Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

WATA RAYUWA....💎💐

phone number:09035784150

telegram :https://t.me/joinchat/-_Qs5O8XH6cwYjQ0

whatpad :@SAKHNA03

......Dedicated to proficient writer association........

chp(19)

Wajen kwalliya aka shiga da duk wata sabuwar baiwa domin gwada yanayin salon ta dakuma roll din dazata taka a matsayin ta na baiwar daza ta na dauke wa bakin masarautar kewa.
Tun daga wajen gyaran jiki fatar fahreeyah tayi wani irin laushi da haske tun kafin a je ga dora kwalliya dakuma kayan sakawa, zalziliyyah ce ta matso kusa da ita bakin ta a bude saboda kyan da taga fatar ta tayi da kwalliyar,
"Gaskiya jikinki yana da kyau sosai,zaki kasance a wajen masu tarar manyan baki"
Wani irin faduwar gaba ne ya riski kirjin fahreeyah sakamakon furucin daya fito daga bakin zalziliyyah, yayin da a bangaren Kirisah kuma bakin cikin ya lullubesu ita da mabiyanta saboda jin matsayin da aka bawa sabuwar baiwa bayan su sun dade a wajen basu samu ba, fahreeyah yace ta daga idonta tana kallon zalziliyyah da take ta kwaro mata bayani kafin tace,
"Shugaba da kinyi hakuri kin barni a matsayina na da din kawai domin inaga kaman shiya dace dani,a matsayina na sabuwar baiwa a wannan wajen"
"Nariga na Yankee hukunci, sannan inaso ki sani cewa abinda ya dace da masarauta nakeyi ba wai ra'ayinku ba, domin inaso kusan cewa tun ranar da kuka shigo wannan masarauta da sunan bayi kuka rasa duk wani yanci da kuke da shi dan haka banason wani yasake saka min baki ko shishshigi a cikin aikina"
Shiru ne ya ziyarci wajen sakamakon yanda sukaji zalziliyyah tana ta fada akan maganar da fahreeyah tayi dahaka wajen ya watse kowa yakama hanyar inda aka kaishi domin yin aiki.
Fahreeyah ce tsaye a bakin dakin su na da, kafin a sauya mata matsayin ta, shiru tayi kaman mai tunani tana cizon yatsa, domin daga ganin ta zakasan cewa tsoron shiga dakin take,waigawa tayi da saurin jin anayi mata magana a bayanta,a jiyar zuciya da sake dan ganin mai maganar ba kowa bace illah Sareenah,wanda suka hadu a wajen wanka jiya, murmushi tayi mata kafin tace," me yasame ki haka kike tsaye a wajen? Ko tsoron shiga kike?"
"Ehh to.... dama kayana zan dauko a dakin"
"Karki damu muje na rakaki dama nazo wajenkine, domin naji dazu shugaba ta mayar dake sashenmu kuma naga baki zo ba har yanzu to shine nazo Naga ko lfy?"
"Ahah bakomai kawai ina tsoron shiga dakin ne"
"Hmm ai naga alamar hakan, karki damu muje na rakaki"
Shiga dakin sukayi amma duk da haka fahreeyah na boye a bayan Sareenah,
"Hhhhhhhhh hmmmm wai ke gaki baiwa mai matsayi ko? to ki saurari zuwana cikin rayuwar ki,sai kin kwammace ba a haifeki ba wlh, hmmmm mujuba ni dake,nadade ina mafarkin zama baiwa mai babban matsayi amma wai zuwan ki yau har kin samu, hakan bazai yiyu ba .......
"Gashi kuma ya yiyu kuma, sannan da kike zancen ta kwace miki matsayi ai ba ita ta Hana a dauke ki ba koh!??baki cancanta bane shiyasa,ke fahreeyah je ki dauko kayan ki kizo mutafi"
