Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ta fara magana "kayi haquri ni inda wanda zan aura" kallon cikin idanunta yayi ta kawar da kanta

"Qarya bata kamaceki ba idan bakyasonshi ki fadamin gskiya"

Bazan iya aurenshi ba saboda bayada imani acikin zuciyanshi,,,

"Juwairiya banajin na taba furta Kalmar da take qarya kodan ceto rayuwata bale nayi miki qarya ki yarda da abinda na gaya miki da zuciya daya"

Kallonshi tayi. Tabbas bayada alaman qarya dan ko abdul tasan bata qarya koda zakasheshi ne

"Zanyi shawara" murmushi yayi "jalilah tazo wurinki dazu ko? Kai ta gyada tana murmushi sai kuma tayi dariya

"Lafia? Da gaske kai kakeyi mata kisto da kuma qunshi? Kai ya gyada mata tare da tashi "atashi lafia" ya juya kawai

Tafia yake yana tunanin taya shi ze nemi mata gashi wannan duk ta sanyashi surutu akan simple issue

Dan tsaki yayi duk yaji haushin juwairiya



_After a week_


Jalilah sai murna take zata kawo juwairiya ummi ta ganta


AJ ne ya daukosu juwairiya tana baya ya shigo ya nemi wuri yayi parking

Gaisuwa ce barorin gidan suke ta zubawa ba wanda ya kalla bale ya amsa ya nufi part dinshi su kuma suka nufi part din ummi

Cike da murna ummi ta tarbeta jalal yana zaune yana kallo murmushi sukayiwa juna suka gaisa


Fira suke da ummi Sama Sama baffa ya shigo suka gaisa ya nufi dakinshi

Ina zuwa juwairiya ummi ta fada


Kusa da ita jalal ya matsa yana murmushi "zan iya introducing dinki wurin mami as her inlow? Sunkuyar da kanta qasa tayi tana murmushi

Tashi muje,,, ba musu tabi bayanshi suka nufi part din mami

Zaune take tana karatun Qur'an sukayi sallama ta amsa tana kallonsu ya nemi wuri ya zauna


"Jalal lafia? Juwairiya ce na kawo ta gaidaki" dan tsaki tayi "ina ummin taka ne?

Abdul ne ze aureta,,,, murmushi tayi "shine ka wani shigowa gaba? Murmushi yayi ya tashi ya fice

Tashi mami tayi ta sanja wurin zama ta kira AJ tana son ganinshi


Shigowa yayi yaje kusa da ita ya zauna ba tare da ya kula da juwairiya ba

"Mami gani? Lafia? Mami ba komi ya yi magana cike da shagwaba

"Hmm toh tashi daga kan jikina juwairiya zata yi maka dariya" mami dan Allah ki daina

Naji tashi ka zauna

Ba musu ya tashi aiko suka hada ido da juwairiya da sauri ya juyo yana kallon mami murmushi tayi "jala ne ya kawota"

Kallonta yayi ta sunkuyar da kanta duk kunya ta kamata

Kaga ni bani wuri mai martaba yana jiranmu zasu gaisa


Hannun juwairiya mami ta riqe suka nui part din mai martaba



Sosai mai martaba ya yaba da hankalinta ya sanya mata albarka


Kyauta ta musamman mai martaba yayi mata sabuwar mota ce qirar vibe haka mami ta zuba mata gwala gwalai suka nufi part din ummi

"Au ashe tana wurinki? Toh sirikatace fa" murmushi ummi tayi "yanzu jalal yake gayama baffan jalal toh Allah ya Sanya alkairi


Jalal ne ya shiga "ummi zan koma school" toh kuma lafia kake wannan bata face din? Ummi ai naga biki soyawa mubarak naman bane

Ni na gaya maka hakan? Ummi ai biki bani ba

Murmushi kawai mami take ya karbi naman yayima ummi sallama ya fice..........
[25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴 JININ SARAUTA 🤴🤴





*Written by Hafsat MN*





IN DEDICATION TO
_AUNTY AMINA ALHASSAN_







Lace guda biyu da atamfofi ummi ta bata suka dawo part din mami


Kallonta ummi tayi tana murmushi "juwairiya nifa ba sirikarki bace ki daina jin kunya na" murmushi tayi

