Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

shikenan na rabu da Hamma Umar na rabu da aurensa na tashi a matsayin matar Hamma Umar?". Tambayar ta bawata tausayi duk da tasaba da shirmen Ummul d'in, cikin sigar lallashi data saba da yimata tace, "Meya kawo wannan tambayar dear?". Shagwab'ewa tayi kamar zatai kuka tace, "Ya Usman ne yadameni kan maganar aure nikuma gaskiya banason kowa kuma banaso inzauna da kowa sai Hammana Aunty Aysha wallahi ina son Hamma na duk duniya yanzu shi nake so".
Ajiyar zuciya tasauke sannan tace,
"Haba Ummuna, tun kafin kiyi tafiyar nan muke magana guda d'aya kuma kinga dukkan mu burin mu mu samar maki da farin ciki wannan shiyasa zakiga kowa nada burin kiyi aure saboda auren shine kad'ai hanyar da zaki sami nutsuwa kuma kisamar wa Hamman ki kwanciyar hankali dan in kinyi aure zaki rege zubarmai da hawaye,
kuma ta hanyar auren Usman ne zaki samu farin ciki mai d'orewa, k'anwata auren Usman shine kwanciyar hankalinki dana iyayenki dakuma na yaronki kai harma dana Hamman ki Allah yamai rahama".
"Amin" ta amsa sannan taci gaba,
"Zai kasance cikin farin ciki kina kulamai da d'anshi da k'anin shi sannan iyayenku su kasance cikin farin ciki kuma su manta da duk abinda ya faru a baya da yafe maki kuskurenki na bijire musu da kikayi a baya".
Sannan taci gaba cewa, "Ki d'aure zuciyar ki nasan dole zakiji babu dad'i kuma dole akwai ciwo a zuciyar ki amma ki daure kiyi hak'uri kinji k'anwata ki yarda da auren Usman".
Hannu tasa tashare k'ollah dake zubowa daga idonta sannan ta fara typing amsa,
"To Aunty Aysha insha Allah zanyi hakan sabida farin cikin Hamma na da iyayena, nagode da kulawarki gareni".
hakanan daga nan kuma hirar takoma rarrashi saboda kukan da dukkansu sukeyi.


K'arfe 12 na dare jigin su yasauka a filin sauka da tashin jirage na Aminu kano a cikin birnin kano,
a Tahir guest palace suka kwana sannan da safe suka d'auko hanyar Potiskum, ya Usman da ya Adam ne sukaje d'aukosu haka suka dungumo misalin k'arfe 10:08 suka iso gida,
Sunsami kowa cikin k'oshin lafiya Umar Farouq tunda suka iso ya haye jikin mahaifiyarshi yanata bata labari na abubuwan da suka faru bata nan haka suka wuni cikin nishad'i sai bayan sallah isha'i ya Usman yamaida Halima da yaranta gida shima Adam yamaida Aunty Shuwa da Inna tunda unguwarsu d'aya,
Adam na dawowa yawuce b'angarensu dan yana buk'atar hutu, shiko gogan Ummul daman Allah-Allah yake bak'in su tafi ya gana da masoyiyar shi tun yana mota yakira wayarta tana d'auka yace,
"Ki jirani a palour Nanne baijira amsartaba ya katse kiran.


A parlour ya sameta tana kwance akan kujera yana shiga da sallama tamik'e zaune ta amsamai kusa da ita yaje yazauna yasauke ajiyar zuciya sannan ya kure ta da ido cikin tsananin so yace,
"gaskiya kin rame baby, dama nayita tunanin hakan".
d'an murmushi tayi sannan ta sunkuyar dakai k'asa tace,
"ya Usman tunda naje a wuraren Ibadan nake tarewa ina yiwa Hamma na addu'a da nema mishi rahamar Allah ko cin abinci bana son fita,
ranar na d'an fara gyagyad'i sai nayi mafarkin Hamma na yana nuna min kai yana cemin inje gareka kar in bari ka zubda hawaye".
sai kuma tayi shiru tana zubda k'ollah,
sai kuma tace,
"ya Usman ka gafar ceni".
A hankali ya sake matsota yakamo hannayen ta duka biyu ya rik'e da kasalalliyar murya shi yace, "bantab'a jin b'acin rai akan duk abinda kike fad'a kinyi ba,
nasha fad'a miki komai kikayi birgeni yake kuma komai kyau yake miki nagode da kulawarki ga d'an uwana".

Shiru sukayi dukkansu yanata matsa hannunta dake rik'e a hannun shi ya katse shirun da cewa,
"Fatana ki yarda da aurena".
sai kumu yasa hannu ya d'ago fuskarta tare da cewa,
"Kamar kinada magana ko?".
K'asa tayi dakai murya na rawa a hankali tace,
"inaso ".
da sauri yace,
"kina son me"?.
ido ta lumshe cikin zubda k'ollah tace,
"Ince son ince maka na amince da maganar auren".
Kasa k'arasawa tayi tafashe da kuka,
jiki na rawa ya janyota jikinshi ya had'ata da kirjin ya ruggume ta da k'arfinshi ta yanda har tana jiyo bugawar da zuciyar shi takeyi ido ya lumshe yanajin wani irin yanayi da bai tab'a jiba hakan yasa yakasa daurewa shima yafara k'ollah,
kamar ya tuna wani abu yasa tafin hannu shi ya goge k'ollar idon shi yasake matso ta yace,
"Yi hakuri kinji, kinga narasa mezance maki dan murna amma dai nasan yau matsalata ta k'are".
Sakinta yayi ya sauka daga kujerar ya durkusa yayi sujjada yayiwa Allah godiya sannan ya juyo yazauna gabanta ya d'ora kanshi akan cinyarta kamar k'aramin yaro yasauke nannauyar ajiyar zuciya yace, " inasonki ina k'aunarki". A hankali takai hannun ta d'aya kan gashin kanshi ta tusa yatsun ta ciki tana d'an tureshi, runtse ido yayi da k'arfi yanajin wani irin abu da baitab'a jiba kuma bazai iya kwatan tawaba,
itace ta dawo dashi daga halin dayake ciki dacewa,
"Naji dad'in samun Aunty Aysha Garkuwa domin ko yaushe shawararta irin ta Ammi da Nenne ce kuma in nabi ina jin dad'i".
d'ago kanshi yayi ya kureta da ido hakan yasa tai shiru cikin kunya tafara wasa da yatsunta,
shi kuwa sake tashi yayi ya zauna gefen ta sannan ya ruk'o hanna yenta murya a raunane yace,
"Nasani my life nasan wannan yafaru da ikon Allah da taimakon ta hak'ik'a ni dai GARKUWA tayi min rana".
sai kuma ya d'an fizgota cikin tsananin shauk'i yace,
"inna fad'a miki toh ki rik'e mini duk tsanani da wuya zana sakar miki sona kiyi rik'ona don Allah kar naga kin gajiya,
in dai kikayi haka so zai habaka zamuga kyen tafiyar,
da shak'uwa aka samu yarda har so yassanya muna kama da juna".
shiru tayi tana jin salon son ya Usman d'in ta mai cike da kalamai masu sanyi gaba d'aya ya kashe mata jiki sai k'ara narke mishi takeyi cikin Shauk'i ya tallabo fuskarta ido ya kashe mata tare da kashe murya cikin rad'a yace,
"Bisa dukkan alama an yabamini Kumar nasan zanga kyen yanayi domin kinmin halin mutuntawa duk kin gwada mini su tunda kin amince na zama mijin ki ni kuwa dole na k'arfafa so da k'auna nayi miki rik'on da ba shayi,
gurin zaman auren mu in kyautata miki domin muyi zama na faran tawa juna rai".
cikin jin kunya murya can k'asa tace,
"Ni nace maka kwarai ina so dan haka karka fidda rebo,
me kake so ya zama alamar sona a gareka don akwai sabo a tsaka ninmu inko yarda ta kake buk'ata to ka sanya a ranka ka samu,
dan kai gudane da bani da kamar ka nida Hamma na da Farouq a zuk'atan mu".
Murmushi yayi cikin jin dad'i yace,
"Ummu na ina da matsala fa ban sani ba ko zaki iya d'aukar nauyin yawan buk'atata gaskiya gwara na shaida miki tun yanzu kar sai munyi aure kice na matsa miki ko na fiye jaraba,
kuma ko a Shari'ance dama in gaya miki kisan irin mijin da zaki aura".
kanta ta sunkuyar cikin jin tsananin kunya hakan yasa ta kasa maga sai kai ta gyad'a mai murmushi yayi cikin tsananin jin dad'i yace,
"Dole in gwada miki farin cikina gaskiya kinyi na yaba miki al'k'awari kuma zan rik'e miki wurin zaman aurenmu wallahi bazan matsa mikiba zan sakaki a cikin farin ciki zuciyar ki na cire mata bak'in ciki da duk wani k'unci tunda kema kin yimin halacci domin kinyi rik'o da amana tunda kin amince dani".
ido ta lumshe cikin sanyi da jin kasala da kalaman ya Usman d'in nata,
a hankali tace,
"Lallai shak'uwa tana sanya yarda a tsakanin mu tabbas idan nace maka a zuciya ta kai na zab'a ka gaskatani ka bani dama,
amman in dai sone har gobe Hamma nane kawai nake so a raina ya Usman sai kayi hak'uri dani".
Ajiyar zuciya ya sauk'e sannan ya kamo hannun ta ya tsaida ita cikin mayen so da juyewar idanu yace,
"zan rayu dake cikin aminci son da kikeyiwa Hamma na ma kawai ya wadatar dani ko baki soniba ba matsala tunda kinso d'an uwana Kuma nasan nima wata rana zaki soni".

Haka suka kasance cikin hirar su ta soyayya duk da bakomai take amsamai ba amma saida suka raba dare suna hira sai k'arfe 3:15 ya rakata har bakin kofar d'aki ta shiga yanajin kamar kada su rabu sannan ya juya ya tafi part ensu.

Yana shiga bedroom ensu yasami Adam yayi d'ai-d'ai a gado yana baccin gajiya kasa hak'uri yayi yasa hannu yad'an bugi k'afar shi, da k'yar ya bud'e ido yad'ago kai yace,
"yadai?".
zama yayi kusa dashi a kan gadon yace,
"Tashi kasha labari naci zab'e Dr Bashir da Mustapha duk sun fad'i jam'iyata ta kafu k'ark'ashin jam'iyar Hamma na naci albarkacin d'an uwana duk da baya raye amman a sana dinshi nake farin ciki".
"a a dan Allah ka barni nai bacci na kaban labarin da safe".
Adam yafad'a yana gyara kwanciya,
da sauri shiko ya rik'oshi ya k'arasa zaunar dashi yana cewa,
"Gwarama ka tsaya kaji wlh dan bazan barka kayi baccin nan ba". Adam da yakeson yacigaba da bacci yace, "To menene?".
"Ummul ce". yace shiko katse shi yayi da cewa,
"ai dama nasani koyaushe maganar kenan".
hannu yasa ya toshemai baki yace,
"Kai ba irin wannan labarin bane,
yau da bakinta tace ta amince da aure na".
"congrat Allah sanya alkhairi". daga haka ya juya yaci gaba da baccin shi,
shiko mik'ewa yayi yaje yayi wanka da alwola yazo yayi ta nafiloli da karatun Qur'ani har aka kira sallah asuba.



Tunda suka fito daga masallaci sallah asuba Abba ya fahimci da magana a bakin yaron nashi dan yanata bin bayan shi yana sosa kai,
kamo hannun shi yayi suka nufi b'angaren Abban,
ya zauna a kujera shikuma yazauna k'asan kujerar ya ton k'oshe k'afa saida suka gaisa sannan yafara sosa k'eya kamar mara gaskiya,
"Haba d'an Abba ya aka yine ? ai babu wannan b'oye-b'oyen tsaka nin mu fad'amin me kakeso?".
K'ara sunne kai k'asa yayi yana murza yatsun kafar shi cikin sanyi yace,
"Daman mun gama magana da Ummul ne shine ".
Sai kuma yayi shiru dariya Abban yayi mai sauti ya dafa kafad'ar shi yace,
"To shikenan nagane anjima zamuyi magana da Ammin ku sai kuma insanar da Hajjajo inyaso idan Daddy ku ya shigo anjiman sai mu mik'a musu sadakin su kaga sai su samana rana ko?".
Baisan lokacin daya kamo hannun Abba ba yana cewa,
"nagode nagode". Saikuma ya saki hannu yana sosa kai.
"To jekai azkar d'inka".
"to ".
Kawai yace yamik'e a kunyace ya fice.


Shi kam Abba mamaki yake dan yana rena shekarun Usman gashi baida wani girman jiki amman ya lura yana son auren sosai,

Dr Bashir kuwa yau da wuri ya tashi dan zaizo yayiwa Ummun shi sannu da dawowa,
a gefen Mustapha ma harda Ummanshi suke shirin zuwa yau din suwa Ummul barka da dawowa Lafiya,

Shi kuwa Usman yana shiga part ensu a parlour ya zauna cikin jin bacci ya kira Ummil d'in
tana kan sallaya woyar na gefen ta juyowa tayi ta d'an kalli Ammi dake karatu,
a hankali ta yi mishi sallama,
yana jin muryar ta cikin,
wani irin yanayi yace,
"wash Noor Hayateeeeeeeeeh bacci nake ji kuma kuma b...........





*By*
*GARKUWAR FULANI*
[07:03, 12/9/2017] 😄😄💲ⓂℹL£®😀😀: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*RUBUTACCEN AL,AMARI*

Page 3⃣6⃣


*Na*
*AYSHA ALI GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇


*MOH ALLAH WUJI FURƊATA*



```A madadin Member's ɗina na Group ɗin
TABITAL FULAKU nake miƙa saƙon gaiduwar ta'aziya ta ga HALIMA Ummu Maryam kano tare Mu'allima Bauchi Allah ya jiƙan iyayen ku Allah yasa sun huta rabbi ya sanyayya konciyan ƙaburburansu Mu'allima Allah ya baki haƙurin rashin mahaifiyarki da kikayi a deren jiya Halima kema Allah ubangiji ya baki haƙurin maihaifiyarki da kika rasa shekaran jiya Allah yasa sun huta muko in tamu tazo Allah yasa mucika da imani```







*M*iƙa yayi cikin kasala da jin bacci murya can ƙasa yace,
"Washhh Ummu na bacci nakeji,
kuma begen ki ya hanani baccin,
gashi ina jin sanyi".
shiru tayi bata amsa mai ba a ranta kuwa mamaki ya Usman ɗin yake bata shi kuwa iska ya furzar a hankali sannan yaci gaba da cewa,
"Inama an daura mana aure Ummu na in samu d'umin jikin ki".
shiru tayi batace komai ba saidai cike take da kunya,
shi kuwa lumshe ido yayi yaci gaba da cewa, "Laisa liyal'huzni inkunti ma'ee=in kina tare dani bani shiga kunci, amma yanzu narasa yadda zanyi".
Dakaji yanda yake magana kasan bacci ke damunshi sai faman mik'a yake da hammah yana magana cikin shogoɓa yana maƙale da woyar yaci gaba,
"Uhhmmmm wash bacci nakeji Ummuna kuma begenki ya hanani lumshe ido".
A hankali ta buɗe baki cikin sanyi ta huramai iska a kunnen shi sannan cikin rad'a tace, "yanzu ina kake?".
ldo ya lumshe sannan cikin shogob'a yace,
"ina palour".
Murmushi ta ɗanyi jin yadda yake magana sannan a hankali tace,
"To tashi ka koma bedroom ka konta a hankali saika lumshe idonka".
Tashi kawai yayi yanufi bedroom ɗin yana shiga ya kwanta kan gadon ya lumshe ido a hankali ya furta,
"Nayi yadda kikace ɗin". Ɗan murmushi takuma yi shogob'ar shinna tana bata mamaki a hankali cikin raɗa tace,
"Gani a gefenka, ga hannuna ka riƙe". Hannu yasa ya damk'e filon da yake kai a hankali yafurta, "Shhhhmm Ummuna Insha Allah sana iyshu ma'aki ma'a habbah=insha Allah zan rayu dake tare da soyayya".
jin haka yasa tafara sauke numfa shi tana murmushi tana kuma hura mai iska a kunnenshi a haka yafara bacci ita kuwa taci gaba,
"Kayi bacci cikin nutsuwa hannuna na riƙe da naka kanka yana cinyata hannuna ɗaya na yawo a cikin suman kayin ka zuwa kunnen ka, ina son kayi bacci kar ya saka ciwon kai".
Shirun dataji dakuma jiyo saukar numfashin shi a hankali yasa ta kira shi ta tabbatar da yayi bacci dan jin bai amsa kiran da tayi mai ɗinba,
haka yasa ta katse wayar ta konta cike da tunani har bacci ya d'auketa.


Gari na k'arasa wayewa Ammi tazo ta tasheta dan tayi break saida tayi wonka tai kwalliya sannan taje tagaida Nanne,
bayan sun gaisa tace,
"Ga abincin Usman can ki ɗauka ki kai mishi".
Amsawa tayi sannan tajuya ta je ta had'a mai komai akan tire ta ɗauka ta fita hannun ta riƙe da hannun Faruq.


A ɓangaren Usman ma yana tashi yashige yayi wanka ya shirya tsaf ya feshe jikin shi da turaren hugo mai ƙamshi yana fitowa palour kunnuwan shi suka jiyemai abinda yafi son ji,
Sallamar da tayi ya amsa sannan ya buɗe hannuwan shi ya ɗan tsuguno da fara a fuskar shi yace,
"come on Daddy boy".
da gudu Farouq yaje ya faɗa jikin shi shima yamaida hannun shi ya rufe sannan ya ɗagashi sama yana kissing ɗinshi tako ina cikin ƙauna shima yayi kiss ɗin shi a kumatun shi cikin gwaranci shi yace,
"Ana Ubbuka Abee". Dariya yayi yana saukeshi ƙasa yasa hannu yana lakace mai hanci yace,
"Ana hubbuka ya bunayya".
Wucesu yayi yaje ya haye kujera yaɗau remote d'in tv yafara wasa.
Shi kuwa dawo da kallon shi yayi kan Ummul dake kokarin ajiye tiren a tsakar palour ya zuba mata manyan idanun shi, tana ajiyewa tasami guri a ƙasan a tsakiyar carpet tazauna sannan ta kalleshi ta ɗanyi murmushi yadda taga ya ƙure ta da ido dakai tamai alamar yazo ya zauna,
aiko kamar rakumi da akala yataho da hannu ta nunamai inda zai zauna,
saida tasa hannu taɗau flate tafara zubamai abincin sannan ta ɗan kalleshi cikin sanyin murya tace,
"katashi lafiya?".
Shima lumshe idanu yayi sannan ya buɗesu ya namata wani irin kallo murya can ƙasa yace, "Inafa lafiya Ummu na bayan a baccin ma zuwa kikayi,
kikayita
DOWNLOAD
DOWNLOAD

4 Comments On RUBUTACCEN ALAMARI
avatar
shukra-sulaiman

8 months ago

Reply

Thanks

avatar
shuraihu

8 months ago

Reply

Replying to shukra-sulaiman

Tnx too

avatar
fatima-idris

8 months ago

Reply

Nice novel

avatar
taskar

8 months ago

Reply

Replying to fatima-idris

Aha tnx

Please Login or Register in order to submit comment