Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[03/12 23:02] Meela Adeel: *GUMIN HALAK...*馃挵3

*Batul Mamman*馃挅
An dauko wannan littafi daga shafin www.dlhausanovels.com.ng ku ziyarci shafin na www.dlhausanovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from www.dlhausanovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



Jirgin safe Alh Sule Chanji ya biyo yana ta tararrabin me zai tarar a gidan. Da shigarsa ko sama bai hau ba yaje dakinsa ya huta yayi wurgi da jakarsa da babbar riga ya sake ficewa. Baya ya zaga dakin BB yana kwala masa kira rai a bace.

Haj Mara tana ji ta fito da sauri don tasan zuciya irin ta mijinta. Kafin ta karaso ya banka kofar dakin BB yana bacci yaji wani mugun bugu domin kuwa da kafa mahaifinsa ya haure shi a ciki.

"Tashi mutumin banza wanda bai san inda ke masa ciwo ba. Yanzu Babawo har kayi girma da wayon danne mace ka gwada mata karfi? Lalacewar taka har ta wuce ace kana bin mata sai dai ace kana yiwa mata fyade? Ni kuwa me na rageka dashi? Tarbiyya ko ilimin boko dana addini"

Tuni BB ya koma bayan Haj Mara yana rike da cikinsa da ya kulle saboda harbin da ya sha. Alh Sule bai hakura ba ya sake yowa kansa tayi saurin tarewa.

"Haba, haba Alhaji! Kashe min yaro zakayi akan wata mai aiki"

Dariyar takaici yayi dama ita akan 'ya'yanta musamman BB kowa bai isa ba.

"Dole kice haka mana tunda ita mai aikin uwarta ba nakuda tayi ta haifeta ba. Nuna tayi a bishiya suka tsinkota ga dukkan alamu" ya fada tare da juyawa zai fita sai kuma ya dakata "ki sameni a mota muje asibitin na dubata. Idan taji sauki har gidansu zamuje kuma wallahi ko kunki ko kunsu Babawo sai ya aureta"

Haj Mara ta tafa hannu alamun dama na fada dinnan "Ahaf ai na sani, to ka makaro don tun jiya na mayar da ita kauyensu"

A harzuke ya juyo zuciyarsa na tafarfasa.
"Kika yi me?"

"Nace tana gidansu. Haba ka shigo babu neman karin bayani duk zaka hatgitsa mana gida. Abin nan duk rashin fahimta ne"

Tsayuwarsa ya gyara yana kallon yadda take wani kare danta kada yayi yunkurin dukansa
"To fahimtar dani"

"A dakin nan na ganta kwance shine nayi zaton wani abu ne ya sameta. Sai da na bincika ashe sata tazo yi masa shi kuma sarkin zuciya yayi mata duka. To ni bazan iya zama da barauniya ba shine na mayar da ita"

Daga bayanta BB ne yake dariyar shakiyanci jin mahaifiyarsa tana gilla karya. Alh Sule yayi murmushi mai ciwo
"Kinga dan naki ma dariya yake miki saboda yaji kina sakin kwai a gabansa. Kukanki lokacin da kika kirani ya isheni hujjar da zance yanzu karya kike yi. Ki gama kwana-kwanar kizo muje garin nasu. Idan mun dawo sai kiyi min bayanin dalilinki na fita ba da izinina ba"

"Alhaji!"

Bai saurareta ba ya fita ta bi bayansa da sauri. A bakin bene ta same shi zai hau sama

"Ko aurena ne zai mutu bazan taba kaika garinsu Mawadda ba. Na riga na bata kudi har dubu ashirin ga kayayyakin sawa. Magana ta riga ta mutu sai dai a kiyayi gaba kawai"

Rasa abin cewa yayi. Wai dubu ashirin. Ko dubu dari biyu ta basu ai bazai zama fansa ga mutumcin 'yarsu da aka zubar ba. Ransa ya kai kololuwar baci har ya rasa matakin dauka. Yasan Mara bata da kirki amma baiyi zaton harda rashin hankali da tunani ba.

"Ni dai na aurar da yarana mata duka ban taba jin wani labari mara dadi game da mutumcinsu ba. Har izuwa yanzu Allah bai taba bani ikon yin lalata da 'yar kowa ba. To Alhamdulillah. Ke da danki ku jira sakamako. Shi sharri dan sakone. Idan ka aike shi ya isar da sako sai ya dawo gareka. Ki rubuta ki ajiye lokaci shi zaiyi muku alkalanci ke da shi da yarinyar da kuka cuta" daga haka ya haye sama abinsa sai karar kofa taji garam.

Tsaki tayi ko a jikinta. Tunda dai ya bar maganar aje a haka.

"Alkhairi zamu gani har duniya ta tashi mugun fatanka bazai bimu ba"

Babawo kuma aure zata masa kafin ya sake sakata a tsaka mai wuya.
******

*Asalin Mawadda*

Mal Fatihu Wali dan kauyen Tariwa ne ta cikin karamar hukumar Bebeji a jihar Kano. Sana'arsa dinkin hula wadda wani dan kasuwa a Kwari yake zuwa sara lokaci zuwa lokaci. Sai kuma 'yan garin wani zubin. Idan babu cinikin hular yakan taba noma da kiwo.

Auren saurayi da budurwa sukayi da Haule. Suna zamansu lafiya Allah Ya azurtasu da 'ya'ya mata har hudu ya dauki soyayya ya dorawa iyalinsa.

Wata rana kanwar mahaifinsa taje ta sami baban nashi da kuka tana rokon ya taimaketa yasa Fatihu ya auri babbar 'yarta Sa'ade. Koda ya tambayi dalili ashe wani ne daga dangin babanta yake neman aurenta iyayen suka hana saboda marainiya ce ba idon uba kuma a cewarsu babarta tana da farar kafa don suna aure komai nasa yaja baya ciki kuwa harda lafiya da tayi masa karanci har tayi ajalinsa.

"Yaya Wali yarinyar nan bana shekararta daidai har goma sha tara. Habaici babu irin wanda ba'ayi min. Shine naga nima ba 'yan uwa na rasa ba. Don Allah kasa baki Fatihu ya aureta tunda sauran duk ta girme musu shine dai zai dubi zumunci ya taimaki 'yar uwarsa"

Mal Wali yayi shiru yana nazari. Baya son shiga sabgar gidajen 'ya'ya saboda rike girmansa. Sai dai ganin hawayen 'yar uwarsa ya taba masa zuciya. Haka ya kwantar mata da hankali sannan ya umarci Fatihu da aurenta. An kai ruwa rana dai saboda shi Fatihu baya son matsawa matarsa tunda suna zaman lafiya. Ita kuma Sa'ade har yanzu Balarabe take so dan wan mahaifinta duk da rashin mutumcin da ake yiwa mamanta.

Haka dai akayi auren. Tsakaninta da Yaya akwai girmamawa sosai amma fa bata ragawa Fatihu ko kadan da farko. Abu na Allah zama yai zama sai gashi sun dinke tamkar tsofaffin masoya. Ba jimawa sai ciki nan fa soyayya ta karu. Ta haihu lafiya aka sakawa yarinya suna Mawadda.

Wata rana a lokacin Mawadda tana da shekara daya da rabi kawar Sa'ade tazo daga Misau inda take aure. Suna hira take cewa "Oh Sa'ade kamar ba ke bace mai cewa idan aka aura miki Fatihu sai kinyi ajalinsa in bai sakeki ba"

Sa'ade tayi murmushi tana cigaba da yiwa Mawadda tsifa "ke dai bari...."

Iya abinda Fatihu yaji kenan ya juya da ledar hannunsa mai cike da magwaro da aka bashi ladan aikin lodi da sukayi a gonar wani. Ganin Sa'ade ce da girki shine ya kawo ta raba yaji wannan mummunan kalami.

Baiwar Allah Sa'ade ta cigaba da cewa kawarta "....kullum nayi sallah sai nayiwa Iya addu'a saboda ita tayi sanadin hadani da Malam. Ina son shi..." ta rufe ido da tafukan hannayenta wai ita kunya.

Dariya sukayi su biyun harda tafawa suna ta yabon mazajensu.

Fatihu kuwa bakinciki kamar ya kashe shi. Ashe duk zaman nan da son da yake mata ita kashe shi take son yi kila ta komawa tsohon saurayinta wanda akace yaki aure har yau saboda ita. Tsabar takaici har kuka yayi.

Da yamma ya dawo Sa'ade ta tashi ta dauko masa ruwa don bata ma san ya shigo dazu ba. Kwanon shan ya tankwabe a hannunta ya mika mata hannu.

"Kwanto min 'yata ki tafi gida na sakeki saki uku"

Gabanta ne ya yanke ya fadi ta dafe kirji sai kuka
"Malam me nayi maka haka da zafi?"

"Kinfi kowa sani. Kafin ki kasheni dai gara na sawwake miki kije ki auri wanda kike so"

Ta ma rasa gane kan zancen shi kuwa ya hauta da fadan ta fice masa daga gida kuma ta bashi 'yarsa. Bayani taso yi masa don duk yadda akayi yaji hirarta da kawarta ta dazu amma yaki saurara. Yaya tana ta bashi hakuri ya daka mata tsawa itama. Haka Sa'ade ta durkusa tana ta ban hakuri amma bakin alkalami ya bushe. Maganganun da ya rinka fada mata cikin bacin rai yasa ta kwance goyon ta dangwarar masa da Mawadda a kasa. Yarinya ta hau kuka ko kallonta batayi ba saboda zuciya ta fice. Yaya ta dauketa zata bita yace idan ta fita kada ta dawo.

Gidansu kawarta ta ta fara zuwa tana kuka ta sanar da ita yadda sukayi. Ta tausaya mata tare da yin tir da bakinta da ya tado zancen. Daga nan suka wuce gidansu Fatihu suka sanar da iyayensa. Rayuka dai sun baci ranar musamman nasa. Balle da akayi masa bayanin karshen maganar gashi yayi hukunci cikin fushi.

Da kyar aka shawo kan Sa'ade ta karbi 'yarta don tayi fushi sosai da abinda yayi mata. Bayan ta yayeta aka mayarwa Yaya ita ta rike hannu bibbiyu. Mawadda ce take kiranta Ade shine sunan a hankali ya bita.

Sai bayan shekara uku da mutuwar aurenta sannan ta sake aure da tsohon saurayinta dai Balarabe. Iya bata so ba kamar yadda iyayensa basa so don ko auren fari baiyi ba sai dai ya kafa naci. Kano ya kai matarsa inda yake aikin walda.

Da farko kamar abin arziki suke zaune kalau. Daga baya ta gane mijin nata maketaci ne. Dan kudinsa a cikinsa yake karewa. Yaci banza yaci hofi. Shine teburin mai shayi shine gaban tukubar tsire. Iyalinsa kuwa kullum suna fama da garau-garau.

Da wahala ta ishi Ade sai ta fara kitso. Kan kace kwabo unguwa ansan da zamanta tana samun 'yan canjinta. Ganin ta soma samun sukuni wanda shi a wautar Balarabe mace tayi ta kwantar da kai gaban miji yana hura hanci shine aure. Sai cewa yayi mata na cika masa gida. Kitson nata sai ya koma bin gidajen mutane nan ma yace ta fiye yawo ga yaransu ba kulawa sosai. Ta hakura ta koma wankau yace danshi ya soma kama gidansa kada sanyi yayi musu illa. Surfe da dakan su yaji yace karar daka tana saka masa ciwon kai. Tuni hakurinta ya kare tace dole ta fita nema ko don yaran suyi karatu. Rigimar yau daban ta gobe daban har dai auren ya mutu shine ta fara aikatau. Shi kuma sai yanzu yake ta neman shiri a mayar da auren taki
******

Wurin shadaya ta gama aikinta na safe har tayi wanka tana shafa mai taji 'yar wayarta na kara. Ta dauko kafin ta dauka duk da rashin boko yau da gobe ta gane sunan Baban Mawadda a wayarta saboda da ita Mawadda take kira su gaisa. Zuwanta Bebeji gidan surukanta kuma kawunta kwanaki da akayiwa autanta kaciya har Tariwa taje aka sanar da ita Mawadda tana Kaduna aiki. Bata ji haushi ba don tasan ba kiyayya bace tasa aka turata. Duka 'ya'yan Yaya dake dakin aure sunyi kafin a aurar dasu. Yadda tasan zafin nema bata so 'yarta ta zama mai matacciyar zuciya ba. Indai zata sami gidan mutanen kirki babu matsala. Aikin da sukeyi ba kwadayi ke kaisu ba sai neman halak kuma kowa da inda Allah Ya rubuta masa abincinsa. Yanzu da taga wayar a zatonta Mawadda ta koma gida ne tunda biki ya gabato.

Da sallama ta dauka sai taji muryar dan uwanta tsohon masoyinta Fatihu. Gaishe shi tayi ya amsa muryarsa a karye alamun damuwa.

"Sa'ade do Allah idan zai yiwu kizo gida cikin satin nan"

Zuciyarta ta harba a take hankalinta ya tashi tasan ba lafiya ba.
"Ita wannan din ina take?" Ta fada a sanyaye.

Sarai ya gane wa take nufi tunda bata fadin sunan Mawadda. Kallonta yayi dukunkune a jikin Yaya tana ta rawar dari. Asibiti zasu je dama saboda zazzabin tun jiya yaki sauka ga sambatu tanayi ko yaya taji sauti mai dan kara ta rinka buge-buge kenan tana neman agaji.

"Bata da lafiya ne yanzu ma asibiti zamu je." Ya amsa a raunane.

Mawadda daga kwance da ta fuskanci da wa ake wayar cikin kuka ta fara cewa "Ade kiyi min addu'a ji nake kamar zai biyoni. Kamar mutuwa zanyi"

Da sauri Baba ya bar dakin sai dai Ade ta riga taji. Kuka ta saka masa tana rokonsa ya fada mata wane irin ciwo ne yace sai tazo. Bai bari ma ta gama magana ba ya katse kiran shima damuwa da bakinciki suna kara baibaye shi.

Ade kuwa da kuka ta fita daga dakinsu hankalinta a tashe sosai. Cikin gidan ta nufa 'yan uwanta masu aiki sunata tambayar ko lafiya ta kasa amsawa. Tana shiga falo tayi sa'a Sakina ta fito cin abinci. Har gaban tebur din taje ta durkusa daga gefe tana sharar kwalla.

"Umman Abbati don Allah ina son tafiya gida. Yanzu baban Mawadda ya kirani bata da lafiya sosai" kuka ne ma yaci karfinta ta kasa bayanin yadda taji muryarta.

Cikin halin ko in kula Sakina tace "Tohhh wace Mawadda kuma?"

Tsabar tashin hankali yau har sunan 'yar ta fada ashe.
" 'Yata da nace miki zatayi aure jiya"

Dariya sosai Sakina tayi tana kada kai ta mike tsaye tana salati "Amma Ade kin raina min hankali. Jiya wato don nace kwana shida na baki na zuwa bikin shine zaki ce bata da lafiya. Nufinki na barki ki tafi ni da ganinki sai an gama biki sai kiji dadin cewa jinya kika tsaya ko"

Ade ta bude baki tana kallonta kafin ta daure tace "idan baki yarda ba ga wayar ki duba da kansa ya kirani duk da bama waya. Yarinyar nan cewa take nayi mata addu'a mutu....wai mutuwa zatayi" sai sautin kukanta ya karu.

Kankance ido Sakina tayi ga masu aikin gidan suna saurarensu.
"Nafi karfin ki kawo min shirme irin wannan na yarda. Idan lokacin da na baki ne yayi kadan kije zan kara miki ya koma kwana goma ince ko ya isa"

Kan Ade har sarawa yake ba don fargabar halin da 'yarta ke ciki ba yanzu sai tsabar wulakancin uwardakinta. Wai shin duk abinda ya shafi rayuwar masu aiki ba shi da mahimmanci? Su ba mutane bane kamar kowa. Basu isa su kawo uzuri ba sai a nemi bin diddigi saboda kawai an rainasu? Da wata mai fada ajin ce tana kawo uzurinta za'a karba kila har a bita garin nasu don neman suna. Iyakar bacin rai tana jinsa a wannan lokacin.

" 'Yata ta cikina zan yiwa sharrin ciwo don ina son zuwa gida? Ba ni na kawo kaina ba har sai nayi haka idan tafiya nake son yi?"

"To wa ya sani ne? Ku maganarku ai ba abar yarda bace. Daga magana dake jiya yau zance ya sauya"

Juyawa tayi zata koma daki ta hada kayanta ta tafi Sakina ta dakatar da ita.

"Idan kika tafi kada ki dawo don a satin nan zan nemi wata"

Ade ta share hawaye "To Allah Ya baki daidai dake. Idan nayi miki wani abu saboda yanayi na zaman tare ki yafe min. Na barku lafiya."

Fita tayi Sakina tana jin kamar tace ta dawo amma har ranta gani take kawai karya take yi. Sai da ta tattaro kamai nata ta dawo falon tayi sa'a tana nan

Tace "Albashina nazo karba na watan nan zan wuce"

Sakina ta tafa hannu "wannan kuma kinyi kadan wata bai kare ba"

Ba tsoro a zuciyar Ade bare kara tunda tayi a baya ansa kafa an shure.
"Yau kwananmu goma sha tara da karbar wancan albashin. Na iya kwanakin da nayi aiki zaki bani"

Mai shararsu Sakina ta nuna da yatsa tace ya kira mata sikuriti tana ganin Ade abin nata harda wulakanci kuma.

Jakarta ta gyarawa zama dama sauran manyan suna bakin kofa guda biyu "basai an kirasu ba zan tafi. Amma ina so ki sani ba kullum ake kwana a gado ba. Zabin Allah ne ya kawoki nan ba iyawarki ko dabara ba. Hakkina kuma ki rike zan karba ranar da baki da kudin biyana."

Tana kaiwa nan ta fita sauran masu aiki suna biye da ita wasu na bata hakuri wasu na mata fatan alkhairi. Godiya tayi musu ta sabi kayanta tayi waje.

Har ta isa tasha tana mamakin hali na wasu masu kudin. Indai haka kudi yake sa zuciya ta bushe daga tausayin na kasa bata fatan samun wannan arzikin. Arziki irin wanda zai sa wani ko wata ta tafi da ita a rai kwatankwacin yadda ta tafi da Sakina tana mai jin zafi tare da neman sakayyar Allah akan yanayin zaman da sukayi.
******

Lokaci yana ta tafiya har uku da rabi kanin Baba da yake da akori kura ta daukar itace bai iso ba. Gudun tonon silili Baban ya nemi alfarmar ya kaisu asibiti yace dama yana hanyar zuwa garin yau. To gashi nan shiru har yanzu. Shima yana can ashe duk ya damu sai dai babu yadda ya iya yana jiran cikon kudinsa daga wurin wanda ya kaiwa iccen. Da kudin zaisa mai a tsohuwar akori kurarsa sannan ya hadowa iyalinsa cefane. Tun safe yake gidan ance maigidan bai tashi daga bacci ba shine fa yake ta jira. Daga karshe hakuri ya kira dan uwansa ya bashi saboda bashi da halin tahowa a ranar. Ya kuma san tunda Mal Fatihu ya nemi alfarma lallai ciwon Mawadda ba na wasa bane.

Tun kafin ya gama bayani Baba yaji idonsa yana neman tara kwalla. Daga zuwan Mawadda zuwa yanzu kwana biyu kacal bai san adadin hawayen da ya zubar ba. Bakincikin halin da suka tsinci kansu yake yi saboda talauci. Yau da shi wani ne da tuni 'yarsa tana asibiti ana bata kyakkyawar kulawa shi kuma yana can ofishin 'yan sanda tare da dan iskan da yayi mata fyade fada sai inda karfinsa ya kare. Yanzu kuwa samun lafiyarta kadai ne a gabansa. Tsoronsa bai wuce firgicin da take yawan shiga ba da sambatu.

Har kofar gidansa achaba ya ajiye Ade da kayanta niki-niki. Tana ta adduar samunsu basu riga sunje asibiti ba. Kafin ta gama sauka Baba ya fito yana ganinta gabansa ya fadi. Baiyi zaton zata zo yau ba. Yanzu me zaice mata? Jikinta a sabule ganin yanayinsa itama ta tambaye shi ko sunje asibitin.

Har wani kwarjini tayi masa na dole da kyar ya iya cewa mota ce babu. Ainihin abinda ya hana samuwar motar garesu dama bai wuce yana gudun fita titi nemanta ba. Yasan duk wanda ya ga ya kawo mota kofar gidansa zai sha tambayoyi. Kauye kuma da bin kwaf baza'a dade ba yasan gaskiya zata fito a tsangwami 'yarsa.

Dan acaban Ade ta roka akan zata biya shi ya samo musu mota a bakin titi. A ranta tana cewa abinda zai hana Malam zuwa neman mota da kansa saboda lafiyar 'yarsa ba kadan bane.

Shi ya tayata daukar kayan ta shige gaba na dukan uku-uku. Tana sallama Mawadda ta fito tsakar gidan kamar an wurgota ta rungume Ade. Yau dai babu kunyar 'yar fari saboda yadda ta ganta ta fige fuskar nan kamar ba tata ba don ma ta fara sabewa.

Yaya ta fito suka gaisa a mutumce tana shimfida mata tarbarma don yaran duk sun tafi makarantar allo. Yaya kunya ta kamata rashin sanin me zata fadawa Ade. Ita kaddarar sai akan 'yar amana ta fada duniya zaginta zatayi kawai ace sakaci ne don ba 'yarta bace. Nata yaran babu wadda tayi aiki a gida irin wannan sai 'yar kishiya.

Ade tana ta rarrashin Mawadda tana kuma son tambayar me yake damunta amma ta kula daga Malam har Yaya babu wanda yake son mata bayani. Ba jimawa Baba ya shigo yace su fito mota tazo.

Duka su ukun suka fito dama Yaya ta fadawa sauran yaran idan sun dawo gidan babu kowa su tafi gidan kakaninsu. Tashin motar sai yayi daidai da zuwan Dahiru da leda a hannunsa ta kayan dubiya. Ya tabbatar su Baba ne a motar hankalinsa duk ya tashi ko jikin Mawadda ne. Yayi sa'a dan acabar bai tafi ba ya tambayeshi ina zasu
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On GUMIN HALAK
avatar
amina-5-7-3

3 months ago

Reply

Allah ya kara basira

Please Login or Register in order to submit comment