita tayi jikinta yana rawa tayi waje ,raleeyah ce ta kalli sarauniya zulaikah kafin tace ,
"to yanzu menene abinyi akai ?"
"hmmm ,inaaa ai dole sai ya mutu ,hakan bazai taba yiyuwa ba ,wani ya kwace daular saraham daga wajena .
A can kuwa sashen sarauniya safeenah hankalinsu kwance ita da jaririn ta wanda yake cikin koshin lafiya ,labarin haihuwarsa ya zaga duk fadin duniya bama iya daular saraham ba .
Meelah ce ta shigo sashen sarauniya saraham din bayi suna take mata baya fuskarta kaman anyimata aiken mutuwa ,koda tazo bakin turakar aka bata izinin shiga saita dakatar da bayin da bakin kofa kafin ta shiga ,bata yiwa kowa magana ba acikin dakin ta wuce wajen jaririn wanda yake kwance cikin gado na alfarma dakuma kayan sarauta ,kallonsa tayi kafin ta tabe baki tace ,
"an tursasani nazo na ganka ,amma ba hakanne yasa ni zuwa ba ,domin babu wani mahaluki daya isa yamin dole ,nazone nayimaka gargadi akan ka tsaya iya matsayinka karka shiga gonata ,don kana ganinka na miji ,dan haka indan ka girma ka tambayi mahaifiyarka yanda ake zaman gidannan a zauna lfy ,kai ba kowa bane ,face dan bayan fili ,dan haka ka rubuta ka ajiye "
tana gama fada ta karewa dakin kallo kafin tayi wani zuyi ta fice .

tohhh nidai nace rayuwa .

SADI-SAKHNA ce

(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)

💎💎💐💐WATA RAYUWA 💎💎💐💐

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

(The legendary novelist),🌄🌄

(The legendary story)
📒💎↗↗🎿👿👽
written by💟 SADY-SAKHNA💟

💎💐 ..... WATA RAYUWA....💎💐

phone number:09035784150

telegram :https://t.me/joinchat/-_Qs5O8XH6cwYjQ0

whatpad :@SAKHNA03

......Dedicated to proficient writer association........

chp(10)

har gimbiya meelah tafara surutunta ta gama babu wanda yakalleta acikin dakin kaman bata samu mutane acikiba .
Dahaka rayuwa tagara har zuwa ranar bakwai da haihuwar yaro yaci suna SHAMAM ake kiransa da AMAM ,biki akayi na kece raini a nahiyar masoya nata farinciki da samun karuwar yaron ,yayinda a daya bangaren kuma wato iyalan waziri suka yi bakinciki da hakan .
Bayan wani lokaci rayuwa ta gara haka kuma abubuwa sun auku ciki harda harin da ake kawowa yarima amam ,wanda daga bayane aka kebeshi cikin sashensa da bawanda yake shiga sai mahaifiyarsa ko wani na kusa dashi .
Ganin sarauniya zulaikah takasa samun ganinsa bare cutar dashi sai kuma shiga hanyar malami ,inda har tayi nasarar tura masa asirin tsanar mace a rayuwarsa da kuma mulki ,babu wanda yasan yana dauke da wannan sihiri sai wanda yayishi da kuma wanda yasa akayi .
Tohh muje zuwa ...................
。。。。。。。。。。。CIGABAN LABARI 。。。。。。。。

Daular saraham ta kara samun daukaka da kuma kawatuwa fiye da yanda take a kwanakin baya ,saida na kare cikin fadara da kallo ,anan naji labarin auren gimbiya meelah da akayi ga dan masarautar KHAIRASH ,wanda ta haifi danta mai MANNEER ,wannan labarin yaban mamaki ,ashedai na dade a tafiyar baya dana yi 😊.
Hankalina ne yatafi zuwa wani arnen gini da'aka yishi da farin dutsi mai walwali ,hanyace mai matuka tsayi ta bi takan wata gada (bridge )daga cikin masarautar har zuwa ga cikin ginin .
Bakomai bane a wajen ginin idan aka hada da cikinsa a bangaren ,babban falo ne da dakuna ,wajen wasa ,motsa jiki1,wajen hutawa ........komai ma akwai a wajen na more rayuwar dan adam dai ,motsi naji a dakin motsa jiki hakan yasa hankalina yakai wajen ,wani matashin kyakkyawan saurayine a tsaye ,daga shi sai wani farin wando iya gwiwa ,jikinsa kuwa gumi ne yakebi takan fatar jikinsa da take fitar da wani haske mai kyau ,abinda yaban mamaki shine tafiya zuwa labarin rayuwarsa shekara 50,amma yanayin girmansa tamkar dan shekara 25,gaskiya halittunnan suna da abin mamaki .
Tafiya yake yana goge jikinsa ,da wani farin nafkin ,kafin ya wuce cikin wani daki da alama wajen baccinsane ,wucewa yayi bandaki.
Yadade kafin yafito daure da towel ,ya nufi gaban wata drawer da aka jera wasu nau'ikan taure masu matukar kyau ,saida yashafe jikinsa da turaruka kafin ya yasaka wasu fararen kayan masu adon sarauta a jiki ,karar bugun kofane yasashi daga daradaran idanuwansa ya zuba su akan kofar ,yadade kafin yayi wata yar kara da hannunsa alamar a shigo .
Wani bawane yashigo tare da tsugunnawa a gabansa yana cewa ,
"ranka yadade sarki ya aiko ganinka a zaman karshen wata dayake da iyalansa a fada ,"
kada kai yayi tare da yimasa alamar ya fita ,
(tohh shikuma baya magana ne ?),
Takawa yake a hankali bayan yafito daga sashensa kana ya wuce wajen mahaifiyarsa ,bude kofar yayi ya shiga bayin na bashi hanya tare da gaisheshi ,saidai ko kallonsu bai yiba bare ya amsa musu.
sarauniya safeenah ce a zaune a bakin gadonta tana kokarin saka alkyabbarta domin hallarar taro daza'yi,juyowa da kallanta tayi zuwa kan dannata ,zuwa yayi ya zauna a bakin gadon kusa da ita tareda rike hannunta da alamar kulawa ,itama kallonsa tayi tana jijjiga kai tare da cewa ,
"hmm nafara gajiya da halinka amam ,kai shikenan ba dama kayi magana saidai kadinga yin abu da hannu ,menene hakan ,in wani abune yake damunka ka fada mun mana ,bakayin abu ,irinna kowa ,meyake damunka ne ?"
"babu komai ummah ,dafatan kina lafiya ?"
yafada muryarsa cikin sanyi kuma mai matukar dadi ,
"lafiya kalau ,ka tabbatar bakomai ko ?"
ta kara tambayarsa a karo na biyu fuskarta dauke da damuwa ,
"ehh bakomai "
"toh shikenan allah yasa hakane ".
Tafiya suke yi ita da dannata har suka iso ga babban dakin da'ake tattaunawa a ciki ,,kowa samun waje yayi ya zauna,dama su ake jira kafin mai martaba yafara bayani ,
"to barkanku da zuwa wannan taro da'aka sabayi a duk karshen wata domin tattaunawa akan matsalar data shafi kowa ,kowa ina masa barka da zuwa musamman ke meelah dakikazo daga wani waje keda danki ,sannan kowa yasani akan dalilin yin wannan taro bai wuce saboda kai ba AMAM ,(yafada yana nuna yarima amam ),koyaushe akan abu dayane ,yanzu ma inaso kasanar dani abinda ka yanke ,shin ka samu wacce kakeso ?ko kuma ka amince da wacce na zaba maka,?"
"ahah abba bani da wacce nakeso "
"to ka amince da zabina,da auren yarinyar dana zaba maka ?"
"ahah bana sonta "
"kanada wata masalane daya hanaka aure ka fadamana ?"
"ahah "
"hmmm to shikenan idan har wannan shine ra'ayinka ,to koban fadaba kasan hukuncin dana yanke akan ka ,idan baka zo min da amasata ba ko ?"
"ehh na sani abba "
"to shikenan zaka fara shirin barin masarautar daga yanzu na sallameka ,ba zaiyiwu ina mulkar dukkan mutane ba ,kai kuma ka bijireminba dan haka ka barmin nahiyata gaba daya ,kaje inda zaka bi ra'ayin kanka "
yana gama fadin hakan ya buga tebur din dake wajen ya tashi cikin bacin rai yabar wajen ,kowa kallon kowa yake a cikin wajen ,daga baya sarauniya zulaikah ita da yar ta suka kece da dariya harda tafawa ,sarauniya safeenah ce ta kallesu cike da mamaki ,yayinda shikuma yarima amam baiyi mamakin abinda sukayi ba ,saboda bai manta yanda suka yita galla masa azaba ba ,dakuma jifansa da mugan kalamai ba sanda yaro ,dan haka batare da yace komai ba yabar wajen dama shi bayi da surutu dan sai ya yini bai ce komai ba ,itama sarauniya safeenah tashi tayi tafita tana neman tsari daga sharrinsu ,saidai al'amarin yana cinta azuciya sosai duk da juriya irin nata .
"Gaskiya ummah keta musamman ce ,yanzu kinga zaiyi nesa da wannan nahiyar watakil ma yayi rayuwar bauta tunda ankarbe duk wani launi da daraja irin na mutanen wannan wajen ,manneer shine zaiyi mulkin saraham ,da sannu badai jinin safeenah ba "
"hakane gimbiyar saraham ,jinina ne zaiyi mulki indai ina numfashi a cikin wannan masarautar ,tun da munyi nasarar fitar masa shi a cikin ransa ai komai ya kare ................hmmm

SADI-SAKHNA ce😊

(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)

💎💎💐💐WATA RAYUWA 💎💎💐💐

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

(The legendary novelist),🌄🌄

(The legendary story)
📒💎↗↗🎿👿👽
written by💟 SADY-SAKHNA💟

💎💐 ..... WATA RAYUWA....💎💐

phone number:09035784150

telegram :https://t.me/joinchat/-_Qs5O8XH6cwYjQ0

whatpad :@SAKHNA03

......Dedicated to proficient writer association........

chp(11)

sarauniya safeenah ce a zaune fuskarta dauke da damuwa hawaye na zuba a idonta ,duk da karfin hali irin nata a yau ta zubda hawaye saboda rabuwa da zatayi da danta da kuma zafin irin kiyayyar da mai martaba yake masa bayan a da ba haka yake masa ba .
Tsayawa tayi da kukan jin alamar shigowa turakar tata ,ko ba a fadamata ba ,daga jin yanayin takun tasan yarima amam ne ,goge hawayen idonta tayi cikin dabara kafin tajuyo da fuskarta izuwa gareshi.
Matsowa yayi kusa da inda take daune ,kafin ya ajiye jakar dake rataye a kan kafadar sa ,muryarta cikin rauni tafara fadin ,
"yanzu menene sunan abinda kayi amam ?dama sokake kadaina kallona ko ,menene yake damunkane haka ?"
"ahah ummah karkice haka ,duk da zan bar nahiyata ,bazan taba iya mantaki ba ,kunmin duk wani abu da d'a yake bukata a wajen iyayensa kuma sannan inda rabo watarana zamu hadu ,inaso kicigaba dayimin addua ,kuma kobayan natafi in abba ya nemeni kice ina naiman afuwarsa "
"yanzu dagaske kake ? daka yi aure gwara ka rabu damu ?"
"kiya femin ummah amma haka zancen yake ,dana zau na kusada mace gwanda gawata ,haka nakeji acikin raina "
"shikenan ina maka fatan alkhairi "
"nagodee ummah ".
Haka tafiyar ta yarima amam ta kasance ,ya fita daga cikin nahiyar tasa batare da ko nadamar zabin da yayi ba .
。。。。。。。。。。。。
Datunanin maganar da
mukayi da saheel na kwana a raina ,dan gaskiya abin yadaure kai sosai .
"Fahreeyah tunanin me kike haka naga kin zurawa waje daya ido uhmm ?"
"ba komai ummi kawai ina tuna rayuwarmune "
"kidaina hakan karna sake gani kinji ,bai kamata mai shekaru irin naki tafara tunani ba "
"shikenan hakan bazai sake faruwa ba "
"yawwa yar albarka "
suna cikin harar su mai dadi irin na y'a da uwarta saikuma sukaji dodon nasu ,wato muryar aryan ta kadamusu hantar ciki ,
"wane irin iskancine bazaku fitoba kuke wani kus kus a daki ,munafukai ,to kujo kowa ta kama aikinta ,badan kuji dadi na siyeku ba tohh "
fahreeyah ce tafara fitowa tana bin jikin bango ,kafin huda itama ta fito ,kallonsu take idonta kaman zai fita dan masifa kafin tazuya tana

Please Login or Register in order to submit comment