Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

a titi da kyar
Direba ya gyara."

Yaranta mata duga guda 4, suka yayyame ta,
kowa son ya dauki Bebi yake yi.

Babu 6ata lkc. Direba ya kwashe kaya suka
rankya.

Tunda daga mota, har gida Antin Jordan ke
balbala tsiya akan abinda ya faru.

Dakin ta daban, aka ware mata ita da Bebin ta,
bayan an gama duk kayaniyar ganin juna har da
maigidan ya tofa na sa albarkacin bakin sa.

Sai dai nasihohi yayi mata akan ta aje hankalinta
waje daya, kar ta sa wa ranta damuwa.Daki ta
koma ta yi wanka, ta yi alwala ta yi sallolinta.
Gefen gado ta zauna tana tanunanin yanayin da
suka hadu da Sakina, fara'a kamar gonar
auduga, amma tashi guda ta sauya fuska, saboda
mijinta ya nuna ya santa.

Ta yi dan murmushi, ta ce,"Allah sarki Antina,
alkhairin Allah ya kai miki."

Ta sa hannu ta jawo jakar Bebi, ta daukko lambar
da Sakinta ta bata a rubuce, ta sa hannu ta
yayyaga, tana fadi a ranta,"Sa ran ki a inuwa
Maman Husna, kullum ni da mijinki haduwar
[Aiport] ce, rabuwar (Airport)." Ta matse a
hannun ta, ta wuce bayi ta watsa (Dosbin).

-----------------------------------------------------------------------------------------------


Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473

Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi



------------------------------------------------------------------------------------------------


~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~

Washe gari da wuri Naseer ya nufi Kaduna. Shi
kadai kuma ya tafi, wannan karon zuciyar sa ta
bushe, matar sa kawai yake son ta dawo.

Shi yasa ya kwashe duk wani tunanin dake ran sa
a game dake ran sa a game da tinkarar Alhj.
>
Yayi fakin, ya fito kai tsaye falon yayi
sallama.

Mariya dake goge-goge, ta amsa sannan, ta
durk'usa ta gaishe shi ya ce,"Hau sama ki kira
min Ummi." Ta ce,"Tana ma kicin, bari na kira
ta."

Ya zauna Mariya ta wuce. Jin kadan ta dawo ta
ce,"Ga ta nan zuwa." Ya share minti 5 nan, kafin
Ummi ta iso falon.

Ya mike kai sunkuye ya ce,"Sannu Ummi." Bata
tanka masa ba, ta wuce ta haye sama. Yayi tsaye
nan kirjin sa na harbawa.Bai sake ganin kowa ba,
wucewar minti 30 har ya gaji da tsayuwa ya
koma ya zauna.

Can Alh.Basheer ya tinkaro falon.

Ummi na rike da jakar sa suna maganganun
su.

Naseer ya kuma mikewa yayi tsaye irin na marasa
gaskiya. Ko inda yake Alhj bai kalla ba, jakarsa ya
karba. Ummi ta ce," A dawo lafiya." Ya ce,"Amin."
Ya fice.

Ummi na ta wuce kicin, ta ci gaba da hidimomin
ta.

Naseer yayi kamar ya nutse a kasa, jiki babu
kwari ya biyo bayan Alhj, amma kafin ya
karaso.

Alhj ya shiga mota. Deriba ya tayar. Haka ya
tsaya kamar dolo, yana kallo aka bude get.

Motar ta fice. Ya wuce ya shiga ta sa, ya bi bayan
sa.

Ofis ya ga sun nufa, shi ma ya bi su. Yana zuwa
zai wuce sakatare, ya ce,"Alhj ya ce ka dan jira
shi a nan tukuna."

Ya ce,"To." Ya zauna.

Shi kansa sakataran dauke da mamaki yake,
domin bai ta6a yi wa Naseer iso ba wajen
Alhj.

Yana nan zaune Alhjn ya kira waya, ya bada
izinin Naseer ya shigo.

Ya mike ya tura kofa, ya sjiga Alhjn na ta aikin sa
bisa (Laptop), bai ko kalle shi ba. Ya duka ya
gaishe shi, ya amsa a dakile.

Yayi shiru, haka shima Alhjn bai dube shi
ba.

A haka ya daure ya fara magana,"Abba, na san
babu abinda zan gaya maka wanda zai faranta
maka rai, amma duk da haka ina mai gurfanar
da kai na gare ka a matsayin mai laifi.Ka yanke
min duk hukuncin da ya dace dani, wanda zai
sanyaya maka rai, har ka huce ka ban Nusaiba,
in koma da ita.

Da sunan Allah na ke wannan rokon Abba, ka
taimake ni don son Manzon mu.

Yayi shiru. Shi kuwa Alhj sai a aikinsa yake
yi.

Kamar ba zai tanka ba, wucewar mintoci, kafin ya
ce,"Ka na iya tafiya, zan neme ka."

Ya durk'usa guiwa 2 ya ce,"To shi kenan, na gode
Abba.

Kuma ina k'ara neman afuwa akan kuskuran da
na yi.

Ka gafarce ni Abba."

Ya ce,"Ka je zan neme ka na ce."

Ya mike yana fadin,"Na gode, a tashi lafiya."
>
Bai amsa masa ba ya fice.

Alhaji ya sauke numfashi, ya dafe goshinsa, bai
san dalilin da yasa son Naseer yayi masa yawa a
zuciya ba, duk lokacin da ya gan shi kaunar sa
karuwa take.

Dole ce tasa ya yanke hukuncin nan, saboda ya
kar6o wa Nusaiba 'yancinta.

Ofishin su Yakubu Naseer ya nufa, can bargar
dawakai, amma wurin na kulle babu kowa, sai
mai ba dawaki abinci.

Bai tsaya 6ata lkc ba, ya damko hanyar dawowa
gida, yana tafe wasi-wasi ne fal cikin ransa, wata
zuciyar na saka masa zai yi wuya Nusiba ta dawo,
wata kuma na tabbatar masa za ta dawo ne,
tunda ya ce zai neme ka.,

Ai kai d'an gaban goshin sa ne. Daya iso shago,
ya tsaya wajen Sageer.

Bai dawo gida ba, sai karfe 1,abu na farko sada
fara gani, shine babu motar Nusaiba dake lullu6e
a wajen.

Gabnsa ya fadi, ya fito da sauri ya fada cikin
gida.

Zarah na zaune a barndar sasan su, tana ta
faman goge kwalla."Menene wai?

Ban ga motar Nusaiba ba a waje!

Murya na rawa ta ce,"An kwashe kayanta, ka ga
shi kenan ta faru, ta k'are, tuntuni na ke gaya
maka, ka je ka k'i................

Ya katse ta da masifa,"Don Allah isa haka, kar ki
kara 6ata min rai!

Ko yanzu daga ina na ke? Ya ce zai neme ni? Ai
shi kenan tunda baya son ta dawo!

Ya nemi waje nan ya zauna dabas, ya cire hula
zufa ta keto masa.

Zara bata iya kara komai ba, ta ma tashi ta bar
wajen.

Umma na jin sa, kanzil ba ta ce da shi ba.

Bayan sallar la'asar, yana kwance dakin sa ya
rasa abinda ke masa dadi, kamar an kwaso son
Nusaiba an kara cusa masa cikin zuciya, sannan a
'yan kwananin nan da bai ga Ameer ba, duk
kewarsa ta ishe shi.Gaba daya abubuwan sun
dagule masa, domin ya sani ba za su ta6a
daidaitawa da Abbansa ba, muddin Nusaiba bata
dawo cikin gidan nan. Ya runtse ido, ya dafe kai
kamar ya kwarma ihu. Zumbur ya mike ya
kwashi makullai, ya fice ko Zarah bata sani ba,
ya fada mota. Ya sake yi wa Kaduna tsinke. Yana
zuwa. Sakatare ya ce Alhj ya tashi.

Yana kokarin fitowa daga get. Motar Yakubu na
shigowa. Suka tsaya kowa ya fito gaba dayan su,
babu mai walwala a fuska. Yakubu ya fara
magana,"Ko ka ji abinda ya faru?" Ya ce,"Na
me ? Ya ce,"Na rufe (Dabai Riders) mana.

Alhj ya rufe kulob, yadda yake gaya min ma ya
sa dawakan a kasuwa har an samu masu siya."
Salati Naseer ya fara yi, kafin ya ce,"Saboda me?
Ya numfasa ya ce,"Wallahi ban sani ba, amma
tun faruwar wannan al'amarin na ku hankalin
Alhj a tashe yake. Iyaka kokari na, akan ya sauya
shawara, amma ya ce ra'ayin sa ne.."

Naseer ya k'ara tarus! Idanuwan sa suka kawo
kwalla, ya ce,"Yakubu ban san yadda zan yi ba,
dazun nan na zo na yi magiya gun sa, ya ce in je
zai neme ni, wai ina zuwa gida. Na tarar an
kwashe kayan Nusaiba kaf. Lambarta ba'a
samu.

Kuma ni na san rufe kulob din nan, duk baya
rasa nasaba da matsalar nan, wata kila yana
ganin ta dalililin Polo ya hadu da ni.Ban san abin
yi ba Yakubu? Ya ce,"Gaskiya ne. Magana kan ta
gama lalacewa. Ka san komai Alhj zai iya yi
saboda Nusaiba, kar ka manta ita ce 'yar sa
kawai. Sannan duk abinda ya faru, kai ka jawa
kanka, domin ba karamar asara ka yi ba. Sai ka
yi addu'a Allah ya sa hakan shine alkhairi. Gida
ka nufa?

Ya kada kai,"Ina nan sai na ga abinda ya turewa
buzu nad'i. Yakubu ya ce,"To sai ka
dawo,"Goodluck." Na gode." Naseer ya fice, shi
kuma ya karaso wajen sakatare, ya aje abubuwan
daya zo da su.

Gidan Naseer ya nufa. Alhj na tare da baki. Yayi
sallama ta gaishe su. Alhj ya bi shi da kallo. Ya ce
"Dama na zo ganin ka ne, bari in jira ka." Ganin
mutane a wajen yasa ya amsa." To ina
zuwa."Naseer ya fita, motar sa ya zauna yayi ta ji


Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100


Ajinisa Yake3-04
Posted by ANaM Dorayi on 05:24 AM, 23-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______

Zan yafe maka komai, ya wuce har abada, amma
sai ka kawo min takardar Nusaiba."Kansa cikin
giuwa, ya girgiza kai, ya ce,"Ba zan iya ba Abba,
ka yi hkr." Ya ce,"Wannan ba hukunci na ba
ne.Nusaiba ce ta buk'ata ta kuma bar min
sallahu jiya kafin su wuce Jordan.." Ji yayi
numfashinsa ya shake gaba daya, yana neman
faduwa.

Ya kasa motsi, balle ya ce wani abu. Ya ci gaba
da cewa,"Na ba ka nan da jibi ka zomin da
takardar, daga nan zan maka bayanan wasu
abubuwa da suka kamata ka sani.

Ka na iya tafiya dare yana k'ar yi." Ya dago
idanuwa jajur! Ya ce,"Ummi ku taimake ni, ku ba
ni lambar ta mu yi magana, na san zata saurare
ni. Amma a raba auran a haka, abin babu
dadi.."Abba ya ba shi amsa,"Ban son dogon nace
Naseer, raina k'ara 6aci yake yi. Kwanciyar
hankalin na da kai shine ka kawo min takardar
Nusaiba. Yadda ba ka so, haka ita ma bata so,
shi kenan magana ta k'are babu lallai babu
tilas."

Ya sunkuyar da kai, yayi shiru. Ummi ta
ce,"Yakamata ka tafi, dare ya fara yi Naseer,
muna sauraronka."Yayi wawan ajiyar zuciya, ya
mike da kyar ya ce da su,"Sai da safe,gaba daya
suka amsa,"Allah ya kai mu, a gaida mutan
gidan."Bai k'ara komai ba, ya sakko a hankali ya
tafi.

------------------------------------------------------------------------------------------------


Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473

Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi



------------------------------------------------------------------------------------------------


Karfe 11 dare, ya shigo gida,. Zarah na zaune a
falo ta ci uban tagumi, ya turo kofar ya shigo." Ta
mike tsaye da sauri ta tarbe shi."

Yayana!

Kai kuwa ina ka shiga yau?

Bai tanka ba, ya wuce kujera ya zauna, ta bi shi
hannun kujerar ita ma ta zauna. Ganin yayi zuru-
zuru, yasa tausayinsa ya rufe ta.

Ta nunfasa ta ce,"Ina ka je yayana? Ya
ce,"Kaduna na koma." Ya aka yi to? Ya mayar
mata da abubuwan da Alhj ya ce,yayi shiru ta
rasa ta cewa. Ya kwanto da kan sa bisa
cinyoyinta, shi ma ya yi shirun Ta dafa kan sa ta
ce,"Kai yanzu me ka shawarta."Ya ce,"Na hukara
Zarah. Allah na gani na yi ikayar kokarina. Abinda
ya fi damuna maganganun da Alhj yayi. Ba
k'aramin dafa min jiki suka yi ba, sbd a zahiri
Alhj masoyina ne.Sai kin ga yadda ya cika hotuna
na a falonsa, kya rantse da Allah ni ne dan masu
gidan.

Ni dai na yi abin kunya, ban san ta yadda zan yi
in wanke kai na ba."

Ta ce,"Gaskiya ne, amma duk da haka ka tuntubi
su Umma ka ji ko za ta ce wani abu." Ya mike ya
wuce bayi, yayi wanka ya ji sanyi a jikin sa,
sannan ya kwanta.

Zarah na k'ara kwantar masa da hankali.

Da safe ya shiga wajen su Umma ya gaishe
su.

Abba bai amsa ba, ya tashi ya koma cikin
daki.

Daga can yana jin duk bayayin da yake wa
Umma.

Yana gamawa ta ce.

"To ne menene nawa a ciki? Duk abinda ka ga ya
dace, ka yi, tunda wannan 'ya ba ta mu bace,
k'arewa ma ka ce bata k'asar.

Ka ga da gaske Abbanta ya ke yi." Yayi dan jim
kafin ya mike, ya bar falon.

Umma ta bi shi da kallo, tausayin sa ya dan
kama ta, ta kada kai ta ce,"Kai ka jawo wa kan
ka."

------------------------------------------------------------------------------------------------


Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473

Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi



------------------------------------------------------------------------------------------------


Sati 1 Naseer yayi yana sintiri Kaduna, wai ko ya
sanmi sauyin baki daga Alh.Basheer, amma sam
babu.

Yau daya je ma. Alhj cewa yayi yau ce rana ta
karshe daya ba shi, idan bai kawo takardar ba, to
kar ya sake zuwa gun sa, kuma duk abinda ya
biyo baya, kar ya ce yayi masa wulakanci.

Babu yadda zai yi, a daren ya rubuta takarda,
saki 1 ya sa a ambulan ya rufe.

Washe gari ya isa gida, ya sami Alhj yana shirin
fita.Bayan sun gaisa Alhj, na kallo irin ramar da
Naseer din yayi. Ummi ta zo suka gaisa. Yasa
hannun aljihu ya ciro ambulan, ya tsugunna ya
mika wa Alhj. Ya kar6a, ya buda, ya karanta, bai
ko karasa ba, ya rufe saboda irin lausasan
kalaman da ke cikin takardar.

Ya dube shi ya ce,"Magana ta kare Naseer, kuma
duniya da lahira na yafe maka abinda ka yi min.
Son ka a cikin jini na yake, na rantse da Allah ba
zan iya cire shi ba, saboda haka ka saki jikin ka,
kai da na ne.

Magana ta 2, ita ce,"Gida da motocin da na ba
ka, mallakin ka ne, ba na bukatar su. Abinda na
ke son ka da shi ne, ka dauki Zarah ku koma can
da zama.

Wannan umurni ne a matsayin na Babanka."Gaba
daya tsigar jikinsa suka tashi yar! Idanuwansa
suka kawo kwalla.

Ya zamo daga kujera ya ce,"Na gode Abba. Allah
ya saka da alkhairi."

Ya ce,"Koma ka zauna. Yanzu yaushe za ka
kammala karatun ka? Ya sunkuyar da kai, kunya
ta rufe shi, ya rasa me zai ce? Da kyar ya daure
ya ce,"Ai dama ban fara ba."

Da mamakinsa ya maimaita ,"Ba ka fara ba? To
da ka ce min ka na zuwa?

Ya sunkuyar da kai, kamar ya ratsa kujera ya
shige. Alhj yayi dan murmushi ya ce,"Allah da iko
yake, yanzu yaushe za ka fara? Kidimewa tasa ya
ce,"Gobe." Ummi ta ce,"Gobo kuwa? Ba dai gobe-
gobe ba, ai kuma sai an sake nema ko? Ko kuwa
ka na da "(Admission) ne a hannun ka?

Ya girgiza kai,"A'a.Duk sun lura a daburce yake,
saboda haka Alhj ya ce,"Shi ke nan, ka je ka yi
duk abinda ya kamata, idan ka sami ( Admission)
din ka kawo min." Ya ce,"To na gode Abba."
>
Ya kosa ya tashi saboda tsarguwa, zufa ce kawai
ke kwararo masa cikin riga.

Yana samu aka sallame shi, jikin sa na rawa yayi
godiya, ya fice.

Alhj ya dubi Ummi ya ce,"Kawai Allah ne ya dora
min son yaron nan, ba don haka ba, inda na ke
ma idan aka ce ya zo da kudi ba zai zo ba."

Ta ce,"Ya za'ayi, ga kuma zuri'a a tsakani, dole a
rage wani abin." Ya numfasa yana kada ambulan,
sannan ya mika mata,"Karanta ki ji bayanan dake
ciki." Ta kar6a ta karanta, ta yi dan murmushi ta
ce,"Allah sarki da alama ya saduda Alhj."

Ya ce,"Kyale ni da shi dai."

Ta ce,"Na kyale."

Kowa ya ji abinda Alhj yayi, sai ya sanya masa
albarka.

A hakikanin gaskiya Alh.Basheer mutum ne
wanda ba'a samun su a wannan zamanin, sai an
shekara ana bincike cikin mutanen kirkin da ake
wa zaton suna da halin mutan da can. Karshen
soyayya Alh.Basheer ya nuna wa, Naseer shi yasa
Naseer din ke k'ara nadama kan nadama, so da
kaunar Nusaiba ke k'ara dabaibaye
zuciyarsa.

Kewar ta ke jefa shi.

Nisan tunanin ta musamman lukutan daya samu
a asibiti yana jinyarta.Ya kan rink'a ganin kamar
wata sabuwar rayuwar soyayya ce suka yi a
tsakanin su, wacce yake mafarkin ci gaba da irin
ta.

Malam Balarabe kuwa kalaman godiya sun kare a
bakin sa.

Washe gari daya tafi Kaduna, ba tare da sanin
kowa ba, don nuna girmamawa ga Alh. Basheer.
Tabbas ya nuna halin girman, dole a jinjina masa.
Haka shi ma Alhjn ya roke shi akan ya daina
fushi da Naseer, tunda ya tuba, to ya kamata ya
karbi tuban sa, sbd fushin sa tamkar dafi ne a
gare shi.

Malam Balarabe ya amince, yayi farin ciki ya
kuma zubda kwallan bakin cikin rabuwar auran
Naseer da Nusaiba.

Ba 6angaran su Malam Balarabe kadai bakin cikin
rabuwan auran ya dama ba, ita kan ta uwar
gayyar, yau ta tsinci kanta cikin wani yanayin da
bata gane masa ba, a tun lokacin da sako ya zo
mata ta waya daga Nijeriya cewar ta fara iddar
ta.

Zaune take dirshan bisa gado, ta takure kanta,
tunanin yayi mata yawa.

Tana tambayar kan ta, ita kuma haka Allah ya
kaddaro mata? Mutuwar aure ita ce matsala ta
farko da ke ci mata tuwo a kwarya, a
rayuwarta.

Ta tsani, ace anyi aure ya mutu, sai ga shi yau ya
tabbata akan ta.

"Kaddara!

Ta fada a ranta hawaye, suka kubce.

Ta dawo tana zargin kan ta,"Watakila Naseer ya
so ya gaya mata wata magana lkcn da ta wayi
gari ta gan shi tare da ita asibitin, amma ta ki ba
shi dama.

Yi hakuri ki ba Bebinmu nono. Haba 'yar gidan
Abba."

Tabbas rarrashin ta yake yi, amma ta dauke kai,
ta nuna bata san abinda take yi ba.

Alhalin ta warke, hankalin ta ya dawo jikinta.
>
Da kenan amarya, amma, a yanzu ina mai
tabbatar miki yayanmu yayi nadama, ko bai gaya
min da bakin sa ba, ni na yi imanin yana son
ki.

Ba ki ga yadda ya fita hayyacin sa ba.

Lokacin da lalura ta kama ki, kuma ya kula dake
yadda ya kamata!

Ta toshe kunnuwanta ta daga kai.

Idanuwanta tamau a rintse, hawaye suka ci gaba
da sauka.

Istaharar ta ta tabbata gaskiya.

Bata sami isashen barci ba, sbd a yanzu take
tunanin ya kamata ace ta ba Naseer dama shi da
ita sun yi magana.

Yanayin daya suka kwana ita da Naseer, domin a
ranar suka koma Hanwa. Yayi sintiri a sashin ta
iya yadda ya ishe shi, wanda a da bai ta6a shiga
cikinsa ba. Tun Zarah na taya shi sintirin, har ta
hakura ta sakar masa. Daga ranar ya daukar wa
kan sa alkawarin zama lafiya da kowa, zuwa
k'arshen rayuwarsa.

Idan ba shi gida, yana shagon dinki ne, daya
samu Abba ya fara amsa gaisuwar sa, kuma bin
sa yake sau da kafa.

Komai bai zartarwa sai abinda ya ce. Haka yake
bin Alhj, bai ketare umurinin sa. A haka aka
share watanin 2. Mamakin sa 1 shine. Alhj ya ki
dawo da wasan Polo, shi kuma yana jin nauyin yi
masa magana.

------------------------------------------------------------------------------------------------


Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473

Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi



------------------------------------------------------------------------------------------------


A 'yan tsakanin ne. Fa'iza ta haihu da namiji
k'aton gaske mai kama da Babansa. Ranar suna,
ya rada masa Mohammad. Zarah gidan sunan ta
wuni duk da ta wayi gari baya jin dadi.

Tun daga ranar jikinta ya k'i yi mata dadi,

tsoro ya fara kamata, sbd fargaba daukan
ciki.

Lalurar ta ta fara bata tsoro.

Lalai kuwa, abinda take wa tsoron ne ya
samu.

Shi kan sa Naseer tausayi take ba shi, shi yasa
wannan karon murnar sa raggiya ce.

Zarah na tsakiyar laulayi, aka biya kudin
jarrabawar (External)

Naseer ya biya duka WAEC da NECO.

Daga nan Sageer ya shawarce shi daya fada
makarantun bada (Lesson), don ya k'ara wanke
masa kwakwalwa.

Babu musu, ya nema ya shiga guda 2, yana
zuwa.

Ranar da za'a kai Zarah daurin mahaifa, ranar ce
suke da jarabawar farko. Hankalin Naseer ba'a
kwance yake ba, babu yadda zai yi.

Haka nan ya hakura suka tafi tare da su.

Umma da Inna Sageer ya kai su a Jeep din
sa.

Shi ya tafi jarabawar sa da Civic.A saukake yayi
jarabawar sa, duk da ba shi cikin nutsuwa, babu
tambayar da ta gagare shi amsawa.

Yana tashi ya wuce asibiti abin sa, ya duba
Zaraha, sannan ya dawo shago yayi ayyukansa.
Can yake zama su ci su yi hira, zuwa karfe 9 ya
dawo gida.

Zaman sa shi kadai yana kara taso masa da
kewar Nusaiba, a lkc irin wannan can baya, duk
da ta san baya maraba da ita cikin dakin sa, ta
kan shigo har ta tambaye shi ko yana da bukatar
wani abu.

Shi yasa ya dauki filo ya nufi sashin ta cikin dakin
barcinta, ya jefa pilo bisa kafet ya kwanta.

Nan ya kasance wajen barcinsa, kodayaushe,
yana laluben inda zai ji motsinta.

Watannin 3 sakamakon jarabawarsa ta fito.

Allah da ikon sa gaba daya sakamakon Naseer
masu kyau ne.

Yayi matukar sa'a.

Allah ya kubutar da shi daga sharrin hukumar
jarabawa da yanzu abin yake neman zama
kasuwanci.

Ko ma ince ya zama din."

Magidanci na fama da kansa, duk da haka ya
dage da karma-karma ya biya zunzurutin kudi,
sai jarabawa ta fito, ace yaro bai ci ba, alhali da
kokarin sa da komai.

Sannan ya dage wajen neman taimakon
makarantun (Lesson), tunda daman makarantun
gwamnati sai a hankali.

Ba duka (Syllabus) ake (Covering) , ba, balle yaro
ya san makamar jarabawarsa.

Allah ya sawwake.

Ilimi ya zama wahala ga 'ya'yanmu talakawa.Shi
kam Naseer yayi sa'a kamar yadda Allah ya
halicce shi, shi mai sa'a ne a rayuwarsa.

Da rawar jikinsa ya kai wa Alh. Basheer takardun
ya gani.

Yayi murna kwarai, daga nan ya shiga neman
makaranta, don samun (Admission).

Sageer na taimaka masa.

Ba jimawa ba, ya sami Poly ta hannun Sageer
din, Babu kudin kirki a hannunsa a wannan 'yan
tsakanin, sbd zaman Zarah a asibiti.

Ya zauna yana tunanin yadda za'ayi.

Ba tare daya takurawa kowa ba.

Abin mamaki yana zuwa Kaduna, ya nuna wa
Alhj,("Admission) din, kamar yadda ya umurce
shi, cewar da ya samu ya kawo masa ya
gani.

Take nan ya ware dubu 50 ya ba shi, ya ce ya je
yayi hidimar makaranta.

Allah mai iko.

Tun daga ofid har ya dawo gida, godiya yake wa
Alhj cikin ransa.

Ya kawo wa Abbansa, suka sa albarka shi da
Umma, balle Zarah da take jin tausayin sa, sbd
hidimar da yake sha a asibiti, ga kuma makaranta
ta kunno kai.

Lallai Alhj ba karamin taimako yayi ma su
ba.

Ciki lafiya, ba ka lafiya, ya kama karatun sa a
(Poly Computer Science) yake karantawa, kamar
almara yake ganin abin.

Lokacin kuwa cikin Zarah ya shiga wata 7.

Zullumi ya ishi kowa, musamman ita mai dauke
da cikin.

Kusan kullun da ciwon mara take kwana.

Bata dai yin magana ne kawai.

Saboda ciwon ba wai ya tsananta ba ne.

Sati 2 da fara karatunsa, abinda ake gudun ya
faru.

Ta haifi da namiji.

Aka sanya shi a kwalba kwana 7. Ya ce ga garin
ku nan kuma shi ya ci sunan Alhaji, watau
Mohammad Basheeeeeeeeeeeeerrr­
rrrr!!!!!.......

------------------------------------------------------------------------------------------------


Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473

Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi



------------------------------------------------------------------------------------------------


Labarin haihuwar Zarah har Jordan, amma da
aka ce ya koma. Jikin Nusaiba yayi sanyi, ta dubi
Ameer yana ta rarrafen sa, yayi k'atob gasket,
dauki da nishi jajur, ga suma baka wulik! Kamar
kan Babansa.

Tausayin Antinta ya kama ta, ta yi tagumi ta ce a
ranta,"Allah sarki Antina." Ta numfasa, Ameer ya
rarrafo gun ta, ya dafa ta ya mike, ta sa hannun
ta dauke shi ta rungume.

Tabbas ta sani dole Naseer ya sa Ameer a
ransa.

Ta k'ara matse shi jikin ta, tunanin ta wai ace
Naseer ya tada k'ayar baya, dan sa yake so a ba
shi. Abinda ba zai samu ba kenan, yadda ta
shaku da Ameer.

Ai mai raba ta da shi, sai wanda ya bata shi. Ta
yi dai yi masu addu'ar Allah ya ba su mai
albarka."

------------------------------------------------------------------------------------------------


Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473

Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi



------------------------------------------------------------------------------------------------


BAYAN SHEKARA DAYA

Shekara guda da rushe(DABAI RIBERS),sauran
kolub-kolub din wasannin polo sai kawo wa
Naseer takardun gayyata suke, suna neman ya
koma kungiyoyinsu.

Gayyata har da Ghana, Kamaru, Benin Republic,
da sauran kasashen makwafta, wadanda suka
san Naseer, suka kuma san irin rawar daya taka a
wasan tsern Polo.

Amma sam ya ki amsa kiransu, duk da ya san
dumbin alkhairin da zai samu a can. Sam-sam
zuciyarsa ta fita daga wasan Polo tunda Alh.
Basheer ya bar harkar.Hakan ya gaya wa Yakubu
ranar da ya same shi da wata takarda da ta zo ta
hannun sa daga Sakkwato. Magana ta kawo
magana, suna hira tsakanin Yakubun da
Alhj.

Shi kuma yake ba shi labari.

Saboda haka Alh.Basheer ya kira Naseer yayi
masa magana. Baya ketare umurinin Alhjn,
amma wannan karon Naseer kad'a kai yai ya
ce,"Abba karatuna ya fi min wannan wasan,
kuma ban jin zan iya wasa da wani (Polo club) a
halin yanzu.

Alhj ya bi shi da kallo, tsaf ya kasa ganeme yake
nufi.

Yayi dan murmushi ya ce,"Shi kenan tunda ka
kawo zancen karatu. Allah ya bada sa'a."Ya
ce"Amin. Alh.Basheer ya dade yana nazarin
maganganun Naseer kuma yana tausaya masa,
domin ya saba da Polo.

Yana sha'awarsa, bugu da k'ari wasan Polo A
JININSA YAKE.Abinda kuwa daka saba da shi zai yi
wuya ya fice maka a rai, sai dole. Alhjn bai yanke
hukunci ba, tukuna, amma yana nan yana nazari
a kai.

------------------------------------------------------------------------------------------------


Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473

Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi



------------------------------------------------------------------------------------------------


Al'amarin Nusaiba kuwa a birnin Jordan, ba yabo,
ba fallasa a yanayin jikinta. Ta kasa samun
natsuwa a ranta, saboda yawan zancen aure da
Antin Jordan ke yi mata, tunda Ameer yayi wayau
sosai, yana gudun sa ko'ina gwanin
sha'awa.

Kullum amsar ta ita ce bata da wani bazawari
tsayayye ko a Nijeriya, balle kuma a nan Jordan
da babu wanda ta sani kasancewar ba fita take yi
ba.Idan ba (Shopping) ba tare da yaran gidan da
Direba. Ta damu kwarai domin ba ta san dalilin
da yasa Antin ta damu da yin sabon aurenna
taba. Shekara 1 kacal da mutuwar auranta.

A yammacin yau (Shopping) din za su da yaran
gidan.

Kowace ta shirya cikin dogayen kaya kala daban-
daban.

Direba ya aje su katuwar (Super market) din da
suke saba zuwa.

Please Login or Register in order to submit comment