Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

d'ankwali bata sakaba tabud'e kofar fuskanta a tsuke wani harar ta maka masa sanna tad'agokai ido biyu sukayi sai gashi duk fad'ar da tafitoyi takasa sabida wani irin kwarjinin da cika idon da ya mata kasa ta 6uka kome tayi sai wasu hawaye dake zuba mata da yake ya fita tsawo d'an rankwafuwa yayi yana smile yace " Didi kinfito fad'ane ko sai kika had'u da Yahya ko toh karki damu Ina sonkine Baby amma kina wani abu kaman yarinya karama akanki nasan me ye so nasan hakikaninsa karki k'i amsan tayyi na plss "yanda yake maganar har tana jin numfashinsa domin kad'an yarage fuskansu ya had'u da juna.

Tattaro sauran jarumtarta tayi tace " wallahi kabar gani ina sake makw fuska zansa6a kama ni ba sa'arka bace kaje kanemin yarinya karama irinka ko kunya bakaji ba wqini ce kake so shegan rashin kunyanku na Yaran yanzu yaro karqmin da kai har kasan kace wai nakarya maka azumin zan had'a kada Umma sai naga karshin rashin kunya " ranshin ba karamin 6aci yayi yarasa me zai mata kawai finciko tayi ya wani irin huci idanunsa sunyi jajar sabida kawai tace masa yaro bakinsa yakai da niyyar sumbatar ta sai yafasa amma ya matsita sosai da jikinki kofar d'akinta yace " wanna yazama kashidina dak na karshi inba haka saikin raina kanki turata yayi ya bar wajen ya koma mazauninsa yana tunanin banda abokinsa Ameer waye zai samu ya tayashi jawo hankalin Rukaiyya ne zurfi yayi cikin tunani har Inna ta shigo bai sani ba sai da tabuga kujeran kusa da shi kafin ya farga tace " tunanin me kakeyi haka na gama anan zaka sha ruwa ko agidan "

yace "Inna nagode gida zantafi dashi na sha a can "

murmushi tayi sanna "wato zaka kaiwa Ummanka ko toh kad'auki lema Deeja ta baka yana cikin y'arkaramin kwando asha ruwa lafiya "

yar dariya yayi yace " Innarmu Allah yabar manake nagode sai da safe "

tace " Amin Allah yakaimu "

fita yayi ya karbi y'arkwando yana murmushi aransa kuma yana tausayin Innane yazo yasata aiki gashi lokaci guda Didi yaga abinda yafi karfinsa tuno yanda take gudu yasa tsigar jikinshi soka mike tafiyar ma dakyar yakeyinta yana shiga cikin gidansu a falo yasa Umma da Y'arkanin Abbansu yasan halin yarinyar bata da kunya yanzu sai tace zata masa magana akan dinner ya aje kwando sanna ya shige d'aknsa kofar ya k'ule yacire kayan yashiga wanka yana fitowa yaji wayarsa tana ruri d'auka yayi ya sunan Abokinsa yace " kaii menakira na " daga can aka abokinsa yace "Ango tsohuwa ina kashi inata kira baka d'auka ba ko kaba waje sugar mommyn kane "
" Ina fa nashiga wankane kaddar ta fad'a kan azumin ne " Abu yace,

darian shakiyanci abokinsa yayi yace " taya haka tafaru "

"wallahi naga abinda yafikarfina nashiga gidansu preety ne " nan ya fad'a masa yanda sukayu yakara da cewa wallahi na narasa yanda zan b'uloma sabda tana da taurinka ga kafiya."


shawara me kyau Ameer yabashi daga nan sukayi sallama da juna.


🌹🌹🌹
Yanzu kan kowa yasan rashin jituwar da take tsakanin Abul da Didinsa kowanne su aka tambaya sai yace bakome domin basa son kowa yasan meke faruwa.


Ana cikin haka duk yaran gidansu Rukaiyya yan mata duk aka turo tambayansu inda Kanen Babansu Rukaiyya suka bata wahadin wata biyu tafi da
miji ko su had'a ta da duk wanda yayi musu.


Abin duniya duk ya dame ta tasar meke shirin faruwa gefe guda Abul ya hura mata wuta da na shi fitinan duk tafi haiyacinta ko abinci ta rage ci sai tunanin mafita.



🌹🌹🌹
Lokacin da aka d'iba mata ya kusan cika duk tasusuci Iyayenta ba karamin tausayi take basu ba Abul kasa hakuri yayi da halin da take ciki Inna ya tambaya meke damun Didi tace Yan uwan Babanku suka bata lokaci ta kawo miji shine hankalinta ya tashi " kallo Inna yayi sanna ya sunkuyar da kai kasa yace " Inna Inna Ina sonta da aure idan zaku bani ita zan sata farin ciki "


a razane Inna ta d'ago kai......πŸƒπŸΎβ€β™€πŸƒπŸΎβ€β™€πŸƒπŸΎβ€β™€πŸƒπŸΎβ€β™€ na fece
[6:49PM, 12/17/2017] REAL ME DAMBU CEπŸ₯—: β˜”β˜”β˜”β˜”β˜”β˜”
*YARO MA NAMIJI NE*
πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦



_🌹LOVE STORY🌹_






*REAL ME DAMBU CE*πŸ₯—



*Hikima Asso Writer's*
Ζ’Ι‘ΙΎΓ­Υ² cΓ­kΓ­nku Ρ•hΓ­nΡ” nΞ±muπŸ‘ŒπŸ»



*Aisha Aliyu garkuwa*
*Yasin masoyan Namiji bayi kad'an suna suburbud'ana fa har wasu na tunani ko rΡ”gΓ­nΡ” Ρ•Ρ”r nΞ±Ρ‡Γ­ wato satan buk dinki na juya don Allah kifito ki shaida musu bashi bane sun biyoni har bauchi narasa yanda zanyi da su Yar manga tana neman a gaji kafin su kadani kasa😍*




_Wallahi sis Sharifat bansanta ba asalima ni yar jahar bauchi ce nagodo sosai_😍



1⃣1βƒ£πŸŒΉ 1⃣2⃣





A razane Inna ta d'ago kai tace " kana da hankali kuwa ko so kake jawo min magana a ce mun lika maka ita ko toh wallahi kafita idanun kafin na had'a ka da Ummanka "

shiru yayi sanna yace " Inna don Allah kiyi hakuri amma wallahi ina sonta haka ni bai dameni ba duk wanda mutune suka d'auka ko'ajikina "

mamakinsa ne yakamata tace " toh kafita min bana son ganinka anan"

kintashi yayi cigaba da zamansa kaman ba dashi take ba abinda ta lura shine kuka Abul yake hawaye ne sosai ke zuba daga idanunsa sai jikinta yayi sanyin tausasa murya tayi tace " Yahya bawai ina k'inka da Rukayya bane a'a kawai bana son tashin hankaline nasan halinka nafi kowa sanin nagartattun halayanka amma me zamu cewa mutane ko a cikin gidan nan wallahi sai Rukayya ta fuskanci matsala ballatana a waje wasu hujjoji muke dashi da zamu kare ta dashi ga matsala kaduba dakyau kaje kayi tunani kadawo karka fad'awa kowa fa"

hawaye ya share yace " Inna kafin na fad'a miki wallahi sai da nayi har istahara nayi kuma wallahi har yanzu ina jin son abu sosai don Allah ki taimaka min ki ceto rayuwata Didi ce kome na"


shiru tayi takasa magana tunda taga yana share kwalla tasan ba karamin son Rukayya yake ba toh ya zatayi da mutane .


Ashe duk hirar da suke akan kune Inna Kulu murmushin mugunta tayi tace" Saima(sunan Inna kenan) wallahi idan ina raye ba karan da zaizo wajen Rukayya sai na hanata jin dadin rayuwa kwafa tayi dole gobe naje wajen me buzun kura asake samata mugun bakin jini wanda dole ka gudu da kafarka yanzu gidan zani na zuga Uwarka ta hanaka "


🌹🌹🌹
kewayarsu takoma tafinciko wani kod'ad'in gelaita tafita sai gidansu Abul tashiga tasame Umma da baki donko cikakiyar sallama batayi ba " gaisuwar ma sama sama sukayi sabida gulma ya ciwu ta kaman har tana tauna harshenta sabida gulma sannu sukaita mata tace "hmm Hajiya Abeeda kina nan ga Abul khairi yana can ana tusa masa wanca ragowar maza don haka kiraba su inba haka ba toh za'a kwaso miki damuwa "

Umma da ta fahimci maganar Inna kulu murmushi tayi tace "Kulu kenan wace miki muna hana yaranmu farin cikinsu duk abinda suke so indai ba sa6awa shari'a ba toh muna Son kuma kina magana ne akan Rukayya toh Wallahi in akwai wacce tafi Rukayya shekaru kuma yace ita yake so wallahi zamu nema masa ita balle kuma Rukayya yarinyar da ba ruwanta zaki iya tafiya"

kunyane yakama mata cike da borin kunya tace " ba kome na gode sai anjima ku"

fita tayi ranta a bace tace "wallahi koda zanyi yawo tsirara sai na hana aure "

wata daga cikin bakin Umma tace " da alamun y'ar kishiyatar ce ko takawo gulmarta "


takaice ne ya kama Umma tace " ko d'aya wallahi y'ar wan mijintane fa take kishi da Uwar yarinyar yanzu tanayi da y'ar kuma " tsaki tayi .

D'aya matan tace "Allah yakyauta "

"Amin "suka ce,

🌹🌹🌹

fitar Inna kulu kuwa ranta ba karamin 6ace yayi ba kasa hakuri tayi tace " indai ina raye sai na hana wanna auren zaku gani gobe me buzun kura zamin maganinku "kwafa tayi.


A zauren tsakiya suka had'u da Abul ko kallo bata ishe shi ba wucewa yayi abinsa.


koda ya isa yasamu bakin zasu tafi wajensu yaje ya gaishisu suka ce toh " Abul yaushe zaka kawo mana sirikar mu munganta "

murmushi yayi yana shafa kai yace "very soon "

suka ce " Allah yasanya alkhairi ." "Amin " Umma tace,

bayan tafiyarsu ne Umma ta harare shi kafin tace " yayi kyau kasan al'adan gidan nan bama hana kowa ra'ayinsa shine kake boye min damuwarka har sai wasu sunzo sun fad'a min bazamu hanaka neman Rukayya ba amma ninafi kowa dacewar kafad'a min "


shiru yayi har suka isa falo tana zama yazo ya d'aura kansa a cinyarta yace " kiyi hakuri ina tsoran kobazaku yarda bane amma kuyi hakuri bazan sake ba" nan ya fad'a mata yanda sukayi da Inna murmushu tayi tace ba kome zansame ta.



🌹🌹🌹

Washe gari da sa safe Inna kulu tayi sanmakon tafi wudil wajen me buzun kura ta fad'a masa kome zane a kasa yayi yagoge har sau bakwai kafin yace " tabbas auren zayu kuma duk wanda yayi kokarin dakatarwa mutuwa zai sabida rabon dake tsakaninsu "

tace " nashiga uku yazamuyi bana son tayi aurene a rayuwar duniya"

yace " akwai mafita d'aya shin..........


Maman waleed ce
[11:47AM, 12/18/2017] REAL ME DAMBU CEπŸ₯—: β˜”β˜”β˜”β˜”β˜”β˜”
*YARO MA NAMIJI NE*
πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦






_🌹LOVE STORY🌹_




*REAL ME DAMBU CE*πŸ₯—



*Ayya wai ina kuka shige ne Auntyqueen mermue da sis Billy ladan sis Meelat ahk ina tanemanku*πŸ˜”Duk inda kuke Allah yasa daku da alkhairi.

*Wato na lura kufin son Abul fa ita Rukky bata da Team sai shi bari naga Abul da Rukky waye yafi Fans saura ku nuna son kai*πŸ€• luv oll😍
idan kuka ba abul zuciya nikuma na zugata takawo wani guy....😜





1⃣3βƒ£πŸŒΉ1⃣4⃣










" A kwai mafita d'aya shine bari na duba wani abu akansu" nanma zane yayi ya goge yasake ya goge wani irin zufane yake karyo masa kama wanda ake watsa masa ruwa kallonta yayi cike da karya yace " a gaskiya Yaro nan bakaramin son yarinyar yake ba gaahi har Uwarsa ta amince haka kuma suna tsaye akan wanna alamarin abinda ya dace shine akan yarinyar zamuyi aikin duk da itama bata wasa da ibada sai dai a duk lokacin da take cikin matsanancin bacin rai bata saurin ambato Allah da wuri don haka zamu tura mata wanda zaisa mata k'iyayyar yaron sosai a rainta yanda zata tsane shi amma shima ba wani dogun aikin zayi ba sabida duk rananar da ya kusanceta karfina maganir zai ragu don haka dole kikula kisan yanda zaki jata ajikinki har tasake dake sai ki hanata yarda da shi kinuna rashin fahimta yasa baki kula amma yanzu kome ya wuce."

shiru tayi tace " anya me buzun kura nasan halinta tuntana Yarinya nake k'inta zata yarda dani kuwa "
tsawa ya buga mata yace " duk abinda kika ga dama kiyi 6ace min da gani kafin nasa a juya miki kanki baya ga wannan hayakine kinayi aljanin k'iyayyar zai baiyana aikin hayakin amma ku lura da lokacin da take cikin da 6acin rai kome kashinsa zaiyi amfani fita min da gani "

jikinta har wani rawa yake sabida tsoran wani banza.

🌹🌹🌹

Bayan ta gama labaran cikin harshin turanci karfin tara na safe d'akin rawotanni ta shiga tasami kawarta Zulfa'u sau d'aya ta kalleta sannan ta kauda kai tayi ta zauna shiru yabiyo baya Zulfa kasa hakuri tayi dole ta katse shiru tace "Rukky magana na gaskiya shine babu yanda za'ayi kisami miji a wata biyu kacal sabida baki san halinsa ba shima baisan naki ba ina ganin kiyi hakuri da Abul mana inda bake koshi wani cikinku yafad'a Abul bai kai talatin ba wallahi bawanda zai sani tunda har yafito ya fad'i miki yana sonki kawai ki amince sabida kinsan halinsa gaba da baya."

cike da masifa ta kalle Zulfa tace " haba dai yaron danayi masa hidima tun yana karamin kice na yarda na amince da shi akan yana sona habawa wallahi da sake duk wani sirrina duk saiya bude har nayi rayuwar aure dashi kai kai mun kwanta gado d'aya sanna nakira shi da Uban Yarana tab badani ba wallahi gwara najira subani kowani irin mutum amma banda sa'ar Yaseer "

dariya Zulfa take kyalkyalewa har tana dukan tebirin tace " wayon cikina Rukky Alhassan zakiyi abin kunya ko na ga haka shiyasa duk lokacin da yazo nan jikinki har wani rawa yake sabida tsoransa amma ba damuwa wata rana kece zakiyi haukansonshi Narantsen da Allah sarki"


bata sake kulata Zulfa ba sabida ta lura zata kara mata wani ciwon kaine.


🌹🌹🌹
Da dare bayan dawowar Alhj Attahir suna hirar yake fad'a mata irin nasaran da suka samu xuwan Abul wajen sayard da motocin ba karamin riba suka samu ba fatan alkhairi Umma ta masa sannan tace " Alhj Abul fa aure yake nema a cikin unguwar nan"


shiru yayi da jin abin dariya can ya sa dariya yace" yaunshe ka haife shi da zayi tunanin aure ? kuma wacce yarinyan ce haka da ta6ata lokacinta akansa ?"



haushin maganar Umma taji tace " ba shikenan ba amma yakamata kasan halin da yake ciki shine gaskiya domin ko azumin da yake ai da yakare kanshi yake amma ba damuwa."


Murmushi yayi kafin yace " wallahi Abeeda ina son yayi nima nasan me yasa yake azumin amma wacece Yarinyar "


"Rukayya ce yar gidan Alhj Hassan ce daga ita yarinyar har mahaifiyar ta sunki yarda sabida suna gudun abindan mutane zasu ce " abinda umma tace kenan,


farin cikine ya kama shi yace" wa Adamu naso haka ashe Abul shine mijin toh gobe da asubahi zama Alhj Alhasan magana shikenan inyaso ita yarinyar kwaji da ita



🌹🌹🌹

Inna kiranan Sa'idu yayansu Rukaiyya tayi ta fad'a masa yanda sukayi da Abul yace zaizo su maganar bata waya bace.


gashi sauran kwana hud'u wahadin yacika duk ta d'imance kaman wacce akace wahadin mutuwar tace.

πŸ€ΈπŸ»β€β™€πŸ€ΈπŸ»β€β™€πŸ€ΈπŸ»β€β™€πŸ€ΈπŸ»β€β™€πŸ€ΈπŸ»β€β™€πŸ€ΈπŸ»β€β™€


Mmn Waleed ce
[8:22PM, 12/18/2017] REAL ME DAMBU CEπŸ₯—: β˜”β˜”β˜”β˜”β˜”β˜”
*YARO MA NAMIJI NE
πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦



_🌹LOVE STORY_





*REAL ME DAMBU CEπŸ₯—*





_Y'AN UWANA MARUBUTA NAGODE ABISA ADDU'OIN DA FATAN ALKHAIRIN DA KUKE MIN INA ALFAHARI DAKU_


*Wanna shafin bana kowa bane nakune sadaukawar*



*_DAMA TA FANS_*

*_MISS _ MARRIAM NOVEL GROUP_*

*_NASIBI WRITER'S ROOM_*

*_MUMMY RABI_*



*_AUNTY BINTA BABANGIDA_*

*_MY RIGIMATION_*😜

*_MAMAN SADEEQ_*
KALPANAπŸ’…

*_MOMIN NASRIN_*😍

*_MMN AMAL,MY SHEMA,ADDAN JELATA,MMN NOOR,MMN'AL'AMIN,NEENA,_*
Da wanda basu ji sunan ba inayinsun sosai😍

Mmn meenat Allah yaba yarona lafiya🀧



*Deeja Waziri tare da Bie bie dee ina tayaku murna k'anmala buks dinku lafiya Allah yabaku ikon fara sabi lafiya*🀝🏼





*Naki daban ne Aunty maijidda musa* Ana tare🀝🏼


🎁H.A.W.🎁


1⃣5⃣ 🌹1⃣6⃣

Bayan Inna ta gama waya da Sa'idu sai takira Yaseer wanda yake service a ondo ta fad'a masa ay shikan kai tsaye ya amince dariya yayi kafin yace " Inna wallahi billahi azim Abul khairi shi yafi dacewa da Didi sabida nasan halinsa ciki da waje banda Didi banta6a jin ya kira wata mace a gabana ba yankance shi in Allah zai bashi mace ya bashi mace kamila kama Didi kullum maganarsa kenan tun muna scndry har muka rabu ya tafi gana duk wani saurayin da yazo wajenta shi yake koransa lokacin da na tambayi shi meyasa yake koran mata Samaruka cemin yayi wallahi baisani ba amma da zarran ta ganta da wasu maza ranshi ke 6aci duk hutun da zai koma Inna wallahi sai yayi kuka sabida Didi Inna Abul nasonta son da wallahi baki bazaiya furutawa ba amma kitunani akan haka duk zuwansa tsarabanta yafi nakowa amma duk yanda kukayi shine mai kyau "

wani farin cikine ya rufe Inna tace "ba damuwa bari naji me Y'ayanku zaice ."

Da wannan sukayi sallama


dan haka yanke hukumcin fad'a ma Babansu da ya dawo ta fad'a masa shima dariya yayi yace " toh shi kuma wato sunna zai d'abaka ko Allah yasa mudace amma fa tayi mashi girma ina shi ina Uwar d'akinsa banda namiji toh Allah ya tabbatar "

"Amin" Inna tace,


🌹🌹🌹

"karfe biyu da rabi na dare mafarkin da yasaba akanta y'au ma shi yayi dole ya tashi yayi wanka ya d'auro alwala sannan ya tada sallah nafila raka'a biyu yayi sanna ya d'auki alqur'an yqfara karatu ya dade yana karatu kafin ya rufe ya fara kwararo addu'a akan Sahibarsa Allah ya dai daita al'amarinsu nanma ya dade kafi ya tashi ya kwanta.

Da asubahi ma saura kad'an ya makara sai da Abbansa ya tada shi bayan an idar da salla ne duk suka fito shikan gida ta tawo Abbansa ne ya tsaya da su Baban Rukayya bayansu gaisa ne da yake dukkansu Baban Rukayya da Kanensa Abban Abul yace " gani dai a gabanku amma narasa me zance muku bansa ya zaku d'auki abinda zan fad'a ba "

shiru yayi


Babansu Rukayya yasan kwanan zance amma yafi son yaji daga bakin Alhj Attahir

duk sun kagu da son jin meke tafe dashi Baba Yakubu ne yace " Alhj karka damu ka fad'a mana kawai "


ajiyar zuciya yayi kafin yace " daman Yahya ne yake niman izinin neman auren Rukayya "

duk mamaki ya rufe su Baba Hameed ne yayi karfin halin cewa " Alhj kansa me kace kuwa "


"ehh dagaske nake fa ba da wasa ba saidai ko baza ku bashine " yace,


Baba Tanimu yace " a'a ba haka bane kawai muna gudun magana ne amma tunda shine yake son mun bashi ita Allah ya tabbatar"


Baban Rukayya baice kome ba sai murmushi da yayi.


Baba Baseeru yace " Yayan baka ce kome ba sai fama murmushi kake "

dariya yayi kafin yace " me zance tunda shi Yahya duk Yan mata unguwar nan basuyi masa sai tsohuwar y'arku " sai kuma yarike baki alamun yayi
kato6ara.

Dariya suka saka dukkansu 6ata rai Abban Abul yayi yace " bana son haka fa Alhj hassan y'artawa ce tsohuwa bakai ba takwara na fad'a maka "


dariya sukayi masa haka suka rabu cike da raha da farin ciki sai tattaunawa suke har suka shiga gida lokacin shida da arba'in da biyar dai dai itama tafito kenan tana da labarun karfe bakwai sai sauri take a dai dai zauren cikin gida suka had'u tsugunawa tayi kasa ta gaishe su , duk suka amsa Baba Hamisu yace " mamana muna sa idonki fa gobe inbaki samun ba toh munyi miki miji "

a razane ta d'ago kai sai kuma ta mayar kasa tace " bani da zabi sai naku "

Baba Tanimu yace " jeki Allah yayi miki albarka a dawo lafiya"

"amin " tace,


sukuma suka shiga gida kowa ya kama gabansa zuwa aiki.

🌹🌹🌹

A wajen aikin ma dakyar tayi aiki domin bata da kuzari har tashi daga aikin me nape ya kawo ta tana sauka tabiya kud'i zata shiga ashe shima yana kan motarsa durowa yayi yasa kananun kaya sajinsa da y'ar gemun wanda suke had'i da juna sunsha gyara fuskansa tayi wani fass da shi cikin takun kasaita ya shiga zauren yayin da ita kuma take tafiya cikin nutsuwa har tashigo zauren kamshin turarensa ya shaka sai da ta lumshe idanun ta kafin ta bud'e akasan shima ita yake kallo yace " Preety barka da dawo nasan kin gaji da yanzu kina da miji ai dasai yayi miki wanka ya baki abincin da ya dafa da hannusa ko "ya d'aga mata gira.

Tsaki ta ja bata san lokacin da bakinta tace " d'an iska Yaro kawa....."😳


Mmn Waleed ce
[11:09AM, 12/19/2017] REAL ME DAMBU CEπŸ₯—: β˜”β˜”β˜”β˜”β˜”β˜”
*YARO MA NAMIJI NE*
πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦




_🌹LOVE STORY🌹_




*REAL ME DAMBU CE*πŸ₯—





*Ba danku ba da daga y'au wanna buk din ya koma tarihi amma kuka bani kwarin gwiwan rubutawa har nake tashi da niyyar rubutawa dan haka bani da Bakin muku godiya sai dai Fatan alkhairi a rayuwarku* kuncire min tsoro kunsamin jarumta
Ρ•tΞ±Ρ‡ Γ­n Π²lΡ”Ρ•Ρ•Γ­ng Ρ•Γ­Ρ•tΡ”r'Ρ•.






🎁H.A.W🎁



1⃣7βƒ£πŸŒΉ1⃣8⃣



"Rintse idonsa yayi da danasani mata magana bai ta6a tunanin zata iya zaginsa ba don haka y'au sai ya ladabtar da ita akan laifinta.



harta bar zquren farko tashiga zaurem tsakiya yana biye da ita itama taji tsoro don sauri take sosai tashiga gida domin jikinta yana bata Abul baza kyaleta ba.



Suna shiga zauren cikin gida da yake yana da zurfi ga d'an duhu kafin ankara ya sha gabanta fuskansa d'auke da murmushin mugunta yace " nine d'an iska ko ? y'au zaki ga iskanci ya ganin idanunki "



jikintane ya fara rawa kaman wacce aka shekawa ruwan sanyin gashin garin ya d'au hadari har wani irin duhu yayi wanda yakarawa zauran duhu sosai.



Takowa yake ita kuma tana ja da bayan sai yarfe hannunta take ta raraba idanu kama kace kyasss ta zura a guje har takai jikin bango sai tsaya ta fara kokaran bashin hakuri had'a hannuwanta tayu alamun yayi hakuri ko takanta baiyi ba




hannunsa yasa ya dafa bangon d'aya hannun yana rike da phone dinsa mayar da phone din yayi aljuhun wandonsa kafin ya kama lips dinta da yatsan hannunsa

guda biyu ya d'anke su sosai yana murmushi mugunta yace Didina kenan dake a tunaninki sumbatarki zanyi koda wasa bazan fara ba amma wannan shine hukumcin laifinki don idan zamu kwana qnan bazan sake bakinki wanda bayi iya magana ba tunda ke haka Allah yayi harshinki muzuba waye zayi nasara ni da ke."

duka da yakushi yashata bana wasa na tun tanayi harta hakura hawaye nazuba shakaf fuskanta ya jike da ruwan hawaye yarfe hannunta take takuka amma ko ajikinsa.


Karshe dataga tana shirin illatata tureshi tayi amma yanda kukasan bishiyar rimi haka taji shi ta kid'ima ta gigice tarasa yanda zatayi dole ta had'a jikinta dana shi yayinda ta tura akanta a fad'id'in kirjinsa dole yasa yacire hannunsa wanda hakan yasa tasake kuka me cinrai jikinsane yayi sanyin domin yasa bekyauta ba kukanta yana dukan zuciyarsa dan haka ya cireta a jikinsa yace "kiyi hakuri haka bazai sake faruwa ba"

jakanta ya d'auka ita kuma tabi bayansa yana tafe yana ambaton Allah.


shigansu kenan wani mugun hayaki me shegen wari ya biyo iska tashiki kamshi amma abin mamaki shine Abul baiji ba sai ma ambaton Allah da yqke jin wanna warin yasa kanta yayi wani irin sarawa wanda sai da tace " wayo Allah na "

jirine yake nema kwashe ta yajuya da sauri ganin tana layi kaman wata y'ar maye yasa da gudu yaso tare tadaka masa tsawa tace" karka tabani na tsane ka bqna kauran ganinka kuma idan baka fita harkata zaka sha mamakina "

Baba Tanimu ne yafito ya ga dawa Rukayya take fad'a yana fitowa ya ga Abul yana kallonta kama wani dolo ranshi ya bace amma ya boye gani Baba tanimu.


Fad'a Baba tanimu yarufeta da shi sosai " yace" tunwuri ki kaman kanki domin baki da mijin da yafi Yahya mun bashi ke daga y'au karna sake jin magana me kama da haka shashasha kawai "

ihu ta saka ta zauna a wajen ta kuka tana cewa " wallahi bana sonsa gwara mutuwana akan na zauna dq shi wallahi kuka kashe kawai dana zauna da wannan d'an iskan Yaro "

tab da Rukayya tasan Kanen Babanta suna gidan dukkasu ta bata fad'i hakq ba abin yayiwa kowa zafi don duk suka fito suka ga yanda take birgima a kasa shi kuwa Abul mamakinta yake ji.
Komawa suka sabon shiri akanta basu fito ba sai da bulala dukkansu shidan suka rufeta da duka bana wasa sabida ransu yayi mugun 6aci a tarihin gidan itace ta fara musu jayaya akan aure idan suka ce farine to farinne Abul gani irin dukan dasuke mata yasa yashiga ya rufera ya rungumeta itama sabida azaba buya yatai a jikinsa duk da tana jin kama ta ana watsa mata ruwan zafi.

Dole suka hakura suna ce mata "aure babu fashi kokiyi rai ko kimutu."


🌹🌹🌹

A d'akin Inna kulu murna take har tana rawq shigowan Baba tijjani yasa ta zauna yana huci.


koda Abul yakai Rukayya Inna ko kulata batayi ba tace" Yahya jeka Allah yayi maka albarka"

"amin" yace,


🌹🌹🌹
gani abinda Rukayya tayi yasa aka saka bikin da yake har ankawo sadaki Abul da kayan na gani ina so kuma haka hanata zuwa aikin gaba d'aya Babanta yace don tana aikin yasa take bijiru musu
daga yau ba'aiki.....


*ABUL KHAIRI BASHI DA TEAM SAI RUKKY*

Inda kuna yinsa mun tani a kasa😜😎

Mmn waleed ce
[6:36PM, 12/19/2017] REAL ME DAMBU CEπŸ₯—: β˜”β˜”β˜”β˜”β˜”β˜”
*YARO MA NAMIJI NE*
πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦πŸ’¦




_🌹LOVE STORY🌹_






*REAL ME DAMBU CE*πŸ₯—






*H.A.W*


1⃣9βƒ£πŸŒΉ2⃣0⃣





Duk abinda Rukayya keyi Inna bata kulata ba kullum Abul yana zuwa idan yazo Inna takan basu waje sai ta dawo kin sukuma suna falon bakar
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment