Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tayi shigan matan aure. Asiya bata kulashi ba dan gaba ɗaya gabanta faɗuwa yakeyi, ta rasa dalilin hakan kuwa.



Koda suka isa gidan Gwamnati ƙarfe goma saura minti shabiyar. Wajen da aka ajiyesu jiyan dai nan aka sake zaunar dasu. Basufi minti goma da zuwa ba fitsari ya kama Asiya, cikin ranta sai dana sanin shayin da ta sha kafin su fito take. Ƙarshe data ga abin zai dameta ta miƙe ta tafi wajen wata mata da ke da office a corridor ɗin lobby ta tambayeta ina ne banɗaki, matar da keta tauna cingam kamar zata haɗa da harshenta tayiwa Asiya kwatance tana haɗe rai, Asiya ta wuce tana mamakin matar da fiskarta ya gama soyewa saboda bleaching.








**



"Na san ka san matsayinka a wannan Jaha. Kuma ka san baya daga cikin ayyukan ka abinda ka aikata"




"Your excellency..."



Gwamna ya ɗaga masa hannu ya cigaba "kar hakan ya ƙara faruwa Mr Lamara Damana. Matsayin Chief of Staff zai iya faɗawa hannun kowa nan gaba. Ina fata ka fahimta"




"Yes your excellency. Hakan ba zai sake faruwa ba da yardar Allah"



"Good. Now ka duba min ko kwamishinan ayyuka ya fara aikin da aka bashi"



Lokacin da COS ya fita Gwamna ya jawo takardar da ya ajiye ya kekketata sannan ya watsar. Ba zai taɓa lamunta da wannan ba. Fitar COS keda wuya Sakatare ya shigo ya sanar da Gwamna cewa 'yan jaridan jiya sun dawo.



COS na shiga office ɗinsa ya cillar da file ɗin hannunsa takardun ciki suka watse. Ya dunƙule hannunsa kamar mai shirin dambe, ya kira sunan Gwamna da ƙarfi "Saifuddeen Kachallllaaaaah!"

Yana cikin huci ya tuna da wani abu nan da nan yai saurin lalubo wayarsa a aljihu ya shiga danna kira, ba aɗauka ana farko ba sai a kira na biyu.



"Akwai matsala Kachallah" abinda ya fara furtawa kenan da kakkausar murya. Bai bari wanda yake maganar ya ƙarisa ba ya katse shi da cewa " har Gwamna zai yi iƙirarin cireni a matsayina. Ya manta ne? Ya manta ne?"




Yai shiru yana sauraron bayani daga ɗaya ɓangaren sannnan ya ɗaura da cewa

"idan har bai san yadda akayi aka ɗaura shi akan kujera ba to kuwa lallai ƙaddarar da ta hau tsohon Gwamna za ta sameshi. Ta inda aka hau tanan fa ake sauka Kachallah... eh inaji.... sai dai abu ɗaya na sani idan har Saifuddeen ya cireni a matsayina saina gayawa duniya cewa Saifuddeen Sa'ad Kachallah ne ya kashe tsohon Gwamna..."



Saura kaɗan recorder da ke hannun Asiya ta faɗo saboda firgita da tayi. Tayi saurin toshe bakinta saboda kar mutumin da take naɗan maganarsa ya jiyo nishinta. Ta fito daga banɗaki kenan za ta koma inda aka ajiyesu ta hango Chief Of Staff ya zo ya shige wani lungu a bircike. Curiosity nata na 'yar jarida ya sa ta bi bayansa. Wani office taga ya shige hakan ya sa ta bi bayansa da zimmar ko za ta iya gano dalilin fushinsa tunda hanyar da ta ga ya fito tanan ne office ɗin Gwamna, koma minene ya ɓata masa rai yanada nasaba da Gwamna ɗin.




Ihun da ta jiyo COS yayi yana kiran sunan Gwamna yasa ta laɓe ta fidda ƙaramar recorder ɗinta ta fara naɗan maganar sa.

Ganin yayi shiru yana sauraron bayanin da ake masa ya sa tayi saurin jan jiki ta bar bakin ƙofar.

Ba ta ji ƙarshen maganar sa ba.

"Eh...ina sane amma... shikenan zan kiyaye sai dai gara a nuna masa cewa mune muka buɗa masa hanya har ya samu ya hau kujeran, idan aka cigaba da ninke shi a baibai zai yi abinda zai jawo masa dana sani... to shikenan zamu haɗu idan na tashi a office"






Da ƙyar Asiya ta iya komawa wajensu CY dan a tsorace take, abinda ta jiyo ya girgizata matuƙa yayinda tsanar Gwamna Saifuddeen ya dira a zuciyarta, dama ya aka ƙare balle kuma...

Ta samu CY na faman saita camera, shi da Sunusi suna taɗi shiyasa hankalinsu bai kai gareta sun lura da chanjawar yanayinta ba.




Bayan minti biyar sai ga Gwamna ya iso fiskarsa ɗauke da annuri. Kallon tsana Asiya ta bishi da shi tana ji a ranta kamar ta shaƙeshi ya mutu kawai.

Maimakon jiya da za a naɗi shirin sannan a editting na shi kafin a ɗaura a tasharsu yau kam live za a saka shirin a gidan talibijin na su.



Yau kam ba kamar jiya ba babu tsoro ko fargaba a tattare da Asiya, cike da nitsuwa ta fara gabatar da shirin. Tambayoyin da aka amince ta masa su takeyi sai da aka kai tsakiyar shirin sannan ta sako zancen tsohon Gwamna wanda ba Gwamna kaɗai ba hatta CY sai da ya sha jinin jikinsa da tambayar




"Gwamna Saifuddeen duba da yadda mutuwar tsohon Gwamna ya zo bagtatan ko za ka iya sanar damu yadda mutuwarsa ta zo maka?" Tambayar offscript ne baya cikin jerin tambayoyin da akace za a masa shiyasa ya ɗan ji abin banbaraƙwai amma ya dake ya amsa da cewa.

"Kowanni halitta dake doron ƙasa sai ya ɗanɗani mutuwa. Dukkanmu lokaci muke jira. Haƙiƙa mutuwar tsohon Gwamna ta girgizani matuƙa saboda yadda ya zo mana lokaci guda..."



"Excellency baka ganin ya kamata a duba mutuwar tasa kodai akwai lauje cikin naɗi duba da cewa Gwamna nada 'yan adawa dayawa"




Ba dan shirin kai tsaye aka ɗaura shi ba da CY tuni ya katse ɗaukan shirin saboda yadda Asiya take chanja alaƙar shirin nasu.



Gwamna ya kalleta cikin zargi amma bai bari hakan ya bayyana a fiskarsa ba yace " Malama Asya mutuwa koda ciwo ko babu ciwo sai anyita. Likitoci sun tabbatar da cewa hawan jini ne yai ajalin tsohon Gwamna Allah ya jiƙan rai"



"Ya yanayin alaƙarka da shi kafin rasuwarsa?"




"Munyi zama na amana da shi, Allah ya gafarta masa kurarensa da ma namu gaba ɗaya"




"Amin"

"Tambayata ta gaba ko miyasa Gwamna ya zaɓi Alhaji Bala Yamai a matsayin mataimakinsa duba da cewa ana zarginsa da cin hanci da rashawa har ma shekarun baya hukumar EFCC sun kama shi?"



Kafin Gwamna ya bada amsa daga chan ma'aikatarsu aka katse shirin aka saka talle saboda a samu daman katse ɓaranɓaramar da Asiya ke yi.





"Jesus! Aseey lafiyanki kuwa?"

CY ya faɗa da ɗan ƙarfi, kafin ta bashi amsa MD ya kirata tana ɗauka ya shiga surfa mata masifa kaman zai zo wajen ya bindigeta. Tana ajiye wayar tareda sauke ajiyar zuciya ta haɗa ido da Gwamna. Duk da tsanar da take masa hakan bai hana tasirin kallon sa gareta ba.



"Yaudara na ɗaya daga cikin abubuwan da na ke ƙyama. Miss Asya na yarda da wannan interview ne saboda babu maganar siyasa a cikinta, kar ki manta da wannan"

A yadda ransa ya sosu da abinda tayi niyyarsa ya miƙe ya bar wajen saidai idan har yai haka ya sani daga lokacin 'yan jarida zasu murɗa labarin da cewa Gwamna ya ƙi amsa tambaya saboda bashi da gaskiya. Ya sani Alhaji Bala Yamai ba shine candidate ɗin daya so ya zama mataimakinsa ba sai dai kamar yadda Alhaji sani ke yawan faɗa masa cewa a siyasa dolene ka yi abinda bature ke kira compromise. Ba zai manta lokacin da Alhajin ya kirashi ya ce masa mataimakinsa shine Alhaji Yamai ba. Ya faɗi maganar kamar bashi da zaɓi, kamar ba shine mai ikon naɗa duk wanda yakeso ba.

"Alhaji Yamai yanada record na rashawa, Baba" ya faɗa da murya mai sanyi.

"Ka zo gida muyi magana" Alhaji Sani ya faɗa. Koda ya sameshi a gida bayani ya masa wanda hakan ya birkita shi har sai da asthma ɗinsa ta fara barazanar tashi.

Ya sani tun kafin ya kawo wannan matsayi Alhaji Sani Kachallah yana ɗaya daga cikin wanda suke riƙe ko yace suke juya jahar Congo. Tun zamanin mulkin soja ake damawa da shi har aka dawo mulkin farar hula.

"Mutane huɗu ne keda alhakin zaɓan Gwamna da Mataimakinsa. Wannan karan ɓangarena ne da Gwamna, ɓangaren Mataimakinsa yana hannun ɓangaren Yellow Group kuma sun zaɓi Alhaji Yamai. Kar ka damu, Alhaji Yamai hoto zai zama kawai" yadda Alhaji Sanin ya faɗi kalmar hoto sai ya tuna da yadda shima watannin baya yake kamar hoto a matsayinsa na mataimakin Gwamna. Ya so yaja da hakan amma bai samu ƙwarin gwiwar yi ba. Tun lokacin da Alhaji Sani ya gabatar da shi a jam'iyyarsu ya sanar dashi ma'anar tutar Jahar Congo. Kalar Baƙi da ta fi yawa a jikin tutar ita ke ɗauke da kaso 45% wanda Yallaɓai ke shugabanta yayinda kalar Blue ke ɗaukan 25%, kalar Red ta ɗauki 18% sai Yellow 12%.

kalar blue ta Alhaji Sani Kachallah ne hakan na nufin da shi ake damawa a Gwamnati, hakan na nufin Saifuddeen ba shi da ikon yin komai sai da yardar sa.



Yanzu da aka dawo daga tallen da aka saka wanda ta kai kusan minti takwas bai ɓata lokaci ba ya amsa tambayar Asiya da cewa ya zaɓi Alhaji Bala Yamai ne a matsayin mataimakin Gwamna saboda an riga an wanke sunansa daga laifin rashawa da ake tuhumarsa da shi shekarun baya, ya haɗa da cewa Alhaji Yamai yanada experience a harkar siyasa fiye da shi shiyasa ya zaɓe shi. Lokacin da ya gama bayanin lokacin da aka ɗibarwa shirin ya ƙare dan haka Asiya bata sake wata tambayar ba ta ƙarƙare shirin.

CY na cewa Cut Gwamna ya miƙe ya tafi yayinda muƙarrabensa suka bi bayansa cikin sauri.



"Aseey kin fuck up Wallahi" CY ya faɗa yana girgiza kai yayinda Sunusi yake jimamin yanzu ɗan alkhairin da za a basu ya wuce tunda gashi ran Gwamna a ɓace ya bar wajen su.



Lokacin da aka katse shirin aka saka talle COS ya zame jiki ya wuce office ɗinsa. Abu ɗayane ya zo masa wato Asiya taji abinda ya faɗa idan ba haka ba babu yadda za ayi ta kawo maganar mutuwar tsohon Gwamna. Tunda aka bashi matsayin Chief of staff lokacin Gwamna Saminu Bacci ya saka CCTV a office ɗinsa saboda shiga masa office da akayi ba da izininsa ba aka bincika masa wasu takardu. Ya kori sakatariyarsa a lokacin amma ya sani ba da saninta aka yi hakan ba, bai jima ba kuwa ya gano wanda yai hakan. Babu wanda ya san yanada ɓoyayyiyar camera a office ɗin nasa. Kasantuwar Sakatariyarsa Jennifer bata desk ɗinta sanda ya shigo ya ƙara tabbatar masa da cewa Asiya ta ji wayar da yai tun ma kafin ya duba CCTV footage ɗin. Bai sha mamaki ba da yaga Asiya laɓe a bakin ƙofarsa da 'yar ƙaramar na'ura da yake da tabbacin recorder ce lokacin daya kalli footage ɗin.



Asiya tana waya da Ubayd wani security ya iso ya ce ta biyo shi. CY da Sunusi suka zaro ido tareda tambayar lafiya. Bai ce musu komai ba yai wa Asiya jagora suka bar wajen. Asiya ta tsorata amma ta dake bata nuna ba saboda kar ta bada kanta, yau duk yadda za ayi sai dai ayi amma bazata taɓa fito da recorder ɗin nan ba.

Office ɗin Chief of Staff ya kaita kamar yadda tayi hasashe. Tayi mamaki da taga Sakatariya a office ɗin farko wanda ɗazo da ta zo babu ita. Lokacin da ta shiga office ɗinsa Mr Lamara Damana yana tsaye ya haɗe gira.

Jakarta security ɗin ya ce ta miƙo tana miƙa masa ya zazzage kayan ciki a walaƙance. Powder, lipstick, hankerchief, jotter, biro da earpiece ne a ciki. Wayar hannunta security ɗin yace ta kawo ta miƙa masa ba musu tana kallon COS da shima ya zuba mata ido yana mata kallon tsana.

Wata na'ura da ke detecting devices security ɗin ya bi ya zagaye jikin Asiya da shi amma bai detecting komai ba.



COS yace ya miƙa masa wayar Asiya sannan ya basu waje. Bayan fitan security ɗin COS ya kalli Asiya ya ce "na san ba a waya kika ɗauki maganarba dan haka ki fito da recorder ɗin"



"Ikon Allah, ina tunanin ka manta cewa ni 'yar jarida ce, wannan cin zarafi da kake min zai ja maka matsala" Asiya ta faɗa a kausashe.



Wani murmushin gefen baki COS yai wanda idan ba lura kayi ba baza ka gane murmushin yai ba saboda yadda gefen bakin ya tattare kamar mai shirin kuka.

"Asiya Shahidah Faruƙ Baba. Na san kina sane da haɗarin da ke tattare da wuce gona da iri a cikin aikin ku"



"Are you threatening me?"



"You know better"...





Lokacin da ta isa wajen su CY ko magana ba ta musu ba ta wuce gaba suka bi bayanta suna tambayar miya faru. Sai da suka shiga mota Asiya ta karɓi jakar camera da ke hannun CY ta buɗe wani ƙaramin zip ta ɗauko recorder a ciki ta damƙe shi a hannunta, yadda ta damƙe shi har sai da hannun ya fara rawa. CY kallonta yake yi cike da tambayoyi a harshensa amma ya yi gum da bakinsa tunda tace musu kar wanda ya mata magana.

Maimakon office gida tace Sunusi ya sauketa. Tana shiga ɗaki ta samu Umma na wanki a tsakar gida, ganin Ummanta duƙe tana wanki ya tuna mata da washing machine da ta ce zata siya tun watan daya gabata. Rashin lokaci ya sa take bada kaya a wanke mata sai ta haɗa dana Umman amma tunda Umman ta ce ba ta son a fita mata da kayan wanki waje ya sa duk weekend indai tana gida take wanke kayan mahaifiyarta.

A tsanake ta gaisheta tace mata ta zo ɗaukan abune dan kar ta firgitata. Tana shiga ɗaki kai tsaye laptop ɗinta ta buɗe ta fara ƙoƙarin tura abinda ta naɗa zuwa Laptop ɗin. Maganganun COS sun ɗan razanata amma idan ta tuna itama tanada abinda zai iya wargaza mulkinsu sai ta tausashi ranta.



Kafin ta gama abinda take wayarta ta shiga ruri. MD ne ta sani kuma ba zata kulashi ba sai ta gama abinda takeyi. A ƙalla ta kai awa ɗaya da rabi a gida kafin ta shirya ta koma office.



Ta ɗauka MD zai mata faɗa kaman yadda ya yi a waya amma sai ta ji ya tausasa kalmominsa gareta "Asiya ban san mi kika naɗa a gidan Gwamnati ba amma ina so ki sani cewa zaki iya taka Gwamna ki kwana lafiya amma Lamara Damana ba zai barki haka ba"



"MD kana so kace..."



"Asiya na san kinada ƙoƙari sosai wajen dukkan ayyukanki amma ki sani ana iya barin halak saboda kunya"



Za tayi magana ya ɗaga mata hannu sannan ya cigaba " already mutane sun fara reacting wa interview da kikayi amma nan da kwanaki kaɗan komai zai lafa, saidai idan kika sake bijiro da wani abun Asiya ba ke kaɗai fitinar za ta shafa ba idan ba ki ji ta ma'aikatarmu ba to ta iyayenki fa?"



Jikinta yai sanyi ta kasa cewa komai.



"Asiya you are a field reporter not investigative reporter, kada kiyi aikin da ba naki ba. Faɗa da 'yan siyasa ba abu ne da ake ƙareshi ta daɗi ba"



"Sir, kana nufin na watsar da gaskiya na rungumi ƙarya kenan?"



"Ban san mi kika sani ba Asiya amma koma minene ki yiwa Allah ki haƙura dashi saboda mutuncin ki. Lamara Damana ba mutumin da za ki iya ja da shi bane"



"Shikenan na ji"



Bayan Asiya ta bar office ɗin. MD ya sauke ajiyar zuciya. Kashedi Chief of staff ya masa ɗazu daya bugo akan in har aka fitar da wata magana da ta shafeshi Hill TV za ta rasa matsugunni a Jahar Congo. Ba wannan ne matsalar ba. Jin ya ambaci sunan Asiya ya sa shi fahimtar dalilin dayasa Asiya ta yiwa Gwamna tambayoyin da tayi, duk da bai san takamaimai mi Asiyar ta jiyo ba amma yanada yaƙinin abune da ya shafi mutuwar tsohon Gwamna. Duk wanda ya ke bibiyar siyasar jahar ya san cewa Lamara Damana shine shugaban munafukan gidan Gwamnati masu hana ruwa gudu. Mr Damana ya fara aiki daga Sakatare ne a hankali ya dinga shiga cikin manya ya zamana anyita ƙara masa matsayi har ta kai lokacin Gwamna Saminu Bacchi aka bashi muƙamin Chief of Staff. Tunda aka koma mulkin farar hula babu Gwamnan da Mr Damana bai yi aiki da shi ba.



"Asiya Shahidah Faruƙ Baba ta naɗi abinda yafi ƙarfinta, idan ya fito waje bana tunanin za ta sake yin rahoto da bakinta" kashedin COS na ƙarshe kenan.



Yana son Asiya tun farkon zuwanta ma'aikatar lokacin da tazo yin bautar ƙasa. Ya nemi soyayyarta ta ƙi shi, wanda yanzu ya riga ya haƙura tunda yaji ance an kawo kuɗin aurenta.



Duk da COS bai buɗa ba ya fahimci mi yake nufi sarai dan ba yau ya fara aikin jarida ba. Ba zai taɓa mantawa da wani ogan sa edita Mr Simon da suka fara aiki tare lokacin yana Lagos ba, shima kamar Asiya taurin kai ne da shi, indai a wajen bayyana gaskiya ne to baya jin tsoro. Ranan da gidan jaridarsu ta wallafa shafi akan wani asiri da Mr Simon ɗin ya jiyo na wani fitaccen ɗan siyasa ranan bai kwana duniya ba domin yana hanyar dawowa daga office motarsa tayi bindiga ta kama da wuta.

Ba zai manta da wani abokinsa Ja'afar ba. Ja'afar Bello investigative reporter ne daya binciko yadda wata Matar Minister ke safarar 'yan mata karuwanci zuwa ƙasashen waje. Yanada isassun evidence a kanta har an fara shari'a haka kawai aka nemi Ja'afar Bello aka rasa, ko sama ko ƙasa. Yanzu shekaru shatara kenan babu labarinsa.

Yana tsoron kada taurin kan Asiya ya jawo mata fitina.



Asiya koda ta koma office tunanin maganganun COS da ta MD ta dinga yi, a wani ɓangare kuma tana tunanin bazata taɓa bari Gwamna Saifuddeen yaci bulus ba. Ta sani cewa abinda ta naɗa bai kai evidence da za a iya kama Gwamna ba amma idan har maganan ta fito zai jawo cecekuce har a fara bincike, koda ya sha yanzu lokacin zaɓe abokan adawa za su yi kamfen da maganar su hana mutane zaɓanshi, ko kuma idan har akabi komai da gaskiya to dole ne ayi impeaching ɗinsa. Babu abinda take ganin yanzu zai faranta mata rai a rayuwa sama da taga an tsige Gwamna Saifuddeen Sa'ad Kachallah ...





***







A office Asiya ta dinga jayayya da zuciyarta akan ko ta bi shawaran MD tayi shiru da abinda ta ji ko kuma dai ta fitar da shi ta tada fitinar da zai jawa Gwamna matsala. Shawara ta yanke akan idan Ubayd ya zo hira za ta nemi shawaransa ta ji mi zai ce. Daga baya ta kasa haƙuri har zuwa lokacin ta kira numbarsa tace ya hau whatsapp akwai abinda za ta gaya masa. Sai bayan minti shabiyu ya hau saboda yana duba wani patient ne a lokacin da sukayi waya.



A tsanake ta masa bayanin komai da kuma abinda MD ya faɗa mata. Bai tsaida ita ba har sai da ta gama bayani ta ce miye shawaransa gareta.



" Asiya Shahidah na roƙe ki da girman Allah ki haƙura da abinda kike shirin yi domin ba zai haifar da ɗa mai ido ba. For God sake! we are getting married soon. Kina so rikicin siyasa ya jawo miki wata fitinar ne? Idan har abinda kika ji gaskiya ne then you are not safe Aseeya ba ke kaɗai ba hatta 'yan uwanki ba su tsira ba. Asiya ina za ki iya rikici da Lamara Damana?, Please ki mayar ma sa da recorder ɗinnan ki nuna masa ba za ki taɓa fitar da maganan da kika ji ba"



Tana gama karanta rubutun ta sauka tareda jan dogon tsaki. Wai sunata maganan Lamara Damana, Lamara Damana, shi waye da za ta ji tsoronsa. Idan har ba za a fitar da labarin a ma'aikatarsu ba ai akwai social media. Ringing ɗin wayarta ya dawo da ita daga tunanin da takeyi. Koda ta ɗauki wayar Ubayd cigaba da roƙonta yayi yana cewa ta masa alƙawarin ba abinda za tayi, da ta ga ya dameta tace mishi ta ji za ta yi shiru sai dai chan ƙasan ranta ta san ba haka bane.



Lokacin da suka tashi CY ne ya nemi ya kaita gida saboda yana son jin labarin miye dalilin sauya tambayoyi da tayi, sannan miye dalilin da yasa COS ya nemi ganinta.



"Na san gulma ne ya kawoka Clement kuma ba za ka ji komai ba"



"Ahn-Ahn, Aseey Darling ya zaki fassarani haka, jiya ma fa ni na kai ki gida"



"Ahaf, ka gama kame-kamen naka dai ka dawo hanya, magulmaci"

CY yai dariya ya wuce gaba.



Suna fita daga ma'aikatar Obinze Maigadi ya ɗaga waya jiki na rawa ya kira wata number ya ce yanzu Asiya ta fita daga ma'aikatar tasu ya haɗa da cewa tare take da abokin aikinta akan machine kafin aka katse kiran.



CY na tuƙi yana yiwa Asiya taɗin budurwarshi mai suna Evelyn da ta ce masa dole sai ya koma ɗariƙar Katolika (catholic) kafin ta iya auren shi, Asiya tana masa dariya. Ba suyi aune ba dai-dai za suyi kwana wata babbar mota da basusan daga ina ta fito ba ta zo ta mangajesu hakan yasa Asiya tsalle sama ta faɗi gefe yayinda motar tabi ta kan machine da ta danne CY ta wuce da bala'in gudu...


*THE GOVERNOR'S WIFE*
...... MATAR GWAMNA....







*©Azizat Hamza*



wattpad Azi_zat





Bismillahir Rahmanir Rahim









Book one







07







"Darling" Bilkisu Kachallah ta kira da fake American accent ɗinta wanda kunnen Saifuddeen ya kasa banbance "Dolin" tace ko kuma "Durling". Ya dai ɗago ido ya kalleta ba tareda ya furta komai ba. Ya sani ya kamata ya ce mata tayi kyau ko kuma yace jan lingerie (rigar bacci) data saka ya amshi jikinta sosai amma bai ce komai ba.





A mafiya lokuta idan ta yi shiga irin wannan tana buƙatarsa ne, ba kawai buƙata ba domin daga ƙarshe idan ta kwanta gefensa tana shafa gashin ƙirjinshi a hankali za ta bijiro masa da wata buƙatar ne, mafiya yawanci abubuwanda take tunanin ba zai mata su ba idan ta tambayeshi kafin ta shigo turakarsa su take tambaya.



Rabonsa da ita tun ranan farko da suka tare a gidan Gwamnati. Ba wai baya buƙatarta bane amma rashin nuna damuwarta gareshi yasa yake haƙuri da ita, ƙila saboda a koyaushe baya son takura mata ne. She's not yet 40 amma kuma lamarin sex life ɗinsu ya lalace tun lokacin da ta haifi Junior.




Takardu yake dubawa ta tura takardun gefe ta shiga kissing ɗinsa, farko daga goshinsa, kunnensa kafin ta kai bakinsa. Ba a jima ba ya tureta yace " ki bani minti goma na ƙarisa aikin dana ke"



"Haba Darling, ka san yaushe rabonka da ni kuwa? Aiki can wait please" ta faɗa tana zunɓura baki.



So yake ya ce mata laifinta ne idan bai nemeta ba tsawon kwanakin nan, saboda duk lokacin daya samu free time yake buƙatar kulawarta baya samu, amma bai faɗi hakan ba sai yayi mata murmushinsa mai shiga rai yace " kar ki damu, ba zan jima ba"




Bilkisu ta kwanta gefen gado tana kallon ceiling yayinda ya cigaba da duba takardun da idan bai duba yanzun ba bashida lokacin duba su gobe. Kusan minti talatin da uku kafin ya gama komai lokacin har Bilkisu ta fara gwarti. Ya je ya ajiye takardun acikin wani file ya saka a briefcase.

Bai tashi Bilkisu ba saboda ya san a gajiye take yau tace masa ta fita duba gidan marayu bai san details ɗinba kuma bai tambayeta ba.



"Shine baka tasheni ba" ta faɗa lokacin da ta tashi da Asuba.


"You're tired"

"Still" ta faɗa tana haɗe rai.



"To barin dawo daga masallaci"

Lokacin daya dawo daga sallar Asuba ta riga tayi wanka ta chanja kaya, ba rigar bacci ta sa ba amma shima kamar na jiya guntu ne mai hannun spaghetti, rigan ya kamata sosai, ya bayyana ƙaton tumbinta da yake a taƙune.



Kamar yadda yai hasashe yana shirin miƙewa ya je yai wanka ta faɗa masa buƙatarta na son buɗe Bilkisu Kachallah Foundation dan tallafawa marayu. Ajiyar zuciya yai sannan yace "Allah ya sanya alkhairi" ya wuce banɗaki tda sauri...








Meeting biyu ya shiga daga zuwansa office, yanzun ma wani meeting ɗin zai shiga nan da minti talatin. Yana duba report ɗin da aka kawo masa. Sakatare ya shigo da wasu takardu a hannunsa.



"Your excellency na samu COS ya reschedulling ziyarar da za ka kai ƙaramar hukumar Antu zuwa jibi laraba"



"Ok" Gwamna ya faɗa yana cigaba da duba takardun da ke gabansa.




"Excellency kafin na manta. 'Yan jaridar da suka zo jiya sun yi hatsari"



"Asya!" Gwamna ya ɗago kai da mamaki




"Ita

Please Login or Register in order to submit comment