Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kamo nata hannun d'agata yayi a hankali ya jingi nata jikin kujerar da take zaune ya kamo hannunta a hankali ya fito da ita ya sake bud'e k'ofar bayan ya dauko jarkar nono da ledar fura yarufe kofar ya juyo yace,
" mujeto". baki ta tsuke cikin kuka ta noke hannu batare datace
Komai ba,
rusunowa ya d'anyi yana kallon fuskarta yace,
"menene kuma? ai nace kiyi hakuri".
Kai kawai ta d'agamai shiko ya aje kayan hannun nashi sannan ya matsota ita kuwa tana yarfa hannu fuska cike da k'ollah jawota jikin shi yayi ya ruggumeta yana maida numfashi. Ƙyana rungume da ita yasa daya hannun yad'au kayan ya jata sukai cikin gida,
Kai tsaye d'akin ta ya wuce ya zaunar da ita bakin gado shima ya zauna yai kasa da murya yace,
"kinga kiyi hakuri kiyi wanka kiyi sallah sai muyi magana".
fuska ta sake raunatawa tace, "gun da ya Adam ya mareni kemin zafi".
hannu yasa yana shafa gun yana hura iskar bakin shi agun itama tana k'ara manna hannun nashi a gurin tana dad'a shigemai, duk ta rud'ashi ta gigitashi bakin shi na rawa yafara magana cikin susucewa da wani irin Shauk'i da wani irin salo yace,
*"Ummul ina sonki* so mai tsanani, bantab'a son maceba saike, wallahi Ummul da sonki nake rayuwa nasoki tun bakisan kanki ba, a jinina sonki yake wallahi duk abinda nake miki bantab'ayi da wata manufa ba face so da kulawa kiyi hakuri da duk b'atamiki danai *ina sonki* dashi na rayu".
Yakare maganar da had'e bakinau guri d'aya yana ma harshenta tsotsa mai ratsa zuciya, gaba d'aya ya gigice ya zauce a kanta cikin rawan jiki da murya yasa hannu biyu ya tallabo habarta tare da k'ara manna lips enshi kan n......






By
*GARKUWAR FULANI*
[2:45PM, 11/6/2017] β€ͺ+234 806 779 9926‬: πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡

*RUBUTACCEN AL, AMARI*

Page 2⃣5⃣

*Na*
*AYSHA ALI GARKUWA*

πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡





*Wannan shafi naki ne Anty Fauzah Allah bar zumunci da k'auna*




*K*issing enta ya rink'ayi cikin wani irin salo mai ratsa zuciya gaba d'aya ya hargitse sai numfashi yake fesarwa a gaggauce cikin kula ya kontar da ita fuskarshi ya saita da nata hancinsu na gogar juna yayin da ya cusa hannun shi yana shafa cikin ta da k'irjin ta ido ya lumshe tare da laso jajayen lips enshi da suke shek'i cikin rad'a da tsantsar so yace,
" Ummul ina sonki tun randa aka haifeki nasoki fiye da zaton zuciya ta,
Khairi ki yarda dani kece farin cikina ki cire zargi ko zaton bana sonki ki sani kece farin cikina zan rayu da sonki a zuciyata har gaban Abadan Khairi ki jik'aina nima ki soni ki yarda dani a matsayin mijinki uban y'ay,anki".
sai kuma yayi shiru yana kallon fuskarta yadda ta lushe ido hawaye na bin habarta,
ita kuwa Ummul lumshe idon tayi tana kallon fuskar Hamman nata ta tsakanin gashin idanun ta,
tana jin yadda ya kife tattausan tafin hannun shi kan k'irjinta yana mata salon so mai wuyar mancewa,
a hankali ta k'arisa bud'e idanun nata jin wani damshi na d'iga kan wuyanta,
cikin raunin zuciya ta Kalli fuskar Hamman nata dake zubda k'ollah,
wani irin yanayi taji a ranta ganin yadda Hamma Umar keyi mata yana yin so,
shi kuwa zuge zip d'in rigarta yayi cikin rauni da sanyi ya cusa kanshi a k'irjin ta a hankali ya rink'a murza kan nashi kan k'irjinta yana wani irin numfashi gaba d'aya jikin shi rawa yake yi ba abin da yake iya furtawa sai,
"Khairi ina sonki so mai tarin yawa kece burin raina,
Anti tamamu sururi,
kece cikon farin cikina".
sai kuma ya kuma kife kanshi kan k'irjin ta,
gaba d'aya ya rikita Ummul ta kasa furtamai kalmar,
"bana sonka".
da take son fad'an sai cusa hannun ta tayi cikin sumar kanshi tana damk'e sumar tana dan yin mik'a,
kiran sallan magrib da akayi ne ya dawo da Hamma Umar d'in hankalin shi,
a hankali ya dago kanshi cikin sanyi ya tsura mata ido tare da cewa,
"Uhibbuki fillah,
ina sonki sabida Allah,
ba dan wata manufa ko surar jikin kiba".
sai ya kuma ruggumeta tare da cewa,
"Kuma wallahi tallahi,
As'attu li wajattu zawajiki,
nayi farin ciki da samun auren ki,
har Abadan bazanyi nadama ba,
domin,
kunti ba'adu jasadi,
kin kasance wani sashi na jikina,
har kullum ina cikin farin ciki tunda,
kunti lagamee,
kin zamo tawa".
sai ya kuma shafa fuskarta sannan ya juya cikin sanyi ya nufi hanyar fita,
har yaje bakin k'ofar sai kuma ya tsaya jin Ummul na cewa,
"Toh ai ni bana sonka Hamma Umar bana k'aunar zama da kai na tsaneka tunda ka rabani da Mustapha".
juyowa yayi cikin zafi da kishi murya na rawa yace,
"Wat...! wata...! wata rana zaki soni Ummul na tabbatar wata rana zaki kasance mai tsananin sona khairi sai dai ban sani ba ko son zai amfanemu,
amman tabbas zaki so Hamma Umar d'inki fiye da kowa a duniya".
sai kuma yayi murmushi mai zafi ya fita ya nufi masallaci,
ita kuwa kife kai tayi tana kuka tana dukan cikin ta daya fara girma tana,
"bana sonka Hamma Umar bana son cikin nan ni bazan haihu da kaiba na tsaneka na tsani cikin naka".
haka tai ta kuka har muryarta ta disashe,
cikin kukan tayi wonka tazo tayi sallah bata tashi a wurin ba har saida akayi Ishah,
sannan ta fito parlour ta zauna a k'asa kan carpet tana kallon TV tashan Bollywood,
shi kuwa Hamma bayan an idar da sallan ishah d'in ne ya dawo gida,
a parlour ya sameta sai ya kauda kai ya wuce bedroom enshi konciya yayi ranshi cike da tunani kala-kala,
ita kuwa tana ganin ya wuce ta mik'e ta biyo bayanshi tana zubda k'ollah dan yunwar da takeji har jiri na d'ibarta,
tana shigowa ta zauna gefenshi cikin tura baki tace,
"yunwa nake ji jiri nake ji duhu nake gani ni zanci abinci".
kallon ta yayi cikin nitsuwa yace,
"plxx karkiyi kuka bari in kawo miki".
Kai ta gyad'a tare da cewa,
"toh Hamma in nayi shiru naci abincin zaka zubarmin da cikin ko?".
Kai ya juya tare da cewa,
"ehh zamuyi shawara".
A haka ya kawo mata abincin da Nenne ta had'o musu ya zauna sukaci suka sha sannan ya taratara wurin,
ita dai binshi da ido kawai takeyi,
she kuwa wonka yayi sannan ya fito ya murza jikin shi da mai da turaruka,
sannan ya had'o mata tea ya kawo mata,
ba musu ta karb'a ta ajiye a gefenta
sai kuma ta juya suna fuskantar juna cikin zak'uwa tace,
"toh a cire cikin".
murmushi yayi cikin hikima da tunanin dabararsa zatayi mishi aiki dan ya gama sanin Khairin akwai wauta,
ita kuwa ganin yayi murmushine ta rink'a yarfa hannu da tutture k'afafu dan tanaga yama maida ta mahaukaciya Keenan,
da sauri ya jawota jikin shi cikin hikima ya tura hannun shi cikin rigarta ya d'an murza cikin a hankali ya d'ago fuskarta cikin rad'a yace,
"kina son in cire cikina ko? ".
da sauri tace,
"eeh a cire yana damuna ".
ajiyan zuciya ya sauk'e cikin hikima da wayo da dabaru irin nasu na doctors yace,
"ki dena kuka zan cire d'ana tunda bakya sonshi amman fa ba yan zuba dan in nace zan cireshi yanzu zaki iya mutuwa,
kuma yarinyar ma zata iya mutuwa,
kinga su Abba da Daddy zasu gane kuma Allah zaiyi fushi damu dan munyi kisan kai".
da sauri ta kalleshi tare da cewa,
"toh Hamma sai yaushe za, a cire cikin? ".
murmushin jin dad'i yayi ganin hikimarsa tayi aiki a sauk'ak'e ruggumeta ya k'arayi cikin sauk'e ajiyan zuciya yace,
"sai cikin yayi wata 7 sai in cireshi sai nasa d'ana a cikin kolba daga nan inci gaba da renon abina kekuma kinga shike nan kin huta,
sai incewa su Abba bakwaini kika haihu".
ido ta tsura mai cikin nazartar maganarsa,
shiko sai shafa cikin yake yana lumshe ido,
a hankali ya bud'e idon nashi jin tana cewa,
"ni dai a a wallahi har wata bakwai gaskiya bazan iya ba".
kallonta yayi cikin sanyi yace,
"ai kamar yaune kinga fa yanzu cikin ya shiga wata na 4 kinga kenan wata 3 kawai zaki k'ara".
da sauri tace,
" a a ni a canza dabara".
Ajiyan zuciya yayi cikin jin dad'i yace,
" yauwa toh dabara ta biyun tafi sauk'i sai dai nasani bazaki yarda ba".
da sauri tace ,
"fad'amin inji zan yarda".
murmushi yayi sannan yace,
"in kina son cikin ya zube da wuri sai kin yarda dani na rink'a yin pakala dake kullum safe da rana da yamma kuma ki rink'a taimaka min muyi sosai hakan zaisa bakin mahaifarki ta bud'e daga nan baby zata fad'o sai incewa Abba zuban gaskene kuma Adam bazai dakeki ba".
cikin rashin fahimta tace,
"Hamma mene kuma pakala da zamu rink'ayi safe da yamma da dere da rana?".
k'ara matsota yayi cikin kauda Kai ya lumshe ido tare da cusa hannun shi kan mararta yana d'an shafawa yace,
"Hmmmm baki san pakala ba?".
"ehh ban saniba".
zip d'in ta ya zuge cikin kasala yace,
"Saduwa ne Pakala ki yarda in rink'a kusantar ki kullum a k'alla sau 3 ki kuma taimaka min muyi komai tare,
in kin yarda dai ba mamaki cikin ya zube kafin wata 7 d'in".
baki ta tura tace,
Kai dai ka fiye jaraba kuma ka sani ni bana sonka".
Kafad'unshi ya d'aga tare da cewa,
"Toh kin huta sai ki jira wata bakwai d'in in baki yarda ba".
Shiru tayi tana tunani shiko kan gado ya koma ya lumshe ido kamar maiyin bacci,
ta dad'e a zaune tana nazari,
sannan can ta mik'e a hankali ta koma kan gadon cikin sanyi ta zauna gefenshi murya can k'asa tace,
"Na yarda Hamma".
kauda kai yayi,
yayi ta murmushi sannan yasa hannu ya jawota jikin shi,
kayan jikin ta ya zare mata sannan ya zare nashi blanket ya jawo ya rufesu a hankali yasa hannun shi yana murza al'barkatun jikin ta,
shiru tayi cikin lumshe ido,
ganin bata taimaka maine yace,
"ko dai bakya so ne in barki da cikin ki?".
cikin kasala tace,
"inaso mana ".
murmushi yayi sannan yace,
" toh ki tayani muyi tare duk abinda nayi miki kiyi min inba hakaba in fasa taimakon ".
ba musu ta fara maida mishi martani,
gaba d'aya sun gigice Sun shiga duniyar ma aurata ita kanta Ummul salon Hamman nata na yau ya wuce zaton ta,
shiko Hamma Umar ya samu gamsuwa iya gamsuwa da y'ar k'anwarshi sai al'abarka yake samata.

Haka suka kwana mak'ale da juna,
koda gari ya waye yana dawowa masallaci kai tsaye d'akin Ummul d'in ya wuce ya kwashi garar kafi shayi dad'i,
haka rayuwa tayi ta juyawa tana tafiya gaba d'aya yanzu Hamma umar ya jarabe ya yaraba Ummul d'inshi wasu lokutan har yana jin tsoron kar dai cikin ya zube dan shida kanshi yasan jarabarsa tayi yawa,
cikin ko yana nan daram sai k'ara k'awari da lafiya da wintsil-wintsil da yake yawan yi,
Ummul ko har kwanan gobe bata tabajin son Hamma Umar d'in ba haka kuma bata tab'ayin wani abu dan ta faranta mai raina.


A gida kuwa randa Hamma Umar ya mari Adam suna tafiya,
Adam ya koma parlour Nenne cikin takaici da jin haushin k'anwar tashi ya shafa kumatun shi ya kalli Sadik dake gefen shi rai a b'ace yace,
"Ni Hamma Umar ya mara a kan na daki Ummul dan tayi mishi laifi".
dogon tsaki Sadik yaja cikin ta kainci yace,
"wallahi tallahi da a bare Hamma Umar ya auro Ummul wallah sai ince ta asirce mana d'an Uwanmu Kalli fa yadda ta maida Hamma kamar bawanta inajin bak'incin yarinyar nan wallahi duk randa na kamata sai na b'allata".
ya k'arishe maganar yana nuna yadda zai b'allatan,
Tsaki Adam ya ja cikin ta kaici yace,
"Duk ta meda Hamma Umar shanyeyye soko ya zama tamkar sakarai".
Aliyu ne ya dan yi k'asa da kanshi yace,
"Ni ina jin tausayin Hamma,
Ummul na wahal dashi".

Ajiyan zuciya Nenne ta sauk'e cikin kallon yaran nata a hankali tace,
"Ba Ummul ke wahal da Farouq ba soyayyar Ummul ce ke wahal dashi".
cikin mamaki Adam yace,
"Son Ummul Kuma Nenne Hamma Umar yana son Ummul ne ai ba sonta yake ba had'asu fa akayi ko kin manta ni dai inaga girman al'k'awarin daya d'aukane ke wahal dashi ko?".
Kai Nenne ta kuma juyawa cikin sanyi tace,
"Farouq yana son Ummul Adam baku gane hakan bane kuma sonda Umar keyiwa Ummul na asaline tun randa aka aifi Ummul".
sai kuma tayi ajiyan zuciya taci gaba da cewa,
"Tun randa aka haifi Ummul,
Umar ya bata matsayi mai girma a rayuwar shi,
bayan na haifi Ummul Umar shine mutun na forko daya d'aga Ummul yana d'agata ya ruggumeta cikin tsananin farin ciki sai kuma ya kalleni yace,
"Nenne da d'a namiji kika haifa da anmin takwara Nenne yarin yar nan dana mijine da na samu magaji,
amman yanzu ma bai b'aciba Insha Allah zata haifomin takwarana kuma Yerimana".
inajin abinda Umar ya fad'a sai nayi dariya nace ai itama takace,
haka daga wannan ramar Umar ke d'awainiya da Ummul renonta kab shi yakeyi a kwana a tashi har ta fara girma so shiko a lokacin an kaishi karatu India bayan ya gama ya dawo kuma,
sai ya zama basa shiri da Ummul sabida shi mutunne mai nitsuwa ita ko Ummul tana da kaud'i da tsiwa ga yawan fad'an da takeyi da Aliyu tana cin zalinshi shiko Umar baya son zalumci da sowa kuma ya zama shine matsayin mahaifinku in Abban ku baya nan shiyasa yake bada kulawarshi akan Ummul sosai yayinda ita ko ta d'auki hakan a mizanin k'iyeyya,".
kai suka jinjina su duka ita kuma taci gaba da cewa,
"Kuma duk da haka dole ku d'auki mataki kan halin Ummul dan a samu ta gyaru,
amman fa karkuyi a gaban Umar".
toh a haka fa daga ranar suke cike da takai cin Ummul d'in a rayu kansu,
kwanaki sun ja makonni sun ja watanni sun ja ya Usman kuwa kullum sai yasa ranar dawowa sai ya d'aga a haka har cikin Ummul ya cika wata 7 ,
yayin da a gefen Umar kuwa kullum cikin tashin hankali yake da matsamai da Ummul take akan a cire cikin ya samu dai yanzu ya lallab'a ta a kan sai cikin ya cika wata 7 da kwana 7...

Yau Monday tun sassafe Hamma Umar ya shiryo da Ummul enshi suka nufo gida dan Ya Usman yau zai dawo a cewarsa yau kam bazai d'aga dawowar ba dan jin kewar Umar yakeji tamkar sun shekara 10 basu had'uba,
Abin mamaki suna isa gida a harabar gidan Hamma Umar ya haggo Usman d'in ya nufo gunsu cikin sauri yana murmushi mai cike da farin ciki,
Hamma Umar kuwa da Ummul har rigerigen fitowa sukeyi,
a motar suna fita Ummul ta ruga a guje cikin ihun farin ciki da sowa da rakad'i tana,
"Oyoyo ya Usman na ya dawo Hamma Umar Kalli ya Usman nawa ya dawo".
shi ko Umar zuciyar shice ta rink'a bugawa da k'arfi yana kallon yadda Usman ya rame sai farin daya k'ara shiko,
Usman ganin Ummul da yayi da k'aton ciki a take jikin shi ya Kama rawa cikin tsananin firgici da tsinkewar zuciya gaba d'aya gabban jikin shi suka rink'a rawa zuciyarshi na harbawa da karfi,
dafe k'ahon zuciyarshi yayi a da-idai lokacin da Ummul ta fad'a jikin shi dai-dai lokacin kuma Hamma Umar ya k'araso garesu bud'e hannayen shi yayi ya had'asu gaba d'aya ya ruggume su,
Lokaci d'aya yaji wani irin karaya a zuciyarshi abin mamaki saiga Hamma Umar yana kuka cur-cur ruggume da k'aninshi da matarshi kuka sosai yakeyi yana shinshina wuyan Usman ,
kukan Hamma Umar d'in ne ya k'ara tono dafin zuciyar ya Usman d'in cikin wani irin yana yi yace,
"Hamma kuka Kuma? ".
sai kuma tari ya sark'a fe mishi tarin yakeyi da k'arfi yana numfashi sama-sama,
a gigice Hamman ya tallabo d'an uwan nashi dai-dai lokacin usman yayi wani irin yunk'uri da kakari sai ga....




*by*
*GARKUWAR FULANI*
πŸ“πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡

*RUBUTACCEN AL, AMARI*

Page 2⃣6⃣

*Na*
*AYSHA ALI GARKUWA*

πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡πŸ‡






*INA KUNE MATAN group d'in TABITAL FULAKU tare da AYSHA ALI GARKUWA FANS da kuma GARKUWAR FULANI Group tare da GARKUWA AYSHA&UMMEE ina Al'afahari daku ina sonku har raina ko a cikin groups na ku din nan da banne a gareni Fatan Allah ya k'addara saduwarmu a jannatul firdausi🀝😍😘*







*S*aiga tari ya k'ara turnu k'eshi tarin ya keyi sosai har ida nunshi na firfitowa woje gaba d'aya jijiyoyin kanshi dana hannun shi suka taso rud'u-rud'u, sai k'ara ruggume Hamma Umar d'in nashi yake yana wani irin murmushin k'arfin hali,
ita ko Ummul gaba d'aya jikinta rawa yake ta rik'o hannun ya Usman d'in tana zaro ido murya a hargize tace,
"Wayyo Allah na Hamma Umar kalli ya Usman".
sai ta kuma fara kuka itama tana,
"ya Usman har yanzu kana wannan tarin da aman jinin ko shin doctors basu duba lafiyar ka bane?".
kai ya rink'a juyawa jikin cushewar numfashi da zufa dake tsatstsafo mishi duk ta inda hutar gashin jikin sa yake,
hannun na rawa ya tallab'o hab'ar Hamma Umar da hawaye ke zuba tamkar an bud'e pompo idanun shi kamar zasu fad'o k'asa yana kuka harda sheshshek'a,
ido ya kuma tsurawa Hamma Umar d'in nashi cikin dauriya Ya rink'a juya mishi kai cikin tarin yace,
"A zatona zuciyar Hamma Umar na tana da k'arfin da zata iya jure mutuwata ma bare dan tarina,
amman kach sai gashi ina rayema kana min kuka,
ashe in namutu gatan da zakayi min kenan Hamma na? ashe bazaka iya cin jarrabawar da Allah zai maka ba,
Hamma Umar ka dai sani dole watara zan mutu ko".
Kai ya rink'a juyawa cikin kuka yana k'ara ruggume shi yana cewa,
"Usman bani da kamarka kullum cikin fargaba nake nima da kaina bansan ya rayuwata zata kasance min ba inba kai,
Usman bazanyi maka gatan kukaba bazan zubdama hawaye ba zan zamema mai gatan yima sutura da addu'a Usman inajin tsoron jinin da kake amayarwa".
cikin sauk'e ajiyan zuciya dan tarin ya dan lafa sai ya kuma yi murmushi ya kalli Ummul ya kuma nuna k'aton cikin ta sai ya Kuma kalli Hamman nashi cikin salonshi na abin dariya ya d'an ture su yaja baya kad'an sannan yayi gyaran murya ya gyara zaman hulanshi ya dan bud'a kafad'a cikin salon girma yace,
"Na zama Baba yanzu na wuce yarinta a dena jimin tsoron mutuwa ko namutu ga magaji na".
sai ya kuma sunkuyowa saitin cikin yace,
"Ni Baba zaka kirani".
cikin jin dad'i Hamma Umar ya kalleshi tare da cewa,
"ai dama kaine baban shi na bar makashi ni dai mahaifinshi ne kawai amman kaine babanshi".
murmushi yayi cikin farin ciki sannan ya kalli Ummul da ta tura baki tana hararan cikin a hankali yace,
"Allah ya d'aiyiba min Baby maman Baby".
cikin zubda k'ollah tayi murmushi tare da kallonshi tace,
"ya Usman ina sonka yayana".
dariya yayi sannan yaja hannun Hamman nashi suka nufi cikin gaida, yana cewa,
"Allah ya d'aiyiba".

Kai tsaye parlour Abba suka nufa inda gaba d'aya gidan suke zaune a parlour sunata hira,
suna shiga su duka uku suka zauna gaban Abba da Daddy cikin Happy Abba ya kallesu tare da amsa gaisuwar su,
sannan ya kalli Hamma Umar yace,
"Farouq ya gidan naka ba wata matsala ko?".
kai ya gyad'a a hankali yace,
"Abba matsalar dai cikin yayiwa Ummul nauyi".
ya Adam ne ya watsawa Ummul d'in harara tare da cewa,
"Toh ai haka kowa ke haifar yaranshi har in ba, ayi daceba yar ta nuna bazata yiwa iyayen nata biyayya ba".
hararan da Hamman ya mishine yasa ya kame bakin shi,
ya Sadik ma sai hararan Ummul d'in yake yana jin tana gaida shi yak'i amsawa,
ya Usman kuwa Hajjajo ya kallah cikin murmushi yace,
"Hajjajo kingafa na girma na zama baba da haka kar ki kuma cemin yaro".
dariya sukayi baki d'aya
sai kuma suka juyo gun Aliyu da yake hararan Ummul yana janye piket d'in abincin gaban shi yana cewa,
"mitssss wallahi ke dai kin bonu da kwad'ayi kina ta kallona salon na kware ni ba baki zanyi ba tunda ai ke yanzu ba yar gidan nan bane".
Hamman ne ya kalleta cikin kula yace,
"Zakici abin cin ne".
Kai ta gyad'a a hankali tace,
"eh yunwa nake ji".
Adam ne ya tsuke fuska tare da cewa,
"Uban me ya hanaki kiyi girkin a gidan ki kici?".
hawaye ta fara k'ok'arin zubdawa ganin haka Hamman ya mik'e tare da cewa,
"Taso mu tafi gidan Ammina zata miki duk abinda kike so bar musu abincin gidan su".
mik'ewa tayi dan tasan inya tafi ya barta zasu iya mareta,
shiko Hamma Umar hannu yasa ya kamo na Usman sannan yace,
"tashi mu tafi".
dariya yayi sannan ya mik'e suka fita,
Nenne ko kallonsu take cikin k'aunar yadda suke k'aunar juna tace,
"ku gaida min Ammin kuce sai gobe Aliyu zai kawo mata aiken nata".
"toh ". Sukace sannan suka fita,
suka nufi gidan Ammin nasu,
suna fita Abba ya kalli Adam dake bin bayan ummul da harara yace,
"Adam me kuma Ummul ta aikata? dan na lura fushi kake da ita".
zama Adam d'in ya gyara sannan ya kwashe labarin yadda sukayi da Ummul da Hamma Umar d'in ya fad'awa Abban,
gaba d'aya parlour shiru sukayi dan yadda Abba da Daddy suka hatsala fad'a sukeyi sosai tamkar zasu bugi babu daga k'arshe fad'an ya dawo kan Nenne cikin tsananin fushi Abba yace,
"khadija na lura kece kike d'aurewa Ummul gindi takeyin abinda taga dama shin dan na had'ata da d'an d'an uwana ai bawai yana nufin tayi ta tozartarmin da shiba,
ashe ban saniba ban isa da Ummul ba toh wallahi zan d'auki mataki a kanta".
ita kam Nenne gaba d'aya takaicin Ummul ya isheta,
tunda gashi laifinta ya shafeta,
dama in yaro yayi abu mara kyau tofa koya uwa zatayi sai anga laifinta,
shiko Abba da Daddy kan Adam d'in suka haura da fad'a,
"ai kaima baka da wani amfani tunda ka kasa d'aukar mataki a kanta kuma tunda na dawo baka gaya min ba sai yau yau d'inma saida na tabbaye ka,
to daga yau ni na baka izini da Umarni in Ummul ta sake yin abu makamancin wannan kayi mata duka sai ta konta jinya tunda bata jin magana".
Hajjajo ce taja tsaki tare da cewa,
"yarinya sai taurin Kai kamar Arnan forko,
a mata dukan shine maganin ta".
ita ko Nenne,
shiru kawai tayi tana jinsu sunata fad'a,
haka dai sukayi ta fad'a daga bisani suka watse.

A gidan Ammi kuwa suna shiga gidan ya Usman ya nufi parlour Ammin yana,
"Ammmmmi! Ammi! Ammina ina kike ne ".
Ammi dake kitchen cikin tsananin mamaki da jin muryar autan nata ta fito,
Inna ma da sauri ta fito daga bedroom nata,
a parlour suka sameshi yana ganin Ammin nashi da
DOWNLOAD
DOWNLOAD

4 Comments On RUBUTACCEN ALAMARI
avatar
shukra-sulaiman

8 months ago

Reply

Thanks

avatar
shuraihu

8 months ago

Reply

Replying to shukra-sulaiman

Tnx too

avatar
fatima-idris

8 months ago

Reply

Nice novel

avatar
taskar

8 months ago

Reply

Replying to fatima-idris

Aha tnx

Please Login or Register in order to submit comment