Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

can a
waje, yana kuka."Ta ta6e baki ta ce,"Ban haihu
ba, Antina ce ta mutu. Ya kamo ha6arta ya
ce,"Dube ni, ki saurara da kyau, za ki ji kukan
Bebi. A kawo shi ya sha? Tayi shiru, tana
kallonsa. Ya sake kiran Zarah, ya ce ta kawo
Bebi,. Ta zo da shi a shawul, ya kar6e shi, ta
tsaya tana kallonta! Ya ce,"Yauwa, dube shi ki
gani." Kyakkyawan kallo tai masa! Ya ce,"Yauwa,
dube shi ki gani, kyakkyawa da shi." Ta leko ta
dube shi,"Abba na wannan k'aton Yaron ai ya
girme ni." Ya ce,"Ban son shirme, ba shi ki gani,
idan bai sha ba, ki min duka." Ya dora mata shi
bisa jikinta, ta 6allo wa Zarah harara, sannan ta
dubi Naseer,"Abba na ka ce wa matar nan ta
fita, ban son ganin ta. Munafuka kawai, duk
sune suka kashe Antina." Hawaye suka kawo wa
Zarah, ta juya ta fita. Ya ce,"To ta fita, ba shi ya
sha. Ta ciro ta ba shi, ya kama sai tsotsa yake
yi, bawan Allah ya sha kuka, shi yasa bai jima
ba, barci ya kwashe shi. Naseeer yayi zuru,
yana kallon su, tsabar tausayinta yake ji, kamar
ya ce wayyo Allah. Ta ce,"Abba na ka daina
kallo na mana." Ya ce, "Ah! Ai kowa dole in kalle
ki, tunda ina son ki, kin zama abar kallona. Ko
kuwa? Ta sadda kai, tana dan murmushi. Ya dan
k'ara matso ta, ya ce,"Kin ga har yayi barci, to
ke ma ya kamata ki kwanta ki yi barcin, ki huta
ko?Ta yi hamma mai tsawo, yana rufe da
bakinta, kafin ta ce,
"Barci?"
Kin ga ni ban son shirmen nan na ce.
Kawo Bebin a kwantar da shi, ke ma ki kwanta
ki gani."
Ta ce,"Bar shi kawai, ya yi min dadin rikewa."
Hirar su kawai suke yi, abin ya ba kowa mmk,
har Alh.Basheer ya gama zirga-zirgar sa, ya
dawo. Ummi ce ta mayar masa da yadda aka yi,
ta yi shiru ta natsu.
Ya shigo dakin a hankali Naseer ya mike yana
masa sannu da zuwa, da ta fasa wata irin k'ara,
gaba dayan su gigicewa suka yi.
Naseer bai san lkcn daya koma gun ta
ba,"Menene? Idanuwanta rufe tana fadin,"Ban
son ganin sa! Ban son ganinsa!! Munafiki
ne.............
Ya rufe bakin ta, yayin da Alh.Basheer yayi waje
da sauri. Naseer ya ce,"Ban son abinda ki ke yi
Nusaiba, gaskiya ni ma zan tafi." Ta ce,"Na
daina Abba." Ta ci gaba da surutu k'asa-
k'asa,"Munafikin banza, munafikin wofi, ya wani
shigo wa mutane ko kunya." Yayi shiru, ya
kyaleta, kwalla suka zubo masa, ya share.
Wannan al'amari da me yayi kama? Kuma fa
duk shine sila ko?
Ya tambayi kan sa. Wasu hawayen sharshar!
Suka fito, ya sake gogewa. Alhj kuwa yana tare
da su Ummi, shi ma sai da ya share kwalla,
sannan ya mayar da yadda suka yi da Likita,
kuma nan ba jimawa, za so zo su tafi da ita
dakin hoto.
Jama'a sun sha Zagi da tsinuwa lkcn da aka zo
daukan ta, har da Naseer din da yake fada aji,
ya zama munafiki, tunda yana gani zai kyale a
tafi a kashe ta.
Dole Likita yasa aka kawo masa wata allura, da
kan sa ya zurkud'a mata.
Take nan ta wuce luuuu....!!!
Ba rai, ba dalilinsa.
Sannan da masu daukan ta suka gara ta wajen
hoto.Har aka dawo da ita, bata sani ba, nan
suka bar ta tana ta barci. Hankalin kam ba a
kwance yake ba. 'Yan dubiya na ta zuwa gaishe
ta, amma tana barci, da yawa daga cikin su
daga Kaduna suke zuwa. Haka Antin Jordan
kodayaushe sai ta bugo ta tambayi jikinta. Bizar
ta kawai take jira a gama, ta kamo hanya.
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
Sakamakon duk gwaje-gwajen da aka yi mata
suka fito. Likita ya kira Alhj ofishinsa, shi kuma
ya kira Naseer, domin mijinta ne, hakkinsa ne
ya san halin da matar sa ke ciki. Kowanne ya ja
kujera ya zauna gaban Likita.
Shi kuma ya firfito da sakamako, ya ci gaba da
bayani."A gaba daya binciken da mu ka yi, babu
wata matsala a tattare da ita. Kwakwalwarta
lafiya lau, zuciya ma haka, k'oda lafiya lau, haka
jirin ta lafiya yake.
Saboda haka abin nan dana fara gaya maka
Alhj, shi din dai za mu ci gaba da kula da ita
akan shi."
Alhj ya ce,"Yanzu ka na nufin tsabar damuwa ce
ta jefa ta a wannan yanayin? Ya ce,"Kar ka yi
mamaki, damuwa tana sanya hawan jini, kuma
babu ga mai juna biyu.
Saboda haka za mu ci gaba da bata taimakon
daya dace, sannan daga wajen ku a matsayin ku
na iyaye da mijin ta, rarrashi ne kawai. A ring'a
lalla6ata, a kodayaushe, hanklinta ya zamana a
kwance yake tare da samun isashshen barci.
Insha Allah za ta warware, sai kun yi
mamaki."Alhj ya munfusa, ya dubi Naseer,"Ka ji
ko? Wannan aikin ka ne, ko dama kai kadai take
son gani, mu duk mun zama munafukai. Don
Allah ka yi hakuri da ita, sannan a rink'a had'a
mata da addu'a.
Idanuwansa cike da hawaye ya amsa,"Ya zama
dole Abba, Allah ya taimake mu."
Duk suka amsa da Amin."
Tun lkcn aka bar wa Naseer ragamar komai
ahanununsa, kowa ya koma gida, sai dai su zo
akai-akai su duba ta, shi ma ta, taga, idan har
idan ta 2, idan kuwa har ka ga wanin Naseer a
kusa da ita, tabbaci hakika barci take yi.
Zarah ma an sallame ta, ta koma gida, amma
kodayaushe zuciyar na asibitin, shi yasa bata iya
daurewa kullum ne sai ta zo, koda za ta wuni a
waje tana lek'en taga tare da renon Ameer.
Haka Likitocin ta ke iyakar kokarin su ba dare,
ba rana akan ta.
Magana ce ta kudi. Alh.Basheer kuwa ya saki
komai ya dace ayi mata, komai tsadar magani.
Shi kuwa d'an gogon, bai gajiya da yi mata
hidima, shi ne cin ta, shine shan ta. Kullum
yana like da ita, suna hiar shirme, domin kuwa
shirme ce, yanzun nan za'ayi magana dai-dai,
lkc guda sai ta ya6o shirmenta. Babu abinda ya
dame ta.Idan dare yayi kuwa tana barci, zama
yake bisa kujera ya zura mata ido, yana yi mata
addu'o'i. Idan ya tuna da bayanin Likita kuwa,
hawaye yake zubdawa sosai, domin ya tabbata
shi ya tara maya damuwar sa ta jefa ta wannan
mawuyacin halin.A haka so da k'aunar Nusaiba
suka zauna kwarai da gaske cikin zuciyarsa, har
yana mamakin kan sa."
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~Sabon
shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
Kwanan ta 11 yau, ya gama kintsa Ameer, ya
kwantar da shi cikin (Net) din sa. Ya dube ta,
tana ta lissafin zucci, ya ce,"Za ki sha Tin ne
kafin ki kwanta? Ta ce,"Had'o Abba." Ya had'o
mata dai-dai wanda ta saba sha. Ya zo da shi
bakin gadon, ya zauna. Ya debo a cokali ya
ce,"Ungo, sha 'yar gidan Abbanta." Ta dube shi,
tayi murmushi," Miss you."Dariya ta ba shi, ya
ce"Za ki fara ko? Ai ni fushi na ke da ke."Me na
yi Abba na? Ya mika mata, ta kur6e ya
ce,"Batan kin kori kowa, mutane na son ganin
ki, amma kin hana, me yasa?
Hmm... Abba na kullum ina raba ka, amma ba
ka ji.
Me za'ayi da munafukai? Ya ce,"Na fa hana ki
ce musu munafukai. Haka dazu ki ka cewa
Umma, sa'ar ki ce?
Ta dan 6ata rai, tayi shiru, ya miko mata Tea ta
ki kar6a. Ya aje cokali ya dago ha6arta."Fushi ki
ka yi? Da ni ki ke fushi, shi kenan bari in zo in
tafi." Ta ce,"Yanzu saboda Allah Abba duk
wanda ya nuna baya so na, ba munafiki bane?
Yanzu dubi yadda ka ke k'aunar Naseer, amma
k'iri-k'iri ya nuna min, baya so na, yayi ta
wulakanta ni. Saboda Allah Abba me zan kira shi
ba munafiki ba, tunda ya munafunce ka."
Tunda ta soma mgn, gabn sa ya yanke ya fad'i,
yayi sukuiti duk jikin sa ya mutu, ya rasa me zai
ce? Ta zura masa ido, ta ci ga,"Abba ai dai ka
san na maka biyayya da ka ce min shi ka za6a
min, ban maka musu ba ko, Amma ka san Allah,
shi baya so na, wannan cikin na jiki na ma, ya
ce da shi zan koma gidanmu, baya so. Na ce ai
ban je da d'a gidan sa ba, ko fan fadi gaskiya
ba?
Hankalin Naseer fa ya yi mummunan tashi, ya
tabbata wata rana a surutanta za ta iya fadi a
gaban kowa. Idanunwan suka kad'a, ya aje Tea
bisa dirowa ya rufe.Ya kamo kafadunta 2, suka
yi wa juna zuru kafin ya ce,"Wannan maganar
bata dace ki na fadar ta ba 'yar gidan Abbanta.
Naseer masoyin ki ne, ni ya gaya min yana son
ki kwarai da gaske."
Ta girgiza kai,"Na rantse da girman Allah, karya
yake maka Abba. Naseer munafiki ne, ina gaya
maka maganar nan, ka yarda da ni Abba." Ya
sake ta ya kama kai.
Ta bi shi da kallo ta ce,"Mamaki ma ka ke yi?
Kai har yanzu ba ka san mutane ba, ka na dai
kallo aka kashe Antina, me za'ayi?
Yayi hucin zafi ya ce,"Duk na ji, amma kin san
abinda na ke son ki da shi ?
Ki kyale maganar nan, kar ki gaya wa kowa, ni
zan yi maganin abin. Kin yarda?
"ka dai gaya masa, idan na haihu zan aje Yaron,
shi zai maida shi cikin lemon
gwangw........................
Ya like bakinta,"Nusaiba na ce ki bar maganar
nan, zan fa tafi abi na." Ta ce,"Yi hakuri." To kin
yarda ba za ki gaya wa kowa ba? Na yarda,
amma ka san Allah, ka yi hankali da wad'annan
mahaukatan da suke zuwa 6arayi ne."
Yayi shiru yana kallonta, duk ta dagula masa
lissafi." Ba ni Tin mana." Ya dauko ya ci gaba da
bata, sai zuba masa surutu take, shi kuwa bakin
sa ya mutu har ta yi barci.
Yayi tagumi bisa kujera, ya rasa abinda ke masa
dadi.Ta dai ce ta yarda ne kawai, ba za ta sake
fadi ba, amma abin maras hankali, ai ba'a sirri
da shi. Dan saukin ta ma, bata kula kowa sai
shi. Daran nan bai runtsa ba saboda tunani.
Safiyar yau kuma daga ya ce, bude baki ayi
burosh, shi ke nan ta fasa kuka. Yayi rarrashin
dunuya, ta k'i yin shiru, ta k'i kuma mgn, a
haka ta shafe sama da mintu 30 ita da kan ta ta
yi shiru. Ta gyara kwanciya, ya sanya mata ido,
tana ta ajiyar zuciya, har barci ya sace ta.
A lokacin shi kuma ya fara na shi hawayen da
kyar ya iya tsaida su, saboda tsabar tausayinta.
Ko me yasa ta kuka?
Oho!
Ya tambayi kan sa, ya ba kan sa amsa.
Idanuwan sa suka kara ja, kamar garwashin
wuta, dama ga rashin barcin da bai yi ba jiya.
Yana nan zaune zuru, ya ji motsin Ameer, shi
ma ya farka. Ya tashi ya zuba masa ruwan dimi
a fida ya zuba glucose ya karkada, sannan ya
dauko shi suka fito waje, ya zauna a kujera yana
ba shi har ya shanye. Idon sa 2, amma baya
kuka, yana ta 'yan wasannin sa. Naseer na taya
shi.
Muryar Alhj kawai ya ji yana masa sallama, ya
dago da sauri yana amsawa. Tare suke da Ummi
da Antin Jordan. Ya mike yana masu sannu da
zuwa. AntIn Jordan ta kar6i Bebi tana
fadin,"Sannu Naseer, don kai ne abin gaisarwa.
Yaro duk ya rame." Yana murmushi ya
tsugunna, ya gaishe su.Alhj ya ce,"Mutuniyar
barci ta ke yi ne? Ya ce,"Eh. Ummi ta ce,"Yauwa
mun yi sa'a, shigo Fatima ki gan ta."Suka
dungoma cikin dakin, shiru suka yi suna kallon
ta kawai, don kar su yi surutu ta farka. Sun
kusa minti 10 a tsaye, sannan suka fito dan
koridon. Naseer ya baza darduma, suka
zazzauna. Ya koma gefe ya zauna, suka ci gaba
da tambayar sa yanayin jikin na ta?
Ya ce,"Da sauki, an gode Allah, amma ko dazu
ta sha kuka, kuma ta k'i magana, abinda ma ya
sa ta barci ke nan."
Antin Jordan ta goge kwalla, ta dubi
Alhj,"Gaskiya yaya idan babu wani ci gaba a fita
da ita waje kawai." Ya ce,"Wannan maganar na
rai na, akwai iiya kwanakin da na dibarwa
Likitocin nan din ne, idan sungaza, zan dauke
ta."
Ta ce,"Wannan tashin hankali da yawa yake." Ya
ce,"Jarabci ne, mun gode Allah, muna rok'onsa
sauki.
Kai Naseer ka yi ta hakuri, ka ji?
Ya ce,"Hak'uri na mu ne duka Abba."
Haka suka kasance tare, jama'a na ta zuwa
kamar kullum. Koda ta farka. Naseer ne kawai
ya shiga, ya kai mata Bebi. Allah da ikon sa
babu kuka, sai hira kamar ma ba ita ta sharari
kukan dazu ba.
Yayi mata burosh, ya bata Tea, ta sha. Abin
yana ta 6a Antin Jordan mmk har ta
tambaya,"Yanzu ina shiga, sai ta fara Ihu?,
Ummi ta ce,"Ko za ki gwada ne?
"Don daukan alhaki? Na gan ta ta taga, ya isa.
Allah ya yaye mata."
Ta ce,"Amin. Kwananta 7 ta koma Jordan.
Ranar da ta tafi, ranar Kausar ta iso da mijinta.
Bata 6ata lokaci ba, ta fadawa dakin, kanta ta yi
ta rungume ta sa kuka. Wani ihun da Nusaiba ta
yi, dole ta sake ta, tana kallo, jiki na rawa. Ta
runtse ido, tana zagi tana fadin.
"Ban son ganin su. Ban son ganin su! Naseer ya
rirrike ta. Mijin Kausar ya fito da ita, me za ta yi
ba kuka ba. Haka ta fada jikin Ummi, tayi ma
isar ta. Naseer kuwa da kyar ya shawo kan
Nusaiba tayi shiru, ta daina zage-zage. Ba
karamin Huashi Kausar ta bata ba, sbd ta6a tan
da tayi.Yini guda masifar da ta rink'a yi
kenan,"Wata munafuka ta zo ta cakume ni za ta
kashe ni! Sai bayan la'asar tayi barci. Kausar ta
je gun ta, tayi mata addu'o'i. Hawaye na zuba.
Da yamma lilis suka koma Kaduna.
Haka Kausar ta tafi da bak'in ciki, a duk lkcn da
ta tuna hawaye, ke zubar mata.
(Allah sarki Nusaiba

Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100



Ajininsa yake 3-02
Posted by ANaM Dorayi on 08:53 PM, 20-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______



Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473

Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi

------------------------------------------------------------------------------------------------


To shi kenan ya wuce." Ya kamo ha6ar ta, yi
dariya,"Yi dariya 'yar gidan Abba!

Ta fado kirjinsa, tana murmushi.

Ya rungume ta, ya runtse ido, wasu kwalla suka
yi masa caa, fadi yake a ransa, "Son ki ya kama
ni Nusaiba, ki yafe min don Allah.". (Hhhhhhh,
Anzo gurin, ammafaaaa...uhm! Maji ma gani)




Bai ko san ta kici-kicin tashi ba, sai da ya ji tana
kira,"Abba!

Ka shake ni!

Ya hanzarta sakin ta, yana goge kwallah. Ta bi shi
da kallo,"Wash!

Ka wani matse ni Abba, ai sai in mutu."Ya tashi
ya bata wuri, ya shige bayi ba tare da ya ce
komai ba.

Jim kadan ya fito, ya wanke fuskarsa, kwance ya
same ta, ya matsa gabanta ya ce,"Hirar ta isa
haka, ki yi barci ki huta." Ta amsa da ka, ya
duk'o ya sumbace ta, ya ja mata mayafi. Ya ja
kujera ya zauna, ya sauke numfashi,"Allah ka ga
iya kokarin da na ke yi. Allah ka taimake ni
yarinyar nan ta sami lafiya.

Ta ce,"Ka kwanta mana Abba." Ya ce,"Zan
kwanta, ke dai yi barcin ki." Ta rufe ido.

Tare da gyara kwanciya.

Da asuba ya fito bayi da alwalar sa, ya shimfida
sallaya, yayi sallah. Ya jima yana addu'o'i kafin
ya jiyo motsin ta.

Ya waigo yana kallon ta, ta tashi zaune, tayi mika
tana salati. Ta kalli can, ta kalli nan, bai ce da ita
k'ala ba.

Ta k'ura wa Bebin da ke barci cikin (Net)
ido.

Ta dago kai ta dube shi, suka yi ido 4.

Yayi murmushi, ya ce,"Kin ta shi?

Fashewa tayi da kuka, ya taso da sauri ya zauna
gefen ta."

Nusaiba, ke Nusaiba, za ki fara koke-koken nan
ko?

Tayi shiru tana tunaniin Antin ta.

Hawaye na ta ambaliya.

Ya rik'o ta, ta kwace jikin ta, kuka take tana
k'arawa.

Ya ce a ran sa,"Na shiga 3, yau kuma da kukan ta
tashi." Ya matso, ta matsa. Ya ce,"Ni Nusaiba, ni
ki ke gudu? Bata kalle shi ba, balle ta ce wani
abu. Ya sake matsowa, ta matsa. Ya ce,"Shi
kenan, bari in yi tafiya ta, in tafi ko? Ta amsa eh,
da kai. Ya ce,"Tabd'i! Da magana yau,"Cikin
ransa.Ya rasa yadda zai yi, dole ya sa mata ido,
tayi ta kuka. Can kuma ta tashi ta fito koridon ta
zauna, bisa kujera. Shi ma ya biyo ta nan ya
zauna, yana gadin ta.

Jim kada ya ji kukan Ameer.

Ya mike ya ce da ita,"Ga Ameer can ya tashi, in
kawo shi ya sha? Ta kyale, bai ma ishe ta kallo
ba, ya shige ciki ya dauko shi, ya tsugunna
gabanta,"Yauwa, 'yar gidan Abbanta kenan, dubi
Bebin mu kuka yake yana jin yunwa, dan ba shi
ya sha." Ta dauke kai, tamkar bada ita yake
magana ba.

Abu fa ya gagara, dole ya dauko wa Ameer fida
ya tura masa, yayi ta tsotson ruwa da
glucose.

Kullum karfe 7 nan take masu. Alh.Basheer suna
nan zaune kuwa, sai ga su.

Naseer ne ya fara hango su, ya mike ya nufo
su.

Su ma tsayawa suka yi cak, ganin Nusaiba a
zaune wajen.

"Yaya dai? Alh.Basheer ya tambaye shi, yayin da
Ummi ta kar6i Ameer a hannun sa.

Ya ce,"Ai yau ko Ameer ta k'i ba shi nono.

Kuka kawai take yi,"Ya ce,"Likita ya zo?

Ya ce,"Ka tsaya nan, kai kuma koma gun ta, bari
in nemo Likitan." Ya koma wajen ta.

Alhj ya zaga ya wuce, ita kuwa Ummi ta
lafe.

Jimawa kadan suka dawo da Likita. Abin ya ba
Naseer mamaki daya ga Lkita ya zo, ya tsaya
gabanta bata zage shi ba.

Ya ce,"Nusaiba, tashi mu shiga ciki, mu yi wata
magana." Kai tsaye ta mike ta wuce. Naseer ya
saki baki, shi ma ya taso ya biyo su. Ta zauna
bakin gado, ya jawo kujera ya zauna ya
ce,"Kukan me ki ke yi?

Ta ce,"Antina ta mutu ko?Ya ce,"An gaya miki
bata mutu ba, Antin ki na gida." Ta runtse ido
wasu hawayen suka tsunke mata, ta sa hannu ta
share. Ya ce,"An ce kin ki ba Bebin ki nono,
saboda me? Haka za muyi da ke saboda Allah?
Ta dube shi da kyau ta ce,"Doctor ka yi min wani
taimako don Allah, lambar Abba na zan ba, ka
kira min shi." Idanuwan Naseer suka k'ara yo
waje, ya koma da baya da baya ya fito waje. Shi
kuwa Likita k'ara tsura mata ido, ya ce,"Abban
ki? Ta ce, eh. Ya ce,"Ina zuwa." Ya leka yayi kiran
Alhj da hannu. Ya taso daga inda yake zaune ya
zo. Likita ya kamo hannun sa, ya shigo da shi a
hankali. Kan ta na duke ya ce,"Wannan Abban
naki ki ke nema? Tana yo ido hudu da shi, ta
mike hawayenta suka yawaita, ta ce,"Abba! Wani
tsananin farin ciki ya kama Alhj, dole kwalla suka
cika idon sa, ya ce,"Bebin Abba! Ta rugo da gudu
ta rungume shi. Tuni Ummi ta fado dakin ta hade
su ta rungume, kuka suke saboda murna. Haka
Naseer ke sharar kwalla. Amma ya rasa abinda
zuciyar sa ke sakawa game da wannan al'amari.
Tabbas Nusaiba ta warke, to me zai biyo baya?
Da alamun zai shiga magana, yanayin da ta
nuna. Yayi ta maza ya shigo. Alhj Basheer ya
rungume shi, suna wa juna barka. Likita ya fita,
ya bar su cikin farin ciki da murna maras
misaltuwa.Bayan sun natsa. Ummi ta dubeta,
duk ta rame ta ce,"Sannu Nusaiba, Ubangiji Allah
ya k'ara karewa." Ta ce,"Amin. Ta miko mata
Bebi ta ce,"Kin ga Bebin da aka ciro miki? Ta dan
dube shi, tayi murmushi , ta dauke ido,"Na gan
shi Ummi ta. Kwalla suka taru fal a idonta, ta
kasa shanye su, sai da suka zubo. Abban ya
rungomu kafadunta, ya ce,"Yi hakuri daina kuka,
komai ya wuce Insha-Allah." Ya ce,"Allah ya
yarda Abba. Bari in yi sallah." Ta mike ta wuce
bayi ta jima bisa sallaya, tana yi wa Allah godiya
daya dawo mata da rayuwarta dai-dai. Ta dawo
gefen gado ta zauna kusa da Abban ta. Ya jawo
ta jikin sa, ta dan numfasa ta ce,"Abba lokaci yayi
da zan gaya maka wata magana, ina fatan za ka
gafarce ni." Naseer na jin haka, ya mike ya bar
dakin. Abba ya ce,"Babu komai Bebina, gaya min,
me ke da mun ki? Ummi ta sa masu ido tana
kallo. Ta k'ara gyara zama ta ce,"Na san za ka yi
mamaki, idan na gaya maka cewa tun aure na da
Naseer, babu kwanciyar hankali tsakani na da
shi. Ai kuwa Alh ya sha mamaki, ba shi da kadai
ba har Ummi da take zaune. Ya kara dubanta,
baki sake, ya tambaya, "Saboda me? Ta
ce,"Abinda na fahinta,"Abba, shine ya kar6i aure
na ne kawai don ka cika masa ido, ba zai iya ce
maka a'a ba. Amma a hakakin gaskiya Naseer
baya so na, kuma ya nuna min kiyayya, ba don
Antyna na tsaye ba, ina ganin wuyar da zan sha,
ba 'yar k'arama bace.

------------------------------------------------------------------------------------------------


Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473

Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi



------------------------------------------------------------------------------------------------


Shi yasa na ke son ta, domin tayi min komai,
kuma tayi iyakar kokarinta wajen jawo hankalinsa
zuwa gare ni, sai dai haka bata samu ba, saboda
babu sona a zuciyar sa." Ransa ya 6aci kwarai, ya
ce,"Me yasa tuntuni ba ki gaya min ba? Ta
ce,"Saboda kai ne Abba. Ba na son wani tashin
hankali ya shiga tsakanin ku. Kuma ina ganin ai
ya girmama ka ne, tunda ya kasa fitowa fili ya
nuna maka baya so na. Shi yasa na yi ta kokarin
zama da shi shekara daya da rabi, sai da Allah ya
kawo rabon wannan Yaron, sannan ya shiga daki
na. Daga baya na yi tunanin bai kamata mu
zauna muna cutar da juna ba, shi yana jin haushi
na, ni ma ina jin na shi. Sai na same shi a daran
da wannan abin zai faru, na yi masa magana.
Abba cewa yayi idan na k'ure shi, zai 6atacciya,
dole in koma gidan mu, har d'an baya so, ya bar
mana...................!!! Tana shiru. Ummi ta
cafe,"Ina, inda kuma yayi karya kenan. Ai ba mu
kai masa ke da Da ba." Alh.Basheer yayi shiru,
zuciyar sa na tafasa, abin kamar a mafarki yake
ganin sa, domin ko alama bai ta6a mafarkin
Naseer zai ci amanar sa haka ba. Ya dubi Ummi
ya ce,"Har hada mata kayan ta mu tafi." Ta mike
tana fadin,"Ashe ga damuwar da ta kusan hallaka
rayuwarki Nusaiba, kenan. Yayi wa kan sa. Kuma
sai Allah yayi miki sakayya." Nusaiba ta kada
kai,"Ba haka bane Ummi ta, ba laifin sa bane,
kar ki manta soyayya, gamon jini ce, laifin sa 1,
shine daya danki amanar da ba zai iya rikewa
ba."Alhj ya ce,"Duk laifin iyayen sa............ Tayi
saurin katse shi."A'a Abba, iyayen Naseer ba su
da laifi kuma ina mai tabbatar maku yadda ya
yaudare ku, haka ya yaudare su. Ba su san komai
ba a game da zaman mu. Sun rike ni tamkar 'yar
cikin su. Idan na ce ga abinda su kai min, na yi
masu karya, sai Allah ya tambaye ni. Abba, rokon
da zan maka daya ne, don Allah, don son Annabi
kar ka k'ullaci kowa akan maganar nan, ni ce
baya so, to ka dauki 'yar ka. Ai shikenan, an
gama magana." Ya ce,"Haka ne Nusaiba, ki yi
hkr, ni ma na gane kuskure na, ni na jawo miki
duk abinda ya same ki." Ta ce,"Ban ta6a ba ka
laifi ba Abba, ba kuma zan ta6a ba ka ba. Ai kai
alheri ka k'ulla, sai dai ka san a wannan zamanin
ba kowa yake son ayi masa za6in abinda ya
kamace shi a ruywar sa ba. Ya fi son abinda
ra'ayinsa ya ba shi. Ka ga kuskuren da aka samu.
Ina alfari da kai Abba na, kuma ko a yanzu ka
sake za6a min miji. Wallahi zan aure shi. Bai san
lkcn da ya rungume ta, ya fara kwalla ba. Haka
Ummi ke ta share hawaye, tana sawa Nusaiba
albarka. Ta mike ta shiga hada kaya. Hayaniyar
hama'a suka jiwo gaba daya jama'ar Naseer ne.
Zarah ma kayan barci ne ajikin ta, ta dora zani ta
sa hijabi. Suka doro cikin dakin. Zarah na
fadin,"Amarya!Ta zaburo da gudu, "Antina! Suka
rungume juna, sun sha kuka, sai da Umma ta
raba su ita ma, ta rungume ta. Daga nan ta
matsa ta gaida kowa. Su Malam Balarabe, Malam
Umar. Ya gaisa da Sageer da amayar sa. Bayan
an gama gaishe-gaishe. Malam Balarabe yasa aka
yi addu'a, kowa ya shafa. Aanan suka lura babu
Naseer tun shigowar su. Inna ta fara
magana,"Jama'a wai ina dan Inna ne? Malam
Umar ya ce,"Kai wai dama babu Naseer a wajen
nan? Sageer ya amsa,"Ai kuwa baya wajen nan,
tunda muka zo? Malam Balarabe ya ce,"Ah to ina
ya je? Ya fadi, yana kallon Alh.Basheer. Ya
ce,"Gaskiya ban san inda ya je ba. Kuma dama
ina son ganin ka, idan ba za ka damu ba." Ya
ce,"Bismillah Alhj, ba damuwa." Suka fito waje,
yayin da Zarah da Nusaiba ke like da juna suna
maida yadda abubuwa suka faru. Alh.Basheer ya
kebe da M.Balarabe, ya kwashe bayanin da
Nusaiba tayi masa kaf, ya gaya masa. Tun da ya
soma magana, gaba daya jijiyoyin jikin Malam
Balarane suka tsinke, jiri ya fara dibar sa. Allah
yasa a zaune suke, da babu abinda zai hana shi
faduwa. Tabbas ya san Naseer baya son auran
nan, aka yi shi, amma ko alama bai ta6a sanin
rashin mutunci da wulakancin da ya rinka
aikatawa ba. Ya jima kafin ya ce,"Alhj wannan
magana ta ban kunya, kuma Wallahi tallahi ban
san komai a game da zancan ba. Nusaiba bata
nuna mana ba, balle ta furta da bakin ta. Don
girman Allah ka yi hakuri Alhj. Ya ce,"Ai magana
ta k'are, tunda baya son ta, ni ina son abata
kuma zan tafi da ita, ba tare da 6ata lkc ba.
Amma D'a, ban sako mata shi cikin gara ba, sbd
haka nan za ta aje shi ko ya kashe ko ya bar shi
da rai, duk ya rage nasa. A karshe, ka gaya masa
na gode. Allah ya saka da alkhairi. Kan
M.Balarane yayi gingirinn! Kunya kamar ya nutse
kasa. Idanuwan sa suka cika da kwalla, ya rasa
me zai ce wa Alhj? Kawai sai ya juya ya dawo
dakin, gaban kowa ya daga murya ya
ce,"Nusaiba, don me za ki min haka???Akan me
za ki zauna sama da shekaru 2 cikin wulakanci da
bak'in ciki,

Please Login or Register in order to submit comment