Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

samu inda zatayi aikiba ko kuma saboda wani boyayyen nufinta dan nima ban yarda da ita ba,"kowa kallonsa ne yakoma kanta ciki kuwa harda fahreeyah wanda tabude baki da ido tareda furta,"KIRISAH😯😯😯!!!!!

SADI-SAKHNA ceh❤❤


(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)

💎💎💐💐WATA RAYUWA 💎💎💐💐

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

(The legendary novelist),🌄🌄

(The legendary story)
📒💎↗↗🎿👿👽
written by💟 SADY-SAKHNA💟

💎💐 ..... WATA RAYUWA....💎💐

phone number:09035784150

telegram :https://t.me/joinchat/-_Qs5O8XH6cwYjQ0

whatpad :@SAKHNA03

......Dedicated to proficient writer association........

Chp(23)
Dan tsabar girgiza da lamarin da fahreeyah tayi ,hakan yasa ko numfashin ta kasa furzar shi tayi ballanta kima ta motsa daga kwancen da take ,wani irin duka da taji a cinyoyinta ne yasa ta jan wani ajiyar zuciya tareda sosa wajen daya yi ja alamun dukan yaratsa fatar ta,kunnen ta nameemah ta kama da karfi kaman zata cireshi tare da jan ta waje cikin huci da zuciya,bata zame ko ina ba sai tsakiyar farfa jiyar fadar tareda zefarta a kasa,tattare siket din take jikinta tafarayi tareda rufe sauran jikinta dayake a bude,duk ta tafara jin alamun mutane sun fara taruwa akanta amma hakan bai sa tayi gigin da go kanta ba,saidai duk wata irin kunya ba wacce bata jita ba a wannan lokacin,dan a yanda take ji ko kasa ta bude zata iya shigewa indai mutanen dake wajen idon su zai dauke daga kallonta.
"Kehh kirisah kika ce sunanki ko me ? Je ki kiramin sarkin horo yanzunnan ina nemansa"nameemah ce mai wannan maganar tana kaiwa tana komowa a gaban fahreeyah tareda aika mata harara kaman tana kallonta,"yanzu dan tsabar raini irin na bayi har kin isa ki hada jiki da masoyina?dan kunga bama yimuku ukuba irin na sauran masarautar koh?shiyasa har raini yashiga ysakaninmu daku koh,yau kuwa zanyi misali dake kowa yagani ,nan gaba sai wata baiwar ko bawa yasake taba abinda yake mallakina".
Tana cikin surutunne kirisah ta dawo tareda sarkin horo rike da bulala a hannunsa yana jijjigata kamar daman mai jira,ko magana batayi ba kawai ta nuna masa inda fahreeyah take da hannunsa,alamun yayi ta dukanta har sai ta ce masa yatsaya kenan.
Cikin gaggawa kuwa yafara aika mata tsimangiya a sassan jikinta babu alamar imani,tun fahreeyah na ihuu har ya zamo ba abinda take sai nishi kawai dan azaba,ganin dukan yaki ya tsayawa ne alamun gimbiya nameemah na kokarin barin sarkin horo ya kashe fahreeyah,ya wata amintacciyar baiwarta sulalewa a wajen tayi hanyar turakar sarauniya wato mamar nameemah domin fada mata abinda yake faruwa.Bayan wani lokacine suka dawo tareda sarauniya,tana isowa wajen tafara tambayar me ya faru,shiru kowa yayi a wajen hakan yasa shima sarkin horo ya tsaya da hukuncin dayake yi.
"Nameemah tambayarki nakeyi mai ya farune haka"shiru nameemah tayi har sannan fuskar ta babu alamar ta sauko daga dokin zuciyar da tayi,"kirisah kiyi mata bayanin abinda kika fada min"
