Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

DARAJAR 'YA'YANA1-01
Posted by ANaM Dorayi on 11:41 PM, 08-Mar-16
Under: DARAJAR 'YA'YANA
___________________NA
___________HALIMA K/MASHI
Cikin sauri sadiya take yin komai dan bata son
mai gidanta ya dawo ya sameta ba yanda idonsa
yake bukata ba.Tuwon (semo) tayi mashi miyar
kubewa danya, sai farfesun kafar sa, sanan ta
tanadifura da nono, tasa a cikin fridge don tana
bukatar yayi sanyi.Ta share ko ina na gidan fes ta
wada tashi da kamshi turare, taje ta fesa wanka
sanan ta bata lokaci a gun kwalliya.Kankwasa
kofar da taji ne ta tuna da 'yan yaranta, da sauri
taje ta bude musu, kai tsaye ban daki tace su
nufa.Wanka ta sake yi musu sanan ta shirya su
cikin sababin kayansu masu kyau ta feshesu da
turaruka.Ta dawo dakinta inda ta rasa wane
kayane ma zata saka, a karshe ta yanke shawarar
saka wani jan material riga da siket.Ta dubi
kitsonta kanana da ta yarfa a madubi, sanan ta
kashe daurin dan kwali. Tasan yau zata burge
mijinta, musanaman da ta kalli lallen hannunta
na fulawa da aka zana mata.Ta kalli agogo karfe
shida da kwata, wayarta wadda ta dauke saboda
rashin chaji, ta jonata chaji.Ashe garin sauri bata
sa dai dai ba, don haka bata samu chajin ba har
aka dauke wuta.
banda haka da taji yanzu mijinta yana dai dai
ina?Kwnkwasa kofar ne ya dawo da ita daga
haushin rashin cajin da wayarta bata da shi, ita
da yaranta suka diba da gudu don taryo
mijinta.Tana bude kofar shine tsaye, sanye cikin
kayan yansanda, daga ka ganshi kasan babban
jami'ine, ta fada jikinshi tare da rumgume shi,
amma me?Sai taga ya sabule tare da cewa sannu
da gida.Cikin mamaki ta amshi ledar hannunsa
tare da jakarshi, ya tsugunna yana sha kan yayan
sa cikin jin dadi da kewa, sadiya ta tsaya cike da
mamakin saboda al'amari da take gani a gurin
me gidan nata.Abin da tasani a duk lokacin da ya
dawo yakan iso ne a marmatse cike da kewarta,
da ya shigo burinsa kawai ya rungumeta tsam a
jikinsa kafin yaran, amma yau sai taga ita ce ta
rumgume shi har yana sabulewa, lallai wanan
sabon al'amarine a gurinta.To ko dai gajiya ce
take damunsa?Kokuma fushi yayi ya gaji da
kiranta bai samu ba?Ta dubi kanta, kokuma
kwaliyarta ce batayi ba?Ta sake wai wayawa ta
kale su inda yake rungumarsu daya bayan
daya.Da kausar ya soma, sanan Al'amen, sai
mama ta tuno yanda yake mata a duk juma'ar
da yazo, ya kamata ya fi dokinta a wanan karon
da ya hada saty biyu bai zoba.Abin duk ya
dameta, tana tsoron kada wata masifa ko annoba
ta ratso cikin kyakkawan zaman nasu, tana tuna
da yadda take makale a gefen damansa sannan
ya dauki mama da hannun hagunsa har cikin
falonsu.Yanxu dai ba zatace ganin yara bane,
domintasan yaransu sun taso sun samesu cikin
wata rayuwa da suka shinfida ta shakuwa da
kaunar juna.Sun saba ganinsu rungume da juna,
sun saba ita da yaran suyi ta kokuwa a jikinshi,
basa yin wani abu da zai kawo matsala ga
tarbiyar yaransu, amma sukan rungumi junako
yin falo da junan ana hira.Sun rigata shiga falo,
ta shigo nan ma ta sake kallonshi, mamaki ganin
ya zauna shi da ke zarcewa dakinsa, can suke
zuwa ya basu tsarabarsu.
Sanan ya basu ta iya ya ce su kai mata, sanan
kada kudawo in na huta zanzo in gaidata, sai mu
dawo tare.Su ce to Abba, su tafi suna
tsallensu.Shi kuwa suna fita wata ran ko wanka
baya yi zai rungumota ya ce Dear my choice a
matse nake.Ya wancin lokacin sai ya samu
natsuwa kafin ya ci abincin ba yan yayi
wanka.Dan Aliyu mutum ne mai matsanan ciyar
bukata.Cikin damuwa ta isa kusa dashi.Yaya Ali
yau kagaji sosai ko?Ya dubeta me kika gani?Ta
ce, baka saba zama cikin falo ba.Ya miko hannu
bani ledar nan in sallami yaran nan.Ya fada ba
tare da ya bata waccen amsar ba.Ta miko masa
kanta daure ta nufi dakinsa da jakarsa, ya ba
yaran tsarabarsu, kayan ciye ciye ne da na wasa,
sanan ya mike ya nufi dakin sa.Kausar tace, abba
yau ina tsarabar iya?Sadiya daga cikin dakinta ta
kaso kunne taji amsar da zai ba da.Ba tare da ya
waiwayo ya dubi kausar ba, yace kinga magariba
ta kusa, bari in anyi sallah sai muje ko?Ya shiga
daidai lokacin ta shiga ban daki dan hada masa
ruwan wanka.Ta fito yana zaune bakin gado yana
kwance igiyar takalminsa ta iso gurin.Da sauri ta
tsugunna tare da cewa abba kausar yau kuma
harda aikina zaka shigar min?Ta ci gaba da
kwance takalmi tana cewa, yau duk na ganka
wani iri daban, ko duk gajiyar ce?Ya ce gajiya
saikace ba jami'in tsaro ba?Ta soma balle masa
maballen riga, to baka jin dadin jikinka ne ko?
Yaja tsaki, dan Allah ki bar ni da tambayoyinnan
naki please, gabanta ya fadi, ta dubeshi da gaske
yake yi fuskarshi daure.Jikinta yayi sanyi, ta gama
balle botiran, ya mike ya nufi ban daki ta mike
zata taimaka mashi kamar yadda ta saba, ya
shiga sai ya banko kofar zata tura sai taji karar
makulli yana kulle kofar.Cike da tsoro taje dakin
tana kallon kanta a madubi, ko dai batayi kyau ba
ne yau?Ta duba ba wata makusa, ta kara jan
baki da turare sanan ta fito ta same shi yana
shafa mai,ta isa gurinshi, ta ciro masa kaftani da
wando na shadda mai ruwan sararin samaniya,
ta ciro hular da zata dace da kayan ta ajeye
masa, amma sai taga ya janyo jallabiya mai
dogon hannu fara sol ya saka.Daga nan sai ta
koma ta jingina da bango dan jiran ganin
sarautar Allah.Ya fita, ta bishi ganin zai fita waje
ta ce, tabban kausar abincin fa?A sanyaye tayi
maganar.Ba tare da ya waiwayo ba ya ce, sallah
zan yi tukunna.Kausar ta ce,Abba ina kayi sallar
ka dawo kaje damu gidan iya, kada kaje daga
can.Ya dubi yaran da murmushi zan zo muje
kunji?Suka ce to Abban mu, bari muyi muma
sallar.Ko da tayi sallar sake zama tayi gaban
madubi tayi sabuwar kwalliya sanan tayi canjin
kaya daga jan yadin zuwa leshin ruwan dorawa
mara nauyi .Ba kamar ko yaushe da yake kashe
waya baina zasu ci abinci wayarshi kunne kuma
jifa jifa yana amsa kira.Guri daya taji dadi ya
zage ya kwashi abinci kamar yanda yake yi ko
yaushe, haka nan
haka nan 'ya'yan shi yana ta surutu da su.Amma
ita ya dauke wuta da lamarinta har ta kasa cin
abincin ma, so take ta tuno kurun laifin da tayi
masa dan kawai ta bashi hakuri.Bata saba da
wanan yanayin da suke ciki ba, zuciyarta ta ce ko
ya ta kiran wayarki ne ba a ji?Da sauri ta dube
shi.Abban kausar nasan kayi ta nema na layi naa
kashe ko?Ya dubeta ban nemi layinki ba, ba wuta
ne ta ce eh ba wuta.Kutashi muje gidan iya,suka
mike cikin murna,Ku ziyarci blog dinmu domin
karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Kausar ta ce,Abba, momi bata dauko hijabinta
ba.Ya ce, bata son zuwa ne, tayi aiki ta
gaji.Wanan ya nuna mata ba a son zuwa da ita
tunda ba a tambayeta ba bare a ce ita ce tace ba
za ta je ba.Sun barta cikin tunani da jimami, ta
gyare gidan musanman gurin da suka ci abinci,
tayi ta jiransu tana zaune a falo tana kalon TV
amma inda zaka tambayeta abinda ake yi a TV
din ba zata fada maka ba.Ita burinta kawai ta
san laifinta, amma ina ta tuna da cewa anjima da
yazo dole zai sauke ko mai dan tasan cewa ba
zasu taba kasancewa gado daya da shi ba ya iya
kauda kai daga gare ta.Itama zata ja aji lokacin
har sai taji dalilinsa, ganin sun kai har sha daya
sai kurum ta cire tayi shirin bacci, kayan baccin
bakake masu matukar daukar hankali, ta dora
hijabi saboda da yara zai shigo.Kausar ce kurun
batayi bacci ba, Al-Amin yana sabe a kafadar
dama, mama a ta hagu, kausar din tana biye
dashi suka shigo.Kai tsaye dakinsu ya nufa da su,
tabi bayan su yana kwantar da su, ya fita ita
kuma ta gyara su, sanan tayi musu adu'a taja
musu kofa.Dai dai lokacin kausar tana cewa
momi sai da safe, sadiya tace, Allah ya kaimu
kausar.Dakinta ta nufa ta sake fesa turare, sanan
tanufi fridge don ta dauki furarshi wadda ta riga
ta dama.Shiru ta tsaya dan ya riga ya dauka, ta
nufi dakin shi.Yana zaune bakin gadonshi sanye
da kayan bacci, laptop ce a gabanshi kan dan
tebirin da ake ajeye mai fura.Kofin yana
hannunshi yana kurbar furar, idonsa sanye cikin
farin gilashi ta ce, tace ashe har ka dauko furar
ka?Ba tare da ya dubeta ba ya ce eh.Ta zauna
kusa da shi wai abban kausar nayi laifi ne da ake
ta share ni?
Ban gane na neke ta share ki ba?Ta ce na gane
yau duk ka canza ko na ce abubuwa sun canza
kamar ba mijina ba maita rairayata?Ya dago ya
dubeta baki min komai ba.Ta dora hannunta a
kan cinyarsa, abba kausar to naganka ne ni yau
irin kamar banyi kyauba din nan.Ya kalleta Dan
Allah ki barni ina yin abu mai muhimmanci ne.Ta
ce, amma dai da aka saurare ni bai fi abin da ka
ke yi muhimmanci ba?Ga mamakinta sai kawai
taji ya daka ma tsawa,kin san me kike fada kuwa
dan Allah tashi ki bani guri a nan,ta zaro ido,
mikewa tayi ta nufi kan gado ta kwanta a ranta
tana cewa ka gama kazo ka same ni ina nan
kwance.Abin ta'ajibi ranar dai haka ya raba dare
yana harkokinshi a internet sabon abu ga Sadiya
mutumin da in yazo satin karshen mako hatta
wayoyin shi kashewa yake suna manne da juna
har sai ya tafi yana cike da kewarsu.Ko da ya
kashe laptop ya kwanta juya mata baya yayi,don
Allah babban kausar me yake faruwa ne?Dan
Allah in wani abu ya faru ne ka sanar dani zan
baka hakuri, ban saba da wanan rayuwar
ba.Cikin zafin rai wanda banta ba ga ni ba ya ce,
nace bakiyi mini komai ba, kina son dole sai nayi
maki karya ne?Dan Allah ki bar ni in huta ki barni
na ce.Ta rike kai to banyi maka laifiba me yasa
ka canza min?Nasanka kai mutun ne mai bukata
a marmatse ka ke zuwa in kayi saty daya, wanan
satyn har saty biyu kayi amma sai naga kazo
bana gabanka.Ya zoro ido to yau ban da bukata
ko dole ne?Ya ja tsaki, tashi dan Allah taf dakinki
bana son jaraba kada ki dameni.Kuka ne ya
subuce mata, ta fita a dakin tunda aka kawota
gidan yau ce rana ta farko da zata kwana a
dakinta ita daya.Dan ko haihuwa tayi basa raba
makwanci, ta fito falo ga mamakinta sai taga
kausar tsaye a falo tayi saurin dai daita fuskarta
tare da share hawayenta ta nufi kausar.Me kika
fito yi?Kausar me kike so?Ta ce, mome naji abba
ne yana fada ne, me kika yi masa?Ta kama
hannun yariyanyar suka nufi dakin yara.Kan
katifarsu ta kwantar da ita ta kuma ta kwanta a
bayanta tare da rungumeta, kausar ta sake
tambayarta momi kinyi laifi ne Abba ya ce ki fita?
kasa magana tayi don al'ajabi ne ke dankare cikin
ranta, ta danne hawayenta ta ce kausar laifi nayi
masa.Kausar ta ce, momi ki bashi hakuri
mana,'to' Sadiya ta ce zan bashi sai da safe in ya
huce kinji?Kausar tace, eh.Sadiya ta ce ki daina
tashi cikin dare kin ji, tadinga shafa kan yarinyar
tana lallashinta hartayi bacci ita kuma ta koma
duniyar tunani tuno farkonsu.Iya mahaifiyar Aliyu
ya ce ga mahaifiyata, uwarsu daya ubansu
daya,su 'yan asalin jahar jigawa ne, a karamar
hukumar Hadeja.Mahaifiyarsu ta rasu ta barsu su
hudu mazabiyu mata biyu, kawu Adamu da kawu
Dauda duk iya ce babbar su.Lokacin da
mahaifiyata ta na budurwa, dan haka iya ta
dauketa lokacin suna zaune a Dutse da mai
gidanta da yaranta hudu.Yaya sulaiman
yayazakari, yaya sani, sai cikin yaya Aliyu.Mijinta
ma'aikacine a ma'aikatar gona ta jahar Jigawa,
daga baya yayi ritaya inda ya dawo kaduna da
zama sana din dan uwansa dake noma.A
unguwar mu'azu ya sai gida madaidaici a ciki aka
haifi Aliyu kuma a nan aka aurar da mahaifiyata
inda ta auri mahaifina wanda yakasance
ma'aikacin gidan Raidio kaduna.Amma dan zariya
ne kuma zariyar aka kaita,yana da mata biyu da
yara kusan goma, ko a lokacin.Maimuna
mahaifiyarta ta kasance mai hakuri da juriya, duk
da cewa bai kasance mutum mai cika hakkokin
iyalansa ba.Amma bata taba kawo kararshi gurin
iya ba,don tasan iya tana da fada sam bata da
wasa.Shekarar da yaya sulaiman yayi aure
shekarar ce mujin iya Allah yayi mai rasuwa,sunji
mutuwar ta farat daya yana cikin sallah yayi
sujjada a masallaci har aka idar bai dago ba.An
dago shi sai gawa, ashe mutuwar kenan.Yaya
sulaiman koyarwa yake yi a makarantar yan mata
dake Tudun wadan wada wato Sai yaya zakari
kasuwanci a babbar kasuwar kaduna, duk da
cewa ba wani babban dan kasuwa bane,Sani
kuma da ya gama secondary sai kurum ya shiga
wurin gyaran motoci dan a lokacin babu halin ci
gaba saboda yanda karatu ya zama a kasarmu sai
yayan masu shi.Talaka yana so yake hakura.Ya
Aliyu karamin su kuma suna tallafa mashi don
ganin ya samu karatunshi, kwanci tashi suma duk
suka yiyyi auransu.Lokacin da mahaifiyata tana
dauke da da tsohon cikina don ta jima bata haihu
ba, har lokacin iya bata gane yar uwarta tana
cikin matsala ba, sai bayan ta haife ni.Lokacin da
taga komai babu, abin ci a gidan gashi ya sake
yin aure ya ciko mace ta hudu,iya ta same shi ta
ce, yanzu tsakanika da Allah Abubakar hakan da
kake yi dai dai ne?A ce ka ajiye mata babu
kulawa ba abinci badai baka da shi ba sai don
zalunci?Ya ce ai za a siyo.Tace, gara ma ka siyo
don ba zan dauki zama da yunwa ba, in an ganka
a waje kwas kwas har da mshin din hawa gareka
amma a gidanka da yunwa.A daddafe akayi suna
inda aka rangada min Halimatu Sadiya, iya ta tasa
mahaifiyata ta tafi da ita, tace ba za a bartaba
haihuwar fari ba kulawa ba,Ita kenan gareni dan
wadan can yan uwan namu sai munyi tafiya mai
tsawo kan mu gansu.Sai da mahaifiyata tayi
kusan wata shida lokacin ni da ita munyi bulbul
tamkar kada iya ta bari mutafi, amma yanda
mahaifina ke ta suntirin zuwa yana kuma turo
mutane don baiwa iya hakuri sai ta hakura tace
mu koma.Amma ta ja masa kunne sosai, to dan
saukin yanzun ba kamar da ba, hakan yasa ki
shiyoyin jin haushinta suna ganin ya fifitata shi
ko tsoron karr a dauke ta ne don iya ta tabbatar
masa in tazo taga ba daidai ba to zata tafi
damu.Shakarata biyu ta sake samun wani cikin
tun yana karami take fama da laulayi iya tana
zuwa tare da yayanta akai akai suna duba
mahaifiyata tare da kawo mata abubuwa.Iya taso
ta tafi dani amma lokacin an ce inna da kalafucin
uwa, kulafaci gareni sosai ta hakuraKu ziyarci blog
dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Gurin haihuwarta kuma taji jiki da kyar ta haifi
yar bubu rai.Sanan itama jini ya balle mata ya
dinga zuba kafin aje Asibiti rai yayi halinsa, ance
iya taji mutuwar nan kaman me.Bayan anyi
bakwai aka raba dan abinda ta bari sanan iya
tace ba zata barni ba dani zata tafi da kyar
mahaifina ya yarda don shima yaji mutuwar yayi
kuka tamkar ranshizai fita , to mafarin zamana a
gun iya kenan.Na taso cikin gata da tarbiya duk
da irin son da iya take yi min, bai sa ta kasa bani
tarbiya ba.Lokacin da aka kawoni gidan yaya Aliyu
yana shekararshi ta karshe a makarantar kwana
ta barewa kwaleji dake zariya.Sam yaya Aliyu
halinsa ba iri daya bane da yayyansa, don su
suna da sakin fuska da fara'a, amma shi kullun
rai a hade ta bakin iya in tana masa tsiya takan
ce na rasa inda ka gado wanan halin naka na
shegen miskilanci, kullun cikin bacin rai sai kace
jakadan yan wuta. Tunda nake gidan bai taba yi
mun wasa ko hira ba, magana in ta hada mu to
bata wuce yazo bai ga iya ba, yace Sadiya ina
iya?Tare da haka ba shi dai raini ko rashin kunya,
sai dai kafi ya ga saurin fushi gami da zafin
zuciya. Yanada matsananciyar tsafta da ibada Iya
na yaba masa a nan, tunda na taso Allah baitaba
nuna mun bacci iya na dare ba, sai dai na rana,
bayan azahar. Duk lokacin da na farka zan ganta
tana yin nafilfilu.
Yaya Aliyu akwai iya saka kaya, bani manta
kawayena in sun biyo mini makaranta suka ganshi
sai kiji suna cewa, sadiya yayan nan naki dan
kwambo ne, ya cika yanga gashi baya
fara'a.Nakan ce kurufa mini asiri kada yaji.Burin
yaya Aliyu aduniya bai wuce ya zama police ba,
kalmar da Iya ta tsana duk lokacinda ya ce mata
shifa in ya gama karatunshi zai shiga makarantar
horar da yansanda.Sai ta ce masa ya daina
wanan tunanin don ita bata son dan sanda, wai a
nata ganin sharri kullun ake koya musu, kullin
suna kan titi suna karbar cin hanci.Wani lokacin
tace, dan sanda da aka ce ko ya mutu gawarsa
tana fita da ban, dan baki take to ban amince
ba.Shi kuma sai yace, iya kiyi min adu'a buri na
kenan zancen zancen ace kaza kaza duk sharri ne
babu ma'aikatan da babu na gari, kuma babu
inda ba battace.Kimin adu'a in zama mai kawo
gyara a cikinsu kuma in na zama dan sanda in
sha Allahu sai kinyi alfahari dani.Takan tabe baki
ta ce, uhm ni rabu dani da wanan zancen, ni dai
insuna yi sauraransu kurun nake yi, don sam in
yaya Aliyu yana fira da iya bana sa baki, domin
tsawa zai daka min ko ya harareni, haka nake
rayawa a raina ba wai dan haka ta taba faruwa
ba.Iya tana yin wainar saidawa a cikin gida,
muna yin ciniki sosai, wani lokacin har da
sha'anin buki suna ko walima duk muna yi da
sana'ar ta take yi mana dawainiyar karatu ni da
yaya Aliyu, sai dan abin da sauran yara suka
kawo mata.Dan suma yanzu ko wanensu yana
nan da dawainiyar iyalansa, karatun ya Aliyu
shine mai cin kudi, dan Alokacin yana karatun
digree sa ne a jami'ar Ahamadu bello dake
zariya.Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Yana karantar (Engineering) ban san yanda zan
kwatanta muku ra'ayinsa ba, amma shi mutum
ne mai babbancin hali da ra'ayi.Bayan ya
kammala karatun sa ne ya dagewa iya yayyinsa
shifa sai yaje police Acadamy, wato makarantar
horar da manyan yansanda dake wudil jahar
kano, dakyar ya sha kansu.Ko da yake har sai da
kawunsu kannan iya dake Hadeja,Kawu Adamu
ne yaje har gida ya lallashi iya.Bayan ta yarda
tace, to ita fa bata da kudi,yaranta kuma suna
fama da iyalansu, dan haka yaje ya nemi
kudi.Aliyu ya ce, iya ai na fada miki asaida gona
ta, ta gadonmu da aka raba mana.Nan ma da
kyar ta yarda kawu Adamu shineya saida gonar
Aliyu yaje ya amsa, haka yayita zirga zirga
tsakanin kano da kaduna har sai da yayi nasarar
shiga police Acadamy.Ranar farko da yaxo ni
kadaice ina cikin wanke kayan waina bayan mun
tashi, iya bata nan taje kai kudin kayan miyan
wainar gobe, sai kurum naji sallamar sai naga
mutum tsaye kyam da kayan dan sanda riga blue
mai haske wando baki, ga wanan takalmin na su
da hula.Nikuwa dama gani da tsoron Dansanda,
sai naji cikina yana kugi, fuskarshi daure yace,
bakinki yana ciwo ne, bakya iya amsa sallama ko?
Cikin in-ina nace, wa...alai...kassalam.Ya zuba
min harara, yau ne kika fara ganina ne da har
zaki tsareni da idanu ko na can za maki ne?Na
sunkuyar da kai, a'a ya nufi dakin nace bata nan
ta je wurin Isa mai kayan miya, ya ciji ya tsa to
dauko min makullin dakina najena duba inda na
san iya tana ajewa na dauko masa da zan bashi
sai da na dan rusuna.Ya amsa ya nufi dakinshi
nazo na karasa wanke wanken na gyara gurin ya
fito cikin gajera wando da yar T-shirt irin ta
yansanda,Ina cikin kicin zan dora tafashen kashin
waina, yace baki san mutun yazo kiyi mai tayin
abinci ba, kenan ina ganin rowa zakiyi?Nace nayi
zaton ko kana azumi ne, na ga kullun kana yin
azumi,yace, oh, dama kina samun ido ne har kika
san cewa kullum ina Azumi?To yau ban yi.Nace,
duk abincin ya kare sai sauran tuwo kuma baka
cin dumame, sai dai in ko na dafa maka wani
abu.Yace barshi nasha cornfilakes,ya juya ya nufi
dakin sa.Na sauke ajiyar zuciya ban san meyasa
ba yaya Aliyu in yana guri bana so in tsaya a
gurin sai in ga duk ya cika gurin,gashi tsananin
tsoransa nake bai dai taba duka na ba watarana
ne dai da yake iya gadanga take ce masa sai tace
in kira mata shi, ni kuma naje nace iya ta ce kazo
gadanga.Wata tsawa da yayi min kadan ya rage
in saki fitsari, ya dora yatsinsa a dan manuni a
goshi na.In kika sake ce min gadanga sai na
zaneki tas kinji ko?Jikina yana bari nace, kayi
hakuri.Don tsoro lokacin har fitsari nayi a
wando.Lokacin da iya ta dawo tai murna da
ganin autanta, nan suka zauna suna yin fira, cikin
hirar ne naji tana yi masa zancen aure, inda ta ce
gadanga dan Allah ka nemi matar aure kasan
shekarunka nawa yanzu?Yayi dan murmushi ni
kwan nasan shekaruna, muke nan kullum cikin
rubuta date of birth ba dole in rike shekaruna
ba?Talatin da uku ne kacal.
Iya tayi dariya talatin da uku shine kacal?Ai dai
cikin sa'anninka ina tsammanin kai kadai ka rage
ba kai aure ba.Ya ce iya ba ni kadai na rage ba,
kin manta da usman?Ta ce, usman bikin shi kafin
Azumi ba kuyi waya bane?Aliyu ya zaro ido, iya
da gaske?Tace, ko jiya na kira shi na fada masa
yau zan shigo shi ne zai ki sanar dani?Iya ta ce
kila sai kazo din za ka ji zancen.Ya ce, iya kiyi
adu'a kawai amma ayanzu ba mata a ga bana,
kokari na in hada wanan course din nawa.Ta ce,
Allah ya taimaka.Ya ce sauran mu wata shida.Ta
ce, to Allah yasa a gama cikin nasara, ni dai fata
na ka zama mai gaskiya da amana, kayi aiki a
kasarka da kishi.Ya ce in sha Allahu, na gode.Duk
ina jin su har suka gama ya dube ni ita waccen
sunyi jarabawar J S. C.E din?Iya ta ce, tin yau she
har sun amso yan zu kici kicin shiga SS din ta
muke yi, ya ce zo ki bani saka makon na ki in
gani, dan nasan bawata kwanya ce da ke ba.Iya
ta ce, in ji wa?Sadiya boko da islamiya tana da
kokari.Na dauko gaba na yana faduwa na bashi
ya duba sanan ya kalleni babu laifi, amma kina
jin turanci?Na sunkuyar da kai, amma ban iya
bada amsa ba.Ya ce shirmen yaran hausawanmu
kenan, kuna jin tsoro ne kada kuyi ba dai dai ba
ayi muku dariya, to ai gara ayi muku dariyar
sanan a gyara muku.To ni dai daga yau kada ki
kara mun hausa.Har in koma duk kuma zuwan
da zanyi in baturanci zakiyi mun ba bana son jin
maganar ki.Iya ta ce, kuji mun fin karfin hali
gurin gadan ga, wanan ai mugun horo ne.Yare ba
na uwarka ba, ba na ubanka ba kace dole sai tayi
maka magana da si.Ya ce, in ba haka ba yau she
zata iya ga yanda zamanin namu ya zama sai da
karatu, ko da ta gama scondary zaki mata aure?
Iya ta ce, tana samun miji zan sallamata, don
haka kar ka takura mata.Ni dai nayi ciki na barsu
nan suna ta jayayya, yana cewa ilimi ko dan
tarbiyar yara ai ko ni ba zan auri matar da bata
ta shiga jami'a ba.Iya ta ce Allah ya taimaka ni
tawa tana samun miji zan turata can gidan
mijinta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment