Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

Ajininsa yake 1-01
Posted by ANaM Dorayi on 07:24 AM, 03-Nov-15
Under: Ajininsa yake
__________________ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
________
Rabe jikin daya daga cikin bishiyon da suka yi wa
filin sukuwar kawanya. Jikinsa kayan mkrntar
firamare ne. Farar riga da koren wando. Gaba-
daya hankalinsa tattare ya dora bisa dawakan da
ke zuba tsere kamar za su tashi sama. Babu
abinda yake tunani, illa ina ma shine bisan dokin
da yayi wa saura fintankau?"
Jama'a suka hau ihu, don taya mai dokin daya zo
na farko murna. Shi ma ya kwasa a guje.
Yana isowa bai ma san ya jefar da jakar
littattafan sa ba. Ana ture shi, yana turawa, sai
da ya kutsa ya ta6a jikin saurayin daya zo na
farko.
Kamar an sanya shi al-janna, haka yake ji cikin
ran sa.
Wasu rukunin dawakan ne za su taso yanzu, shi
yasa duk jama'a suka koma inda suke.
Haka shima ya nemi wata bishiyar ya kuma
ra6ewa jikin sa na tsuma, tamkar na 'yan dambe.
Caraf!
Ya ji an cafke kunnunwan sa 2, a firgice ya juyo,
su kai ido 4 da mahaifinsa. Ido warwaje ya daga
hannayen sa sama, amma ya kasa cewa komai.
"Ba za ka daina bata min rai ba Naseer?
Makarantar kenan?
Ya 6ata rai kwarai, manyan idanuwan sa suka
kada jajir!
Haka ya tsurawa Baban sa ido.
"Zo mu je mkrntr, jikinka ne zai gaya maka,
tunda kai kunnan kashi gare ka, ni ma ba zan
fasa ba!
Ina jakar ka?
Ya shiga dube-dube,"Au jakar ma ba kasan inda
take ba?"
Ya maka masa duka a keya,"Wuce mu je ka nemo
jakar, dan banzan yaro marasa jin magana!"
Yaja kunna sa suna tafiya har suka yi karo da
jakar,"Duka ka dauko ta!"
Ya sa hannu ya dauko, a haka suka shiga. Cikin
mota, kunci kamar Naseer zai yi bindiga sabo da
kunburi."(L.E.A Primary School) da ke kusa da
ofishin "Yan-sanda na Tudun Wada Zaria nan
suka shiga shugaban makaranta.
Ya tsura masa ido ya-ce,"Ba za ka bar Babanka
ya huta bane Naseer! Kai wane irin yaro ne?" Ya
juya gefe ya tura hannunwan san a aljihu.
Hedimasta ya dankwafar kan sa ya ce,"Rage
tsawonka, ka kuma cire hannayen ka daga
aljihu!"
Ya durqusa yana huci, saboda tsabar zuciya,
kirjinsa na bugawa muraran kowa na gani."
Malam Balarabe ya ce,"Zane min shi za ka yi a
gaba na in gani.
Idan kuma ba za ka iya ba, ni zan dauki bulalar
in hukunta shi bar ni da shi.
Ya ce,"nan da nan ban zuwa Hedimasta, sai na
ga jikin Naseer yayi rudu-rudu.
Ina bulalar take? Miko min ita nan!"
Hedimasta ya jawo dorina, Baban sa ya cire masa
riga da karfin tsiya yana kallo aka rinka tsala
masa dorina dai-dai har goma sha biyu.
Amma Naseer ko gezau bai yi ba, balle ya fidda
hawaye.Takaici kamar ya kashe Malam Balarabe,
ya ja kujera ya zauna, ya ce,"Ban san yadda zan
yi da wannan yaron ba, shi kadai gare ni, amma
gaba d'aya ya buwayeni."
Hedimasta ya ce,"Sai addu'a, yaran yanzu addu'a
ce ke ladabtar da su, don haka ka yi tayi masa
ita.
Babu komai, ka na iya komawa ka bar ni da shi
kawai.
Ya karkada kai cike da damuwa, yasa aljihu ya
labubo Naira 2 ya dora bisa tebur ya ce,"Ga
kudin tarar sa nan don na san da wadancan ya
shiga mota ya je filin sukuwar."
Ya ce,"To shi ke nan.
Allah ya shirya mana."
Ya mike yana fadin,"Amin.
Ya mika masa hannu suka yi Musabaha.
Ko ta kan Naseer bai sake bi ba, ya sa kai ya
bar ofis din.
Hedimasta ya duba shi ya ce,"
"Naseer!"
Ya sunkuyar da kai kasa, ban tanka ba."
Haba Naseer, ka na da kokarinka, kaf ajinku
babu mai kwakwalwar ka, amma ka zauna cikin
aji, sai ya gagare ka?
Kai kullum hankalinka na filin Sukuwa.
Idan ba kayi karatu yanzu ba, sai yaushe za ka
yi?"
Ko alama kai ba ka koyi da abokanka, ba ka
tausayin mahaifinka.
Kodayaushe shine zarya filin sukuwa yana kamo
ka.
Ka yi wa kanka fada Naseer, ka ga yanzu aji 6
ka ke, a gantale, a gantala dai ka kusa zana
jarabawar shiga sakandire, idan ba ka maida
hankali ba, ka na ji ka na gani abokanka za su
wuce su bar ka anan.Yanzu abinda na ke son ka
da shi, shine ka maida rigan ka, ka wuce aji, ka
ga sauran minti 10 a fito (Break), sai ka zo ka
amshi kud'in ka.
Ga su nan aje su waje na. Idan ba ka zo ba,
wannan zai tabbatar min cewa ka gudu ne.
Tashi ka wuce."
Ya mike ya maida rigarsa, bayan sa rudu-rudu
da zanan bulala.
Kai tsaye ya wuce ajinsu.
Malamin da ke cikin ajin yace , "Sai yanzu ka ke
zuwa?" Yayi shiru yana hura hanci.
Ya ba shi rankwashi 2 masu kyau, sannan ya-ce
ya je ya zauna.
Ya taho a kunbure ya tsaya gaban bencin baya,
inda ya saba zama.
Kallon sauran yaran kawai yayi, suka hau
matsawa ya sami wuri ya zauna. Ya ci gaba da
kunci, bai ko sauranon Malamin turancin da ke
ajin har aka kada Break tara. Malam ya fita,
kowa yayi waje, sai Naseer kadai ke zaune yana
tunanin yaya za'a kare wasan da ya baro ana
yi? Wani yaro dai-dai tsawon sa wankan tarwada
ya shigo, ya zauna kusa da shi.
"Naseer, ashe ka zo?
Ya dube shi ido jazur!"
"Eh,
Ya kura masa ido ya-ce,"Yau ma dukan ka aka
yi?"
"Ban sani ba!"
Ya fada cikin fushi.
Ya-ce,"Ai na gaya maka, kar ka je, amma ka ki
ki, don na san dole ne Babanka zai zo nan ya
bincika."
Ya nuna shi," Kar fa ka dame ni Sageer, meye
ruwan ka!
To!"
Ya mikie ya-ce,"Allah ya ba ka hkr. Ni zan je
wajen masu abinci, in sayo maka gyada ne?"
Ban ci!"
Ya amsa, bai kalle shi ba.
Sageer ya wuce abin sa.
Tsaki yayi, ya jawo jakarsa ya fidda littafin sa da
biro yayi ta zana dawaki suna tsere, ko alama
bai yi tunanin ya je ya amso kudin sa ba. Duk
da cewar Hedmasta ya-ce idan bai zo ba, to ya
san ya gudu ne.
Kuka yake ta ji, ta bayan tagar ajin da yake
zaune. Kwarai kukan ya dauki hankalinsa, don
haka ya mike ya leka.
Wata 'yar yarinya-ce rabe take ta gurshashan
kuka ba ji, ba gani.
Akalla za ta kai shekaru 8 ko fin haka.
Ya sanya mata ido, duk tayi zufa, majina sharaf-
sharaf, nan take tausayin yarinya ya lullube shi.
Ta tagar yayi tsalle, ya diro gaban ta, don haka
ta dube shi a firgice.
"Ke da wanene?
Ta kasa magana, saboda kuka da ya ci karfinta.
Ya kamo kafadun ta, ya-ce,"An ce wa ya duke
ki?"
Cikin muryar kuka ta amsa,"Kudi na ne suka
fad."
Kudinki?"
Ta amsa da ka.
"To ina yan-uwanki?
Ko ba ki da su?"
Da ka tasa ke amsawa.
Yayi dan shiru, ka-fin ya-ce,"Ki yi shiru, zo nan
ki zauna ki jira ni.
Ya jawo hannun ta, suka zagayo barandar ajinsu
ya zaunar da ita," Zauna nan ki jira ni."
Ta zauna tana share hawaye.
Wasu na sake zubowa.
Kai tsaye ofishin Hedimasta ya nufa.
A kofa suka yi kicibi6.
Hedimasta ya-ce,"Ai na dauka ka yi halin naka
ne.
A jinku da za ni yanzu, shigo ka amsa."
Suka shige tare, ya jawo dirowa ya dauko, ya
mika masa." Ana tashi kuma, ka zo nan kafin ka
wuce gida."Can kasan makoshinsa ya amsa da
"To."
Ya fice.
Malama Abu da ke zaune ta ce ,"Ina son yaron
nan, amma bai son karatu, ga shi da kokori.
Hedimasta ya ce,"Ke ko ni wallahi akan dole na
ke dukan sa, saboda baban sa tausayi yake ba
ni, koma yana son yayi karatun."
Ta ce,"Yara ai sai hkr, Allah dai ya shirya mana."
Ya ce,"Amin."
Shi kuwa wajen yarinyar nan ya koma, har
yanzu tsiyayar hawaye take yi.
Ya kamo hannu ta yana fad'i,"Har yanzu kukan
ki ke yi?
Ta so mu je ki zabi abinda ki ke so ki ci."
Ya ja ta zuwa wajen masu abinci.
Can ya hadu da Sageer."
Ina ka samo wannan?"
Ya ce,"Kudin ta ne ya suka fadi, shine take
kuka, kuma bata da kowa anan.
Zo ki zaba, me ki ke so?"
Kankara kawai ta nuna.
Ya siya mata, sannan ya kara mata da aya mai
siga da gyada mai gishiri.
Ta ce,"Na gode.
Ya kamo ta suka dawo da Sageer.
Nan bisa baranda suka zauna su 3 tana ta shan
kankara ta."
Ya sunan ki?"
Ya tambaya ta.
Ta-ce,
"Zahra Umar.Ya ce,"Wane aji ki ke? Ta amsa,
"Aji uku." Ya ce,"To maza ki cinye, ki koma aji.
Ya juya suka ci gaba da hira da abokan sa.
Labarin wasan da ya baro ana yi, shi yake ba
Sageer.
"Abinda ke hana ka karatu kenan Naseer, kai
kullum hankalinka ka akan polo yake.
Ya gyara fuska, don shi Naseer akwai iya tsare
gida tamkar wani babba, ya ce,"Kowa ya dame
ni akan Polo, ni kuma ina so, burina in ganni ina
sukuwa, kamar Yakubu Jah-Jah. Yau ba karamin
burgeni yayi ba, sai da na kukkutsa na ta6o
shi."
Ya ce,"To ai komai dan lkc ne Naseer. Ina
amfanin kullum sai an yi maka bulala? Dubi jikin
ka, ko'ina ta6on bulala ne, sam ba ka jin
magana Naseer." Ya ce,"Ban ji din idan ka yi
min iskanci yanzun nan, zan kwashe ma hakori
wallahi, ka kuma sake magana, ka gani."bai ce
kala ba, ya juya ya ci gaba da murza gyad'ar sa,
yana afawa baki. Naseer ya juyo kan Zarah, sai
ya ga wayam!
Tuni ta kama gaban ta. Yayi dan shiru, kome
yake tunani? Oho.
Ya dubi Sageer, ya ce,"Yaushe Zarah ta gudu?"
Yayi banza da shi, yana ta jan gyadarsa.
Tsaki yayi shi ma, ya mike ya haura aji ta taga.
Yara cike da ajin ga littattafin sa da biro, amma
babu wanda yayi gigin ta6awa, don sun san
kayan Naseer ne.Yana zama ana kada
kararrawa. Muryar Sageer ya ji ta taga yana
cewa,"Dama ana tashi ka yi tafiyar ka, kar ka
sake ka neme ni!"
Ya ce,"Kai din banza, wa zai neme ka?
Mts!
Ya dauke kan sa daga kallon sa.
Shi ma tuni ya bar wajen ya nufi ajin su."
Karfe sha biyu da rabi aka tashi.
Naserr ya fito rataye da jakarsa, babu abinda ya
tsinana da littafin sai dai dan banzan zanen
dawakai.
Yana tsaye bisa barandar yana kallon yara na ta
wucewa.
Can sai ga Zarah a gujeni ta za ta wuce." Da
sauri ya kwala mata kira,"Zarah!"
Ta dawo gunsa da fara'a ta,"Sai ku gudu, babu
sallama?"
Ita dai dariya ta sani. Sai gobe kenan?" Ta ce,"
Eh."
Ya ce, shi kenan, amma ki dina gudu, kar ki fadi
kin ji?"
Ta ce,"To." Bata saurari komai ba, ta juya ta tafi
a hankali, kamar yadda ya ce. Ya kasa dauke
idonsa a kanta, har ta sha kwana.
Kawai ya ji kaunar sukuwa. Ya sakko daga
barandar, ya nufi ofis din Hedimasta, yana fadi
a ran sa,"Shi kuma wancan dan rainin wayau,
wai sai na je gun sa, kafin in tafi gida.
Mts!
Ya ja tsaki.
Fuska murtuke ya shiga ofis din.
Kaf Malaman da ke ofishin, sai da suka tanka
masa.
Ba su ishe shi kallo ba ma, balle ya tanka ma
su.
Gaban tebur ya tsaya, yana kallon
Hedimasta.Shine ya yi masa magana,"Manya!"
To akama hanya, kar ayi kwana ko'ina sai gida.
Ka ji ni da kyau?"
Ya juya manyan idanuwan sa ya ce,"Uhm
"
Gobe kuma 7 da rabi ka same ni anan.
Kama hanya ka wuce."
Ya juya ya ce a ransa,"D'an rainin wayau!"
Malama Abu tayi kiran sa.
Ya matsa wajen ta ya tsaya.
Ta kare masa kallo sannan ta ce,"Ayi kokari, a
zo, makarantar gobe don Allah."
Ya murza ido ya amsa,"Ai zan zo."
Ya wuce tana kallon sa.
Yana fita ya saki tsaki,"Wannan matar, wata
rana sai na tara ma duwatsu wallahi!"
Bai nemi Sageer ba, ya kama gaban sa.
Dai-dai wata kwana yahango Malamin
turancinsu, wanda ya rankwashe shi da safe, ya
rabe jikin kwanar, ya waiwaga bai ga kowa ba.
Yasa hannu ya dauki katon dutse, ya wulwula
masa.
Kau!
Malami ya ji saukan dutse bida ga keyar sa.
Ya dafe keya yayi ta neme-neme, amma bai ga
kowa ba. Cikin hanzarinsa ya dawo kan kwanar,
ba kowa a wajen.
Makale yake jikin wani gida, yana hango Malam
na ta murza keya yana kwafa.
Sai daya bar wajen, sannan ya fito ya dafe a
guje.
Ya kusan isowa gida, ya ci karo da wasu yaran
'yan makarantarsu suna tafe su hudu sun gara
kwallon nan sama,Babu bata lkcn kwallo ta
haura katangar mutane, ta fada cikin gidan.
Yara suka tsaya suna kallon Naserr.
Ya gyara fuska ya ce,,"Ku shiga ku dauko mana."
Guda ciki ya ce,"Malam kar ka raina mana
hankali ma na, ba kai ka jefa ta ba?"Yana rufe
baki. Mai-gidan na fitowa da kwallon a
hannunsa. Suna kallon yasa wuka ya yanka ta 2,
ya jeho musu, ya juya cikn gida abin sa.
Me Naseer zai yi?
Ba dariya ba.
Yaro mai kwallo ya ci kwalar Naseer,"Wallai sai
ka biya ni kwallo na!" Haka sauran yaran suke
ta fadi, duk suka yayyame shi.
Wani dan murmushi yayi yace,"Malam ka sake
ni girma da arziki.
Idan ka yaga min riga, kaf hakorinka kaf, sai na
kwashe ma su." Ya ce,"In ka isa.
Allah ya tsine min!" Koda Naseer ya dunkule
hannu, sai kwaf!
Bisa hancin mai kwallo.
Nan take jini ya tsinke. Dambe ya kwaure da
abokan mai kwallo. Su 3, amma ba su ishi
Naseer komai ba, haka ya ringa wuji-wuji da su,
ya na jefarwa. Mutane suke fara taruwa, aka
raba, binicike ya tabbatar da Naseer ne bai da
gaskiya.
Amma bakin sa yaki mutuwa, saboda haka
samari 2 suka cukuikuyo shi, har gida da yaron
nan jini na ta fita ta hanci. Hayaniya Malam
Balarave ya ji zauren gidan sa, don haka ya fito
yana tambaya ko lafiya?
Ganin Naseer da gayyar yara. Shi ya tabbatar
masa Naseer ya sake dauko masa wata
maganar. Akai masa bayani, dole Malam
Balarabe ya biya kudin kwallo.
Sannan ya kai wanda aka fasawa hanci kemis
aka wanke masa da magani, kuma ya kai shi har
gidan su, saboda gudun tashin hankali.Naseer
na zaune, ya kunbura suntum, da gani ya sha
fada wajen mahaifin sa. Malam Balarabe ya
shiga tsakar gida ya zauna bisa tabarma ya sa
wa Naseer ido.
Ya kada kai, ran sa bace ya ce,"Kai
jama'a,"Naseer ko kauye zan maida ka ne?
Wannan fitina, ta ishe ni! Jin muryan sa yasa ta
fito da daki.
"Ka dawo Malam?"
Ya ce,"Na dawo Mairo.
Zo ki zauna ki ji." Ita ma ta zauna a
tabarma."Naseer ya ishe ni, zan maida shi
kauye, ya je can yayi noma, tunda karatun ma
ba son shi yake ba, sai dan bazan daukan
magana." Ta ce,"Malam ka ce ya kara lalacewa
kenan.........."Ya katse ta,"To ya ki ke son in yi?
Karatu fa Naseer ba yin zai yi ba, ai gara ya
koma can yayi Noma."
Ta ce,"Wannan mai kunnen kashi ne zai yi
noma?
Bai yi karatu ba, sai aikin wahala? Malam, barin
Naseer a gaban mu, shine mafi alkhairi a gare
mu, don ko banza ba mu gan shi ba a
makaranta ba, in ka je filin Sukuwa za ka gan
shi.
Duk rigimar da zai kwaso, zai fi kyau ya kwaso ta
a gaban mu.
Da ka dauke shi ka kai wurin da bai sa ba, ba
kuma shakkar su yake yi.
Mu yi ta yi masa addu'a.
Allah zai duba mana."
Malam Balarabe yayi shiru, jin ka fin ya sauke
numfashi ya ce,"Ya ci abinci?"
Ta ce," Ina fa.
Ai ka san yadda ya kumbura, ya dankare anan,
haka zai yi ta zama, idan ba Sageer ya shigo
gidan nan ya daga shi ba.
Ya ce,"Allah ya shirya.
Ta ce,"Amin.
**********
Satin nan tsaf! Naseer na zuwa mkrnt kamar
abin ya dore a haka. Kuma kodayaushe aka fito
tara. Zarah na tare da shi, ya siya mata
wannan, ya siya mata wancan.
A 'yan kwanakin nan sosai ta saba da shi, don
har gida tana ba Innar ta labarin Naseer.
Ba karamin mamaki Naseer ya ba kowa ba,
ganin bai ta6a jera kwana biyar cur, yana zuwa
mkrnt ba.
Yau litinin yayi shirin mkrnta, sai dai zuciyar sa
bata raya masa ya je makarantar ba.
Kai tsaye bakin titi ya nufa, ya shiga motar
sabon gari. PZ. Daga can ya karasa filin sukuwa
a kasa. Baban sa bai neme shi ba, don ya ga
abin yayi sauki wancan satin, saboda haka
shima yayi zamansa a runfar sa da ke kasuwar
Tudun Wada, inda yake siyar da kayan miyan sa.
Naseer kuwa can ya wuni, domin wasan da yake
son gani ba a fara ba ma, sai 10 na safe. Gab
da sallar azahar ya dawo gida cike da farin ciki,
don yau sosai ya sha hannu da mutuminsa
Yakubu Jah-Jah.
Umman sa ba tayi masa magana ba, duk da
cewar ta fahimce ba makaranta ya je ba.
Bayan ya ci abinci, yayi Sallah. Nan ya gungura
bisa tabarma yayi ta barci har karfe uku da
rabi.
Umman ta shi, ta tashe shi ta ce yayi sallah, ya
tafi Islamiyyar sa.
"Sai ka ki zuwa mkrnta yau?" Inji Sageer. Ya
ce,"Ban je din ba, sai me?"
Ya ce,"Sai me kuwa? Hedimasta na nan yana
jiranka." Ya ce,"Kar ya rage min rai. Sageer yayi
dan murmushi ya ce,"Ba ka ma san wani abu
ba, na je ajin ku neman ka, sai na ga yarinyar
nan Zarah ta sha kuka, ta gaji, wai bata gan ka
ba.
Ni ne ma na rarrashe ta, na je na siyo mata
kankara da gyada.
Tun da yake magana, ya sanya masa ido har ya
kare.
Hankalinsa tashe ya ce,"Inna lillahi. Wallahi
mantawa na yi." Ai kuwa ta sha kuka, har da
'yan mangwaron guda 2 a hannu, na yi na yi ta
sha mangwaron ma, ta ki wallahi.
Nan da nan ran sa ya 6aci ya fada tunanin
Zarah.
Can ya nisa ya ce,"Gobe zan je mkrntr. Ya
ce,"Da dai ya fi.
Suka isa Islamiyya suka shiga aji.
Fadan sa biyu da yara ka fin Malam ya shigo
cikin aji.
Washe gari Naseer ya je makaranta, kuma Zarah
ya fara nema a jin na su, ka fin a shiga asanbili.
Tana tsaye bisa barandar ta hango shi tafe.
Da gudu ta sauko ta kama shi, tana murna.
"Zarah!"
Ta dube shi,"Jiya ban zo ba ko?"
An ce ki na ta kuka."
Ta ce,"Inna ce ta ba ni mangwaro ta ce,"In sha
daya, in kawo maka daya.
Ina ta neman ka, ban gan kaba."
Yayi dan murmushi, ya ce,"Kuma sai aka ce ki yi
kuka?
Kar ki sake kin ji?"
Ta ce,"To.
Tana lalubar Jakar ta.
Mangwaron ta dauko ta mika masa,"
Ga shi nan, na boye maka shi a jaka ta.'a
Ya amsa yana fara'a sosai,To na gaode, idan kin
koma gida, ki cewa Inna na gode."Ta amsa da
,"To."
Tana fadi ana kadawa, don haka ya ja hannun
ta zuwa layin su, ya sanyata a layi har yana ba
na kusa da ita gargadinka kar su sake su ture
ta.
Da (Break) tare suka yi kamar yadda suka saba.
Koda aka tashi, sai da ya tsallakar da ita titi,
sannan ya dawo suka wuce tare da Sageer. Har
cikin ran Naseer, yayi alkawarin ba zai sake
fashin mkrnt ba, sbd Zarah, kar ta neme shi, ta
rasa, hankalin ta ya tashi ta yi kuka.
Ranar laraba ya je mkrnt, ya nufi ajin su Zarah,
aka ce masa bata iso ba tukuna. A asambili bai
gan ta ba, har aka fito break. Ya shiga damuwa
kwarai, dn haka ana tashi, ya binciki wadanda
suka san gidan su.
Ya samu, suka dunguma tare da Sageer da
sauran yaran.
A gangare gidan su yake, suka tsaya a zaure.
Baban ta ya ritsa su, sai ya wucr cikin gidan. Ya
ce,"Lafiya yaya aka yi?"
Naseer ya ce,"Ba mu ga Zarah a mkrnt bane,
shine mu ka zo mu duba ta.
Cike da fara'a ya ce,"Ayya!
Zarah yau babu lafiya, zazza6i take yi.
To ku shigo mana, shine za ku tsaya a zaure ku
na leke?
Ka yaro ho!"
Suka bi bayan sa har dakin Innar Zarah.
Tana kwance, anyi mata shimfida a bakin kofa,
an daga labule don ta sha iska.
Malam Umar ya ce,"Ku shigo, ta nan a kwance.
Ina A'in take ne?"
Zarah ce ta gaya masa tana bayi.
Su Naseer suka shigo suka zauna gefe suka,
gaishe ta, bata iya amsawa ba, wai kunya sai
6oye fuska take yi.
Innar ta ta shigo tana fadin Baki mu kayi?" Ya
ce,"Yan makaranta ne, suka zo duba autar
ki."Ta ce,"Ah! Sannun ku da zuwa." Suka gaishe
ta, ta amsa tana zama kusa da Zarah, hakan ya
ba Zarah damar hayewa jikin ta, tana mata
rada.
Cike da fara'a Innar ta ta dube su,"Wanene
Naseer din? Ya sunkuyar da kai, yayin da Sageer
ke nuna shi. Ta ce,"Kullum sai an ba mu lbrn
Naseer. Ya tare fada, ya siya min wannan, ya ba
ni wancan.
Ashe babba ne.
Ajinka nawa?"
Ya ce,"Shidda 6,."
Ta ce ,"Ashe ma ka ku san gamawa.
Lallai Zarah za ta yi kewa, don shekaran jiya ne,
ba ka zo ba ko?
Nan ta ishe ni da magana, Inna yau Naseer bai
zo mkrnt ba.
To mun gode Naseer.
Allah yayi ma ku albarka."
Duk kunya ta rufe shi da kyar ya ce,"Amin.
Malam Umar ya ce,"To an gode, sai ku tashi
kowa ya tafi gida ko?" Kar aga kun dade ba ku
koma gida ba. Mun gode." Suka mike suna
fadin,"Allah ya kara sauki." Iyayen ta suka ce
"Amin."
Sun fice, jim kadan wani yaro ya dawo cikin 'yan
rakiyar Naseer.
Wani kulli leda ne ya shigo da shi,." Wai ga shi
in ji Naseer.
Ya aje gefen Zarah ya ruga a guje.
Inna na ta dariya. Ta kwance bakar ledar, kullin
gugguru da gyada ne a ciki da aya soyayya. Ta
kada kai ta ce,"Allah sarki yaro, shi kuma jininsa
da na Zarah ya hadu.
Malam Umar ya ce,"Shiririta ke nan.
Ko ina ne gidan su?
,"Oho."
Ita kuwa Zarah tuni ta fara diban abin ta tana
ci.
Kwana 2 Zarah na kwance a gida.
Kullum sai Naseer ya je gidan da safe da
yamma. Hakan yasa iyayenta suka san Naseer
sosai.
Innar ta ke cewa"Lallai Zarah Allah ya ba ki
yaya daga sama."
Shi yasa da ya zo, sai ta ce, "Zarah ga yayanki
ya zo." Ko barci take kuwa za ta tashi. Sai dai
Zarah ta warke ta koma Mkrnta, sannan
hankalin Naseer ya kwanta.
A dalilin Zarah. Naseer ya nutsu a mkrnta, ko
sau daya baya fashi, duk da cewar bai bar Polo
ba, domin duk asabar da lahadi in dai akwai
wasa, toh yana can. Ba karamin mmk ya ba
kowa ba. Iyayensa na ta murna, suna yiwa Allah
godiya, duk da dai rigimar sa ta neman magana,
tana nan babu abin da ya sauya.
Naseer kam bai iya zama na cikakkiyar awa 3,
sai ya nemi abokin dambe.
Duk sa'o'insa tsoronsa suke yi, sbd karfinsa,
balle kananan yara.
Ganin ya nutsu a mkrnt, yasa Hedimasta ya
nada shi (Labour prepet). Sosai yake gudanar da
aikinsa, don ba sauki, ga yara.
Zarah ko ajin su kuskuran kallon banza, babu
mai yi mata shi, sbd kanwar Naseer ce.
Kokarinsa da komai, sai ya nuna shi babba ne,
ke sawa yana kara kwarjini a idon kowa.
Allah yayi masa kyau, surar jikinsa kaf bai da
makusa.
Shi ba fari bane, kuma ba baki bane,."
Sannan ya zarce wankan tarwada.
Wasu manyan idanuwa da Allah yayi masa
farare sol!
Su ke sawa duk wanda ta kallai, sai tayi
sha'awar sa.
Ubangiji yayi wa Naseer wannan baiwa.
Wanda adalilin haka ne kawai yake shiga ran
jama'a su kamu da kaunar sa.
Yau suke zana jarabawar share fagen shiga
karamar sakandire (Common Entrance). A
kwalejin Alhuda-huda. Sun yi, sun gama cikin
sa'a kowa ya koma gida.
Ranar litinin suka taru a mkrnt, kamar yadda
aka bukace su.
Hedimasta ya raba masu satifiket da
Testimoniya, sannan ya sallame su, sai ranar da
jarrabawa ta fito, za'a neme su.Suna fitowa,
ana tashi tara. Naseer ya kama hannun Zarah
ya kai ta siyen kayan kwalama. Daga nan aji ya
zagaya da ita, yana ba yara kashedi da gargadin
NI duk wanda ya kuskura ya ta6a masa Zarah,
musamman zai zo mkrntr kuma kashin mutum
ya bushe, idan ya kama shi.
Shi dai Sageer bin sa kawai yake yi, yana dariya.
To wa zai ta6a ta? Bayan Naseer sunan ya gama
firamaren ne kawai, amma kodayaushe yana
can, sai ya tabbatar da Zarah ta yi break, an
koma aji, sannan ya kama gaban sa.
Idan ya ga

Please Login or Register in order to submit comment