Saida tayi kifikifi da ido kafin tafara magana tana sunkuyar da kai kaman wata mutuniyar arziki.
"Eh dama lokacin da shugaba zilziliyyah tace mata ta jira ta bari taje wani waje ta dawo su koma,saboda ita bata samu aikin dazata yiba,nikuma nazo zan wuce saina ga ta hade fuska alamar bata amince da abinda tafada ba,sai naga tafito da wani abu a gefen rigarta tafesa ajikinta,alamun tsimin turare ne tayi amfani da shi ,sai na ga tayi hanyar dakin mai girma yarima,sai da taga ba wanda yake kallonta sai bude kofar ta shiga,shine nikuma ganin haka kuma an hana kowa ya doshi hanyar kofar ,ya sani zuwa da gudu na fadamiki abinda yake faruwa,shikenan abinda nasani ni"
Kowa shiru yayi yana tunanin labarin da kirisah ta bayar tareda mamakin abinda fahreeyah tayi.
Zilziliyyah ceh ta iso wajen sannan da alamun sannan labarin ya isa gareta,nameemah ce ta kalleta tareda da tambayarta ya sukayi da fahreeyah a daren jiya itama,"ehh ranki yadade lokacin da nace mata ta jirani nakai sako ga jakadiya na dawo tacemin to,amma danaje na dawo saina ga babu almar ta a wajen,dana duba ban ganta ba sainayi tunanin ko ta koma dakinsune shiyasa kawai namanta da lamarinta nima".
Maganar da masoyin nameemah yayi ne yasa kowa maida hankalinsa Kansas,"amm nima lokacin da ta shigo dakin ina zaune kawai saina ga ta fara matsowa kusa dani tana lumshe idonta dana shaki kamshin dayake jikinta ne naji hankalina ya gushe shigowar gimbiya nameemah ne yasani dawowa hankalina"
"Kin ji ko AMMEEH? kinji abinda tayiwa masoyina koh?,yanzunnan a kira min manyan dogarai😠😡"
Kowa shiru yayi ana jiran aga mai zai faru,can bayan wasu yan lokutane shugaban dogarai ya iso tareda tawagarsa,saida ta kalli dogaran ta kalli fahreeyah dahar yanzu kanta kasa yake,"inaso ki amsa min na karshe shin kin aikata abinda ake zarginki da dashi ko a'a,dan yanzunnan zan yanke miki hukunci ba sai anjima ba".
"""Tabbas duk halin danake shiga a baya,tun daga tsangwamar da kawayena sukemin,da kangin bautar dana shiga harma da rashin mijina jigona,babu wanda na shika tsaka mai wuya acikinsa kaman wannan laifin da aka lakamin na kokarin yiwa masoyin gimbiya nameemah fyade!!!,yau naga ta kaina ni fahreeyahtul sharmeelah,wace irin duniya na tsinci kaina wannan wace irin rayuwa ce haka,yah allah kasan ina cikin WATA RAYUWA!!!! yah allah ka nuna min haske,sananna..........","kehh ba magana nake miki bane ko kin shirya karbar komai?"
"Kiyan kemin duk hukuncin dakika san yadace da laifina ya shugabata, a shirye nake da karbar sa hannu bibbiyu,tunda ya riga ya shigo cikin RAYUWATA"wannan shine iya abinda tace kafin nameemah ta bada umarnin hukuncinta.
"Ku kaita magarkamar bakaken bayi"
Hahhhhh kowa ya dauka a wajen saboda jin irin hukuncin da gimbiya nameemah ta yanke mata,wasu nacewa yadace da ita maganin masu halinta yayinda wasu ke cewa komai tayi laifinta bai kai a kaita wannan magarkamar ba,saboda ba kowa acikinta sai yan leken asirin da aka kama ko kuma wanda suka yi babban ha'inci acikin fada na ban mamaki,hakan ma ba kowace mace ake kaiwa wajen ba.
Su Kansu dogaran saida jikinsu yayi sanyi kafin suka dagata daga tsugunnen da take,wanda sai a sannan ne takalli dunbim mutanen dake wajen,idonta ne ya sauka akan kirisah,wanda tayi mata murmushi da alamun babu damar tayi bayan abinda ta aikata mata,idonta ne yasake sauka akan shugaban wato habeebin nameemah😊,ganin kallon da take masane yasashi juyawa yabar wajen shima ko a kwalar rigarsa tunda yafita kunya kuma masoyiyarsa bata zargeshiba shikenan.
Har sun juya sun fara tafiya taji kukan sareeenah wanda hakan yasata sake juyawa itama tana kallonta,wanda sai a sannan hawaye yazubo mata da ta tuna cewa bayan mahaifiyarta da mijinta akwai wata wacce take santa kuma zatayi kuka idan ta tafi,tausayin sareeenah ne yakamata data tuna yanda suka zauna duk da na yan kwanakine awajen amma hakan bai hana sun shaku da juna ba😢😢😢!!!.
Jan ta sukayi kaman kayan wanki suka bar wajan.saida sukayi tafiya mai tsayi kafin suka shiga wata kofa wadda zata kaika gidan yari na karkashin kasa ta wani bututu mai tsayi,tun suna tafiya fahreeyah na ganin hannunta har komai ya bacewa ganinta.
Tafiya sukeyi har suka shiga wani waje mai fili saidai yafi hanyar yalwar haske amma ba kaman haskaen sararin duniya ba,wucewa akayi da ita wani daki ita dai banda bin su babu wani aiki da takeyi,jefata sukayi a wajen batare da sunce komai ba suka juya suka a wajen.
Had suka tafi bata dago kantaba domin a tunaninta ba wani rai a cikin dakin,saida taji motsin mutanene ta dago kanta suka hada ido da wasu manyan mata masu bakar halitta,dayace acikinsu ta wullo mata wani kaya baki na saki tareda cewa,"maza ki cire wannan kayan jikinnnaki masu haske,domin mu bama ta'ammali da abu mai haske kuma kiyi shirin karbar sakamakon laifin dakika aikata, dan mu nan ba'a tambayar mai mutum ya aikata kawai idan an shigo dakai to babu alamar sassauci dazaka fuskanta daga garemu"
Kayan dake jikin fahreeyah tasa hannu ta ja,kaman masu jiran a janyesu suka yage daga jikinta,ganin kaman kiftawar bismillah tarasa suturar jikinta,yasa tafara kakkare fatar jikinta daga kallonsu,wata dariya suka sa dasuka ga abinda take saida suka gama dariyar kafin suka darara mata tsawa tareda sanar da ita cewar basason sanyar jiki a wajen.
Cikin hanzarin kuwa ta gama abinda suka umarceta,wata daga cikinsu ce ta finciketa tareda yin wata hanyar daban.
Saida sukayi wata yar tafiya mai nisa kafin suka iso wani daki mai kama da keji wanda aka yishi da bakin karfe,zefata tayi ciki ta fadi akasan wajen kafin ta juya ta tafi kaman batayi komai ba.
Bayan tafiyr matarne ta daga kanta suka hada ido da wasu mata guda biyu wanda tsabar ramar dake jikinsu kaman ba a taba halittar tsoka a cikin jikinsu ba,dayar cikin su ce tace mata"barka da zuwa cikin ukuba yar uwa muna miki jajen zuwa wannan wajen.............tofahhhhh🤫🤫🤫


SADY-SAKHNAceh


(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)

💎💎💐💐WATA RAYUWA 💎💎💐💐

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

(The legendary novelist),🌄🌄

(The legendary story)
📒💎↗↗🎿👿👽
written by💟 SADY-SAKHNA💟

💎💐 ..... WATA RAYUWA....💎💐

phone number:09035784150

telegram :https://t.me/joinchat/-_Qs5O8XH6cwYjQ0

whatpad :@SAKHNA03

......Dedicated to proficient writer association........

Chp(24)
Kallon su kawai ta tsaya tanayi,duk da cewa bata nuna ba amma yanayin ta tabbatar ta girgiza da abinda taji daga garesu,idonta ne yakai kan wacce tayi mata magana daga farko da alamun tafi sauran dan dama daga yanayinta,
"Shin me like nufi da cewa gidan ukuba?"
Murmushin takaici tayi dajin kalar tambayar da fahreeyah tayimata kafin ta bata amsa'
"Duk abinda zan fadamiki ba lallai ki sani ba saidai inaso kisani cewa,babu banbancin dare ko rana a wannan wajen sannan taka maimai hukuncin daya kamata a miki na dadai da laifinki wanda aka ga dama za'a miki,abinci kuma za'a dunga baki duk bayan kwana biyu ruwa kuma bayan kwana daya,baruwansu da rashin lafiya koh laluri saidai idan kin mutu a jefarki a jeji saboda kar ki damesu da wari,sannan babu wani tausayi daya taba wanzuwa a fuskar wani ma'aikaci anan wajen,kuma............"
Days daga cikin wanda basuyi mata magana ba ce ta dunguri wadda takeyi mata bayanin tareda cewa,
"Saleeerah taka mata kiyi shiru haka ,sauran abubuwan zata gani da kanta ai,ko so kike ki karar da dan karfin da muka samu bayan munci abinci akanta,?"
Shirun tayi kuwa alamun taji bayanin da daya matar tayi mata,bata sake magana ba saima juyawa da tayi ta koma daya gefen ta zauna,shiru ne ya ratsa cikin wajen yayinda bayan wani dan lokaci sai su juyo su kalleta kafin kuma sai juya.
Wata irin kara mai tsananin kara da kuma tausayi ne ta ratsa kunnensu wanda hakan yasa fahreeyah firgita har saida ta tashi tsaye batare da tasani ba,kallon fuskar su tayi amma taga babu alamar wani razana a garesu,hakanne yabata alamar cewa kenan sun saba da jin irin wannan karar,wai!!!.
Kasa jurewa tayi hakan yasa ta tambayi wacce tayi mata magana da tazo wajen wato SALEEERAH,
"Wannan kuma wace irin kara ce haka?"
Da kamar bazata amsa mata ba sai kuma tace,
"A kurkun gaban mune ,an kama wani dan leken asirine shine yayi taurin kan fadar waya aikoshi,jiya an cire masa hannu guda daya yauma kuma suna cire masa dayan shine kawai"
"Kawai!!! kuma?sai a cirema masa kuma Bakomai bane a wajensu?"
Dariyar dukkansu suka sheke da ita kafin dayar data hana saleeerah magana tace,
"Kina nufin kice baki taba jin labarin magarkamar cikin kasa bane?koda a kasar ku?"
Kallon su fahreeyah tayi da alamar tambayar su kafin ta jijjiga kai alamun bata sani ba,saida suka yi shiru kafin dayar ta tambayeta,
"Abin mamaki baki san labarin irin wannan wajen ba,amma wane irin laifi kikayi aka kawoki wannan wajen,kin yi kokarin kashe sarki ne?,leken asiri aka turoki daga wata kasar ko kuma hada baki kikayi da wani domin jawo silar yaki?ko kuma............."
Bata gama koro bayanin ta ba fahreeyah tayi saurin rufe mata baki tareda girgiza kai jikinta har rawa yake,
"Ahah ahah ahah,ban.....taba .....kkkki...saba,kawai gimbiya nameemah ceh ta kamani da mijin dazata aura ,wata yar wajen da muke tare ceh ta sakani na je ashe bahaka bane shine tayanke hukuncin a kawo ni nan dan na amshi horona akan hakan"
"Eeeehhhhhh"
Dukkansu suka fada a tare kaman ance musu ga nan aljani a bakin kofarsu.
"Kina nufin kice iya wannan laifin kika aikata ta bada umarnin akawoki nan,kuma babu wanda yayimata magana akan hakan,to ai ko wanda ya aikata yafi naki za a kawoshi nan wajen ba,gaskiya ba'a zartar miki da hukuncin daya dace ba sam"
Har saleeerah ta gama bayanin ta suna jijjiga kai saboda Mamakin abinda suka ji anyiwa fahreeyah,ganin da tayi sun dulmiye cikin Labarinta yasata karsesu tareda cewa,
"Naga kina ta Mamakin abinda nayi aka kawoni nan wajen amma ku toh mai kuka yi aka kawo ku nan wajen?"
Shirun sukayi kowa tana kallon kowa kafin saleeerah ta yanke hukuncin fada mata,
"Gaskiyar magana ni turoni akayi leken asiri daga kasarmu,basai kinji inane ba an kamanine lokacin danake tabb da haura ganuwar garinnan.
Ita kuma wannan,'ta fada tana nuna wacce tahana ta magana dazu'sunanta leelah ita kuma ana zarginta da taimakawa abokan gaba na yamma da wannan kasar.
Sai dayar wadda tunda kika zo bata miki magana ba ita kuma laifin mu daya wato leken asiri.
Toh wannan shine laifikanmu saidai ana tambayarmu muka bada amsa batare da taurin kaiba ni da leelah,iya waseelah ceh da taki fada suka yanke mata hannu guda daya"
Tana fadar hakan fahreeyah takai idonta kan hannun waseelah wanda aka yanke shi saura gudu lumi,ganin kallon da waseelah taga fahreeyah tana yima hannun ta ne yasata boyeshi a bayanta tana sunkuyar da kai,sauke ajiyar zuciya tayi bayan taji takaicaccen tarihinsu kafin tace,
"Gaskiya abin akwai abin mamaki a cikin,amma yawancin wanda suke wajennan irin laifinsu kenan?"
"Ahah akwai wasu laifukan da dama,dan kurkukun gefen mu su anka masu dasa ka guba ne a cikin abincin sarki",
Suna cikin magana ne fahreeyah taji sunyi shiru suna kallon bakin kofar wajen,saboda ita ta bawa kofah baya bata kalli abinda suka hangoba,saidai jin motsin sawun mutum yayi kusa da wajen na su,sai ta juya sukayi arba da wani mutum kato.
Makulli yasa yabude wajen batareda yace komai ba,ya finciki kafadar fahreeyah yayi hanyar wani lungu mai dan tsawo.
Sun yi mai dan tsawo kafin suka isa wani waje mai jan haske,duk yakushin da fahreeyah take masa tun sanda ya daukota hakan bai sakashi ajiye ta ba har saida yakaita wannan filin tukunna.
Tana tsugunne a wajen har wani mutumi yafito mai dogon gemu har kusan cikinsa,saida yazo daff da ita kafin ya zauna a wata kujera da take gaban fahreeyah,
"Kehh kece karyar da aka kawo dazu kenan,?,dukvda cewa ba nan ne inda za'a kawoki mu karbeki ba,amma ba laifi hakan ma tunda har an bamu cin hanci ,dan haka yanzu inaso ki fadamin gaskiya shin kin aikata kuskuran ake tuhumarki koh kuma a'a,"
Shiru fahreeyah tayi ko dago kanta batayiba bare ta amsa maganar da'akayi mata.
Dara DA mata tsawa yayi sannan yakara da cewa,"ba tambayarki nake ba,toh inaso ki sani cewa ko kin amsa ko baki amsaba dolene saikin karbi horo dan shine abinda nayi alkawarin yi agareki"
"Ehh na aikata abinda suka,ceh nice na je har dakinsa"
Haka takare maganar muryar ta na rawa cikin kunan rai,
"Saboda ke karya ce mai bin mazan mutane koh? Sannan kuma anturoki domin ki lahantashi koh?,sarkin horo,ku mata bulala hamsin da zanen wuta abaya '
Yana gama fadan hakan yatashi yabar wajen,ko waiwayo wa baiyyiba.
Fahreeyah na nan tsugunne har aka suka gama shirye shiryensu ,bata zata ba sai jin zafin bulala tayi a bayanta,haka bulalar tayi ta sauka akan jikinta tun tana karewa har karfinta yagaza aikata hakan.
Abubuwa dayawa ne suka dawo mata a rai,ga zafin Kalmar daya kirata sannan kuma ga zafin abinda suke aikata mata.
Jikinta ne yagaza bata hadin kai lokacin da aka fara danna mata bakin karfen da yayi juwur a cikin wuta a bayanta,inda komai na dunyar ta yadauke daga cikin kwakwalwarta kaman an dauke ruwa.

SADY-SAKHNAceh❤


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels


Please Login or Register in order to submit comment