Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

TASKAR AJALI 1
Littafi na daya 1
Na Abdulaziz Sani M gini
Ebook creat by Shuraih Usman
Ebook publish by www.hausaebooks.cf
Ebook din nan yazo maku ne daga shafin www.hausaebooks.cf
Kuna ziyarci shafinmu don samun sababbin littatafai
Ga duk wanda ke bukatar ebooks nashi ya samu shiga cikin wepsite namu sai ya turo mana da littafin ta Email namu hausaebooks@gmail.com

[2BUDUWARCE 'yar kimanin shekaru
goma sha
tara,ma'abociyar kyawu irin wanda
a ganin farko zata
ruda dukkan 'da namiji dayayi
arba da ita
musamman a cikin irin wannan
shiga da tayi ta
ratso tsakiyar kasuwa.Riga da
wando ne na fatar
damisa matsatstsu ta sanya
wadanda suka baiyana
dukkan kyakyawar siffar
jikinta,kuma a bayanta ta
ratayi wata zabgegiyar takobi.Kallo
daya zaka yiwa
wannan budurwa ka tabbar da
cewa jaruma ce
domin tana da kira irin ta
sadaukai.Ta daure dogon
gashin kanya mai kyalkyali ya zuba
a bayan
kafadarta har bisa
mazaunanta.Tsananin kyawunta
da kwarjinita ne yasa gaba dayan
jama'ar dake cikin
kasuwar suka tsayar da harkokinsu
suka zuba mata
na mujiya kai wasu ma yan
kasuwar basu san
sa'adda suka rinka tsallake hajarsu
ba suka rinka
binta a baya domin ta tafi da
imaninsu.Bawai maza
ba hatta mata masu siye da masu
siyarwa watsar da
komai sukayi suka rinka bin
wannan bakuwar
budurwa a baya don kawai su san
ko ita wacece da
kuma abinda ya kawo ta cikin
wannan kasuwa.Dama
a guje wannan budurwar ta fado
cikin kasuwar
sannan ta tsaya cak ta dubi gabas
da yamma kudu
da arewa ga dukkan alamu dai
wani ko wata ta biyo
a fusace tane neman inda ta shiga
amma bata gani
ba,don haka sai ta sake nausawa
cikin kasuwar da
sauri ta rinka leke cikin rumfuna
da lunguna lunguna
na cikin kasuwar.Dukka da cewar
taga jama'a sun
biyo bayanta da yawa ko kada
bata damu ba,itadai
kokarinta shine taga wanda take
nema ruwa a jallo
amma ko alamunsa bata gani
ba.Al'amarin daya
dugunzuma hankalinta kenan.Koda
taga ta karade
kasuwar gaba dayanta har tsawon
kusan sa'a daya
da rabi ba labari kuma jama'a
sunyi cincirindi a
bayanta sai ranta ya baci ainun
bata san sa'adda ta
yunkura ba ta kurma uban ihu mai
tsananin
firgitarwa tane mai zare
takobinta.Kafin kace wani
abu tuni an tattake kayayyakin
jama'a tamkar yaki
akeyi kuma kowa ya watse
kasuwar tayi tsit tamkar
mutuwa ce ta gifta.Tsananin shirun
daya wanzu ne
yasa jarumar ta jiyo sautin
numfashin mutum a cikin
wani dogon durum na karfe wanda
ke cike da
ruwa.Saidai wannan ruwan durum
ruwane na
kazanta wanda ake wanke
kwanukan abinci dashi a
kusa da rumfar da ake siyar da
abinci.Koda jarumar
ta jiyo numfashin mutum a cikin
wannan darum sai
ta daka tsalle sama ta dira akan
durum din tana mai
raba kafafunta a kansa duk da
cewar bakin durum
din siriri ne matuka amma ko
girgidin faduwa batayi
ba.Kawai sai ta sunkuya ta tsoma
hannunta cikin
ruwan take taji ta kama gashin
mutum ai kuwa sai
ta fincikoshi sama ya na kwala ihu
sakamakon
tsananin zafi da zugin da yaji.Take
ta kwalashi a kas
yana jike sharkaf ya sake kurma
ihu a lokacin yaji
kamar kashin bayansa ya karye ba
wani bane face
matashin saurayi dan kyakyawa
wanda shekarunsa
bazasu haura ashirin da uku
ba.Koda wannan
saurayi yaga wannan jaruma ta
dirfafoshi rike da
takobi tsirara sai ya zube kasa a
gabanta ya kama
tuba yana cewa tayi masa rai.A
lokacin da jikinsa ya
kama kyarma a daidai wannan
lokaci ne mutanen
kasuwar suka fara dawowa,nan da
nan suka taru
wajen sukayi musu kawanya suna
kallon abinda ke
faruwa cikin al'ajabi.Budurwar
ma'abociyar kwarjini
ta iso daf da saurayin ta dora
kaifin takobinta akan
wuyansa take gumi ya karyowa
saurayin sa'adda yaji
kamar ya saki fitsari a wandonsa
sannan ta dubeshi
tace,ina abinda ka sata a cikin
jakar guzurina?Jikin
saurayin na kyarma ya zura
hannunsa cikin aljihun
wandonsa ya fiddo wata guntuwar
jemammiyar fata
wacce ke nannade yamika
mata.Cikin hanzari
budurwar ta amshe ta bude jakar
guzurinta tasa a
cikin sannan ta cire kaifin
takobinta daga kan wuyan
saurayin koda ganin haka sai
saurayin yayi doguwar
ajiyar zuciya kuma fuskarsa ta
fadada da murmushin
murna bisa ganin cewa jarumar ta
kyaleshi bata
kashe shi ba kawai sai ya mike
tsaye zumbur ya
juya da baya ya falfala da gudu
izuwa wani bangaren
daban na kasuwar yana cikin gudu
ne yaga wannan
budurwa jaruma tsulum a gabansa
cikin tsananin
kaduwa yayi tirjiya a gabanta ya
dubeta cikin alamun
tsananin tsoro yace,tundai na baki
abinda na satar
miki kiyi mini rai don girman
iyayenki kada ki kashe
ni.Koda jin haka sai jarumar tayi
masa murmushi
lokaci guda kuma ta murtuke
fuskarta tace,ba
kasheka zanyi ba amma dole ne ka
amsa wadansu
tambayoyi daga gareni tunda kana
biye dani tun
daga birnin Misra har izuwa nan
birnin
Yamein,kasashe uku muka ketare
ta cikin teku duk
jirgin da nashiga kaima saika shiga
ashe akwai
abinda kakeso a wajena?Ina da
kudade masu yawa
a cikin jakar guzurina amma ko
dinare daya baka
dauka ba sai ka dauki abinda yafi
dinaren daraja
kuma yafu duk wata dukiyar a
wannan duniya.Dole
ne nasan dalili kuma nasan wanda
ya turoka
watakila sanin hakan ya kaini ga
samun nasarar
gano inda nake nema.Koda wasa
kada kayi tunanin
guduwa daga hannuna ko kuma
kayi mini karya bisa
abubuwan da zan tambayeka
domin yin hakan
daidai yake da siyar da
ranka.Kasani zan iya
shaftare makogwaron bil'adama da
kaifin takobina
kamar yadda kullum ake yanka
kaza ko naman miya
a kasuwa,ni da kai duk nasan cewa
muna jin yunwa
don haka ka biyo ni muje mu nemi
abinci muci
domin mu sami nutsuwa.Koda
gama fadin hakan sai
jarumar ta juya ta nufi cikin
kasuwa cikin razana da
dari dari saurayin ya bita a baya
kamar ace kyat ya
saki gudawa a wando,su kuwa
jama'ar kasuwar
wannan karon sai aka rasa wanda
zai sake bin bayan
wannan budurwa saboda an razana
da ita ainun bisa
ihun da tayi a wancan karon
wanda ya zamo
sanadiyar tarwatsa kasuwar gaba
daya.Kai tsaye
jarumar ta nufi rumfar wata mata
mai siyar da abinci
jama'a suka rinka ratsewa
suna bata hanya har suka shiga
cikin rumfar ita da
saurayin suna shiga sai gaba dayan
jama'ar dake
zaune bisa kujeru suna cin abinci
suka tarwatse
suka gudu suka bar abincinsu
alhalin basu gama ci
ba,wasu ma anan suka bar
takalmansu da yan
kayayyakinsu.Ita kuwa matar mai
rumfar sai ta
durkusa kasa bisa guwiwowinta a
gabanta.Matar
tace kiyi mini zan baki gaba dayan
cinikin yau.Koda
jin haka sai jarumar tayi sauri ta
kama kafadun
matar ta tashe tsaye ta dubeta
cikin alamun
tausayawa tace,ni ba yar fashi bace
abinci mukazo
mu siya muci kuma sauran
kwastomomin kima da
suka gufu basu biyaki kudade ba
sakamakon firgita
dani zan biyaki kudin abincinsu,ki
kwantar da
hankalinki ni ba mai cutarwa
bace.Koda gama fadin
hakan sai Jarumar taje ta zauna a
kan wata kujera
dake karkashin wani tebur mai
kujeru biyu
kacal,shima saurayin sai ya zauna
tare da ita amma
har a sannnan akwai alamomin
tsoro a tare
dashi.Mai abincin ta dubi Jarumar
tace,ya shugabata
wane irin abinci zan kawo miki?
