Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

cikin kayan duk ba wanda Asiya ta saka. Hannunta dai zoben Azurfa ne da Ubayd ya siya mata sai kuma awarwaro na Azurfa shima da Maama ta bata da jimawa.



Takalmi flat ta saka ruwan gwal sai Queen Bee ta bata wani purse ruwan gwal shima. Ba su yi amfani da ko ɗaya daga cikin kayan da Bilkisu Kachallah ta aiko musu ba.




Hajiya Umma ce da kanta ta shigo yanzu dan duba shirin na su tunda Gwamna yace mata zasu iso nan da minti uku zuwa biyar.



Asiya tayi kyau sai dai ga wanda ya gaji arziƙi zai ga kamar shigar bata dace da irin wannan taro ba.




"Hajiya kayan da aka kawo bai d..."



"Kar ki damu, Bilkisu ai da gayya ta aiko miki kaya. Kinyi kyau sosai, ni dai roƙona kar ki bata dama akan ki domin yau ranan ki ne"






Asiya tayi murmushi. Ba wai dan taji daɗin abinda Hajiya Umman ta faɗa ba sai dan kawai dama abinda tayi niyyar yi kenan. Yau zata fara haɗuwa da Bilkisu Kachallah kuma sai ta nuna mata cewa ita ɗin ba hajar Kamfen ba ce. Tana cike da ita da abinda ta fitar na cin zarafi data mata, iyayenta da kuma Ubayd. Da sannu zata bata kashinta a hannu.





***







Gwamna ne da matarsa Bilkisu zaune a bayan lemosine wanda motar Alhaji Sani Kachallah ce aka fito da ita takanas saboda tafiyarsu wajen dinner.

Gwamna bai shirya yin hidima ba bayan reception da aka yi jiya suna dawowa daga wajen ɗaurin aure. Akwai abubuwa dayawa a ƙasa da suka fi hidiman bikinsa mahimmanci. Bilkisu ta riga ta shirya komai ba tareda ta tuntuɓeshi ba, abokinsa kuma ɗanuwansa Abdullahi ya takura masa akan sai yaje dinner ɗin sannan a ƙarshe kuma Alhaji Sani ya kirashi ya faɗa masa manyan mutanen da zasu halarci dinner ɗin.



Ya sani sarai Bilkisu neman suna take da abinda ta shirya, fatansa kawai ayi taro a watse lafiya.



A dai dai sashen Alhaji Sani Kachallah motarsu ta tsaya.



"Here's the plan, zaka zo tareda ita, ni kuma zan tareku a bakin ƙofa daga nan sai mu wuce wajen zamanmu. And, ka gayawa 'yar kurma ta yi murmushi saboda hotunan da za a ɗauka"



Bai amsa mata ba sai kawai ya shiga kiran numban Hajiya Umma.

Ana buɗewa Bilkisu Kachallah mota ta fita tana murmushi ta wuce inda jerin wasu motoci ke jiranta, Saudah Kachallah na bakin wata mota tana zuba mata murmushi na jinjina.



Hajiya Umma da Queen Bee ne suka fito da Asiya daga cikin gida, dake daga ɓangaren da suke zuwa inda motar Gwamna ke jiransu akwai tazara ko ina suka wuce sai guɗa da kirari ake mata ana taka musu baya. Sanda aka kai wajen motan Gwamna mutanen da suka rako Asiya sunyi Ishirin. Wani security ya buɗewa Asiya mota Hajiya Umma ta yi kane-kane a wajen saboda masu ribibin son ganin Gwamna. Sai da ta tabbatar Asiya ta zauna da kyau kafin ta rufe ƙofar tun ma kafin security ɗin yayi.



Kallo ɗaya ta masa ta kauda kai gefe. Yana sanye da farin babbar riga. Fari na ƙarawa baƙinsa haske, yana ƙara fito da kyaunsa. A kallo ɗaya data masa wanda hankalinsa ma na kan waya sai taga ya mata kwarjini, duk wani haushinsa da take ji sai taji wani nitsuwa ya sauka mata.



Ba ta san dalilin da ya sa ta ɗago dan sake dubansa ba, sai dai rashin sa'a lokaci ɗaya suka kalli juna. Ƙirjinta ya shiga lugude musamman da zuciyarta ya ankarar da ita cewa ita ɗin matarsa ce.



"Ina fata babu ruwan zafi a purse ɗinki?" Yai maganar yana nuna purse ɗin data riƙe.





Bakinta ya kafe na wasu sakanni, ta kasa bashi amsa har sai da ya sake cewa "Abubuwa sun faru a ƙurarren lokaci Asya. Amma a hankali zaki fahimci banyi komai dan na cutar da ke ba"





Maganar da ya faɗa ya tunzurata. Tace



"Mai girma Gwamna, a sannu zaka fahimci cewa bana barin sai ta kwana"



Daga haka ba wanda ya ƙara furta komai.



Suna isa hotel ɗin da aka shirya taron kafin a buɗe ƙofa Gwamna ya kalli Asiya yace "banda rawa" kafin Asiya ta bashi amsa aka buɗe masa ƙofa.

Tana jira a buɗe sashinta ta fita sai taga Gwamna ya ɗan rankwafa ya miƙa mata hannunsa.

Ta so ta buge hannun amma ta sani idon mutane akansu yake, duk abinda za tayi dole tayi takatsantsan. Ba mamaki akwai 'yan jaridar ƙwaƙwaf da ke ankare da samun hoto mai jan hankali.



Bata sani ba ko tunaninta ne, ko kuma dai gaske ne amma taji wani shock ya ratsa ilahirin jikinta sanda tafin hannunta ya shiga cikin nashi. Ko kaɗan hannunsa babu taushi da aka sani da hannun maza. To ina zai yi taushi kullum cikin AC.

Lokacin da ta fito maimakon ya sake hannun sai ya ƙara damƙe shi da kyau, a haka suka shige cikin hotel ɗin, Securities sun saka su a tsakiya suna basu kariya.





*to yanzu dai zamu dakonci shigowar Mai girma Gwamna Alhaji Professor Saifuddeen Kachallah da Amaryar sa Hajiya Asiya Kachallah. Dan haka kowa ya tashi tsaye a nuna musu soyayya*



MC kenan da wannan magana.



Daga inda suke tsaye suna jira a buɗe ƙofa Asiya ta ja tsaki jin sunan da MC ya kirata, kwana ɗaya da ɗaura aure amma har an fara laƙa mata Asiya Kachallah.



Daga bakin hall ɗin 'yan mata da maza ne masu ji da kansu suna tsaye daura da juna kowa ɗauke da ƙaramin kwando na alfarma da aka cika da flowers.



Security biyu da suke gabansu Asiya suka juyo garesu suka sara musu sannan suka koma gefe dan basu waje.



Bismillah Asiya ta furta a bayyane hakan ya sa Gwamna ya juyo ya kalleta kan kace me an musu hoto yayi goma.

Hannunsu sarƙe cikin na juna Suka fara takawa a hankali. Waƙa na tashi yayinda 'yan mata da samarin nan ke barbaɗa musu flowers a duk inda zasu taka.



Daga inda Bilkisu Kachallah ke zaune wani abu mai tsini ta ji ya soki zuciyarta. Abu biyu ne ya zo mata lokacin da ta kalli Asiya da Saifuddeen suna takowa fiskarsu ɗauke da murmushi.

Na farko dacewa na ban mamaki da suka yi wanda tamkar an halicci Asiya dan Saifuddeen ne dama. Shi baƙi dogo, ita fara doguwa. Ita ga ushirya daya ƙara hasko da kyaunta, shi kuma dimple ɗinsa daya bawa fiskarsa kyau da kwarjini na ban mamaki. Asiya bata saka kayan data aika mata ba, hakan na nufin babu abin yaɗawa gobe kenan, asalima kayan da ta saka da kuma kwalliyar da ba ta yi ba zai ja a yabeta a kafafen yaɗa labarai.



Na biyu kalaman malamin taurari Tsu Zhang ne ya sake dawo mata. *akwai wani tauraro daya fito a gefen tauraron mijinki. Yadda tauraronki ke haskawa tareda ta mijinki, haka wannan tauraro zai dinga haskawa tareda shi har sai tauraron mijinki ya haskaka fiye da tunaninki. Idan kikayi ƙoƙarin disashe wannan tauraro babu makawa da taki tauraron data mijinki haskensu zai dinga disashewa. Ki sani taurari uku a waje ɗaya suna bada haske na ban mamaki*



Murmushin yaƙe tayi a ranta ta furta "in dai ni Bilkisu Kachallah ina raye sai na juya ƙaddararki, tauraronki ba zai taɓa haskawaba. Saifuddeen nawa ne ni kaɗai, idan na gama dake har Saifuddeen ya shige cikin ƙasa babu macen da zata sake karambanin shiga rayuwarsa"



Kamar wacce aka tsikara sai ta miƙe da sauri tana faɗaɗa murshinta kamar bakinta zai taɓa kunnenta. Tana isa gabansu Asiya ta buɗe hannu ta rungumesu duka biyu nan da nan mutane aka sa tafi, hasken camera ta ko'ina sai wawal-wawal kake gani a hall ɗin.



Lokacin da ta sake su ta kama hannun Gwamna, ɗaya hannun kuma ta sa yatsa tana ƙoƙarin taro ƙwalla.



"Ikon Allah" Asiya ta faɗa a zuciyarta.



Dukkansu uku sai da suka zauna a mazaunin da aka tanada musu sannan mutane suka zazzauna banda ɗaiɗaikun manyan mutane irinsu Alhaji Sani, Umaru Kwom da Yallaɓai da basu tashi ba tun farko.



Kujerar Gwamna ce a tsakiya, gefensa na dama ta Bilkisu, gefensa na hagu kuma Asiya. Bilkisu Kachallah ta kalmashe ƙafa sai wani bushashatul wajahi take yi kamar itace Amaryar.



MC ya shiga yabon Bilkisu na yadda ta ajiye kishi gefe ta rungumi Amaryar mijinta. MC da azarɓaɓi harda cewa Bilkisu Kachallah tana koyi ne da matan Manzon Allah wanda suke kishi da ilimi. Asiya da jin haka ta ja tsaki.



Babu wanda zai ce Amarya bata fito ba. Babu kwalliya na hauka, babu takalmi mai tsini, babu sarƙa na Gwal ko Diamond, babu babu babu. Amma duk da haka Asiya Shahidah Faruƙ Baba ta burge kowa, shigarta mai sanyi ne daya fito da sahiihin kyaunta, babu ƙyalƙyalin shirme.





Queen Bee ce ta bada tarihin Asiya yayinda Alhaji Abdullahi babban abokin Gwamna ya bada tarihin Gwamna.

Lokacin da aka zo yanka cake su duka ukun suka haɗa hannu suka yanka. Gwamna ya fara bawa Bilkisu cake ɗin a baki, zai kuma yankawa ta karɓi wuƙan ta yanka ta kai cake ɗin saitin bakin Asiya tana murmushi...





Asiya bata yi mamakin ganin 'yan adawa a wajen ba saboda dama haka siyasa ta gada. Umaru Kwom sai washe haƙora yakeyi kace bikin ɗansa ko 'yarsa ake. Haka yazo yai musabaha da Gwamna aka ɗau hoto.

Da aka fara ɗaukan hotuna har sai da Asiya ta fara jin hajijiya, sai lokacin ta ankara ma ashe tun karyawar safe bata sake saka komai a bakinta ba.



Hoto za'a ɗauka tareda 'ya'yan Gwamna, Asiya tayi baya kamar zata faɗi sai jinta tayi jikin mutum, idonta na rufe dan haka bata san ƙirjin wa ta faɗa ba.

Ba ta ma san duk abinda ke faruwa ɗaukansu kawai ake a hoto ba. Bata ma samu kanta ba sai da mutumin da take ƙirjinsa ya jata ya zaunar da ita a kujera mafi kusa da su. Ya miƙa mata ruwa a baki, ta kafa kai ta shanye ruwan tas.



Dai dai kunnenta ya furta "are you alright?"

Sai lokacin ta ankara da mutumin da take tare da shi shine mutumin data fi tsana a duniya.



Gwamna ya murza hannunta yace "kar ki damu hoton ya isa haka"



Bai ƙarisa maganar ba Bilkisu ta iso wajen ta saka hannunta a kafaɗar Asiya ta raɗa mata magana a kunne.



"What's the meaning of this, na san ba zaki so gobe a rubuta ciki gareki ba ko"



"Idan an rubuta, zan faɗa musu cewa cikin Gwamna ne"



Babu wanda ya san mi suke faɗa. Ko Gwamna da ke wajen bai ji mi suka faɗa ba. Mutanen da ke wajen sun ɗauka Asiya na yiwa Bilkisu bayanin abinda ke damunta ne.



Dinner yayi kyau kowa ya samu abun gulma idan anje gida. 'Yan jarida kuma gobe zasuyi rububin bada bayanin abubuwan da suka faru a wajen taron dinner.



Bilkisu ce ta yiwa mutane bayanin cewa Amarya na tare da gajiya dan haka za'a ƙarƙare taron da wuri.



Ƙarfe goma da kwata na dare Hajiya Umma da Hajiya Batula suka wuce da Asiya Kachallah house inda aka sa tayi wanka ta shirya cikin wani haɗaɗɗen lifaya kalar baby pink mai zanen flowers ja, fari, purple da kuma yellow.



Dake daga wajen dinner kowa gida zai wuce shiyasa babu ko ɗaya cikin 'yanuwan Asiya lokacin da aka kaita ɗakin mijinta. Hajiya Umma da Hajiya Batula kawai ta sani cikin waɗanda suka rakota amma akwai wasu matan kusan su shida da bata taɓa ganinsu ba.



Addu'a suka mata da 'yar nasiha sannan suka mata sai da safe.

Bayan kowa ya tafi Asiya ta ɗau wayarta ta turawa Umma text. Allah Sarki UWA ko minti biyu bai cika ba Umma ta turo reply tana yiwa Asiya addu'ar Allah ya bata zaman lafiya sannan ta kwantar da hankalinta ta yiwa mijinta biyayya.



Asiya na gama karanta saƙon ta fashe da kuka. Kukan taka umurnin Umma da zata yi, kukan hukuncin data yankewa kanta ta ke, wanda shi kaɗai take ganin zai kawo mata kwanciyar hankali a rayuwarta.



Bayan ta sha kuka ta ƙoshi ta kwanta akan gadon tana tunanin inama inama. Inama wannan dare tasu ce ita da Ubayd...





***





"Mutumina irin wannan soyayya haka. Ka ganka a wajen nan kuwa, kaman wani super man tamkar ƙyaftawar ido har ka tarota jikinka, ni na ɗauka ma ɗaukarta zaka yi sai na tuna akwai sauran burbuɗin kunya a tattare da kai"



Gwamna ya harareshi yace "ban san yaushe zaka girma ba" Alhaji Abdullahi ya sa dariya.



Bayan sunyi sallama da Abdullahi Gwamna ya haura sama yana takawa a hankali kamar mai tsoron wani abu a saman. Cire kayansa yai ya watsa ruwa sannan ya fito ya shirya cikin riga da wandon bacci masu tsantsi kalar navy blue.



A hankali ya sauko ƙasa ya shige sashen da aka gyarawa Asiya. Falo da ɗakuna biyu. A da wajen an ginashi ne saboda Juniour idan ya kai kaman shekaru shabiyar sai ya koma wajen amma yanzu wajen ya zama ɓangaren amaryarsa.



Saifuddeen Kachallah bai taɓa tunanin ƙara aure ba tunda ya auri Bilkisu. Bayan ya rasa Misturah bai taɓa sawa ransa zai auri mata biyu ba.

Asiya ta zo gareshi ne saboda akwai ƙaddararta a cikin rayuwarsa. Sai dai yayi alƙawarin idan har aka gama ribibin zaɓe komai ya lafa zai sawwaƙa mata ta je ta auri wanda take so, alokacin babu wanda zai yi farautar Kamfen da ita. Bai faɗawa kowa hakan ba amma shawaran daya yanke a zuciyarsa kenan, kuma ya sani hakan ne daidai...





Da sallama ya shiga ɗakin Asiya. Tana kwance a tsakiyar gado tana sheshsheƙar kuka. Tausayinta ya ji ya shigeshi. Shi mutum ne da bayaso ya takurawa kowa balle kuma mace.



Bata ankara da shigowarsa ba sai da taji ya ɗan taɓa hannunta. Ta yi saurin tashi zaune tana faɗin "lafiya?"



Lifayarta da ya saɓule ya bashi damar ganin dogon baƙin gashinta mai tsantsi.

Ya ƙurawa gashin ido yana tantamar gashinta ne ko kuma wig.



"Na ce lafiya?"



"Ahm. Na zo ne na..." lura yai da hannunta na rawa alamar ta tsorata da shi hakan ya sa shi matsawa gefe, sannan ya cigaba.



"Kin sani daga jiya matsayinki ya tashi daga Asya 'yar jarida a jihar nan. Hakan na nufin akwai nauyi a kanki. Play your part a matsayinki na Matar Gwamna ni kuma zan sawwaƙa miki a lokacin da komai ya lafa"



"Lallai kam, to barin gaya maka idan ma wani abun kake nema ba zaka samu a wajena ba. Gangar jikina, zuciyata, ruhi na duka mallakin Ya Ubayd ne"



Magananta na ƙarshe ya shigeshi fiye da zato



"Ki faɗi koma minene, hakan ba zai chanja cewa daga yau gangar jikin, zuciyar da ruhin duka Allah ya mallaka min ba"



"Babu wanda na tsana irin ka, babu wanda na ke Allah wadarai da rayuwar sa irin ka, sannan ba ni da maƙiyi a duniya da ya wuce ka Your Excellency Governor Saifuddeen Sa'ad Kachallah. Ba za ka taɓa maye gurbin Ya Ubayd ba ko mi zaka yi kuwa" Ta ƙare maganar tana huci. Ta ɗauka zai fusata, ta ɗauka zai nemeta ta ƙarfi amma sai gani tayi ya tashi ya fice daga ɗakin ba tareda ya furta komai ba.



2g Novels




Home / THE GOVERNOR'S WIFE / THE GOVERNOR'S WIFE 15
THE GOVERNOR'S WIFE 15
2g novels THE GOVERNOR'S WIFE






*THE GOVERNOR'S WIFE*
...... MATAR GWAMNA....







*©Azizat Hamza*



wattpad Azi_zat





Bismillahir Rahmanir Rahim









Book one







15





Washegari da Asiya tayi sallar Asuba komawa bacci ta yi sai ƙarfe goma aka fara buga mata ƙofa. Jiya bayan Gwamna ya fita daga ɗakin kullewa tayi dan bata yarda da shi ba.

Lokacin da ta buɗe ƙofa wata mata ta gani sanye da uniform riga da wando da ƙaramin hijabi kalar ruwan ƙasa.





"Ranki shi daɗe fatan kin tashi lafiya. Na zo tambaya ne shin abin karinki a kawo shi falonki ne ko a barshi a dinning room?"



"Ki kawo min ɗaki"





"Shikenan, barin kawo"



Bayan ta karya kiran Faty da Sumayya ta yi ta musu ban gajiyar biki. Da ta kira Queen Bee tsiya ta dinga mata wai ƙila an samu ɗan Gwamna jiya da dare. Asiya tace Allah ya sawwaƙa.

Duk da ta yiwa Ummanta text da Asuba sai da ta sake yi mata wani text ɗin tana tambayarta ko 'yan biki sun gama tafiya.




Ƙarfe shaɗaya da rabi, Uwani matar data kawo wa Asiya abinci ɗazu ta zo ta sanar da ita cewa tayi baƙi. Asiya ta zura hijabi ta fito babban falo inda baƙin ke jiranta.

Wasu mata ne guda huɗu dukkansu babu wanda ta sani a ciki. Jagorarsu ta mata bayanin ko su ɗin su waye, sannan suka faɗi abinda ya kawosu wai sun zo gaisheda Amarya.



Women leader ce ta jam'iyya da kuma shugaban ƙungiyan Mata 'yan kasuwa da Sakatarorinsu.

saura kaɗan Asiya ta ce musu ko uban mi zuwansu zai ƙara mata sai kuma ta dakatar da harshenta.


Ta musu godiya bayan sun ajiye mata kyauta, ta haɗa da cewa da basu yi wahalar kawo komai ba.



Asiya ba tayi minti shabiyar da shiga ɗaki ba aka sake zuwa kiranta wai tana da baƙi. Wannan karan su Hajiya Batula ne da wasu 'yanuwan Gwamna suka zo mata sallama dan zasu wuce garuruwansu.

Haka baƙi suka dinga zuwa mata gaisuwa har dare. Ƙarfe bakwai na yamma ta ce da Uwani duk wanda ya sake zuwa ace ya dawo gobe.

Bayan ta bada umurnin sai kuma chan ƙasan ranta ta fara tunanin tun yanzu har ta fara bada umurni, ita ɗin fa ba kowa bace.





***






"Mommy zan je gidan mu, akwai wasu kayana da na ke son ɗebowa"



"Nana duk kayan da suke nan basu isheki ba"



"Kai Mommyyy, kin san dai ba komai muka ɗauko ba da zamu dawo nan"




"Naji, je ki amma ki dawo da wuri, sannan ba ruwanki da jikar maiƙusumbi"



"Yes Mom"




Daurewa kawai take amma tun safe take neman hanyar da zata zo ta ga Asiya. Airah data kasa ta tsare ne ta hanata zuwa.



Asiya na sallah Nana ta faɗo mata ɗaki babu ko sallama. Sai da Asiya ta sallame ta juya ta ga Nana zaune a kujera tana murmushi.



Ta ganeta saboda kamannin Gwamna gareta har dimple ɗinsa.




"Lafiya za ki shigo min ɗaki babu sallama?"



"Haba Amaryarmu, nan ma fa gidanmu ne"




"Idan gidan ku ne, ai ba ɗakin ki bane. Tashi ki fita "



"Haba Anty nah" ta faɗa tana bubbuga ƙafa tana tura baki



Lallai yarinyar nan sangartacciya ce. Asiya ta faɗa a ranta.




"Anty dan na zo gaishe ki shine zaki kore ni"



"Ya sunan ki ma?"




"Nana Khadijah"



"Fita min daga ɗaki Khadija. Nagode da gaisuwa"



Nana ta miƙa mata hannu tace " please be my friend"




"Kin san Allah idan baki fita ba zan wanka miki mari"



"Ok, goodnight Sweet Anty"



Asiya ta bi bayanta da kallo tana taɓe baki...







Washegari ƙarfe tara na dare Gwamna ya shigo gida. Asiya na jin shigowarsa ta fito da sauri tabi bayansa suka haura sama tare. Da safe ya bata key ɗin mota wai kyauta daga Alhaji Sani Kachallah sannan yace duk lokacin da zata fita akwai Dreba da zai fita da ita



Zai buɗe ƙofar falonsa tace " inada magana"



Bai amsa mata ba ya kutsa kai ciki.

Sai da ya zauna ya ɗaura ƙafa ɗaya akan ɗaya sannan yace " ina ji"



"Ina so ƙanwata ta zo ta tayani zama. Sannan ina son kawo Driver nawa na kaina"



"Mi ya samu Dreban da aka baki?"



Yai maganar yana tsareta da idanu.



"Na fi son wanda zan yarda dashi ɗari bisa ɗari"



"I see. Ki submitting CV ɗinsa a duba"



" Yayana ne, Ubanmu ɗaya, akwai wani CV daya wuce wannan?"



"Ta ya zan yarda cewa wanda ki ka faɗa shi ɗin za ki kawo?"



Ta ji zafin maganansa amma ta dake tace " ka iya sawa a mana DNA test da ni da shi"



Yai murmushin gefen baki yace " abu ne mai sauƙi ai"



"Sannan abu na gaba. Bana son kuɗin jini, kuɗin talakawa. Kasan yadda za ka yi ka cire kuɗin da ka zuba a account ɗina yau da rana, bana buƙatarsu"



Miƙewa yai yace " gudummawa ce da Ahalin Kachallah suka miki, idan ba kya buƙata ki tuntuɓi Hajiya Umma ki mata bayani"



"Zan iya kawo Sumayyan? ko itama sai da DNA test"



"Zasu iya zuwa" ya furta sannan ya wuce wani hanya wanda take ganin a nan ɗakunan sashen suke.





Tana shiga ɗaki ta kira numbar Yaya Bello. Yana nan teburin mai shayi ana rikici da shi akan kuɗi ta kira.



Daga wajen da yake yana ɗaukan kira ya fara cewa "gashi nan ai ƙanwata Matar Gwamna ke kira"



"Yaya Bello"



"Hello Asiya, Hello esselenci. Esselenci kina jina"



"Ina ji Yaya, ya kuke"



"Lafiya lau muke. Ya Gwamna?"



Asiya ta katse zancen da cewa "Yaya inada aiki da zan baka, idan babu matsala"



"Wallahi zan yi"





Lokacin data faɗa masa direbanta take so ya zama wani tsalle ya daka yana ihu. Yaya Bello ya girmeta da kusan shekaru shahuɗu amma bai damu da cewa ƙanwar bayansa zai dinga tuƙawa ba.



Shine babban ɗa namiji acikin 'ya'yan Ale Faruƙ amma kuma shine marar aikin yi walaƙantacce. Shaye-shaye ya lalata masa rayuwa. Lokacinda yake yaro shekara goma shabiyu zuwa shabiyar haka, ya taɓa halin ɓera, da abin ya ishi Ale sai ya kaishi wajen Gwani. Gwani ya dinga masa addu'a yana bashi ruwan rubutu har ya zo ya rabu da abun.

Daga baya daya bi wasu abokai suka tafi chan kudu leburanci shikenan ya lalace da shaye-shaye. Baya bin mata, dan akoda yaushe addu'ar Gwani Allah ya raba shi da sata da kuma zina.



A shekarar da Gwani ya rasu a shekaran ya dawo gida. Bai dawo da komai ba saboda komai ya tafi a shan abubuwan maye.

Ale ya masa aure ya buɗe masa shago ko zai nitsu amma inaa. Kafin wata shida komai ya ƙare a shagon, ita kuwa Amarya shekara ɗaya tayi da 'yan kwanaki iyayenta suka sa ya saketa saboda tunda aka kawota ko hannunta bai taɓa riƙewa ba.

Ale ya kaishi wajen wani abokinsa mai maganin gargajiya a duba shi ko bashida lafiya ne, amma akace lafiyarsa lau.



Ƙannensa maza biyu sun yi aure harda 'ya'ya, sannan suma kasuwancinsu ya fara bunƙasa tun lokacin da Ale ya yaye su daga kasuwancinsa, amma Yaya Bello kam sai zaman daba...





***



Asiya na aiki a laptop ɗinta Sumayya ta shigo ɗakin da sallama.

"Kai Anty na gaji" ta ajiye jaka ta faɗa kan gado



"Tun yanzu? Shekara huɗu zaki yi, idan kuma aka shiga yajin aiki ƙila kiyi biyar ko shida"



"Kai! Allah ya sawwaƙa"



"Welcome to the game sister, haka muma muka yita cika bakin nan, daga ƙarshe sai da muka ƙara wata biyar akan shekaru huɗun daya kamata muyi"





"Anty kin san me, wata a ajinmu tace tana son ƙawance dani, ta nuna min hoton da mukayi a wajen dinner ashe nima na zama celebrity"



"Ban yadda ba"



"Iye?"



"Ban yadda da ƙawancen nan ba. Duk wacce za ta shiga jikinki saboda ke ƙanwar Matar Gwamna ce ba ƙawa ce da zata ɗore ba. Sannan ina so ki sani cewa matsayina na Matar Gwamna na lokaci kaɗan ne"



Sumayya tayi saurin miƙewa zaune.



"Anty dan Allah kada kice min za ki bar gidan nan. Kwana biyu dana yi a gidan nan ban taɓa gani kin shiga sashen Gwamna ba, idan ya dawo ko..."



"Bana son gulma. Kada ki bari wani matsayi ya ruɗe ki dan ba mai ɗorewa bane"





Sumayya ta riƙe baƙi tana kallon Asiya da hankalinta ke kan abinda take ta rubutawa a laptop ɗinta.



Ƙwanƙwasa ƙofar ɗakin aka yi, Sumayya ta je ta buɗe.

Da ta dawo ta miƙawa Asiya wani envelop tace Uwani ce ta kawo.



Asiya ta karɓi envelop ɗin ta yaga ta fito da wasiƙar ciki.



"Shegiyar mata wai office of the first lady, ko uban wa ya bata office oho"



"Anty minene?"



"Bilkisu Kachallah ke gayyatata taron gajiyayyu da naƙasassu da za ayi gobe Asabat a foundation ɗinta"



"Anty zaki je?"



"Idan ban je ba ai ta ci nasara a kaina"...



Tunda aka kawota bata taɓa fita ba, a ranan da ta yiwa Yaya Bello maganan zama Direbanta washegari ya niƙo garinsa ya taho.



Kiran Yaya Bello tayi a waya tace masa gobe za su fita za ta aiko Sumayya da key ɗin mota ya duba lafiyar motar.





Washegari kuwa ƙarfe shaɗaya Asiya da Sumayya suka wuce wajen taro.

Lokacin da suka je an tanada mata waje na musamman kusa da Bilkisu Kachallah. Tana zama Bilkisu tace "ƙarfe goma aka fara taro, nan gaba ki duba agogonki da kyau"



"Ohh sorry! Kin san yau Excellency zai bar gidana, dole na kimtsa shi kafin na fito. Kin san ai yana jimawa a banɗaki idan zai yi wanka, da muka shiga tare kuwa na yi ƙoƙarin na dirzashi da kyau amma dana taɓa shi sai jikinsa ya ɗau mazari..."



"Shut up!"

Please Login or Register in order to submit comment