Cikin sanda kaman za'a ce arrrrr ta ruga da gudu,taje ta dauko kayan a wajen kwanciyar ta jiya, hanyar kofa suka nufa zasu fita,sai kuma muryar Kirisah ta kara ziyartar dodon kunnensu,
"Da gake har mai daure miki kan macijin kina wasa da wutsiyar zaku ga abinda zan muku hmmmmm"
Ko ci kanki basu ce mata ba suka fice daga dakin,tana ta bambamin fada ita kadai.
Bayan sun fitone Sareenah ta kalli fahreeyah kafin tace,
"Gaskiya kina da sanyi dayawa sannan tsoron ki yayi yawa"
"Kiyi hakuri nasaka ta zageki koh"
"Ina zancen kinada tsoro amma kina ban hakuri"
Murmushi kawai fahreeyah tayi mata kafin tace,
"To ai bansan mai zance miki ba saboda ban tashi cikin mutane sosai ba, shiyasa"
"Menene tarihinki to?zanso naji sannan kuma mai yasa kika tsinci kanki a wajen nan?kada kiyi tunanin ni macuciyace, kawai tun ranar da nafara ganin ki nasan bakiyi kama da irin bayin nan wajen ba,naji kawai kin burgeni sosai".
"Shikenan nayi alkawarin zan baki tarihin rayuwa ta amma inaso kidan bani lokaci kadan, sannan inaso kibani takaitaccen bayani akan wannan masarautar ko kadanne"
"Shikenan inshallah zan sanar dake dan abinda nasani akan wannan masarautar,amma kafin sannan mudan zaga sauran wajajen da baki saniba tukunna"
Sareenah ce ta jaa fahreeyah sukayi cikin fadar domin zagawa da ita ko ina.
Tafiya suke suna dan taba hira,duk inda suka wuce sai Sareenah ta fada mata inane sannan kuma ya ko'ina yake dakuma tsarin sa, fahreeyah yace ta tsayar da Sareenah tare da nuna mata wani gini mai kyau amma da alama bakowa a wajen,bayan ta nuna matane kuma ta tambayeta to wajen shikuma inane,ajiyar zuciya Sareenah tayi kafin tace,
"Fahreeyah ba'ason a dunga maganar da ta shifi wancan ginin a wannan masarautar saboda hukunci yakan iya hawa kanki idan akaji hakan,tunda na gama nuna miki komai yakamata muko ma haka kuma,"
Zanta Sareenah tayi suka fara komawa muhallin su,amma har sannan idon fahreeyah yana kan wannan ginin da tagani, haka kawai taji wajen ya birgeta sosai.
Saida sukaci abinci kaman kullum kafin suka koma dakin su, fahreeyah ce ta kalli Sareenah cikin kaguwa da san jin labarin masarautar,
"Uhmm Sareenah ina jinki bani labarin to"
"Uhm dama kinada surutu haka fahreeyah? Sanda na fara ganin ki ban zata zakiyi surutu haka ba"
"Eh nidai naji,mufara labari tunda kinmin alkawarin koh?"
"Shikenan to"
""Da farko naji kince baki san ko sunan masarautar nan ba, to sunan ta*masarautar BAHMEER* ita wannan masarauta tana da karfin mulki da iko domin itace da biyu a duk duniya mai fada a ji,dazu kin tambayeni wani gini muna tafiya,to wannan ginin ba mallakin kowa bane face na babban dan sarkin wannan masarauta wanda yayi batan zana shekaru uku dasuka wuce sanadiyyar wani sabani sa suka samu shi da iyayensa,mai suna yarima SAHEEL, kuma har yanzu ba wanda yasan inda yake, saidai labari ya taba zuwa cewar anganshi a garin bardugu ...........
Ehh saheel, kuma garin bardug????!!!!😯..

SADI-SAKHNA ce

(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)

💎💎💐💐WATA RAYUWA 💎💎💐💐

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

(The legendary novelist),🌄🌄

(The legendary story)
📒💎↗↗🎿👿👽
written by💟 SADY-SAKHNA💟

💎💐 ..... WATA RAYUWA....💎💐

phone number:09035784150

telegram :https://t.me/joinchat/-_Qs5O8XH6cwYjQ0

whatpad :@SAKHNA03

......Dedicated to proficient writer association........

chp(20)

Fahreeyah ce a tsaye kamar mai tunanin wani abun, maganar da Sareenah tayi ne ya katseta daga tunanin da ta tafi,
"Meyasa kika samu waje haka kika tsaya,tun ban fara baki labarin ba"
Tunanin tane yadawo mata hakan yasa tayi saurin boye mamakin ta tareda barin koma menene a cikin zuciyar ta,komawa tayi ta zauna tareda cewa,
"Eh kiyi hakuri nadan tafi wani tunanine,cigaba da ban labarin ina jinki"
"Toh nayi zatan ai wani abune yasame ki shiyasa"
Toh kaman yanda mukayi bayani a baya na wannan masarautar mai suna BAHMEER,bazan baki labarin yarima saheel sosai ba saboda abinda ka iya zuwa ya dawo saidai abinda nasani nima akansa shine;bashida yawan magana sannan bai fiye shiga abinda bai shafe shiba,baida yawan magana sannan yanada tsayawa akan ra'ayinsa sosai.
Karna cika ki da surutu akansa shikadai, sai kuma na biyun shine yarima Sameer, sai kuma gimbiya NASREEMAH,sai yar autar su NAMEEMAH, dukkan su basuda damuwa sosai,saidai bawa ko wani acikin gidannan na fuskatar hukunci idan ya sabawa bukatar su ko kuma dokarsu, dukkan su uwa daya uba daya suke saboda babbar sarauniya bata haihuwa, Sai yakasance ta rike su tamakar yayan data haifa a cikin ta.
Kasance war babban yarima yayi batan zana ba asan inda yakeba saiya zamo cewa yanzu yarima Sameer shine mai jiran gadon sarauta.
Wannan shine dan takaitaccen abinda zan iya baki game da wannan masarauta sai kuma sauran abubuwan da in muna tare zaki gansu da kanki yau da kullum"
"Nagode sosai da amsamin tambayoyina da kikayi, Allah yabarmu tareda aminci"
"Ameen"
Tashi sukayi tareda uzurinsu na yau da kullum, Sareenah ce ta kalli fahreeyah kafin tace" to bani labarin ki kafin mukwanta"
Shiru taji babu alamar magana daga wajen fahreeyah, hakan yasa ta lekata kafin tace,
"Me yake damunki haka naji kinyi shiru uhm"
Nanma shiru taji babu alamar amsa daga wajen fahreeyah n,komawa tayi dagabanta domin ta juya mata bayane, idonta ne yafito da alamar mamaki matuka,
"Fahreeyah mai yasameki haka naga jikinki yana kar karwa haka,"
Daga kai kawai fahreeyah tayi tana kallon ta batare da tayi magana ba,
"Fahreeyah kiyi magana mana bai kamata kiyi shiruba fah,fada min mai yake damunki"
"Uhmm...kar ki damu Sareenah zazzabi ne kawai zai sauka karki damu"
"Ehh zazzabin ne kar na damu? Tun yaushe kika fara zazzabin to,dan naga dazu kalau kike ba abinda yadameki"
"Yau kwana uku kenan ina yi, kullum dashi nake kwana in na tashi kuma sai naji kamar bantaba yiba, ranar farko nayi zatan zazzabin ne haka,sai kuma naga ya tafi da safe, to jiya ma haka yayimin gashi yau ma kuma ya shirin yimin"
"Zazzabin dare kuma? Toh mai yake kawoshi haka? Sannan kuma kin tabbatar ba abinda yasameki koh?"
"Ni ba abinda yasameni, kawai haka na tsinci kaina, karki dama Sareenah zuwa gobe zai tafi kawai ki kwanta abinki"
"Shikenan amma abin akwai daure kai, yakamata dai asan abinda za'ayi"
Kwanciya tayi akan shimfin Sareenah, yayin da tasake rufa mata kayan ta, saboda sanyin dayake ratsa cikin jikinta, baccine yadauke ta mai wahala.
Washa gari da safe haka fahreeyah ta tashi ba zazzabi a jikinta saidai rashin karfin jiki da take fama dashi, Sareenah ce ta debo mata ruwa tareda kai mata bandaki,bayan ta dawo dakinne ta fada mata,
"Nagode da dawainiya dani da kike Sareenah,hakika ke yar uwace sannan kuma abokiya da ta ke da wahalar samu a wannan lokacin, nagode sosai"
"Kinga kibar wannan maganar haka kije kiyi wankan muje cin abinci saboda kimaida dan karfin jikinki, sannan nagode da fahimtar da kuma yardar ki a gareni"
Tashi tayi taje tayi wanka kafin tazo suka tafi cin abinci,daga can kuma suka tafi zuwa wajen da zalziliyyah take koya musu karairaya dakuma yanayin saka kaya da kwalliya idan an bukace su a wajen taryar baki,
Duk salon da'keyi musu a wajen shiga sukeyi su fita ta bayan kunnen fahreeyah, domin abu kadanne ta fahimta a wajen, saboda har yanzu bata yarda cewa zata bada jikinta wani can bakin masarauta suji dadi ba, hakan bazai taba yiyu wa ba,bayan angama yimusu bayanin daza,ayine kowa yakama hanyar inda zai nufah.
Fahreeyah ce itada Sareenah suna tafiya a hanyar su ta dawowa daga wajen koyarwar zalziliyyah, fahreeyah ce takalli Sareenah kafin tace
"Yanzu Sareenah wata rana haka zanje na bada jikina ga wani?
"Eh toh ya mutum zaiyi fahreeyah,dolene ka yarda da kaddara ko ya tazo maka"
"Yanzu kenan kema kin taba taryar wani da jikinki,kema?"
Murmushi tayi kafin tace,
"Fahreeyah babu abinda yafi kaddara,idan akace miki kaddara angama cemiki komai,tabbas na taryi mutane da jikina ba sau daya ba ma kuwa, domin hukunci ne mai tsauri zai biyo baya sakamakon bijirewa akan hakan"
"Gaskiya yanda nakeji bana tunanin zan iya bawa wani jikina a halin yanzu"
"Kidaina fadin haka fahreeyah domin kowa dakika gani ba asan ransa yakeyi ba,saidan dole kawai,dan haka inaso kimanta da rayuwar ki ta baya ki rungumi ta yanzu dan hakan shi zai taimaka miki ki maida komai ba komai ba"
"Shikenan zanyi kokarin hakan amma zuciyata har yanzu bata amince da hakan ba sam,"
Da haka suna cikin tadi har suka zo izuwa dakinnasu,.
Rayuwar tasu ce ta dunga tafiya da dadi da babu dadi,har takai cewa fahreeyah ta samu tsawon sati guda a masarautar BAHMEER,abubuwa dayawa da saba dasu yayin da wasu kuma har yanzu bata ci karo dasu ba,ciki kuwa harda abinda tafi tsoro shine bada jikinta ga wani a matsayin ta na baiwa mai shakatar da bakin masarauta.
Wata rana ne bayan sun gama duk wani abu dazasuyi, inda yakama kusan kwana goma da kenan da zuwan fahreeyah,sakone ya zowa dakinsu cewar an zabi bayi guda uku wanda zasu shakatar da bakin daza, ayi a a gobe,mai kawo sakonne ya zayyano musu wanda zasu kasance a wajen,sunan fahreeyah ne yafito dodar a cikin jerin bayi bayin, yayin da dan tashin hankali ta samu kanta a zaune a kasa

SADI-SAKHNAce


(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)

💎💎💐💐WATA RAYUWA 💎💎💐💐

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

(The legendary novelist),🌄🌄

(The legendary story)
📒💎↗↗🎿👿👽
written by💟 SADY-SAKHNA💟

💎💐 ..... WATA RAYUWA....💎💐

phone number:09035784150

telegram :https://t.me/joinchat/-_Qs5O8XH6cwYjQ0

whatpad :@SAKHNA03

......Dedicated to proficient writer association........

chp(21)
"Nikuma???, Sareenah bakyajin mai yace wai,wai zan kasance masu tarar baki a gobe"
"Eh naji fahreeyah, yakamata ki daina damun kanki akan wannan rayuwar daki ka tsinci kanki hakan ba komai zai haifar ba illah cutar da zuciyar,idan har hakan zai baki wuya inaso ki rufe idonki kana ki dauki akanki a matsayin bake bace a yanzu fahreeyah, banason naganki cikin damuwa haka,dan Allah karki kasance cikin wanda basa yarda da kaddara a rayuwar su,kinji?"
"Inaso nayi kokarin hakan Sareenah, saidai zuciyata ta kasa aminta da hakan kwata kwata"
Takarisa maganar cikin kuka da karayar zuciya ,
"Zaki iya fahreeyah ni nasan zaki iya"
Dahaka Sareenah ta cigaba da karfa fa mata gwiwa akan abin har takai ta fara kwantar da hankalinta, mutane ne suka fara zagaye su, Wanda ganin hakanne yasa Sareenah janta daki suka bar wajen.
Kaman yanda aka tsara kuwa haka abin yake tafiya domin washa gari zalziliyyah tazo ta tafi da wanda zasu kasance masu tarar bakinnasu wanda zasu iso da maraice, fahreeyah ce ta marairaice zata fara kuka, inda Sareenah tacigaba da bata hakuri da karfafa gwiwa har ta amince da yadda da kaddar tata,
Kwalliya aka fara musu tareda kara yimusu bita akan aikin dazasu gabatar,ba abinda yake a cikin zuciyar fahreeyah illah fargaba da kuma bakin cikin cin amanar mijinta da take shirin yi,bayan angama ne ta dan koma dakinsu kafin lokacin dazasu shiga cikin fada yayi.
Zama tayi a gefen Sareenah tayi shiru kamar mai tunanin rasa wani muhimmin mutum a rayuwar ta, zabura rayi jin dafata da da Sareenah tayi,
"Yanzu har yanzu baki cire abinnan a ranki ba fahreeyah?"
"Ahah Sareenah bahaka bane,ina jin tsoro a cikin raina kuma ina jin zafin yanda dazanci amanassa a wannan ranar Sareenah 😭😭😭"
"Wa zakici amanar, fadamin"
"Mijina, Sareenah zanci amanar mijina a yau,idan kaddara tasake hadani dashi da wane ido zan kalleshi?"
"Toh wata sabuwa,amma meyasa baki taba fadamin ba har saida lokaci ya kure, yanzu bansan wane irin taimako zan miki ba a halin yanzu"
"Karki damu yar uwa banaso ma nasaka ki cikin wani Hali nagode da taimako na ma da kika yi a baya, yakamata na fidda ran sake kallon sa ma a karo na biyu a rayuwata, kuma bana da tabbacin zai amince dani idan ya kalleni a matsayin baiwa a halin yanzu,bari na tafi kar zalziliyyah tazo nema na"
Batare da ta tsaya sake jin wani abu daga wajen Sareenah ba ta juya tareda fara tafiya cikin kayan ta da aka mata kwalliya da su,suna daukar hasken rana a jikinsu.
Fadar BAHMEER ce ta cika da mutane da kuma masu busa sarewa da algaitu, Wanda duk wanda yagani yasan cewar bako mai muhimmanci za'ayi a cikin masarautar.
Yariman masarautar HAIRAAN ne ya babban tattaki domin zuwa ga masoyiyar sa gimbiya
NAMEEMAH kasance war dama ita kadai ce a gida anyi auren yayarta da dadewa.
Duk wanda yaga gimbiya Nameemah a wannan ranar yasan tana cikin farin ciki da zuwan masoyinnata.
Masauki aka fara kai kowane bako daya taho tareda yariman, sannan kowa aka kaimasa wacce zata dauke masa kewa a lokacin .
A bangaren su fahreeyah kuwa lokacin da aka kaisu ga masaukin bakin sai yakasance kowacce an kaita inda zata kasance saura fahreeyah kadai,kasancewar dama sauran bayin zumudi suke da kwanan dazasuyi da bakin shiyasa kowa yasamu inda zaije itakuma aka barta ita kadai, zalziliyyah ce takalleta tareda cewa jirani yanzunnan na dawo mu tafi,kiyi hakuri baki samu aikin dazakiyi ba"
"Toh bakomai"
Tsayawa tayi tana jiranta ta dawo daga inda tace ta jirata take ta dawo,ita kadai take murmushi jin cewa ba da Wanda za'a hadata su a Daren kamar yanda aka tsara,tsayawa tayi da murmushin da takeyi hade da murmushi,jin muryar da ko a mafarki bataso sake jinta,
"Uhm fahreeyah me kike anan ke kadai? Dama shugaba zilziliyyah tace narakaki dakin dazaki yi aikinki Dan haka kizo muje ko"
Tsayawa tayi tana kallonta batare da ta motsa kafarta domin Binta ba,
"Wai ba magana nake mikiba ne kike jina batare da kin taho ba,ko Dan kinga ina lallabaki iyee?,"
Saukar da kanta tayi daga barin kallonta saboda haka kawai take tsoron kirisar kamar ajalinta,ganin alamun da kirisah ta ganinne a fuskar fahreeyah ne ya tabbatar mata da cewa,hakarta ta fara cimmah ruwa kamar yanda ta tsara.
Tafiya take tana wani kwarkwasa yayinda a bangaren fahreeyah kuma tafara binta a baya kaman rakumi da akala,tafiya sukeyi ta wani siririyar hanya mai tsayi Wanda zai sada su da inda take burin kaita.
A gaban wata kofa suka tsaya,wanda ko daga ganin yanayin yanda aka kebance dakin daga sauran dakunan zaibawa mutum damar cewar dakine na musamman a wajen.Kallon kallo suke tsakanin fahreeyah da kirisah yayinda kowa da abinda yake sakawa acikin ransa,shirunne daya fara alamun zaiyi yawa yasa kirisah gyaran murya kafin tace,"uhm dama wannan dakinne inda zilziliyyah tacemin na kaiki,sai a bashi nishadi kamar yanda yadace ,dan shine dama aikiniki koh?",
Had da juya tafara tafiya,har saida takai karshen hanyar dazai sadata da barin wajen kafin tajuyo takara kallonta ,"ohh namanta ban fadamiki yanda akeyi ba,kodayake tunda gar kika shiga matakin manyan bayi ai nasan kin iya komai bakya bukatar wani maimaici,sai anjima allah yabada sa'a,"tafada tana daga mata hannu tareda yimata dariyar mugunta.
Saida alamun wanzuwar Kirisah yabace daga wajen kafin fahreeyah taza wani ajiyayyayen numfashi mai dauke da ajiyar zuciya tukunna ta maida kallonta izuwa kofar dakin da aka bata a matsayin inda zatai aikin ,har ta rike marikar kofar zata bude sai kuma wani tunani yazo mata tare da faduwar gaba ,sakar zuci tafayi ""to idan kuma abinda kirisah tafada mata ba gaskiya bane kuma fah ,kawai tayi mata haka ne dan batasonta ,kuma tana nufinta da mugunta?"""sakin hannun kofar tayi cikin sanyin jiki tareda juya zata bar wajen ,wani tunanin ta sakeyi akaro nabiyu cewar"""idan kuma dagaske ne zilziliyyah ce ta aikota fah,sannan kuma idan aka gane ta bijirewa umarnin da aka bata wane hukunci zata fuskanta a wajen shigabar bayi (zilziliyyah),""saddakarwa tayi kawai tayi ,tareda juyawa tabude kofar dakin tasa kanta a hankali,saida takarewa dakin kallo a haka kafin karisa shiga tareda maida kofar dakin ta rufe.

Sady-sakhna😍 ceh



(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)

💎💎💐💐WATA RAYUWA 💎💎💐💐

тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsт ιмρσятαηт qυαℓιтү α ωяιтεя cαη нαvε, ωε *_ρяσғιcιεηт ωяιтεя's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαяε тнεsε qυαℓιтιεs.

(The legendary novelist),🌄🌄

(The legendary story)
📒💎↗↗🎿👿👽
written by💟 SADY-SAKHNA💟

💎💐 ..... WATA RAYUWA....💎💐

phone number:09035784150

telegram :https://t.me/joinchat/-_Qs5O8XH6cwYjQ0

whatpad :@SAKHNA03

......Dedicated to proficient writer association........

Chp(22)
Shi run da taji a dakin alamun bakowa,yabata damar tsayawa tana karewa dakin kallon,"""waiii irin wannan daki haka,saikace ba'a zama acikinsa dan kyau ,gaskiya wajennan yayi kyau sosai,""",
Saboda nisa data yi cikin yaba dakin,ta sau baki tana zuba murmushi har bata kula da mitumin daya ke bayanta ba,gyaran muryar da taji ne yasa ta juyawa da sauri tana zare ido,
"Wacece ke?,ko bakyajin magana ne inata gyaran murya amma hankalinki yana can wani waje,ko abinda ya kawoki kenan,uhm?"
Dago fuskarta tayi jikinta har rawa yake tana kallon mutumin dayake gabanta ,ganin daga shi sai farin kyalle a kigunsa ga kuma ruwa na bin farar fatar jikinsa ne yasata kara tsorata da lamarin tsayawa a kusa dashi.
Saida ta bata jinkirin lokaci na wasu mintuna kafin ta fara magana cikin in-ina,
"U hmm ...dama anturoni nan ne aiki"
Saida yayi jimm da bayanin ta kafin ya sauke ajiyar numfashi tareda wani murmushin gefen baki yana karewa dukkan ilahirin surar jikinta kallo saboda yanayin yanda kayan da'aka yi mata kwalliya dashi suka dauki surar jikinta.
Karar kofar daya jine yasa shi tsayawa da abinda yace kafin yanufi kofar dan ganin waye ,wasu bayine yagani ajere kowa da kayan abinci a hannun ta,basu hanya yayi suka wauce cikin dakin tareda jerawa akan daddumar cin abinci.
Bayan sun juya sun fitane shima ya nufi wani waje a dakin domin saka kaya.Duk abinda yake fahreeyah natsaye a wajen da yasameta bayan fitowsrsa daga bandaki,ko motsawa batayiba kaman wanda akace za'a yankata.
Bayan yagama abinda zaiyine yazo ya zauna agaban kayan abincin,har sannan idanunsa na kanta,magana tafara mata cikin sanyin murya,
"Meyasa kike tsaye a wajen?zonan!!!"
Takawa tafara yi a hankali kaman mai tsoron tafiya har ta isa ga inda yanuna mata,duk da dauriya take na ganin ta boye bayyanar bugawsr zuciyarta ,amma duk wanda ya kalleta yasan tana cikin tsoro da fargaba,sunkuyar da kanta tayi tana jiran taji mai zai faru kuma.
Jikin ta ne yafara rawa sakamakon jin hannun sa akan nata hannun, dagowa tayi da fuskarta izuwa kan tasa fuskar, aikuwa idonta ne yayi arba da mayun idanuwansa wanda yazuba mata su ko kiftawa bayayi,wani murmushi gefen baki yayi mata kafin yace cikin wata sansanyar murya,
"Meyasa jikinki yake rawa ko ba abinda kikazoyi kenan ba?"
Koda maganar ta doki dodon kunnenta sai ya kasance maimak on jikinta yadaina rawa saima kara mazari daya sake yi, ganin hakanne yasashi sakin hannun ta tareda sake matsowa inda take,
"Saka hannun ki muci abinci"
"Ahh.....yallabai..na..koshi,naci kafin na zo"
"Baambayarki nayi ba umarnine na baki"
Hannun ta saka acikin abincin cikin sanyin jiki kafin ta kai ga bakinta.
Haka cin abincin yakasance,yazamana cewa idonsa yana kanta yayin da itakuma takasance a takure,bayan sun gama cin abincin ne fahreeyah ta dauki kayan abincin da nayyar fitar da su daga dakin, saidai kafin da tashi yayi saurin dakatar da ita,
"Kibarsu basai kin fitar da suba,in kika ajiye su gefe ma yayi"
Ajiyewar tayi kaman yanda ya umarce ta,tana juyowa kuwa tasake hada ido dashi akaro na biyu yana karemata kallo,
"Ke kyakykyawace sosai, menene sunanki?"
Cikin muryar sa da ta kashe mata jiki dazu yasake tambayar ta,
"Fahreeyah"
"Wow suna mai dadi,zo kiji wani abu"
Yafada yana mika mata hannu alamar ta zo,kwalkwalwar ta ce tatafi wani tunani na wucin gadi,game da sakamakon abinda zai faru idan ta amsa kiran dayake yimata, sannan rashin takawar ta izuwa gareshi dadai yake da fuskatantar hukunci daga wajen horo.
Share duk tantama da kuma wani fargaba dake jikinta tayi,tareda mikawa mai duka dukkan lamarinta ta hanyar jan jikinta har izuwa gaban sa,yazamana cewa cinyoyinsu na gogar na kowa saboda tsananin kusantar su da juna,hannunsa yasaka yana shafar gefen fuskar ta yayinda idanunsa suka sauka a kowane sako na jikinta,magana yafara mata cikin wani irin murya wanda ta sanya cikin wani irin yanayi.
"U hmm fuskarki akwai laushi sosai dafatan dai nine wanda yafara taba wannan lallausar fatar kohh"
Yafada yana dago da fuskarta izuwa ga tasa fuskar.Idonta ta bude wanda su ke rufe tun lokacin da ta matso kusa dashi wanda suka cika da hawaye masu dauke da ma'anoni da yawa,
"Lah Lah Lah,karki bata wannan fuskar mai kyau mana,"
Cikin maganar maza masu shakiyanci yake magana ,yayinda hannunsa kuma ya fara yawo a jikin ta.Duk abinda yake aikatawa ko motsawa fahreeyah batayiba sai sakar zuci da tunanin ta yake tayi"""ohh allah ya saheel kana ina? Yah Allah ka taimakeni agun wannan bawa naka,"""
Rintse idanunta tayi jin sanyi ya jiyarci fatar jikinta alamun babu wata sutura da tayi mata katanga da sanyin dakin sai rigar maman dake jikinta,"""ohh allah ohh allah,koda yake bani bace,sareena tace banice bace wannan wata daban acikin wata rayuwar daban,baneee bace,😭😭😭"'""
Sun dau wani lokaci yana shafa wasu sassa na jikinta kafin ,tsayawa yayi na wani lokaci kafin yakalli fuskarta da niyyar yi mata magana,duk da yasan cewa bazata kalleshiba bare kuma mai da masa martanin amsar sa ba ,amma hakan bai hanashi yiba"
"U hmm sanyi da almun yanaso yakama ki yakamata mu isa ga kan gado danna lura jikinki har rawa yake koh,"yana gama fadin abinda ke bakinsa ya sureta izuwa ga kan gadon dake cikin dakin.
Abinda yake shirin aikatawa ya fasa tareda kallon yanda jikinta ke fitar da wani irin turiri na zafin zazzabi ga kuma jijjiga da takeyi kaman an jona mata wutar lantarki.
A dadai lokacinne kuma aka bugo kofar dakin da karfin gaske kaman ana shirin cireta,nameemah ceh a tsaye a bakin kofar tana murmushi kaman wanda ta hadiye maciji,saida ta saita numfashinta ta hanyar furzar da wasu numfashi kamin ta taka har izuwa ga bakin gadon da su fahreeyah ke kwance.
"Dama abinda aka fadamin dagaske ne mai wannan baiwar take akan gadonnan,ko bataji umarnina bane na cewa,kar wata baiwa ta tako kafar ta izuwa ga turakar da aka saukeka"duk maganar tanayinta ne cikin zafin kishi irin na mata masu jin kansu,katsata yayi da maganar da take tareda boye razanarsa yace,"nima bansaniba kawai shigowa tayi tana wani salo najan hankali sannan tace aikota akayi,"shiru nameemah tayi tana nazarin maganarsa yayinda muryar mace ta katse mata tunani ta hanyar cewa,"ehh hakane ita da kanta ta shigo domin taga bata

Please Login or Register in order to submit comment