Jarumar tayi
murmushi tace suna na Yazirina
bin Salmara karki
kara bani girma domin nida
sarauta ko wata
daukaka,shinkafa da kaza zaki
kawo mini amma shi
abokin tafiyar tawa bansan abinda
yake so yaci
ba.Cikin nutsuwa mai abincin ta
dubi saurayin tace
kai kuma fa?Saurayin yayi
murmushi cikin yake yace
suna nan Mujahid Ibini As Sudusi
nima ki kawo mini
irin abincin da abokiyar tafiyata ta
bukata.Koda jin
haka sai Jaruma Yazirina ta yiwa
Mujahid wani irin
murmushi na mugunta tace wato
kaga banza ta fadi
ko zaka kwashi bati shine kai ma
kace a kawo maka
kaza to kasani bayan cin kaza
akwai cin kwakwa a
gaba.Cikin razana Mujahid ya zaro
idanu yace me
kike nufi da cin kwakwa?Yazirina
tace karka damu
lokaci zai baka amsa.Nan da aka
kawo musu
shinkafa da kaza dafaffiya kowa
farantinsa daban
kuma aka kawo musu ruwan inibi
a cikin tambula da
kofuna guda biyu suka kama
kintsa cikinsu.Muhajid
ya bude cikinsa yayi ta zuri har
saida ya koshi yayi
gyatsa amma duk da haka bai rage
ko fiffiken kazar
ba duk da cewar kazar katuwa ce
sosai,sai mutum
yana da matukar cin abinci yake
iya cinye rabin
wannan kaza.Ita kuwa Yazirina
kaso daya cikin kaso
hudu na kasar ta cinye shinkafar
ma cokali uku tayi
kawai,itama kanta tayi mamakin
yadda Mujahid ya
cinye gaba dayan abincinsa.Nan
take Yazarina ta
bude jakar guzurinta ta fiddo da
kudi ta biya abincin
da suka ci ita da Mujahid sannan
ta biya na
kwastomomin da suka gudu kamar
yadda tayi
alkawari,kawai sai ta dubi Mujahid
tace zo mu
tafi.Maimakon Mujahid ya bita da
sauri sai ya tsaya
yanason ya tambayi mai aminci
yace ta bashi wani
abun daga cikin kudin da Yazirina
ta bata,kawai sai
yaji Yazirina ta kamo wuyan
rigarsa ta baya ta
fincikoshi.Ba shiri ya bita a baya da
sauri suka fice
daga cikin rumfar,Koda ganin haka
sai mai abinci ta
daka tsalle sama ta kama rawa
saboda murna bisa
ganin cewa kudaden da Yazirina ta
bata yau yakai
adadin cinikinta na mako
guda.Al'amarin daya baiwa
Mujahid mamaki kenan ya dubeta
a dan tsorace
yace wai shin ina kike son zaki kai
ni ne?Ni fa ban
san ko ina ba a garin nan kuma
bansan kowa
ba.Koda jin haka sai Yazirina ta
juyo a fusace ta
cakumi wuyan rigarsa da hannu
daya ta dagashi
sama sai gashi kafafunsa na wutsil
wutsil a sama
tamkar sillan kara ta daga,sannan
ta daga kanta
sama ta dubeshi tace,Kai tsohon
barawo kada ka
rainan hankali,gaba daya kasashen
dake nahiyar nan
kasan cikinsu da wajensu kamar
yadda kasan
yunwar cikinka saboda kwarewarka
a iya sata.Kana
zaton bansan ka bane?Kaine ka
sace hular sarautar
Sarki Atman Bin Ka'ab na birnin
Kisra.Kaine ka sace
dukiyar attajiri Katadata bin Al
Aswad na birnin
Sham kuma kai ne ka sace lemar
sarauniya Iklaira
bin Aslam ta birnin Hindu kuma
Boka Kaisu Bin
Alkama ya baiwa dukkan
wadannan abubuwan
uku,ya biyaka ladanka yau kusan
shekara biyar
kenan kana aiki a karkashinsa yana
baka sa'a akan
sana'arka ta sata.A halin yanzu duk
fadin duniya
babu wani barawo daya kaika
shahara,dauka da tarin
dukiya.Tana gama fadin hakanne
sai ta dire shi
kasa.Lokacin da Jaruma Yazirina
tazonan a
jawabinta sai gumi ya tsatstsafowa
Mujahid saboda
tsananin mamaki da firgitar da
yayi saboda yanzu
ne ya tsorata sosai da Al'amarin
Yazirina ya gane
cewa tabbas ta cika shu'umar
bokanya domin in
bata kasance haka ba babu yadda
za'ayi tasan duk
wannan sirrmallaketa.Bisa wannan dalili ne
boka Salmara yasa
aljanu suka kwashe gaba dayan
dukiyarsa suka kaita
can wani kogon dutse wanda ake
yiwa lakabi da
TASKAR AJALI,Masana tarihin
wannan kogon dutse
sun tabbatar da cewa fiye da
shekaru dubu uku baya
babu wanda yasan hanyar da
za'abi a je inda
wannan kogo yake kuma kogo ne
wanda babu komai
a cikinsa face tarin dukiya ta
zinare,lu'u
lu'u,jauhari,murjani da sauran
duwatsu masu
daraja,wadanda aljanu ke satowa
daga sassan
bangaroro na duniya suna kaiwa
can su boye tun
daga farkon wanzuwar duniya
kawo iyanzu.Su kansu
aljanun da suke kai wannan dukiya
izuwa kogon
Taskar Ajali a makance suke shiga
dajin kuma su
fito a makance domin duk wanda
ya shigeshi
idanunsa a bude toya daina gani
kenan har
abada.Tsananin mugunta ce tasa
aljanun suka rinka
kai duniyar izuwa taskar ajali
saboda kawai basa son
waninsu ya mallaki dukiyar
kwatankwacin irin tasu
ko ta iyayen gidansu,inda za'a ce
su koma izuwa
taskar ajali idanunsu a bude ba
zasu iya gane
hanyar ba dama da karfin sihirin
tsafi kadai ake
zuwa wajen.Boka Salmara ya gano
cewa shi ko wani
jininsa zai iya zuwa taskar ajali
idanunsa a bude
kuma harma ya sami nasarar zana
taswirar zuwa
can din amma dayaga cutar ajali
ta kamashi sai ya
yanke shawarar yakai tasa dukiyar
izuwa can yadda
babu mai iya mallakarta har
abada,sannan kuma sai
ya raba taswirar izuwa kaso uku
kaso na farko na
taswirar sai ya barshi a jikin
jemammiyar fatar
dabba,kaso na biyu sai ya zanashi a
gadon bayan
wata yarinya yar shekara tara a
duniya wacce ta
kasance hadimarsa ce,ita dai
wannan yarinyra ana
kiranta da Suna Sarila.Asalin Sarila
tsintarta Boka
Salmara yayi tun tana jaririya a
wani daji inda aka
tare wadansu fatake aka kashesu
aka kwashe
dukiyarsu.Boka Salmara yazo
giftawa ne ya hango
Sarila tana ta tsala kuka irin na
jarirai har ya gifta ta
sai tausayi ya fado masa a rai ya
dawo ya
dauketa.Daga wannan rana yaci
gaba da renonta
amma sai ya baiwa wata farkarsa
tana shayar da
ita,ita kuwa wannan farka tasa ana
kiranta da suna
Basma.Saida Basma ta shafe
shekara uku tana renon
Sarila ya zamana cewa ta shaku da
ita tamkar itace
ta haifeta amma dare daya boka
Salmara yazo ya
rabata da ita.A wannan rana
Basma tayi kuka kamar
ranta zai fita kuma babu irin rokon
da bata yiwa
boka Salmara ba akan ya bar mata
Salira amma yaki
kawai sai ya tafi da Salira izuwa
gidansa yaci gaba
da renonta kuma ta zama kamar
tafinta a tsakaninsa
da aljanun da sukeyi masa hidima
ya zamana cewa
tana taimaka masa matuka a
harkokinsa na tsafi
amma har tsawon shekara shida
bata taba fita ba
daga cikin gidansa tun daga ranar
daya kawota.Sau
daya a cikin wata guda Boka
Salmara ya amincewa
Basma tazo gidansa taga Sarila
kuma bai taba yarda
ta kusanceta ba saidai suga juna a
daga nesa.A
watan karshe da Basma ta kawo
Ziyare ne izuwa
Gidan Boka Salmara bayan taga
Sarila zuciyarta tayi
fari sai ta juya da nufin ta fice
daga cikin gidan kawai
saitaji boka Salmara ya kira
sunanta.Cikin mamaki ta
tsaya kuma ta juya ta fuskanceshi
saboda rabon
daya kira sunanta ma tsawon
shekara shida kenan
tun daga ranar daya rabata da
Sarila bare wani abu
ya shiga tsakaninsu.Kawai sai taji
Boka Salmara ya
kama hannunta ya jata izuwa can
dakinsa na
tsafi.Ashe kamuwa yayi da
tsananin bukatarta don
haka a wannan lokaci hankalinsa
ya dan gushe bai
san sa'adda ya kaita cikin dakin
tsafinsa ba ya
kawar da bukatar tasa.Faruwar
hakan keda wuya sai
yaji rabin jikinsa ya shanye ashe ya
karya tasirin
tsafin nasa ne bai sani ba.Koda ya
gane hakan sai
ya kurma uban ihu kuma ya fashe
da kukan bakin
ciki a yayin da nadama tazo
masa.Al'amarin daya
razana Basma da Sarila
kenan.Sarila ta fashe da
kuka tana mai tambayarsa tace
yakai Abbana ina
dalilin wannan kuka naka?Waishin
ma menene dalilin
da yasa ka nisantani da wannan
mahaifiyar tawa?
Koda jin wannan tambaya sai boka
Salmara ya dubi
Sarila cikin alamun tsananin
tausayi tace yake 'yata
ki gafarceni bisa abinda zan gaya
miki yanzu domin
wani babban sirri ne wanda ban
taba gaya miki
ba,kafin haka inason ki sani cewa
daga yau duk
sirrikan tsafina sun mutu bazan iya
yin komai ba da
karfin sihirin tsafi face abu
guda,wannan abu kuwa
shine zan iya kwashe duk dukiyata
dana mallaka na
kaita can kogon Taskar
Ajali.Wannan dukiya tawa
zan kaita canne saboda babu
wanda zai iya
amfanarta face ni kadai ko kuma
jinina ke ba jinina
bace,tsintarki nayi a daji an kashe
iyayenki da
dukkan jama'arsu kece kadai kika
tsira da rayuwarki
kuma a wannan lokaci kina
jaririya.Koda jin wannan
batu sai idanun Sarila suka zazzaro
ta cika da
tsananin mamaki gami da dimbin
bakin ciki kuma
taji ta tsanin komai da kowa kawai
sai ta fashe da
kuka.Boka Salmara yace waccan da
kike kallo a
matsayin mahaifiyarki kuwa ba ita
ce ta haifeki ba
amma ta shayar dake kuma ta
reneki har tsawon
shekaru uku daga nan na karbeki
daga hannunta
naci gaba da renonki kawo izuwa
yanzu da kika cika
shekara tara a duniya.Yake Sarila ki
sani cewa
rayuwata ta zo karshe nan da cikar
kwanaki kadan
zan mutu na barki amma ki sani
cewa ba zaki taba
wulakanta ba a duniya domin zaki
sami daukaka da
arziki mai yawa amma zaki nisanta
da kowa da
dukkan mutane kuma zaki yi
rayiwa ne a wurin da
dan adam bai isa yaje ba koma
hatsabibancinsa
kuma aljanu ne zasu rinka yimiki
hidima sai kuma
tsurarun bayi na bil'adama da zaki
iskesu acan
wadanda dama can nine na
tanadesu domin ki.Koda
Boka Salmara yazo nan a
jawabinsa sai Salira ta
rungumeshi ta sake fashewa da
matsanancin kuka
da kyar ya rarrasheta tayi shiru
sannan ya janyeta
daga cikin jikinsa ya dubi Basma
yaceYa dubi Basma yace ke kuma daga
yau dinnan kin
sami gaba dayan sirrikan tsafina
kuma babu wanda
zai iya gadarsu daga gareki face ki
sami juna biyu
dani wanda sai tsananin sa'a da
rabo sannan hakan
zata iya kasancewa.Ke kanki baki
isa ki iya zuwa
kogon taskar ajali ba ki dauko
wadannan dukiya
tawa amma inda zaki sami juna
biyu sakamakon
sadauwar da mukayi to duk abinda
kika haifa walau
mace ko namiji zai iya zuwa Taskar
Ajali ya dauko
wannan dukiya tawa amma fa sai
ya gwammace
baije ba saboda tsananin wahalar
da zai sha a cikin
tafiyarsa izuwa Taskar Ajaki don
saiya gwammace
MUTUWA akan RAYUWA.Ke ma
zaki sami
daukaka,mulki da dukiya kuma har
ki bar duniya ba
zakiyi aure ba kuma babu wani da
namiji daya isa
ya sake tarawa dake.Da wannan
furuci nakeyi muku
bankwana na karshe don haka na
sallameku saiku
kama gabanku amma ku sani cewa
zamanku a tare
ba zai haifar muku da komai ba
face masifu,tashin
hankali da annoba iri iri don haka
dolene ku rabu ko
wannan ku yabi hanyarsa
daban,amma idan kuna
shakka ne akan hakan to ku
jarraba zama a waje
guda zaku sha mamaki.Koda gama
fadin hakan sai
Boka Salmara yayi tari sau uku
saiga gudan jini ya
furzo daga cikin bakinsa.Take
idanunsa suka juye
sukayi jawur ya kife kasa yana
numfashi sama sama
al'amarin da yasa Sarila da Basma
suka kamu da
tsananin tausayinsa kenan kuma
suka fashe da
kuka.Cikin matukar karfin hali
boka Salmara ya mike
tsaye ya nufi inda kofar dakinsa na
tsafi yake har ya
sanya kafarsa guda izuwa cikin
dakin saiya tsaya
cak ya juyo ya yafito Basma da
hannu ta taho
gareshi,kawai sai ya zura hannunsa
cikin aljihun
rigarsa ya fiddo da taswirar zuwa
kogon taskar Ajali
dake jikin jemammiyar fata ya
mika mata ta karba
yace wannan taswira ce izuwa
kogon taskar ajali
amma kaso daya cikin ukunta ki
duba gadon bayan
Sarila kaso na biyu na zane
akai,kaso na uku kuwa
yana can inda zaki zauna ki karasa
sauran rayuwarki
ta duniya rubuve akan wani allo na
katako.Dole sai
an hada wadannan taswira guda
uku sannan za'a iya
samun cikakken zance na hanyar
da za'abi aje
kogon taskar ajali.Kinga kenan
idan kin sami damar
samun juna biyu na kin haifeshi to
zaki iya baki
taswirar guda biyu,ta cikon ukun
kuwa dolene ya tafi
neman Sarila.Ki sani cewa Sarila na
fita daga nan
yanzu Aljanu ne zasu dauketa su
kaita can tsakiyar
birnin Jannatul Duniya.Wannan
tsibiri shine wurin da
yafi ko ina tsaro da ni'ima a cikin
kaf din wannan
duniya,kuma yana tsakanin
karshen birnin sin da
Mastur Kusa da dan karshen
bangon duniya.Ba'a
tsufa a wannan tsuburi ba'a rashin
lafiya koda kuwa
mutum ko aljan zai shekara dubu
a wajen,amma ana
mutuwa.Koda Boka Salmara yazo
nan a jawabinsa
sai ya yiwa Basma kallon karshe.A
lokacin da
hawaye ya zubo masa sannan ya
juya da nufin ya
shige cikin dakinsa na tsafi amma
sai Basma ta
dakatar dashi tace,yakai Salmara
yanzu ta yaya zan
kai kaina inda zan karasa sauran
tawa rayuwar kuma
inane wannan wuri?Koda jin
wannan tambaya sai
Boka Salmara ya numfasa yace
kamar yadda aljanu
zasu kai Sarila Tsuburin Jannatul
Duniya kema
akwai wanda zai yi miki jagora
izuwa masauki
wanda shine Darul Azmin,shi kuwa
wannan wuri a
karshen bangon duniya yake daf
da birnin
Hindu,zamanki acan shine kadai
kubutar dukkanin
matsafan duniya,in ba haka ba
kuwa sai ki zame
musu annoba mai shayar dasu
mugunyar mutuwa
domin sai an wayi gari babu
sauran boka guda daya
a raye a doron kasa face ke.Idan
kuma kinason ki
zama sanadin mutuwar miliyoyin
wadannan rayuka
to ki cigaba da zama a cikin
mutane kada ki tafi
izuwa wannan masauki naki.Koda
gama fadin hakan
sai Boka Salmara ya shige izuwa
cikin dakin halwar
tsafin nasa bai yarda ya sake
waigowa ba ya dubi
Basma da Sarila.Ai kuwa yana
shigewa sai kofar
dakin ta kullo kanta,wannan shine
ganin karshe
wanda Basma da Sarila suka yiwa
Boka Salmara.Ba
tare da bata lokaci ba kuwa Basma
da Sarila suka
fice daga cikin gidan Boka Salmara
suna fita sai
gidan ya bace bat tamkar bai taba
wanzuwa ba a
wajen.Faruwar hakan keda wuya
kafin Basma ta dubi
Sarila tace wani sai sukaji wata iska
mai karfi a
samansu.Kafin su daga kawunansu
suma suga
abinda yayi musu inuwa tuni an
suri Sarila anyi
sama da ita,ita da abinda ya
dauketan kafin dakika
guda sun kule a cikin gajimare.Ita
kuwa Basma sai
ta hango wani mutum akan wani
farin doki sanye da
bakaken tufafi ya durfafo inda
take a sukwane,abinda
ya razana ta dangane da mutumin
shine ya lullube
kansa da bakin mayafi amma
kuma bashi da
fuska,ma'ana babu fata,tsoka ko
kashi akan fuskarsa
bare a sami hanci,baki ko ido
kawai sai wani irin
haske mai dallare idanu tamkar an
ajiye madubi a
rana.Babu shiri Basma ta sunkui da
kanta kas ta
daina kallon fuskar mutumin da
isowar wannan
mutumin daf da Basma sai ya
sureta da hannu daya
ya azata a bayansa bisa wannan
farin doki ya
zabureshi cikin azababben gudu na
gaba
misali.Tunda Basma tazo duniya
bata taba ganin
doki mai gudun wannan doki ba
domin ko walkiya
bata fishi saurin baiyana da
bacewa ba,ai kuwa ko
rabin sa'a basuyi ba da fara
wannan tafiya ba sai
barci mai nauyi ya dauke
Basma.Lokacin da Basma
ta farka daga barci sai ta tsinci
kanta a cikin wani
kasaitaccen daki wanda komai
dake cikinsa anyi
shine da gilashin lu'u lu'i mai launi
fari hatta
luntsumemen gadon da take kao
kuwa.Tana bude
idanunta taji kanta yayi mata
nauyi tamkar an dora
mata katon dutse haka kuma taji
ciwon kai ya
kamata,tsaitsaye a gefe daya a
bayanta gadon da
take kwance a gabansa kuyangi ne
na bil'adama su
arba'in da daya,koda kuyangin
suka ga Basma ta
farka daga barci sai biyu
daga cikinsu sukayi sauri suka
matso gareta.Daya
na ruke da tambulan cike da
sabuwar madarar
shanu mai gardi da dumi dayar
kuma na rike da
dogon kofi na gilashi take suka
zuba mata madarar
a cikin kofin suka cika shi taf
sannan suka bata ta
kama sha.Bata san sa'adda ta
shanye shi tas
saboda dadin dandanon tana gama
shanye nonon taji
ta daina ciwon kan take ta dawo
cikin haiyacinta tare
da lura da cewa ashe an canja
mata ma suturar
jikinta an sanya mata wata.Farar
doguwar riga cikin
dimauta da firgici Basma ta dubi
kuyangar data bata
madarar da tasha tace yaushe ne
nazo nan kuma
ina abokin tafiya wanda ya kawo
ni nan akan farin
dokinsa?Koda jin wannan tambaya
sai kuyangar tayi
murmushi tace ya shugabata ai
abokin tafiyarki
manzo ne kawai ba kowa ba,ya
gama aikinsa ya tafi
izuwa can kasarsu ta birnin
matsafa a wata nahiya
dake cikin kasashen aljanu.Ki sani
cewa yau
kwanaki arba'in da daya kina barci
tun akan
hanyarku daga can birninku zuwa
nan dajin Iblas
dake daf da birnin Hindu,ki
kwantar da hankalinki ya
shugaba kiyi sani cewa indai kina
nan baki da wata
fargaba ko bakin ciki ko kewa
kuma duk abinda
kikeso indai akwai shi anan cikin
duniya zaki
sameshi face abu guda wato
abokin rayuwa.Kowacce
'ya mace tana bukatar namiji
abokin rayuwarta
amma ke ba zaki taba samun saba
har ki kammala
rayuwar kwanakinki na
duniya.Koda kuyangar tazo
nan a jawabinta sai hankalin
Basma ya dugunzuma
ainun ta rasa abin dake mata dadi
a duniya.Daga
wannan rana Basma ta tsinci kanta
a cikin sabuwar
rayuwa irin wadda bata taba
tsintar kanta a ciki ba
domin rayuwa ce wadda babu
matsalar ci da sha ga
makwanci wanda ma yafi na
wadansu sarakan,kuma
babu abinda takeyi da kanta
komai saidai kuyangi
suyi mata,abinda ya daurewa
Basma kai shine ganin
yadda sauran kuyangin suke
rayuwa a wannan tsibiri
a cikin daji haka ba tare da wata
rayuwa ba domin a
ganinta babu rayuwar da tafi dadi
face ta zama a
cikin gari tare da al'umma koda
kuwa dadin da
mutum zaiji a irin wadannan
gidaje na bokaye babu
kamarsa a duniya.Koda Basma tazo
nan a jawabinta
sai idanunta suka ciko da kwallah
hawaye ya zubo
mata,nan ta kamu da tsananin
bakin ciki gami da
takaici taji tayi nadamar kaddarar
data hadata da
Boka Salmara a tafarkin
barikanci.A kwana a tashi,a
ranar da Basma ta sami kwanaki
sittin daidai a
wannan kayataccen gida na daji,sai
ta wayi gari a
cikin tashin zuciya har da
kumallo.Nan da nan ta fita
daga cikin haiyacinta har ta fadi
kasa a lokacin da
taji jiri ya kwasheta kuma kanta ya
kamu da ciwo
cikin hanzari kuma a guje
kuyangin suka rugo da
gudu suka dauketa suka kaita can
cikin turakarta
suka kwantar da ita a kan
gado.Shugabar kuyangin
wata tsohuwa tasa aka rinka gasa
gashin Basma
sannan ta kama tsintsiyar
hannunta ta rike tana
nazari irin na likitoci.A daidai
wannan lokaci ne
Basma ta farfado daga dogon
suman da tayi,koda ta
bude idanunta saitayi arba da
wannan tsohuwa
zaune a gabanta ta kura mata
idanu tana yi mata
murmushi.Kawai sai tsohuwar ta
bude baki tace yake
Basma muna ta yaki murna saboda
kin sami juna
biyu tare da shugabanmu Boka
Salmara kafin
ajalinsa ya cika.Tabbas abinda zaki
haifa zai zamo
babban jarumi abin kwatance
kuma shine kadai zai
iya zuwa TASKAR AJALI ya dauko
dukiyar da
mahaifinsa ya tara wato Boka
Salmara.....
,TASKAR AJALI!!!
Littafi Na Daya (1)
Part D
Ya tara wato Boka Salmara.Yake
Basma kiyi sani
cewa duk mahalukin daya mallaki
wannan dukiya ta
Boka Salmara zai iya amfani da ita
wajen mulkar
wannan duniya gaba
dayanta,domin gaba dayan
attajirai da sarakai sai sun zamo
almajirai masu yin
bara a gabansa.Akwai matsaloli
guda biyu a gaba ga
Jarumi ko Jarumar da zaki
haifa.Matsala ta farko
itace dole ne a baiwa dan naki ko
yar taki horon
yaki mai tsananin gaske yadda zai
iya tsare taswirar
da zaki danka masa guda biyu
saboda matsafa da
masu mulki zasuyi kokarin rabata
da su.Matsala ta
biyu kuma waccan yarinya Sarila
wacce zannen
taswirar na uku ke bisa gadon
bayanta zata baro
can Jannatul Duniya a lokacin da
yarki ko danki ya
shiga duniya nemanta.Zai kasance
suna farautar
juna a wannan lokaci,ita Sarila zata
kasance
azzaluma ainun kuma karfin
damtsenta dana sihirinta
sai ya ninka na danki ko yarki
saboda albarkacin
rayuwar datayi a tsibirin Daulatul
Duniya.Burinta
shine taga danki ko yarki ta kashe
ta ta dauke
Taswirar biyun dake hannunta,ita
ma yar taki ko dan
naki burinsa ya kashe Sarila ya
kwafe taswirar dake
zane a bayanta domin ya sami
damar zuwa Taskar
Ajali.Wannan 'da naki ko ya taki
ba zai sami nasara
ba akan Sarila face da taimakon
wani bakon saurayi
wanda ba'a san daga nahiyar dazai
fito ba,shidai
wannan saurayi ya kasance
kyakkyawa abin
kwatance kuma bashi da karfin
damtse ko kadan
kuma bashi da karfin sihirin tsafi
sannan bai iya yaki
ba,asali ma bai taba rike takobi ba
saidai ya kasance
yana da wata irin baiwa ta
musamman sannan yana
da tsananin sa'a da rabo bisa duk
abinda yasa a
gabansa duk da cewa shi mutum
ne mai matukar
tsoro,wannan saurayi shine kadai
zai iya takawa
Sarila birki a cikin zaluncinta kuma
shine kadai zai
iya kare abinda zaki haifa daga
sharrin Sarila.Koda
tsohuwar tazo nan a jawabinta sai
bakin ciki ya sake
turnuke Basma hawaye ya zubo
mata tace yanzu
kenan Sarila da abinda zan haifa
zasu zamo
ABOKAN GABA har dayansu ya
zamo sanadin ajalin
daya alhalin su
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment