Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

/>
Suka shige kowa, yayi na sa wuri, yana neman
abinda yake so.

Nusaiba na jaye da Ameer cikin kwandon
Shopping din ta saka shi, don kar ya rink'a bata
wahala, yana gudu, tana kamo shi.

Bata ko lura da mutumin dake tsaye 6angarn
kayan abincin yara ba, sai da ta ji yana
fad'in,"Ameer!

Haka ka yi girma?

Ta waigo da sauri ta dube shi.

Ibrahim ne ke wasa da habar Ameer.

Bai kalle ta ba, ya ci gaba da cewa,"Ka ba Husna
kewa, kullum maganar ka take."

Ameer washe baki yake yana dariya.

Ita kuwa Nusaiba jikinta rawa ya dauka, ta tsura
masa ido.

A hankali ya dago, ya dube ta yayi dan murmushi
ya ce,"Hajiya Nusaiba."

Ta yi yake, tana fadin a ranta, "Ibrahim ko maye
ne?Kafin ta ce ,"Ya ku ke? Ina su Husna da
Mamanta? Ya ce,"Lafiya lau suke.

Amma ba ki da kirki? Ta gyara fuska,"Da aka yi
me?

Shekara 1 ki na garin nan, ki kasa kawo mana
ziyara, ba ki yi alkawari ba.

Sakin ta ce min ta ba ki (Phone Number), amma
ba ki kira ba." Lambar ce ta 6ace. Ka gaida min
Husna."

Ta fadi tana tura keken (Shopping) tana ci gaba
da kiran yara,"Sumayya ina ku ke? Ku zo mu tafi!


Ya dan sauke numfashi, ya biyo ta a hankali.
>
Suka hadu da yaran a wata kwana,"Anti ba mu
gama ba,"Inji babbar cikin su Sumayyah.

Dai-dai Ibrahim na tsayuwa wajen.

Ta ce,"Gaskiya ba zan jira ku ba, gobe Direba ya
sake kawo ku." Yayi fit yasa masu baki,"Haba
Anti, bai kamata ba, ki kyale su su gama."

Duk suka bi shi da kallo.

Ya juya kan sa,"Ga Sumayyah ko? Ke fa? Ya nuna
mai bi mata, ta ce,"Khadija."

Ke fa? Ta ce,"Mahadiyya." Ya duka ya kamo 'yar
kamar ,"Ke fa? Ta ce,"Zainab." Ya runtse ido ya
ce"Wash! Uwa da magani. Sannu Husna.

Mahadiyya ta cafe,"Ba husna sunanta ba ZEE
AFLAN! Ta kai mata duka, suka kwashe mata da
dariya. Takaici ya ishi Nusaiba, ta tura keke ta yi
gaba.Ta bar shi yana rabon fada, wa ya radawa
uwa ta ZEE AFLAM? Lalai ba zai sha (Ice-cream)
ba yau."Mahadiyya ta ce,"Ba ni bace. Anti
Sumayyah ce."

Ya kada kai,"Ba ki kyauta ba.

To ku tsaya in tambaye ku, yaushe Anti Nusaiba
ta zo nan? Sumayya ta ce,"Ta dade, tun Ameer
na jariri." Baban Ameer yana nan garin ne? Ta
ce,"A'a yana Nijeriya." Wai ko ba za ku zo mu tafi
ba ne?

Yau na ga yara.

Nusaiba ta leko tana kiran su.

Sumayya ta wuce da saurarinta. Khadija ta biyo
bayanta. Ya kamo hannayen su. Zainab tana
tambayar sa,"Kai ya sunan ka? Ya dube ta ya
ce,"Suna na mai son Anti."

Suka kwashe da dariya,"Wannan suna, ban ta6a
jin irin sa ba."

Inji Mahadiyya,"Ya ce,"Ga shi yau kin ji. Ko a gida
aka tambaye ki, ki ce mai son Anti, sunana."
>
Ta ce,"To."

Ya debo kwalayen cakulet 2 da biskit 2, ya mika
ma su. Suka yi godiya.

Wajen biyan kudi, suka same su, duk cin
maganin Nusaiba sai da Ibrahim ya biya
kudin.

Suka shiga mota, yana tsaye yana tunanin ta
yaya zai binciko gaskiyar lamarin? Sun bada baya
kadan, ya manta bai ma tambayi inda gidan su
yake ba.

Ya zabura da sauri, ya fada motar shi, ya bi
bayan su.

A haka a hankali yake bin su.

Nusaiba na jin Mahadiyya na tambayar su,"Kun
san sunan mutumin nan? "Wai mai son
Anti."

Gabanta ya fadi, ta zaro ido.

Sumayya ta ce,"Ah lallai ma wannan.

Antin Nusaiba, wai kin san shi ne? Ta ce,"Ina fa
na shan shi, ku da ganin mutum kun tsaya ku na
surutu da shi." Ta ce,"Anti ba ki san shi ba, shine
ya san sunan ki da na Ameer? Ta ce,"To saura in
ji maganar a bakin Anti, sai na murje bakin
yarinya." Sumayayya ta kwa6e fuska, ta dubi 'yan
uwanta, suka kama dariya,

suna toshe baki.A haka suka iso gida, yana biye
da su. Yana kallo suka shiga get, yana kallo duk
suka wuce cikin gida.

Farin cikin ya kama shi, domin ya san mai
gidan.

Injiniya Ahmad Kaita.

Abokin ogan sa ne a ofis, kuma yana aiki da
(Internet Global Services Jordan) ne."

Suna da manya rassa a Potugal, Iraq, Swedan,.
Hedikwatarsu na birnin New-York. Hamdala yayi,
sannan yayi ribas ya koma, farin cikin zuciyar sa
ya dawo sabo ful!

Washe gari karfe 9, yana (Internet Globar
Services). Ofishin Injinya Ahamd Kaita.

------------------------------------------------------------------------------------------------


Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473

Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi



------------------------------------------------------------------------------------------------
a

Bai sha wahalar ganin sa ba, saboda dama sun
saba gaisawa idan ya zo wajen ogan sa.

Bayan sun gaisa, yayi masa bayanin abinda ke
tafe da shi. Nan take dadi ya kama Injiniya,
domin ya san Ibrahim mutumin kirki ne, ogansa
ma na yabon sa.

Nan take yayi maraba da shi, ya kuma ba shi
kati, ya ce idan ya zo ya kira wannan
lambar.

Yayi godiya, ya fito.

Ofishinsu ya wuce yana mai murna da farin ciki,
babu abinda yake hangowa, sai an daura auran
sa da Nusaiba.

Wai! Yaya zai ji ranat? Yayi sauri ya dafe kirji,
dadi zai kashe shi.

Injiniya na koma wa gidan kan sa ya kira
Nusaiba, ya gaya mata anjima za ta yi bako,
kuma yana rokon ta, don Allah ta ba shi hadin
kai, domin mutumin kirki ne.

Ta amsa da to.

Ta koma dakin ta, ta yi iya tunanin ta, amma ta
kasa gano mai neman dama mata lissafi. Su
Sumayya da sun rantse sun maya ba su gayaea
Ibrahim gidan su ba, balle ya san mai gidan.
>
To ko hadin Injiniya ne? Ta tambayi kan ta. Ta
runtse ido takaicin duniya ya isheta.Dan ta
karami, an dame ta da maganar aure.

Ita kuma ba shine a gaban ta ba, tana son
isashen lokaci, don kula da dan ta.

Ta sallaci isha'i. Bayan cin abinci.

Wankan ma ta ki yi, balle ta gyara jikinta.

Yadda take tun safe, haka take zaune tana tana
jiran ta ga dan rigimar dake neman auranta.
>
Bata gama tunanin ta ba.

Zainab ta zo da gudu ta gaya mata sako, inji
Abbanta.

Ta kura wa Ameer ido dake barci, sannan ta
wuce ta fito.

Zuwa karamin falo, inda aka ce bakon yake.

Kai,"Inna-lillahi"Wa-Inna-ilahir-raji'un!

Haka ta fada lkcn da ta yi ido 4 da Ibrahim.
>
Ya ce,"Dole ki yi salati, kin ga mayaeb zai cinye
ki."

Ta ce,"Saboda Allah menene na bn diddigi? Ya
girgiza kai,"Ba ki ma sani ba?

Lallai yau ne na gane cewa da hadin bakin ki
Abba ya hana ni auran ki."

Ta dan yamutsa fuska,"Allah ne,Abba bai isa ya
hana ka ba."

Kin di ni baki Nusaiba, kuma hakan yana k'ara
min son ki.

Wannan karon da alamun nasara, ki dubi tsawon
tazarar dake tsakanin Najeriya da Jordan, amma
Allah ya ce je ki Nusaiba mijin ki na can." Ta yi
dan murmushi, ta rasa me za ta ce da shi."

Ba karamin dadi murmushi ta yasa shi ba.

Ya dan langwabar da kai, ya sake fadin,"Kamar
an fama min gyambo Nusaiba, tun ranar da na
sake ganin ki tare da Sakina, kodayaushe sai mun
yi hirar Ameer ni da Husna, shi yasa har yanzu
bata mance da shi ba.

Da gangan ki ka batar da lambar da Sakina ta ba
ki, saboda ba kya son in san komai game da ke?


Ta ce,"Tabbas haka ne, na kuma kar6i lambar ta
ne kafin in san ko ita wace ce, da na zo na sani,
sai na kiyayi kai na, saboda tunanin me zai je ya
dawo?

Ya jinjina kai,"Kin yi gaskiya, amma da yake
Ibrahim mai sa'a ne sai ga shi abinda ya je, ya
dawo din.

Ko ba haka ba? Saura a ban dama, ayi ta ta
kare"

Ta ce,"Yaro na karami ne, ban ko yaye shi ba, da
dai............

Ya katse ta,"Ki na nufin Ameer? Je ki ji yadda yayi
suna a gida na, balle kuma ki kawo min shi, gaba
daya zai zama da na.Ta ce,"Ban tsara masa
hakan ba."

Ko?

Ta ce,"Tabbas."

Yayi dan shiru, kafin ya ce,"Ba kya so na dai ke
nan."

Ta ce,"Ban fad'a ba."

Ya ce,"Idan ba haka ba,"Ameer ne kawai zai
hana ki k'i aure na? Ta nisa kafin ta ce,"Har da
matarka, domin na lura Sakina na son ka da
yawa, bai kamata in shiga tsakanin ku ba.

Mun yi hira sosai da ita a jirgi, amma ka na
zuwa, ka nuna mata ka sanni, shi ke nan ta
sauya min fuska.

Ka ji dalilin yaga lambar da ta bani, don ba na
son tashin hankali."

Hankalinsa ya tashi kwarai, ya ce,"Ba ki fahimce
ta ba ne Nusaiba.......

Ta ce,"Haka ne Wallahi, ai ka ga lokacin ba ta ma
san halin da na ke ciki ba.

Ta ganni da Bebi, ba ita ba, kai kan ka ka yi
zaton ina gidan mijina.

Quite O.K a lokacin ba mu rabu ba, sai daga
baya.

To ina ga ace ga shi za ka aure ni?

"Babu abinda zai faru. Haka Sakina take, bata iya
rufe kishin ta, amma bata da fada, idan ku ka
fahime juna za ki gane tana da hakuri."

Ta ce,"Na ji."

In turo kenan?

"Ai na gaya maka ba yanzu na shirya yin aure
ba."

Ya runtse ido, dafe da goshi ya ce,"Nusaiba ba
kya so na.

Please!

Ki je ki yi shawara, abinda ki ke fadi ba hujja
bace."

Ya bata tausayi kwarai, amma gaskiya ba za ta
iya aure yanzu ba, shi yasa haka suka tashi hirar
babu fahimtar juna, kowannan su ya koma cike
da tunani.Musamman Ibrahim da yake ganin
Nusaiba na son ta yi wasa da rayuwarsa, bayan
ya lashi takobin wannan karon, sai ya ga abinda
zai ture wa buzu nadi."

------------------------------------------------------------------------------------------------


Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473

Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi



------------------------------------------------------------------------------------------------


Abubuwa da dama suke damun Nusaiba, ta kan
ji kamar ta tsero ta bar k'asar, domin Injiniya da
Antina sun tasa ta gaba, akan zancan Ibrahim,
kamar yadda shi kan sa ya addabe ta da
zuwa.

A hak'ik'anin gaskiya tana tunanin Istaharar ta,
kuma tana aji a jikin ta akwai maganar da Naseer
yake son gaya mata, dama ce kai bata ba shi
ba.

A wannan gwagwarmayar suka shafe shekarar
har ta yaye Ameer, yana neman wata 6 da
yaye.

Ibrahim bai hakura ba, ita kuma bata sakar masa
ba.

Anti kam har ta yi fushi ta daina yi mata
magana, kamar yadda Injiniya ya sa ido, abinda
ya sa a ransa shine wata kila Ibrahim din ne bata
so.

Shi kuwa Ibrahim har su Husna ya kwaso ya
kawo mata tabbacin cewa Sakina ta sani
kenan.

Wannan bai dami Nusaiba ba, domin bata san
irin bala in da ya sha a gida ba, akan hakan.
>
Ta fara riga ta ga duniya, babu wata yaudar da
Da namiji zai nuna mata.

Idan gaskiya ne, ya ce zai kai ta gun Sakinar
mana?

Bai ta6a gigi ba, sai dai ya kwaso mata su
Husna.

Kwatsam! Sai ga Alh. Basheer a Jordan, ba zato
ba tsammani. Kai murna a wajen Nusaiba, kamar
ta zuba ruka k'asa ta sha.Tana kewar sa sosai,
tunda ya zo take like da shi.

Shi kuwa Ameer ke zuciyar sa, ji yake kamar in
zai koma ya wuce da shi, ya zauna gidan sa.
>
Yaron yayi saurin girma kamar ba dan shekara 2
da watanni ba.

Suna zaune dare ya fara yi ga Injiniya ga
Antinta.

"Alhaji ya tambaya,"Wai 'yar gidan ta ku bata
fidda wani ba? Jin haka yasa Nusaiba ta tashi ta
bar falon.

Injiniya ya ce,"Ai mu Nusaiba ba mu san inda ta
dosa ba."

Kamar yaya?

Ya ce,"Wani yaro ke son ta kamar zai yi
hauka,

amma ba ka ga yadda take wahalar da shi
ba.

Ni Wallahi tausayi yake ba ni.

Yana da mata da 'ya'ya'yen sa 3.

Ibrahim sunansa, yana aiki da (Nijeriyan Embasy)
, yaro mai hankali, amma ta ki ba shi goyon
baya."

Ya ce,"Ibrahim?

Ni kuwa kamar na san sunan nan?

Anya kuwa ba yaron nan ba ne daya so auran ta
da?

Fatima ta ce,"Oho,"Nusaiba wani bayani za ta
zauna ta yi.

Yarinya da ka fara magana, sai kuka.

Ni dai yara suke gaya min wai a (Super market)
suka hadu, amma sun ga kamar dama can ya
san ta.

Ya ce,"Lalai Ibrahim din da na ke magana
ne.

Kuma da akwai alamun tana son sa, ni ne na
cusa mata Zancen Naseer.

To me yasa yanzu ba za ta aure shi ba?

------------------------------------------------------------------------------------------------


Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473

Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi



----------------------------------------------------------------------------------------------



Zaharaddeen shomar
Whatsapp 08168575100




Ajinisa Yake3-05
Posted by ANaM Dorayi on 11:43 AM, 25-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______
Ta ce,"Ba zai wuce wannan yaron da ta
kwallafawa rai ba.
Ta shaku da Ameer ko alama bata son a raba su.
Ameer kuwa dole ya koma gidan ubansa, sanin
kan ta ne ba zai kyale mata shi ba.
Alh. Basheer yayi shiru, Injiniya ke fadin,"Nusaiba
manya,
abubuwanta dariya suke ban, na ga yadda za'ayi
wannan al'amari."
Alh. Ya ce,"Ku kyale ta, zan yi maganin
abin."Suka saki wannan shafin, suka kama wani,
dare yayi Alhj ya tafi masaukin sa.
Yana tunani tare ba tare da yayi wa Nusaiba
maganar Ibrham ba.
Koda dama bisa hanya yake, harkokinsa ne, suka
kawo shi, hanya ta ratso da shi nan.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Yana zaune cikin ofis a gida Nijeriya, misalin 11
rana.
Naseer yayi sallama ya shigo.
Ya amsa,"Lafiya lau.
Ya jikin na Zarah?
Ya ce,"An gode Allah.
Wannan karon dai Likita ya ce dole ta huta daga
wannan, saboda mahaifar ta ta yi rauni da
yawa.
Ya dan kada kai,"Ayya, gaskiya ya kamata ta
huta, saboda lafiyar ta, ayi hakuri da abinda
Allah ya kaddaro."
Ya ce,"Haka ne.
Dama tun jiya na zo in nuna maka Result.
Ya fito na kammala Diploma." Ya washe
baki,"Ah!
Lallai abin ba wuya a wurin Allah."
Yasa hannu ya kar6i takardu, ya duba,"Kai!
First class!
Gaskiya takardun sun yi kyau.
Yana 'yar dariya ya shafi keya, ya ce,"Sun ba ni
(Adimission ABU), Direct.
Next month za'a fara Rigistireshon.
Alhj ya miko masa hannu,"Congrat! Kai na ji
dadi., Allah ya bada sa'a."
Amin."
Ya fadi bakin sa ya ki rufuwa, ganin yadda Alhj
ke murna.
Ya mike yana fadin,"Zan koma Abba, na gaishe
ka."
Ya ce,"To na gode.
Zan tura ma da sako(Acconut) din ka, ba yawa,
sai ayi Rijistireshon ko?
Ya tsugunna yayi godiya.Alhjn ya jawo dirowa,
ya dauko farar ambulan ya mika masa,"Wannan
ma sakon ka ne."
Cikin mamaki yasa hannu ya kar6a ya kara
godiya ya fice.
Yana shiga mota da rawar jiki, ya buda
ambulan, don ganin me ke cikin su? Wasu
zaradan hotunan Ameer, ya rinka zarowa daya
bayan daya guda 24 kala-kala. Wasu tun yana
dan wata 4 a zaune, wasu yana rarrafe, da
yawa a tsaye yake.
Ya zura wa hotuna ido, kamar ya sume, saboda
doki da farin ciki.
Ya sumbata, ya rungume ya ma rasa inda zai
aje su.
Take nan ya kira wayar Zarah,"Kin ga yadda
Ameer dina yayi girma?
Ta ce,"A ina ka gan shi?
Hotunansa Abba ya zo min da shu, sai kin ga
yaron Zarah, kamar dan larabawa."
Ta ce,"Ka na ta sa min rai, yayana ka kawo min
in gani mana."
Ya ce,"Ki jira, yanzu zan baro Kaduna."
Ta ce,"Allah ya tsare."
Ya ce,"Amin.
Ya kashe waya.
Ya bi hoton hannun sa da kallo, can ya sauke
numfashi, ya sake sumbatar sa, sannan yayi wa
mota key, ya ya wuce.
Yana isa Zariya. Su Umma ya fara kai wa
hotuna suka gani.
Umma ta dauki daya.
Ya kai wa Inna ita ma ta za6i na ta.
Daga nan ya cilla Shika ya kai wa Zarah.
Wai ta ga hotuna kamar ta dauko Ameer yayi
motsi a gaban su.
Nan ya bar mata 2.
Fitowar sa asibiti a hanya ya shiga shagon sai da
(Gift) da (Frem) na sa Hotuna ya siyo kanana
guda 24.
Gaba daya hotunan sai da ya sa su cikin frem
har da na wajen su Umma da Inna.
Sageer an ba shi.
Yakubu ma, ya samu har da dakin Hajiyar
sa.Naseer B ma ya ce yana so a ba shi. Naseer
kamar zai hauka ce, saboda son Ameer. Bayan
kwana 2 daya koma Kaduna. Haka ya ga hoton
bisa tebur din Alhj gaba dayan firem din mai
kyan gaske.
Ba k'aramin dadi ya ji ba.
Shi yasa ya k'ara kaimi wajen addu'ar sa.
Allah ya dai-daita auran sa da Nusaibansa.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sati 3 tsakani, cikin Zarah ya k'i zama, wannan
karon ko wata 7 bai kai ba, watan sa 6. Dole aka
bi shawarar Likitan nan take aka juya mata
mahaifa, don ta huta da wahala, domin ba
k'aramar wuya take ci ba kafin ta haihu, ban da
jinin da take zubdawa.
Yaya za ta yi?
Haka Allah ya kaddaro.
Ubangiji yasa kaffara ce. Bayan ta gagije, lafiya
ta zauna mata sai Naseer ya neman mata F.C.E.
Ta samu a saukake, shi ya gama mata komai ta
fara karatu.
English/Islamic.
Asabar da lahadi ya fita da ita koyon mota, tun
tana tsoro har ta kware.
Cikin sati na 3, ita ke kai kan ta makaranta. Shi
ke nan ya sakar mata (Honda Civic) din sa.
Shi yana amfani da Jeep kawai.
Kasancewar Sageer zai tafi sabis din sa bana, sai
shagon dinkin sa yayi rauni. Ba sosai yake zama
ba, su Abbas ne kula masa da shi.
Idan ya taso makaranta yake zama ko ranakun
da babu karatu.
Kusan ace hankalin Naseer kwance yake, amma
Allah kadai yasan abinda ke damunsa a
dangane da son dawowa da Nusaiba gidan
sa.Ba shi da bakin magana ne kawai, ko kuma
mu ce babu wanda zai kai wa kukan sa balle a
share masa hawaye. Shi yasa wani lokacin za ka
gan shi a rame, wani lokacin kuma babu laifi.
Bayan wata 2 da dawowar Alh. Basheer Jordan
yana ta binciken halin da Nusaiba suke ciki da
Ibrahim.
Babu wani sauyi, kodayaushe nuna masa take
ba za ta aure shi ba, shine dai ya k'i hak'ura.
Jin haka yasa Alh.Basheer ya ce maza-maza ta
dawo gida Nijeriya ta yi aure anan.
Ta shiga shirin kaya, cikin bak'in ciki da 6acin rai
har ta rink'a jin kamar ta cewa Ibrahim ya fito,
don ta san tabbas Ibrahim na tsananin sonta.
Amma da ta tuna abinda Sakina ta yi mata a
filin jirgi, sai ta yi turus!
A tunanin ta da kyar Sakina za ta bar ta sakewa
gidan Ibrahim.
Saboda haka ta watsar da maganar Ibrahim, ta
ci gaba da shirinta ko gaya masa bata yi ba.
Ana gobe za ta dawo.
Alh. Basheer ya kira Naseer ya same shi a ofis.
Yana zaune, yayi shiru yana jiran ya ji dalilin
kiransa.
Alhj ya dan gyara fuska ya ce,"Gobe Nusaiba za
ta dawo maka da Ameer, saboda ta sami miji za
ta yi aure.
Shine nace zan gaya maka, idan sun iso, ka zo
ka kar6i abin ka, ka sa shi makaranta, tunda da
bakin sa.
K'iris ya rage ba'a zare ran Naseer ba, daga
inda yake zaune, domin ilahirin kwakwalwarsa
sa ta daina aiki.Yayi zugudun, kai sunkuye, bai
motsa ba, balle ya ce wani abu.
Alh. Basheer ya zura masa ido, jim kafin ya sake
fadin.
"Ka na iya tafiya, dama shi kenan sak'on, da
zarar sun iso, zan kira ka a waya."
Ya dago ya dube shi, ido cike da kwalla, sun
kada jajur, bakin sa dauke da magana, sai dai
ya kasa furtawa, sai ya ce to kawai.
Da kyar ya mike ya nufi kofa.
Alhj ya bi shi da kallo.
Goge hawaye yake da bayan hannu.
Yasa kofa zai buda. Alhajin ya kira shi.
Ya waigo a gigice, yana amsawa.
Yayi jim kafin ya ce,"Don Allah ka gaida min
Malama Balarabe da kyau."
Ya hadiye miyau, ya ce,"Zai ji Insha-Allahu."
Ya buda, kofa ya fice.
Ya shigo gida karfe 7 na magariba.
Kwanciya yayi a dakin sa ya rasa abinda ke
masa dadi a duniya.
Zarah ta yi tambayar duniya, ya kyale ta.
Ta yi mita har ta gaji, bata samu wata amsa ba,
duk ranta yayi mata k'unci.
Cikin dare ta farka, ba shi cikin dakin."
Ta fito ta biyo shi, yana falo zaune cikin duhu,
sai da ta kunna fitila sannan ta gan shi.
Ta matsa gaban sa ta ce,"Ikon Allah, watau
yayana she akwai wani lokaci da zai zo, wanda
ba dole ba ne in san me ke damunka? Gaskiya
ne..............
Ya katse ta,"Zarah ba wata magana bace. Ameer
ne za'a dawo min da shi. Nusaiba za ta yi
aure."
Ta numfasa ta koma dirshan ta zauna kafin ta
ce,"Amma yaya ka na da abin mamaki.
Nusaiba za ta yi aure, ba dole ta dawo maka da
danka ba?
Menene abin damuwa a nan? Yayi mata wani
mugun kallon da bai ta6a yi mata irin sa ba, ya
ce
"Babu!
Rok'ona gun ki shi ne ki koma ki sha barcin ki.
Please and Please!Ta bi shi da kallo, bata ma
san me ke bata mamaki ba.
Ta buda baki za ta yi magana, ya kwarara mata
tsawa,"Ki tashi na ce ko? Ban son jin komai
nace!
Idanuwanta suka cika da hawaye, ta tashi da
gudu ta nufi.
Sashin ta kuka kala-kala ta rink'a yi, kamar
yadda tunanin ta yake kala-kala. Lallai son
Nusaiba ya zauna masa, ko kuwa don yana
ganin ita bata aje masa da ba ne, shi yasa ya
fara yi mata kwakwazo?
To ai daga Allah ne, kuma bata bakin cikin
soyayyar sa da Nusaiba.
Me yasa zai juya mata baya yau? Kafin safiya,
idanuwanta sun kunbura.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Naseer na kallon ta, tana shirin tafiya
makaranta. Ransa ya k'ara 6aci. Tana ta wanke-
wanke a kicin ya biyo ta, bayan ta ya rungume,
ya sumbace ta, ya rada mata,"I'm sorry.
Jini na ne ya hau, kar ki yi fushi da ni sweet
Zarah."
Ta runtse ido, hawaye suka zubo, ya juyo ta ya
share su."
Ya isa haka, ai ya wuce ko? La66anta na rawa
ta ce,"Yayana ba na bakin ciki. Ko ka fara son
Nusaiba, kuma ina maku murna idan da za'a ce
gidan nan za ta dawo.
Amma menene na yi min ihu saboda na fadi
gaskiya? Saboda ban aje maka da ba ko?
Nan da nan idanuwan sa suka kada,"Kin san
abinda ki ke fadi kuwa Zarah? Kin maida ni jahili
kenan, ban san Allah ba? Ya juya mata baya,
ban ta6a zaton wannan maganar ba daga gare
ki Zarah."Take nan ta amsa laifinta, sai dai ka
fin ta mik'a hannu, ta kamo na sa, yayi waje ya
bar kicin din. Tana kokarin biyo shi, ta ji tashin
motar sa. Tana fitowa wajen Mai gadi na rufe
get, ya riga ya fice.
Ta koma falo ta zauna, tana mai nadamar
furucin ta.
Daga ita har Naseer babu wanda ya fahimci
karatun ranar. Shi kam Naseer caji 2 ke kan sa,
shi yasa ya kashe wayayinsa, baya son magana
da kowa.
Bai dawo gida ba sai bayan issha, yana shigowa
falo, ya ji ta a jikinsa, kiris ya rage ta kada shi.
Mafarin daya rike ta sosai kenan.
Ta ce,"Yayana na tuba. Allah na tuba ba zan
sake ba."
Yayi ajiyar zuciya mai karfi, ya kamo hannunta,
suka zauna.
Ya dube ta ya ce,"Magana makamanciyar
wannan kar ki sake min ita, idan ki na son farin
ciki na a duniya."
Ta kama kunuwanta 2, ta ce,"Ba zan sake ba
yayana."
Ya jawo kafadar ta, ta kwanto masa,"Ya wuce,
shi kenan."
Ta ce,"To yaya su Nusaiba, sun iso?
Ya ce,"Ni wayoyina ma kulle suke tun safe, ba
na son ya kira ni, so ban san halin da suke ciki
ba."
Ta ce,"Hakuri za ka yi yayana, su gani suke har
yanzu ba ka son ta ne."
Yayi shiru ya rasa me zai ce?
Ta dan dube shi.
"Zo mu ci abinci ko?
Ya ja hancin ta, ya ce,"Sure."
Suka tashi suka nufi tebur don cin abinci."A dai-
dai wannan lokaci Alh.Basheer da Nusaiba tare
da Ameer suka shigo gida.
Alhj ya dauko su daga filin jirgi.
Ummi ta tar6e su, murna kamar su lashe juna.
Duk da Ameer bai santa ba, ya saki jikinsa da
ita sosai.
Da yake shi ba mai bakunta ba ne.
Bayan sun ci abinci, an yi masa wanka yai barci,
ita ma ta kintsa, ta tafi kiran Abbanta, yana
falonsa kwance labarai yake kallo.
------------------------------------------------------------------------------------------------
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi
------------------------------------------------------------------------------------------------
Tana shigowa ya tashi zaune yana fadin,"Zo nan
'yar albarka."
Tana murmushi ta zo gun sa ta zauna.
Ya ce,"Yauwa.
Magana za mu yi.
Kin tuna alkawarin da ki kai min a asibiti?
Ta dube shi,"Wane alkawari Abba?
Ya ce,"Lokacin da rigamar auran ki da Naseer ta
taso.
Ina ganin laifina ne, amma ki ka ce a'a, kuma
ko nan gaba na sake za6a miki wani mijin, za ki
aure shi.
Kin tuna?
Ta kada kai, ta ce,"Na tuna Abba."
To za ki iya ciki min shi?
Ta dan yi shiru, kafin ta ce,"Zan cika Abba na,
umurnin ka kawai na ke jira."
Ya rungumo kafadar ta ya ce,"Allah yayi miki
albarka.
Kafin nan na riga na gaya wa Naseer za ki dawo
masa da Ameer.
So kafin ya zo, ki tsaya ki duba wannan
takardar, wasika ce daga mijin da na sami miki."
Ina fatan za ki aje hankalin ki waje daya."
Ya sa hannu kasan filon kujera ya dauko
amblun, ya mika mata ta amsa jiki ba kwari.
Tashi ki je ki karanta, ki yi nazari akai, kafin
Allah ya kai mu gobe inji ta bakin ki."
Ta mike ta wuce babu wani ishashen kuzari a
jikinta.
Ameer ta tsurawa ido, ta fashe da kuka.
Shi ke nan za'a raba ta da shi.
Rayuwa kenan, abinda ya kamata ita da
Babansa su ba shi tarbiyar da ta tace
Hakan ba zai samu ba ko? Ta tambayi kanta,
gocewa ta sake yi da kuka.
Can wata zuciya ta ce,"Ba ga Antin ki ba? Ai za
ta iya rike miki shi tsakani da Allah. Ta goge
hawaye, ta ce,"Haka ne. Na san Antina za ta
iya."
Ta ci gaba da share hawayen, tana ajiyar zuciya.
Ta dauko ambulan din dake gefe ta jujjuya ta,
sannan ta farke ta, ta warware ta fara
karantawa, "Gaisuwa irin ta addinin Islama.
Kafin na ce dake

Please Login or Register in order to submit comment