Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

juya mata baya.



Halayyar ta na baya su suka bayyana wa kowa da ke son zuwa aurenta.

Tabawa ce dai da ta gudu da wani Arne na kusan shekaru uku. Tabawa ce dai da ta kai ƙaran mahaifinta wajen Maigari, Tabawa ce dai... Tabawa ce dai...





Tun tana zaune ba ta komai, da abubuwa su ka fara kwaɓe ma ta ɗan sauran kuɗin da ta samu na gadon Malam ta fara sana'ar tuyar ƙosai. Wasa-wasa sai da Faruƙ ya shekara shida kafin ta samu miji ta yi aure. Aure ta yi amma ɗan ƙaran wahala take sha a cikinsa ko da wasa Ƙaura Mafarauci bai ɗauketa da daraja ba. Tana zaune da matan sa biyu amma duk ciki ta fi su wahala. Bayan duka da ya ke mata da har ya zame mata jiki 'yan kuɗaɗen sana'arta duk shi ya ke karɓa ya sha giya da su. Ƙarshe jari ya ƙare. Ta yi zagin ta yi faɗan duk dan ya saketa amma ya ƙi.

Ga shi shekaru bakwai tare amma ko ɓari ba ta taɓa yi ba, shiyasa ma ta kasa miƙawa Gwani Lukman ɗansa Faruƙ lokacin da ya buƙaci hakan. Duk yadda ba ta son Ubansa haka ta ɗaurawa Faruƙ tsananin so. A shekara ta tara da auren Ƙaura ya rasu. Ta yi farin ciki da mutuwar sa sosai. Tana ƙarisa takaba ta dawo gida lokacin ba wanda zai ganta ya ce zai waiwayeta saboda yadda ta tsofe ta lalace.



Bata yi niyyar sake Aure ba amma ganin Indo da Gwani Lukman suna zaune lafiya ya sa ta kasa zaman gidan nasu. Lukman shi ya gaji Malam, tun bayan rasuwan sa Makarantar Malam ba ta watse ba. Wani fili da ke gefen gidan Malam wanda tun Malam na raye ya ba shi kyauta ya samu ya fara ginawa, cikin shekaru biyu kuwa ya kammala shi da Indo su ka tare a gidan da yaransu guda biyu maza AbdulWahab da su ke kira da Malam sai Zakariyya da su ke cewa Zakari.



Cikin shekarun nan Allah ya ɗaukaka sunan Gwani Lukman Baba fiyeda ta Malam Falke. Babu wanda ke duba ƙusumbinsa sai tarin Ilimin da Allah ya bashi. Daga garuruwa daban daban ana zuwa ɗaukan karatu wajen sa. Tuni sunan sa ya koma Gwani Baba.



'Ya'yan sa Malam da Zakari kuwa sun zama abun kwatance cikin gari. Ga tarbiyya ga karatu.



Kukan Lukman kullum akan Faruƙ ne wanda Tabawa ta janye shi daga jikinsa. Tun yana yaro idan ya sa shi ya zo wajen sa karatu yake guduwa. Da ya fara masa duka sai ya dena zuwa kwata-kwata, Tabawa ta ɗaure ma sa gindi har da samun Lukman akan ya bar ma ta ɗa ba lallai ne sai ɗanta ya zama Malami kamar sa ba.



"Ba a chanjawa tuwo suna Ruma. Duk lokacin da ki ka kalli Faruƙ na san fiskata kike gani a tasa. Ki bani ɗana Allah ya taimakeni na ɗaura shi akan tarbiyya mai kyau"



Ruma ta ce ba ta san zance ba.

Lokacin da ta koma gida haka ta titsiye Faruƙ a gaba tana kallo wani abu na sukanta a zuciya.

Kallo ɗaya za ka yiwa Faruƙ ka san jinin Gwani Lukman ne. Idan ka cire ƙusumbi da bashi da shi komai na Gwani ya ɗauko, hatta da murmushi idan yai sai ka ɗauka Gwani ke yi.

Ta sani Lukman kyakyawane sosai, Ƙusumbin da ke bayansa da kuma ƙaramin jiki da Allah ya bashi shine kawai naƙasu da Allah ya mishi.



Bayan ta gama takaba da shekara ɗaya ta auri Saleh. Ganin Saleh babban mutum ne dan ya ɗara shekaru hamsin alokacin kuma shine sarkin noman Doka wani garin da ke maƙotaka da su ta yi tunanin samun lamuni a auren.

Da Faruƙ ta tare duk da kuwa alokacin yana kusan shekaru shashida a duniya ya ƙi karatun Arabi ya ki ta Boko. Ko Primary bai gama ba ya dena zuwa.



Ta ɗan samu zaman lafiya na ɗan wasu watanni kafin asalin halin Sarkin noma ya bayyana ma ta. A gidan Sarkin noma ne ta ƙwammaci tun asali da ba ta rabu da Lukman ba. Bayan munanan halinsa kuma ga uƙubar kishiyoyi. Lokacin da ta fara Sana'a tana ɗan samu abun rufawa kanta asiri ɗaya daga cikin kishoyinta ta je aka mata surkulle kasuwan ƙosai da ɗanwake da ta keyi ya lalace ga uwa uba ciwo da aka sa ma ta. Ko shekara Faruƙ bai yi da ita ba ya tafi Birni neman aiki, bai sake waiwayanta ba. Haka ta zauna cikin ƙunci ita kaɗai.



Dama tunda ta rabu da Lukman zumuncinta da 'yan uwanta ya yi rauni. Lokacin da ta koma Doka da zama da abubuwa ke mata daɗi ba wanda ta waiwaya a cikin su.





A shekara na uku da rashin Faruƙ wata rana da Adda Karime ta kawo ma ta ziyara. Ashe Allah yayiwa mahaifiyar su Iyaji rasuwa kusan wata biyar da su ka wuce ba ta sani ba. An aikawa Saleh lokacin mutuwar amma bai gaya ma ta ba.

Tabawa ta yi kuka sosai.

Lokacin da Adda Karime za ta tafi ta roƙeta da Allah akan ta faɗawa Gwani ya nemo ma ta Faruƙ tunda Karimen ta faɗa ma ta suma rabon su da Faruƙ ɗin tun bayan tarewar ta.





Addu'a sosai Gwani ya sa gaba akan Allah ya dawo ma sa da Faruƙ gida tunda Tabawan da ya ke tunanin yana wajenta ma tace ba ta san inda ya shiga ba.



Allah maji roƙon bawa a cikin wata na huɗu sai ga Faruƙ ya shigo gari. Idan ka ganshi ba za ka ce ɗan Malam kuma jikan Malami bane. Ya tara uban gashi yana sanye da wando na yayi wanda ta matse daga sama daga ƙasa kuma ta buɗe.



Cikin ikon Allah da Gwani yai ma sa maganar aure sai ya amince. Ɗan kuɗi da ya zo da shi da kuma abinda Malam ya haɗa mi shi da shi yai jari ya fara kasuwanci.



A hankali kuma Allah ya sa ma sa albarka a ciki, cikin lokaci kaɗan ya samu rumfar kan sa a kasuwa.











***





A wani madaidaicin gida kuwa wata budurwa ce ke aikin wanke-wanke. Kwanukan yawa garesu, kuma yawancin su robobi ne madaidaita hakan zai sa ka kira su da kwanukan saida abinci.



Daga yadda budurwar ta duƙa tana wanke-wanken wani yaro wanda ba zai wuce shekaru goma ba ya ɗira ma ta dundu a baya. Budurwar ta juyo a zabure tana zare ido.



"Kurma ki je inji Mama" ya faɗa yana nuna mata dai dai barandar da ɗakuna uku su ke jere reras.



Maimakon ta ɓata rai da abinda ya mata sai ta masa murmushi. Ta goge hannunta ajikin zaninta ta wuce ɗakin Mama Asabe.



Tana ɗaga labulen ɗakin sai da ƙirjin Mama Asabe ya buga saboda ta ɗauka mijinta Malam ne. Ganin Kurma ce ya sa ta ɗan sauke ajiyar zuciya.

Cinikin da su ka yi da safe da kuma na rana ta ke irgawa.



"Yawwa Kurma zo ki je ki auno min shinkafar gobe wanda ya rage ba zai kai ba"

Ta ƙarisa maganar tana miƙa mata wani dunƙulen kuɗi da ta ajiye a gefe.

Bayan da Kurma ta karɓi kuɗin a hannunta ta cigaba da yi ma ta bayani da hannu ta yadda za ta gane. Tun tana shekara huɗu aka kawo mata ita kuma cikin shekaru goma ba abinda ba ta iya ba a yaren kurame.



Yadda ta jaddada ma ta cewa a rumfar Ale Faruƙ ta ke so ta siyo ma ta shinkafar hakan ya sa ta yi saurin zuwa ta ƙarisa wanke wanken da ta ke yi dan daga gidan su zuwa rumfar Ale Faruƙ aƙalla sai ta yi tafiyar minti shabiyar zuwa ishirin.





Lokacin da za ta fita daga gidan ne ta ci karo da Malam a zaure. Ta ɗan risina ta gaida shi kafin ta wuce.



Malam Sabo Yayan Mahaifinta ne. Bayan rasuwan mahaifiyarta lokacin tana watanni bakwai da haihuwa Mahaifinta Malam Inusa bai ƙara aure ba har Allah ya ɗauki ran sa shekaru uku bayan rasuwan matar sa. A wajen Inna Talatu Zainab kurma take tun rasuwan mahaifiyarta amma bayan rasuwan Malam Inusa, Yayansa Sabo ya karɓota ya kawota wa matar sa Asabe. Da niyyar zai ɗauki nauyin marainiyya ya karɓeta amma ba wannan ne gaban sa ba irin gadon gona da gida da ƙanin sa ya bari. Ba ayi shekaru biyar ba ya cinye komai, ya siyar da gida ya siyar da gonan duka sun bi ruwa babu ko ɗaya yanzu.



'Ya'yan Mama Asabe Maza huɗu ne shiyasa ta ke moran Zainab Kurma son ranta tun tana ƙarancin shekaru.





Yau rumfar Ale Faruƙ a cike ta ke da mutane magidanta da zawarai. Benchi uku aka jera kuma duk sun cika da mutane. Yankan farce akewa Ale Faruƙ lokacin da ya ɗaga ido yaga Kurma na tahowa rumfarsa kanta a ƙasa saboda kunya.



Yana ganin yaron shagonsa Iro ya miƙe yai saurin miƙewa ya ƙariso wajen.

Da hannu ta ke nunawa Iro daron shinkafar da ke kan teburi tana nuna ma sa yatsunta biyar alamun mudu biyar zai auna ma ta. Ba yau ta fara zuwa ba shiyasa Iro ya fahimci bayanin ta. Zai fara aunawa kenan Ale Faruƙ ya dafa kafaɗan sa ya ce ya koma ya zauna zai auna ma ta.

Mudu biyar ta ke so, Iro ya faɗa kafin ya bar wajen dan ya san halin Uban gidansa indai ya ga mace to hankalinsa ya tashi kenan.



Sai da Ale Faruƙ ya auna mudu biyar zai zuba na shida Kurma ta yi saurin kai hannunta dan ta dakatar da shi aka ci sa'a hannunta ya taɓa nashi. Dama tuni kyakyawan fiskanta ya riga ya zautar da shi balle kuma yanzu da ya ji sanyin hannunta akan na shi. Ta yi saurin ɗage hannun tana yi ma sa bayani akan mudu biyar ta ke son siya.

Ya san biyar ɗin ne yana so ya ƙara ma ta mudu ɗaya ne saboda neman guri a wajenta.



" 'yan mata ai ba a hana Ihsani. Idan na kyautata miki na san Allah..."



"Maigida kurma ce fa" Muryan Iro ya katse shi.

Ale Faruƙ ya wangale baki yana kallon Iro da mamaki. Yana kallo Iro ya karɓi kuɗin hannun Kurma ya miƙa ma ta ledar da aka zuba shinkafan bai iya cewa komai ba.



Sai da Kurma ta yi nisa ya samu daman tambayar ko ita ɗin 'yar gidan waye?. Wani cikin abokansa ya ce " shege mutumina, yanzu kuma kan Kurma za ka koma kenan" yana maganan yana dariya.

Kafin a tashi a kasuwa Ale Faruƙ ya samu duk wani bayanai da ya ke so gameda Kurma.

Ya san marigayi Malam Inusa, balle uwa uba Baffanta wanda abokin karawan sa ne, yanzu haka yana bin Malam Sabo bashin kuɗi ma su yawa.



Ya so haƙura zuwa washegari kafin ya je ya samu Malam Sabon amma kuma zuciyar sa ta kasa nitsuwa, kyakykyawar fiskar Kurma ce ke ta ma sa gizau. Kusan ƙarfe tara da rabi ya nemi babban riga ya saka ya wuce gidan Malam Sabo.



Tun a daren suka gama magana. Tunda Ale Faruƙ ya ce ya yafewa Malam Sabo bashin da ya ke binsa ya fara washe baki saboda ya san ba haka kawai Ale Faruƙ zai yafe ma sa kuɗi ba sai dai idan akwai wani abu na shi da ya ke so ne. Da farko dai ya sa a ransa indai maganan Injin niƙan Asabe ne to kuwa za ayita dan ya san halin Asabe sarai. Sai kuma ya ji zancen akan 'yar wajensa ce Zainabu Kurma, indai ita ce ba shi da matsala da wannan.



*THE GOVERNOR'S WIFE*
...... MATAR GWAMNA....









*©Azizat Hamza*

wattpad Azi_zat





Bismillahir Rahmanir Rahim









Book one







10













Lokacin da Ale Faruƙ ya auri Zainab Kurma matan sa uku ne, dan bai jima da sakin ta huɗun ba. Da ganinta da auren duka-duka sati huɗu ne.



Mama Asabe har ga Allah bata so aka yi auren ba, ba kuwa saboda halin Ale Faruƙ ɗin bane na auri saki sai dan saboda ayyukan da Kurma ke mata. Duk wani ƙarfin sana'arta to Kurma ce.



Ita da Malam Sabo dai sun yi ƙarfa-ƙarfa sun mata gado da tabarma da buta daga nan kuma kowa ya tsuke Aljihun sa. Duk da kuwa irin kuɗin da Malam Sabon ya yaga a wajen Ale Faruƙ ɗin.



Inna Talatu wacce ta reneta lokacin tana yarinya da kuma wasu cikin 'yan uwan mamanta su suka haɗu suka mata sauran kayan ɗakin.







Lokacin da aka kawo Kurma gidan ɗakin Iyani aka fara kaita wacce ta ke Uwargida sannan aka wuce da ita ɗakin Fulani wacce ta ke matarsa ta biyu a gidan, matar da ta zame masa ƙarfen ƙafa ita bata haihu ba amma ta ƙi tafiya duk da kuwa rashin mutuncin da take shukawa a gidan. Sai ɗakin Halime matarsa ta uku wacce shekaransu uku kenan da aure.



Lokacin da aka kaita ɗakin Tabawa ko kallon kirki bata yi musu ba, ta ɓantari goro tana taunawa tace "Faruƙu kenan. Abin nasa yanzu ya koma kan Miskinai. Allah rufa asiri"

Inna Talatu ta harzuƙa zatayi masifa wata yayarta ta hanata. Kafin su fita kuwa Inna Talatun ta kirata da tsohuwar banza. Tabawa ta biyosu tana zagi tana tsinuwa amma babu wanda ya kulata.





Rayuwar Zainab a gidan Ale Faruƙ tamkar 'yar aiki ce a gidan iyayen gidanta. Sati ɗaya da Ale Faruƙ yai yana kwasar amarci ya dinga tattalin Zainab, shi yake siyo mata abinci daga waje: nama, bredi, ƙwai da madara sune cimarta. Baiwar Allah har ta fara sake jiki tana godewa Allah tunda rayuwar da take ciki yanzu akwai daɗi ba kamar gidan Mama Asabe ba.

Lokacin da aka fara rabon girki nan ne ta ƙwammaci kiɗa da karatu. Gidan Ale Faruƙ babban gidane wadatacce dan kowacce mata ciki da falo gareta, shima sashensa ciki da falo ne, sai ɗakuna huɗu na yara sai ɗakin mahaifiyarsa Tabawa, sannan akwai ɗakuna uku a zaure na saukan baƙi. A lokacin daya auri Zainab 'ya'yansa goma shabiyar ciki kuwa bakwai ne da iyayensu. 'Ya'yan Iyani su guda shida, maza biyu,mata huɗu sai Halime dake da 'ya ɗaya.



Da farko Fulani ce ta fara ɗaurawa Zainabu nauyin girkinta daga baya Iyani da Halime suka biyo baya. Kafin kace me gaba ɗaya ranakun girkinsu ita ke yi. Fulani kam hatta Sana'arta na shinkafa da wake da take da rana sai da ya zamo Zainabu ce ke yin komai , ita dai sai kawai idan ta gama ta zauna ta dinga siyarwa.

A hankali Yaran gidan da suka ga iyayensu na saka Zainab aiki sai suka fara taɓawa suma. Lokaci lokaci sai su bar mata wanke-wanken gidan ko kuma su jiƙa kayan wanki su ƙi wankewa saboda idan Kurma ta zo ta gani tana son amfani da baho ko bokiti dole sai dai ta wanke musu kayan tunda bata da mugun zuciyar da zata bar musu kayan a ƙasa. Ranan da ta fara zuwa ta ga sunyi haka, ɗakin yaran ta je tana musu bayani akan za tayi amfani da bahon wanki. Haka suka manna mata hauka akan basu san mi take faɗa ba, abin takaicin yawanci bahon nata ne dan Fulani da Halime basa taɓa barin nasu a waje. Ita kuwa Kurma ko bata fito da su ba yaran sukan shiga ɗakinta su ɗauka babu yadda ta iya.



Cikin zalunci da ake yiwa Zainabu ba abar Tabawa a baya ba. Itama ba ta taɓa ragawa Zainabun ba, dama duk cikin matan Ale Faruƙ babu wanda ta ɗauki mahaifiyarsa da daraja haka ma jikokinta. Kafin zuwan Zainabu gidan Tabawa ke wanki da kanta, haka ma abinci sai abinda aka zuba mata amma Zainabu Kurma bata taɓa mata rowan abinci ba haka nan wankinta da gyaran ɗaki duk ita ke yi.



Kafin shekara ɗaya Zainab ta zabge ta koɗe. Aikin da take a gidan Ale ko rabinsa bata taɓa yi ba a gidan Mama Asabe.

Ale Faruƙ ya san mi yake faruwa a gidan tunda shi ba makaho bane amma halinsa dama shine idan mace ta shigo gidansa komai ta tarar ruwanta ne, sai dai ta ƙwaci kanta daga sharrin sauran matansa amma shi ba zai tanka ba.




Akwai lokacin da Zainab tayi ɓarin cikin sati uku bata sani ba bata ma san cikine ba dan jinin al'ada ta ɗauka.

Tana zaune ne a gidan amma gaba ɗaya komai na gidan ya fita mata aka. Akwai lokutan da take tunanin gara kawai Ale Faruƙ ya saketa. Sai dai dokar sa ce baya sakin mace kafin ta cika shekara biyu. A cewarsa lokacin bai gama morar kuɗinsa ba.



A cikin shekara na biyu da auren Zainabu da Ale Faruƙ ta sake samun ciki. Cikin yazo mata da laulayi mai tsanani amma babu wanda yake tausaya mata a gidan. Ba ta son warin abinci, bata cin abinci sai ƙanzo da kunun tsamiya. Idan za ta yi girki sai dai ta sa tsumma ta rufe hancinta saboda kar ta ji ƙanshin. Ranan da ta ƙi yiwa Fulani girki ta nuna cewa sai dai tayi tunda ranan girkinta ne haka ta mata chaa har da mata kashedin indai bata yi girkin ba za ta mata duka a gidan.




Ranan da Ale Faruƙ ya dawo ɗakinta, tace masa ya gayawa matansa cewa ba zata sake yiwa kowacce girki ba. Abin mamaki sai cewa yai tunda ta riga ta fara sai dai ta cigaba da hakan har zuwa lokacin da zasu ce ta dena. Abin ya ƙona mata rai. Bata taɓa tunanin kai ƙaran Ale ko matansa ba, koda wasu cikin 'yan uwanta sun kawo mata ziyara nunawa take bata cikin matsala.



Washegari ta saka hijabi ta wuce gidan mahaifinsa.

Ɗan karatun allo da tayi kafin aurenta da shi ta iya rubuta bayaninta da rubutun ajami a takarda ta miƙawa Mama Indo matar Gwani. Mama tana karantawa sai ga hawaye ya cika mata fiska. Tana tambaya ne akan ko addini ya bayarwa namiji daman ya yi rashin adalci tsakanin matansa. Sannan idan ta ƙi yiwa matan mijinta aiki akwai zunubi awajen Allah?




Mama bata bari Gwani ya gama karatu da almajiransa ba ta aika akan ya zo akwai matsala. Koda ta bayyanawa Gwani abinda Zainab ta faɗa ransa ya ɓaci sosai. A kullum tsakaninsa da Faruƙ shawara da addu'a domin muguwar tarbiyar da Tabawa ta bashi da kuma jahilci da ke damunsa shiyasa yake tafiyar da rayuwansa bisa ra'ayin kansa. Arziƙi dai Allah ya bashi amma ni'imar ilimi da kakansa Malam Falke keda shi, da Gwani keda shi da ƙannensa Malam da Zakari keda shi ya barranta masa. Bai nemi ilimi yana ƙuruciya ba kuma har yanzu da yake da damar neman ilimi kuɗi da mata sune a gabansa.



Gwani ya fayyace mata hakkin mace akan mijinta da hakkin miji akan matarsa hakan yasa zuciyar Zainab ya ɗan yi sanyi.

Mama da kanta taje gidan ta tara matan Ale Faruƙ ta gaya musu saƙon Gwani akan duk wacce ta sake takurawa Zainab zai mugun saɓa mata. Yadda basa shakkan Tabawa haka suke tsananin shakkan Gwani.


Tabawa na zaune ƙofar ɗaki tana tauna goro ta fara faɗin "su matar Malam manya. Duk tsiyar ki dai Faruƙ ɗana ne. Idan Allah bai bashi ilimi ba ai ya bashi arziƙi" ...



Daga ranan kowacce mata ta karɓi girkinta.



Cikin Zainabu na wata bakwai Gambo wata maƙociyarsu ta fita daga takaba hakan ya sa Ale Faruƙ ya fito nemanta. Kamar kowacce mace arziƙinsa, kyaun surarsa da kuma gulmar ƙarfinsa da matan daya saka suke, shi ya kwaɗaita wa Gambo shiga gidansa, sai dai ta san mata huɗu gareshi.




Halime, Ale Faruƙ yai niyyan saka saboda ta kwana biyu a gidansa amma tunda ta masa rantsuwar duk ranan da ya saketa sai ta yanke masa gaba sai ya chanja tunani. Ba zai saki Iyani ba saboda itace uwar manyan 'ya'yansa sannan Fulani kuma ya rasa dalilin da yasa ya kasa sakinta. Kurma ce kawai zai iya saka a halin daya samu kansa sai dai kuma gaskiya bai shirya rabuwa da ita yanzu ba, har yanzu akwai ƙuruciya a tareda ita. Kuma ita kaɗaice macen da idan yace tayi abu za tayi idan yace ta bari ma zata bari.

Da dai yaga Alhaji Mato na ƙoƙarin kauda shi a wajen Gambo sai ya yanke ɗanyen shawaran sakin Zainabu.



Da sassafiya ya shiga ɗakinta ya miƙa mata takarda ya mata bayanin zata iya zama a ɗaya daga cikin ɗakunan gidan har ta haihu. Ba tayi boko ba shiyasa ko karanta hausar daya rubuta bata iya yi ba. Zuwa tayi wajen Jamilah ɗaya daga cikin yaransa wacce take da ɗan hankali tace ta rubuta mata abinda Ale ya rubuta da ajami. Jamilah ta rubuta mata kamar yadda ya rubuta da Hausa *na saki Zainabu saki ɗaya* bayan ta karanta rubuntun da Jamilar tayi a ƙasan na Ale, ajiyar zuciya ta sauke sannan ta ɗauki takardar ta koma ɗakinta ta shiga haɗa kayanta. Zuwa ƙarfe sha biyu na rana ta gama tattara kayanta ta wuce gidan Inna Talatu. Ba zata iya komawa wajen Mama Asabe ba saboda a halin da take ciki wajen da zata samu kwanciyar hankali take nema.


A wajen Inna Talatu yar mahaifiyarta ce kaɗai zata iya samun wannan.



Haka kwanaki suka dinga tafiya har wata ranan Jumma'a ranan da cikin Zainabu ya shiga wata tara da kwana biyar ta haifi kyakykyawar 'yarta.

Suna dawowa daga Asibiti da ɗanyan haihuwa haka ta ɗauki 'yarta ta wuce gidan Gwani da ita haɗe da takardar da ta rubuta ranan da Ale Faruƙ ya saketa.




Gwani na alwalar sallar la'asar Zainab ta shigo ɗauke da jaririya a hannunta.

Tana zuwa gabansa ta ɗan rusuna sannan ta miƙa masa takardar hannunta.



Gwani da hankalinsa ya tashi da ganinta haka ya karɓi takardar yana ƙwalawa Mama kira.

Lokacin daya karanta takardar hawaye ya taru a idonsa. Tausayin ɗansa Faruƙ ya fi kamashi akan na Zainabu. Mama ta fito daga ɗakinta tana tambayar Zainabu yaushe ta sauka amma Zainabu bata kulata ba.

Gwani ya ajiye takardar ya ƙarisa alwalarsa sannan yai wa Zainabu alamar ta miƙo masa jaririyar. Zainabu ta miƙa masa 'yar.

Gwani yai wa yarinyar kiran sallah a kunnenta na dama sannan yai mata iƙama a kunnenta na hagu kafin ya gama Mama ta shiga ɗakinta ta ɗauko masa dabino, dake cimar Gwani ne ba a rasawa a ɗakinta.



Huɗuba yaiwa 'yar da suna Asiya Shahidah sannan ya shiga tofa mata duka addu'o'in da Zainabu ta rubuta a takardar data kawo.



Yai addu'ar kada Allah ya sa ta ɗauko ko ɗaya daga cikin halayen mahaifinta da ta kakarta Tabawa. Yai addu'ar ta zamo mai ilimi, mai tausayi, mai imani da riƙon amana. Yai addu'ar kada ta zamo azzaluma mai tauye hakkin mutane, yai addu'ar yadda mahaifiyarta bata ji bata magana Allah ya sa ta ji ta kuma yi magana. Yai addu'ar ta zama jaruma marar tsoro wacce akoda yaushe neman gaskiya da aiwatar da gaskiya shine halinta, yai addu'ar Allah ya kareta daga sharrin Mutane, Aljanu, Dabbobi da kuma Shaiɗan la'ananne. Yai addu'ar ta zamo abin alfahari ga iyayenta dama al'ummar musulmai gaba ɗaya. Ya ƙara da cewa yana addu'ar ta samu tabarakkin mai sunanta wato Nana Asiyah.



Bayan ya gama addu'o'in sannan ya karɓi dabino a hannun matarsa ya gutsura ya tauna sannan ya sakawa Asiya a baki. Sai alokacin Zainabu ta fara murmushi.

Ita da Mama ne suka koma gidan Inna Talatu wacce ta birkice saboda rasa Zainabun da akayi a gidan...






A gidan Gwani aka yi suna dan kwana huɗu da haihuwan ya nemi Zainabun ta dawo gidansa. Kunyar Baban tsohon mijinta ya sa bata iya musawa ba. Ale Faruƙ ma dai nauyin Gwani daya ji ya sa shi kawo rago da kuɗi dan a yi suna da shi.





***





Tun kafin Asiya ta cika shekara biyu Inna Talatu ke yiwa babban ɗanta mai suna Nuhu kwaɗayin ya auri Zainabu. Matarsa ta farko ta rasu sannan Yahanasu da ya aura wacce ita ɗin 'yar dangin mahaifinsa ce sai ta kasance fitinanniyar mace.



Shekarar Asiya uku aka yi auren Malam Nuhu Principal da Zainabu Kurma. Lokacin da Ale Faruƙ ya ji labarin auren baƙinciki kamar ya kashe shi, duk cikin matan daya rabu da su babu wacce yake jin rabuwar da ciwo kamar rabuwarsa da Zainabu. Ya rabu da Halime ita kuma Gambo data shigo gidansa tama fi Fulani fitina.



Malam Nuhu Gidaɗo Malamin makaranta ne da ya kai matsayin Principal inda yanzu yake shugaban makarantar Special School Congo.

Matarsa ta farko Hassana sati biyar da haihuwa ta rasu hakan ya sa rainon ɗansa Ubaydullah ya koma wajen 'ya

Please Login or Register in order to submit comment