AJ ne ya shigo "mami zata koma school" tun yanzu? Eh zan tafi school din ne bros jalal nakeso ya tayani wani aiki kuma bazan dawo da wuri ba


"Toh shikenan ai zaka kawota idan maryam tazo ko? Murmushi kawai yayi


Barorin gidan mami tasa sukayi mata rakiya har mota

Tada motan yayi yana sanye da farin yadi ya sanya driving lens dinshi sai faman zuba qamshi yake

Gate din gidan aka bude mishi kafin yakai ga main gate din wayanshi yayi ringing yaga sunan ummi

Hello jalilah ya akayi? Ya abdul adalci kenan? Nifa nazo da ita

Sorry zan dawo muyi magana ya katse wayan

Kallonta yayi ta sakar mishi harara ya kawar da kanshi yana murmushi yaja suka nufi school din

A kusa da hostel din yayi parking ya juyo yana kallonta ta wani hade face "ya dai? Bansani ba kawai ka hana jalilah tamin rakiya kamar gunka naje" murmushi yayi "am sorry" kallonshi tayi daga still face dinshi dauke yake da murmushi tasa hannu zata bude motan ta fita yayi saurin dakatar da ita

Kafeshi tayi idanunta farare tas dasu wani murmushi ya sakar mata "meye abin fushi kinfison jalilah akaina kenan? Harara tayi mishi "zaka hada kanka da jalilah ne? Kai ya girgiza yana murmushi tare da kawar da kanshi

Kallonshi take a tunaninta baya ganinta ba tare da saninta ba ta saki wani sanyayyar murmushi kawai taga yayi dariya

Juyowa yayi tayi saurin kawar da kanta "bafa hanaki kallona zanyi ba kici gaba kawai" hannu tasa ta rufe face dinta ya shiga yi mata dariya

"Pls can I ask you? Kai ta gyada mishi "me bros jalal ya gaya miki har kika bawa zuciyanki haquri kika yafeni? Kallonshi tayi tana murmushi "komi be gayamin ba kawai nayi zuciyan muslunci ne na yafeka" girgiza kanshi yayi yana murmushi "kinga yanda qarya tayi miki kyau ko? Ga baki dayansu dariya sukayi


"Hmmm bros jalal he is very kind and jovial" kai ya gyada mata yana murmushi

Bari naje kasa salma tayi tunanin na bata "oh zaki tafi ki barni kenan? Bafa mami bace wannan

Dariya yayi ya fita yaje ya bude mata ya fito mata da kayanda aka bata ta dauka yana kallonta har ta shiga hostel din murmushi yayi yaja ya nufi male hostel

Kallonshi sukayi daka ganshi kasan yana cikin farin ciki

"Bros jalal typing nakeso kamin dan Allah"

Bacci nakeji "saifa kamin zakayi bacci"

Tsaki yayi "sai kamin dole"

"Bros jalal kaine babba dolene kayi haquri fa" sam be kula AJ ba ya shiga baccinshi sosai AJ yayi fushi yasan da mubarak ne jalal bazeyi bacci sai yayi mishi


2days su jalal basuga AJ ba kuma be kira ko daya a waya ba basusan cool AJ soyayya tayi dadi ya manta dasu fa amma kuma yana fushi jalal din


Zaune suke shida juwairiya tana sanye da wani material ya qara fito da kyauta sosai sai faman zuba soyayya suke


Jalal da mubarak ne suka shigo yana ganinsu ya wani bata rai

Kusa dasu suka qarasa "bros jalal shuru haka ba labari? Murmushi kawai yayi

Kallon AJ yayi ya zuba mishi harara aiko ba shiri yayi dariya ya matsa ta kusa dashi "meye na hararana? Kyaleshi yayi "bazakamin maagana ba? Eh "sai fa kayi" sai kamin dole

Wai wannan fushin na menene bros? Ai nasan kanku a hade yake

"Sweet muje" dariya jalal yayi "sorry idan inajin bacci bana iya typing ne shiyasa"

Harara yayi mishi "sis juwairiya kawo na tayaki aikinki kisa bros abdul zae daina fushi damu" bataso"


Dariya mubarak yayi "ka iya fitina wallahi" kallon mubarak jalal yayi wai mubarak yake cewa wani ya iya fitina? Hmmm lallai

Malam daina kallona,,, dariya jalal da AJ sukayi ganin yanda ya hade face kamar dukan jalal zeyi idan be dena ba



Juyawa jalal yayi AJ yayi saurin riqeshi "saifa ka tayani aikin nan ai ba fushi nayi ba" dariya jalal yayi ya karbi system din juwairiya ya qarasa typing dinda ta fara



Saida ya kammala ya miqa mata suka nufi wurin da zasu zauna


Cike da sallama tazo kusa dasu jalal sam jalal be daga kai ya kalleta ba


"Jalala Ibrahim............
[25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴





*Written by Hafsat MN*





IN DEDICATION TO
_AUNTY AMINA ALHASSAN_






_Afuwa gareku masoyana na samun tsaiko da nayi ba tare da nayi posting ba kasan cewar wani sha'ani da na shiga sai kuma ban haquri a bisa kuskuren da nayi_. _Page 96-100 bayada page number sai a gafarceni_






101-105






Ahankali ya dago yana kallonta ba tare da ya sake face dinshi ba, ga baki daya sai taji ta muzanta


Mubarak ne yayi mata magana "boyar Allah lafia?

Amm dama inaso muyi magana da jalal ne,,, toh ki fadi abinda yake tafe dake



Kallon jalal din tayi wanda tuni ya daina kallonta


"Jalal dan Allah idan bazaka damu ba zanso ka bani contact dinka idan na koma hostel zan kiraka sai muyi magana saboda naga kamar yanzu bakada time"



"Malama dan Allah zo ki tafi bama son surutu" amma jalal nace bakai ba ko? Wani tsawa jalal ya daka mata wanda ya sanyata fita hayyacinta ta juya da sauri


Murmushi mubarak yayi "hurt jalal me yasa kayi mata haka? Tsaki yayi ya tashi mubarak yabi bayanshi yana dariya

Kallonsu kawai cool AJ yake yana dariya har suka fice


Kallon juwairiya yayi face dinshi dauke da murmushi "bros jalal akwai zafi idan kikayi bincike mubarak ta taba duk shine ya janyo mata wannan" dariya juwairiya tayi


Lafia? Kaine ka bani dariya Allah" toh me nayi? Kai kake cewa bros jalal yanada zafi? Murmushi kawai yayi dan bayason tuna baya


"Hubbi na manta ban gaya maka ba gobe zan tafi katsina" wani kallo ya watsa mata


Menene? Meyasa biki gayamin ba? Sorry mantawa nayi fa,,, kawar da kanshi daga kallonta yayi "fushi kakeyi dani? Mummy zanje in diba fa" juyowa yayi yana kallonta "me ya sami mummyn?

Ahankali take mishi magana "kawai nayi missing dinta ne harda mafalkinta nayi shine nakeso nake naje na ganta" murmushi ya sakar mata


"Idan mukayi aure kenan kikaji kinyi missing dinta banida kwanciyar hankali har sai munje katsina? Dariya tayi

Nafa dade ban ganta ba,,, murmushi yayi suka shiga firan katsina


Washe gari AJ ya shirya ya gayawa mami zai tafi katsina kuma ze dawo gobe tayi mishi fatan alkhairi


Mamakin sammakonshi tayi cike da murmushi ta qaraso wurinshi "hubbi wannan sammakon fa? Hmm ai banaso ki tafi ki barni ne shiyasa

Dariya tayi "hubby shine kayi wannan sammakon? Murmushi yayi


Ga driver dinda zai tafi da motanki ni kuma zmuje a nawa ni da ke,,, murmushi kawai tayi mishi ta koma cikin hostel ta qarasa shiri suka dauki hanya



"Pls hubby ka rage wannan gudun katsina za muje fa" murmushi yayi ba tare da yayi mata magana ba ahaka har suka qarasa ta shiga bashi direction na gidansu



Sosai tsarin gidan ya burge AJ tun kafin su qarasa


Mai gadi ne ya bude muau gate suka shiga ya nemi wuri yayi parking tare da sauke ajiyan zuciya


Kallonshi tayi "hubby ka gaji ko? Kai ya girgiza mata yana murmushi bayan a agjiye yakejin kanshi dan be taba driving mai wahala ba irin wannan


Cike da tsari irin na manyan mutane ta fito da alama fita zatayi


"La hubby ga mummy ta fito" da sauri ta bude motan harda hadawa da gudu taje tayi hugging dinta

"Juwairiya tafiya haka ba sanarwa? Mummy kawai nayi missing dinki ne fa shine nazo"

Waye wancen? Oh na manta da baqo nake fa,,, harara tayi mata ta juya ta nufi ciki

Da sauri aka bude mishi parlour'n da yake waje aka saukeshi mummy sai faman fada takewa juwairiya


Mummy mantawa fa nayi,,, idan abbanki yazo sai ki gaya mishi mantawa kikayi

Mummy dan Allah ki rufamin asiri kice kece kika manta bani ba


Harara tayi mata aka hada abinci da snacks da juice aka kaiwa AJ



Zaune suke bayan laasar juwairiya sai faman roqon mummy take akan tyi haquri amma taqi suka nufi parlour'n abban yana yiwa juwairiya kallon mamaki

Juwairiya yaushe kika zo? Abba dan Allah kada kamin fada" murmushi yayi mummy ta tashi ta fita bata wani jimawa ba ta dawo tare da AJ cike da girmamawa ya gaida abban

"Halima wannan waye? Tamabayi juwairiya kaji" turo baki tayi "mummy dan Allah fa nace"

Au so kike nayi qarya? Baqon juwairiya ne kuma tare sukazo amma koni bata gayamin tare sukazo ba bale a tanadar mishi wani abu sai dan abinda muke da ya tarar"



Kallonta abban yayi "meyasa kikayi haka? Abba mantawa fa nayi" kai ya gyda suka qara gaisawa da cool AJ

"A garin nan kake? Kai ya girgiza ba tare da yayi magana ba

Kallon mummy abba yayi da mamaki a face dinshi

Daga wane gari kake?

Ahankali ya furta zaria


Okay toh sannu ko Allah yayi mana albarka

Murmushi kawai yayiwa abban tare da sunkuyar da kanshi

Kai asalin dan zaria ne? Sai a lokacin ya amsa da eh shima cen qasa yayi magana


Ya sunan mahaifinka? Ahankali ya dago yana kallon juwairiya

Kallonshi ya mayar gun abba "Alhaji Mahmud Yusuf"

A wane wuri kuke zaune acikin zaria?


Sunkuyar da kanshi yayi dan bazai iya fadan shi dan sarki bane


Kallon juwairiya abba yayi da alaman tambaya

"Abba dan sarki Mahmud ne shine ma da naje gaidashi ya bani wannan vibe din da kagani a parking space"


Kallonshi abban yayi ya qara sunkuyar da kanshi


Mummy kam aranta cewa tayi ba banza ba wannan rashin maganar



Ahankali ya dago suna hada ido da abba ya sunkuyar da kanshi

Ya sunanka? "Abdul jabbar"


Murmushi abban yayi "masha Allah, Allah yayi muku albarka ya sanya alkhairi" mummy ce kawai ta amsa a bayyane

Shuru ba wanda yake magana sai abba ne ya katse shurun "juwairiya sai ki rakashi ya samu ya huta ko?

Tashi tayi mummy tayi mata harara "oh mummy me nayi kuma daga zuwana kuma fa saboda ke nazo"

Da gudu ta shiga ta fada kan jikin mummy

"Jawahir lafia? Mummy na gaji ne" murmushi tayi toh tashi ki gaida yayanki

"La aunty juwairiya yaushe kika zo? Dan Allah ni bansani ba kawai daga zuwa kitso shine kikayi zamanki"

Qawatace fa tazo mukaje tare kinga bazan tafi in barta ba

Murmushi tayi mata sukayi hugging din juna


Jawahir ga mijin juwairiya nan fa

Juyowa tayi suka hada ido da AJ

"Wow aunty juwairiya wallahi you are lucky, kin samo mai kyau saura ni na samo wanda ya fishi"

Tashi abban yayi ya nufi dakinshi yana murmushi


Alama juwairiya tayi mishi da su tafi


Zaune suke a parlour'n da aka saukeshi sai faman kallon jawahir yake tana zuba...................
[25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴





*Written by Hafsat MN*





IN DEDICATION TO
_AUNTY AMINA ALHASSAN_






106-110






Jawahir ki barshi ya huta mana,,, aunty juwairiya wulaqanci zakimin? No ba wulaqanci bane a gajiye yake kinga yana buqatan hutu"

Okay naji amma zan tambayeshi kafin in tafi nima zanyi wani aiki ne,,,

Murmushi yayi mata "pls kanada qanwa mace? Kai ya gyada mata

Ya sunanata? "Jalilah" ya bata amsa a takaice "okay yaya fa? Kai ya girgiza mata

Sorry lissafin ku nawane saboda anan gidan kaga ni da aunty juwairiya ne kawai

Dan murmushi yayi "ni da jalilah ne kawai" dariya tayi kace kawai we are equal

Tashi tayi "bros abdul zan baka saqo ka kaiwa jalilah dan nasan zamu zama qawaye idan kukayi aure amma yaushe zaka tafi? "Tomorrow" kai ta gyada ta fice

Kallonshi ya mayar gun juwairiya "sweet meyasa kika korarmin qanwana? Habibi bakasan jawarib bane yanzu ba gajiya zatayi ba koda cewa akayi ta kwana anan tana maka questions bazata rasa abin cewa ba


Murmushi yayi suka ajiye zancen jawahir suka nemo nasu daga inda suka tsaya



**********************************



*8:30pm* jalal da mubarak ne a dakin ummi sai faman fada sukeyi ba wanda ummi ta kula daga cikinsu jalilah sai faman kallonsu take


"Allah baka isa ka hanani rawan gaban hantsi ba anan zan kwana bazan koma school ba, kai kenan mutum ko yaushe sai yayita faman hawa kan raayinka toh yau ba inda zani"


Kawar da kanshi yayi daga kallon mubarak din ya mayar gun ummi "ummi zan tafi" kai kawai ta gyada mishi ya tashi ba wanda ya kalli wani daga cikinsu

"Ya mubarak kayi haquri kuje mana" harara yayi mata tayi dariya "ya jalal muje nayi maka rakiya yau fitina ya mubarak yakeji" tare suka fito shida jalilah wani sanyayar iska ne yake kadasu


Cike da murmushi take kallonshi "ya jalal fushi kakeyi har yanzu? Ko kallonta beyi ba "ya jalal fa? Ta fada kamar zatayi kuka


Juyowa yayi yana kallonta "wai ke bazaki daina wannan shagwabar ba ko? Toh meye abin kuka anan? Kawai saboda kinyi magana na kyaleki sai ya zama abin shagwaba? Aiko tasa mishi kuka


Tsaye kawai yayi yana kallonta sai faman kukan shagwaba take mishi so kawai take ya lallabata shi kuma ya zuba mata ido


Ganin ba gajiya zatayi ba ya sanya jalal fara magana badan yana raayin maganar ba "jalilah rakiyan nan yamin tsada dan Allah ki koma banason wannan kukan"

Kusa dashi ta qara matsawa "kawai dan na tambayeka shine zaka shareni? "Sorry, ba fushi nakeyi ba kawai dai na fahinci lectures din gobene bayaso yayi attending" turo baki tayi "toh muje ni sanyinnan bayamin dadi

Murmushi yayi sukaci gaba da tafia


Kallonshi yayi ya kawar da kanshi da sauri

Jalilah ce ta janyo hannunshi "ya jalal mai martaba muje mu gaidashi" taja hannunshi da sauri


Ba yanda jalal ya iya suka qarasa gaban mai martaba


Har qasa taje dole jalal yabi bayanta "sannu da zuwa abba" murmushi yayi "jalilah ina zuwa haka? "Ya jalal ne zai tafi shine zanyi mishi rakiya" kallonshi yayi ya sunkuyar da kanshi


Murmushi yayi ya gyada mata kai suka tashi tana riqe da hannunshi sukaci gaba da tafia


Kinga rakiyan ya wadatar ki koma,, ya jalal gobe zaka so? Jalilah sai na gama exam gaskiya" ido ta zare

Ya jalal Allah yayi nisa, murmushi yayi "zanzo before exam din "yafi gaskiya" murmushi yayi ya zame hannunshi daga nata ya juya

Hannu ta daga mishi yayi mata murmushi kawai


*main gate*


Jeep ce black tana dauke da tambarin masarautar

Da sauri ya qaraso kusa dashi "Allah ya taimaki magajin sarki, umurni daga maimartaba zaa saukeka a makaranta"




Kallon jeep din yayi wanda yasan sarkine kawai yake shiganta


Ba musu ya shiga aka rufe direct sai school


Kwance yake shi kadai ga baki daya duk rashin mubarak a dakin ya sanyashi jin wani iri

Call ne ya shiga wayanshi yaga new number kuma number din ba wani wahalan dauka akai

Cike da natsuwa ya daga tare da kwarara sallama

Shuru yayi jin voice din mai martaba

"JALAL" ya kira sunanshi cikin wani yanayi kamar na cikin damuwa


"Naam"

"Duk da ban taba daukanka a matsayin dan da na haifa ba na cancanci girmamawa a wurinka, jalal ban bayar dakai ba saboda bana sonka saidan kyauta da abinda kafiso, Kaine na farko da aka fara haifamin a lokacin da nake cikin tsananin neman ganin jinina wannan ne yasanya na badaka saida hakan ya sanya mana tsanata acikin zuciyarka wanda har ya shafi hafsa da ba hannunta aciki,, jalal zan baka zabi acikin tsarina babu cutarwa inaso ka zabi rayuwar da kafiso ni kuma zan baka wannan rayuwar koda hakan zai rabani da komi nawa harda rayuwata"


Duk wannan jawabin na maimartaba ba abinda ya Sanya jalal face zubar da hawaye


Cikin rawar murya ya fara magana "abba dan Allah ka yafeni wallahi ni sam ba wannan ne araina ba, abba kunya nakeji nayi muamala daku saboda ko kasan banason su baffa suji wani abu aransu wanda ni a wurina sam ba haka bane

Abba na samu yata da tarbiya wanda nasan ba kowa zeyi dace da iyaye na gari irin nawa ba ban tabajin hakan araina a matsayin cutarwa ba sai bata da kayiwa rayuwata ka badani ga iyaye na gari,,, abba dan Allah kayafeni zan gyara kuskurena abba ka yafeni dan Allah"


Sosai mai martaba yayi mamakin zancen jalal dan sam beyi tunanin hankalin jalal din yakai hakan ba sosai yayiwa Allah godiya ganin jalal sam bai kasan ce cikin masu butulci ba


"Allah ya albarkaci rayuwarka abdul jalal"


"Ameen" ya furta ahankali "abba ka yafeni din? Murmushi cike dajin dadi a ranshi "sam bakayi laifi ba jalal haka akeson da nahalat ya kasance " ajiyan zuciya ya sauke sukayi sallama ya ajiye wayan......
[25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴





*Written by Hafsat MN*





IN DEDICATION TO
_AUNTY AMINA ALHASSAN_






111-115






Shuru yayi na tsawon lokaci yana tunanin toh idan har abba yaji hakan aranshi mami fa? Ya zataji aranta?

Shuru yayi yana tunani har yayi bacci


Washe gari ya nufi lecture hall bashi ya fito ba sai 2 ya nufi hostel yayi wanka ya shirya ya nufi cikin gari




Tsaye ya sami mubarak yana waya sam be kalleshi ba ya nufi part din mami



Sallama yayi ta amsa tare da zuba mishi ido



Kusa da ita yaje ya zauna ya sunkuyar da kanshi

"Jalal lafia? Kallonta yake kamar zeyi kuka

"Mami dan Allah ki yafeni nasan banyi dai dai ba dan Allah ki yafeni wallahi injin kunyar ummi taga nayi miki kallon mahaifi sai nake ganin kamar na saka da sharri akan alkhairi ne"

Murmushi tayi aranta tace "tabbas jalal yafi abdul jabbar shagwaba" a zahiri kuma cewa tayi "jalal hakan da kayi shine dai dai ban dauki hakan a matsayin komi ba koda a hannunmu ka tashi ai bazaka wuce hakan ba dan ko yanzu ba abinda abdul jabbar zai nuna mana dan har ka fishi da ilmin addini"

Sunkuyar da kanshi yayi tare da sauke ajiyan zuciya


Shuru na tsawon lokaci ba wanda yayi magana daga cikinsu


"Jalal kana buqatar wani abu ne? Kai ya girgiza mata "murmushi tayi "toh ai sai ka tashi kaje ko?

"Mami korana kike yi? Kallonshi tayi sai kuma ya bata dariya "jalal ai yanzu ummin jalal zatazo nemanka gara kaje ko?


Tashi yayi da alaman fushi

Har ya kusa fita ta kirashi ya dawo

"Jalal yanzu fa ka gayamin kanajin kunyar taga kayimin kallon mahaifiya shine dan nace ka tafi kake fushi?

Mami ai naga bakya yiwa abdul haka

Abdul din ai nawa ne kai kuma fa? Murmushi yayi ya tashi kawai ya fice



Zaune ya sameshi a dakin ummi sai faman cin abinci yake yaje ya gaida ummi

"Ummi baffa ya fita ne?

Eh ya tafi kafancen

"Ummi wurin me? Wurin aikin da yake gabanshi mana


Kusa dashi mubarak yaje ya zauna

Amma ai ka ganni ko? Ko kallonshi jalal beyi ba ya zauna ya fara cin abinci kawai har ya kammala baya magana da kowa

"Ummi zan tafi school"

"Mubarak tashi ku tafi" ba musu ya tashi suka fice amma jalal baya mishi magana koda ya mishi magana


*Main gate*


Kamar jiya suna qara sowa aka bude jalal ya shiga kawai haka mubarak ya shiga shima sai hostel aka saukesu



Zaune suke ba yanda mubarak beyiwa jalal magana ba amma yaqi kulashi har mubarak din shima yayi fushi ya kyaleshi


Har dare ba wanda yake yiwa dan uwanshi magana


Girki jalal ya kammala yaje ya siyo coke yazo ya zuba a plate ya turawa mubarak aiko ya ture abincin har ya zube

"Bazan ci dolene nima ka kyaleni"

Ya tashi kawai ya fice sosai ya bawa jalal dariya


Tashi yayi yabi bayanshi ya sameshi zaune sai faman fushi yake

Dariya yakeso yayi amma ya jure


"Meyasa zaka zubar da abincin idan bazakaci ba?


Ko kallonshi mubarak beyi ba "tashi mu tafi" bazani ba

Sai fa kaje "ai sai kamin dole"

Janyo hannunshi jalal yayi da qarfi aiko yasa qara

Kallonshi jalal yayi "wai kai meye haka? Ni da na kwana ni kadai banyi fushi sai kai dan kamin magana naqi kulaka?


Harara yayi mishi "sai fa kaje kaci abincin nan" tsaki yayi ya nufi cikin block din nasu

Sai faman cin magani yake jalal ya tasashi gaba da abinci "dolene sai naci abinci? Murmushi jalal yayi "idan bakaci ba meye amfanin wahalan da nasha kafin nayi girkin? Ko a naka tunanin saboda inajin yunwa ne nayi girkin?





*kuyi haquri ban samu nayi typing da yawa ba*




*written by mum haneef*
[25/12, 14:04] Hassan Atk: 🤴🤴JININ SARAUTA 🤴🤴





*written by Hafsat MN*





IN DEDICATION TO
_AUNTY AMINA ALHASSAN_





116-120






Harara yayiwa jalal ya kawar da kanshi ya tashi ya zuba mishi wani abincin ya bashi


Sam mubarak be wani cin abincin ba yace ya qoshi "wai mubarak me kakeyi haka ne? Wannan abincin ne bazaka iya cinyewa ba? Harara ya aikowa jalal


Tashi jalal yayi da alama fushi yayi ya fice

Tsawon lokaci mubarak bega jalal ya dawo ya kirashi a waya yayi rejecting

Tashi yayi ya shiga nemanshi amma ba labarin jalal

Wuri ya neman ya zauna yana tunanin ko jalal ya tafi gida ne


Haka yayita faman nemanshi amma ba labari dole ya haqura ya koma ciki


Kallon mamaki yayiwa jalal dake zaune yana karatu


"Amma kaga
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment