Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

*************************⬇**********************
************* Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************

DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.

Email > [email protected]

******* FOLLOW US ******

Facebook: Ai Hausa Novels

Twitter: Ai Hausa Novels

Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels



Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.

********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************

BABBAN GORO BOOK 1

By Sumayyah Abdulkadir


BUDEWA Shekara ta 1980 G ida ne na gani a bada labari cikin unguwar Gwamna Road dake cikin garin Kaduna, kafatanin harabar gidan an_ kakkafa ‘canopies’ (rumfuna) da kujeru na alfarma.

Gidan cike yake da gawurtattu kuma tsofaffin ‘yan siyasar Najeriya wadanda suka dade ana damawa dasu a siyasar kasar, na jiya dana yau, har ma da na shekaranjiya duk ba’a barsu a baya ba, musamman yankin Arewa.



Daga cikin gida Najeriya da wajenta ma abokan huldar sa na siyasa duka sun halarta, manyan jifa-jifai (Jeep) kadai ke ta neman wajen adana motocin su, to haka kekuna da Baburan ‘yan achaba, kekenapeps, hade da kananan motoci na talakawa ma duk ba’a bar su a baya ba. Sun taru ne musamman domin taya Alh. Aliko Dan Kasa murmar hayewa kujerar Gwamnatin garin Kaduna, a sanarwar da aka yi yanzun nan a kafafen yada labarai, ciki har da gidan rediyon BBC da gidan talabyjin na CNN da dukkan jaridu da mujallun da suka fita a safiyar yau, karkashin jamiiyyar NPC _ (Northern People Congress) jam’iyya mai farin jini a wajen talakawa.



Kowa ka gani cikin farin ciki da nishadi

yake, ana ta shige da fice domin fitar da Hausawa, Igbo, Yoruba, Arabian har na Turai babu irin wadanda ba a fito dasu ba. Sai da kowa ya cika tumbinsa aka soma gabatar da makasudin taron cikin tsari na ‘yan siyasar da suka wadatu da ilmin zamani suka kuma san ciwon kansu; (ba mahandama ba), suke kuma aiki da iliminsu wajen gudanar da siyasarsu.



Cikin wannan halin ne mai girma Gwamna ya fito cikin rakiyar jama’a masu dimbin yawa, ya fara da gabatar da jawabin godiya ga mahalarta taron, sannan aka ci gaba da gudanar da taron kamar yadda aka tsara.



Mai girma Gwamna Alh. Aliko Dan Kasa, ya yi maganganu masu zafi a kan yadda gwamnatinsa za ta bambanta da sauran gwamnatocin da suka shude. Ya yi alkawarurruka masu ma’ana da yake fatan Allah Ya bashi ikon saukewa.





Ba shi ya samu kansa ba sai karfe goma na

dare, ya shigo gida a gajiye matuka, mai dakinsa Hajiya Zainab ta tare shi cikin murmushi mai nuna tsantsar farin cikin da itama take ciki a yau.



Suka tari juna da runguma cikin nuna godiyarsu ga Allah, kamin ta taimaka mishi ya cire babbar rigarsa, safa da takalmi, sannan ta gabatar masa da abin sha mai sanyi, kafin su zauna a tebir tayi ‘serbing’ din shi wainar masa, sinasir da miyar agushi data ji tsokar naman tolotolo, wannan shine nau’in abincin da Alh. Aliko ya fi so a rayuwarsa.



Saidai bai kai ga yin loma hudu ba, wayarshi dake gefe ta soma kurarin neman agaji. Yayi wa Haj. Zainab alamar ta amsa, Sal ta amsa a ‘hands-free’ cikin yin sallama.



“Kwamishinan ‘yan sanda ne, Ibrahim Rigasa. Muna son yin magana da mai wannan wayar, saboda shine ‘last call’ (kira na karshe) da muka gani a wayar Alh. Zubair Dan Kasa, wadanda suka taso daga Abuja shi da iyalinsa a safiyar yau’’.

Kasancewar a handsfree (murya waje) suke maganar, don haka yayi azamar amsawa da cewa, “Da mai wayar kuke magana”. Kwamishina ya ce, “To ku gaggauta kuzo nan asibitin ABU sun samu hadarin mota da shi da matarsa da ‘ya’ yansu biyu mace da namiji’”. Alh. Aliko ya tsame hannu daga abinci ya soma Salati yana fadin “Innalillahi wa’inna ilaihi raji’ un!” Itama Haj. Zainab salatin take yi. Suka mike a tare suka fito harabar gidan. Direba da masu tsaron lafiyarsa suka fito da mota suka shiga, a daren suka dauki hanyar Zaria. Da suka iso basu sha wahalar samun kwamishinan ‘yan sanda ba. Nan da nan ya yi musu jagora zuwa dakin da suke. Ya dubi tilon dan uwansa Ministan FCT Zubairu Dan Kasa, ko’ ina a jikinsa jini ne, bandeji ne plasta ce, yana numfashi da taimakon abin janyo numfashi. Daga shi har matarsa Haj. Kaltume cikin

yanayi daya suke. A gefe yaransu A\lmustapha da ake kira (Imam) da kanwarshi Shahidah ne suke ta kuka.



Al-mustapha da plasta a kansa da karaya a hannun dama, ita kuwa Shahidah abin mamaki ko kwarzane ba ta yi ba, amma hakan bai hana ta kuka ba, musamman ganin iyayenta duk a kwance cikin wani hali duk da kankantar shekarun ta.



Suna shiga Alh. Aliko ya karasa ga dan’uwansa hawaye na zuba a idonsa, yayin da Hajiya Zainab ta nufi su Almustapha tana rarrashin su. Ta kama Shahidah ta rungume tare da shafa kan Imam tana rarrashinsa.



Ko minti goma basu yi da shigowa ba Haj. Kaltume ta cika. Washegari da asuba shima Alh. Zubair ya ce ga garinku nan.



Tashin hankalin da mai girma Gwamna Aliko Dan Kasa ya samu kansa a ciki, ya mantar da shi farin cikin da yake ciki bakidaya.



Dan’uwansa tilo da ya rage masa duk fadin

duniya, yau ya tafi ya barshi. Abokin shawararsa kwaya daya rak, a duniya, su fadi tare, su tashi tare, yau babu shi. Kai shi da za’a kwace mulkin a dawo masa da Yayan sa Zubairu, da yafi farin ciki. Kuka yake wiwi da shi da mai dakinsa.



Gari na wayewa aka shiga watsa mutuwar FCT Minister Zubairu Dan-Kasa a kafafen yada labarai. Da motar asibiti aka dauko gawarwakin zuwa_ ainahin _ gidan mahaifinsu, inda mahaifiyarsu take zaune a Unguwar Rimi.



Jama’a suka _ shiga_ tittudowa domin halartar jana’izar mazan jiya, wadanda tarihin Najeriya bazai taba mantawa dasu ba, tun bayan rushewar mulkin soja (return to cibil rule), wadanda suka taimakawa Najeriya ta kawo matsayin da take kai a yau: (from agrarian to industrial) irin su Minista Zubair Dan Kasa. Nan mai girma Gwamna ya zauna karbar gaisuwa, yayin da Haj. Zainab ke tare da su Imam a asibiti.

Haj. Maama, tsohuwa ba tukuf ba, wadda ta kasance mahaifiya ga Alh. Aliko da Alh. Zubairu, wadda samun kulawar ‘ya’ya nagari ya boye zahirin shekarun ta, ta sha kuka har ta gode Allah. Sai dai da yake mace ce ma’abociyar imani da rikon addini, cikin kwanaki uku da _ rasuwar babban dan nata da mai dakinsa ta dawo cikin nutsuwarta. Tana amsa gaisuwar kowa. Saidai bata umh bata umh-umh, sai jan carbin dake hannun ta, sai kuma in an yl mata ta’aziyyah ta amsa.



Da ganin mai girma Gwamna Alh. Aliko Dan-Kasa, ka san mutuwar ta buge shi yadda ba a zato. Ya rame ya yi duhu, ya manta da wata baiwa da Allah yai mishi na ba shi shugabancin al’ummar jihar su ko rantsar dasu ba a yi ba.



A ranar da aka yi sadakar bakwai ya hattama komai na marigayan ya adana a babban bankin Iloyds TSB na kasar Ingila. Sannan suka taho Kaduna, inda aka rantsar da shi a washegari.



Suka tattara shi da mai dakinsa da

‘ya’yansu Al-mustapha da Shahida, suka koma Gobt. House Kaduna State. Mulki ya soma kankama.



washegarin komawarsu gidan gwamnati, ya shiryawa gyatumar shi tafiya da Imam wani asibitin kashi a kasar India, garin Punjabi. Bayan ya yi magana da hukumar asibitin ta yanar gizo (Internet). Suka tashi ranar asabar, inda Imam (Al-mustapha), ya soma karbar treatment daga kwararrun likitocin kashi.



Cikin sati biyu ya warke ragas suka dawo gida Najeriya, kowa na murna da samun lafiyar Imam, kasancewarsa yaro mai shiga rai, babu wanda zai kalli Al-mustapha bai ce yana son Sa ba.



Bayan kyau tsurar sa, da Allah Ya halicce shi dashi. Wani irin hazikin yaro ne mai kwarjini da kuzari hade da nutsuwa ta banmamaki. Haj. Zainab ta dauki kaunar duniya ta dora a kan marayun nan da maigidanta ya damka mata amanarsu. Bata taba haihuwa ba, a tsayin shekarunsu ashirin da aure. In har suna da matsala a rayuwarsu, to wannan ce.



Anyi jelen asibitin, anyi na gargajiyar shiru har yau. Don haka suka dauki komai suka mikawa Allah. Wanda ba’a sa Shi, kuma ba’a hanaShi. Shine mai bayarwa da hanawa ga wanda Ya so. Don likitoci sun tabbatar musu kowannensu lafiyarshi lau, lokaci ne Allah bai kawo ba.



Akwai aminci na hakika tsakanin Haj. Zainab da marigayiya Haj. Kaltume. Basu san wata kalma wai ita ‘faccalanci’ ba da

matan hausawa ke yi, musamman idan mijin wannan ya fi na waccan, duk da ratar arziki mai yawa dake tsakanin Zubairu da Aliko a lokacin da suka aure su. Don haka su Imam tuni sun saba da Haj. Zainab da Kawunsu Alh. Aliko, don a kan kawo su hutu wajensu lokacin da iyayensu na raye. Don haka ne da Imam da Shahida suka bude ido suka gansu a gaban Uncle dinsu da Haj. Zainab, sai basu damu sosai ba. Sai dai jefi-jefi Imam da yafi wayo kan tambayi Haj. Zainab Mummy da Daddy. Ta kan ce sun je Kano sai hutu ya kare za su zo su dauke su. Ita Shahida da yake karama ce ko ambaton iyayen ba ta yi, wasanta kawai take da ‘toys’ da ‘teddies’ (‘yar tsana) da aka cika mata gadonta dasu ba abinda ya dame ta. Alh. Aliko ya dauko gyatumarshi Haj. Mama daga Unguwar Rimi (gidanta da Alh. Zubair ya gina mata) ya dawo da ita Govt. House, sassa guda aka ware mata, babu abinda babu na jin dadin rayuwar

duniya, babun ce kurum babu. Kun san dai tsari irin na gidan Gwamnati.



Mulkinshi mulki ne mai cike da takawa (wato tsoron Allah), tsantseni (da dukiyar al’ummah) da tausayin talakawa.



A shekara daya kacal da ya yi yana mulkin jihar Kaduna da local governments dinta (kananan hukumomi) guda ashirin da uku (23), ya kawo sauye-sauye na ci gaba da dama, musamman ta fuskar tsaro da kariyar lafiyar al’umma.



Ya tsayawa malaman makaranta ta hanyar kara inganta albashin su, da basu rancen motoci a dinga diba da kadan da kadan daga albashinsu.



Haka ya tsayawa iyayenmu ‘yan fansho (pension) tare da taimako ta hanyar bada kayan aiki ga makarantun firamare da sakandire na jihar Kaduna.



Bai tsaya a nan ba, gwamnatinsa ta tsayatsayin daka kan wutar lantarki da ruwan sha, wadanda sune manyan matsalolin da jihar ke fuskanta. Haka ya_ taka


BABBAN GORO BOOK 1 CHAPTER 2

By Sumayyah Abdulkadir


muhimmiyar rawa a kan harkar ilmin manya (adult education) a jihar bakidayanta, da karo karatun malamai na jami’a dana sakandire a kasashen ketare ta hanyar daukar nauyin’ karatun§ da ‘accommodation’, da baiwa mata sana’o’l da tirenin akan sana’ar, haka matasan da basu samu damar yin ilmin zamani ba.



Kan ka ce meye wannan? Ya zamo zakaran gwajin dafi cikin gwamnonin Najeriya tsararrakinsa, sannan abin koyi, kuma abin so a zukatan al’ummar jihar. Sunanshi ya yi tambari a jihar baki dayanta, babu abinda ke fita daga bakunan al’ummar jihar, sai fatan alheri ga gwamnatinsa.



Wadanda suka san matsalarshi ta cikin gida kuwa (wato rashin haihuwa) sai addu’a suke masa Allah Ya ba shi magajin kyawawan halayensa.



A wurin shi kuwa, bai tsanantawa kansa kan rashin haihuwa ba. ‘Ya’yan dan uwansa sun isheshi, har gaba da abada in akwai, ‘ya’ya ne a gareshi da yake so fiye

da ‘ya’yan da zasu kasance shi ya haifesu. Wato Imam da Shahidah. Fatansa Allah Ya raya masa su cikin tarbiyyar Islam ameen.



H aj. Zainab ce zaune a katafaren falonta tana kallon tashar MBC da ‘remote’ a hannunta, Al’mustapha na ‘game’ cikin wata na’ura ta yara. Shahida ta lallaba ta zagaya ta kashe, ya dago a fusace ya yi kanta da duka, da kyar Hajiya ta kwace ta. Ta ce, “Haba Imam, irin wannan duka kamar ka samu sa’an ka? Baka ganin Shahida yarinya ce ne?” Ya zumbura baki, “To wa ya ce ta kashe min ‘game’ dina?”

Ta ce, “Ka yi hakuri ba za ta sake ba. A bar ‘game’ din haka, aje ayi alwala ayi sallah, sannan ayi shirin fita lesson (darasi) kafin teacher (malam) ya zo”.



Duk suka amsa, suka fita. Ta bisu da kallo, tana jin kauna da tausayin yaran har cikin zuciyarta.



Ta tashi ta nufi sassan surukarta Hajiya Maama, ta tarar da ita tana sallar la’asar. Ta samu kujera ta zauna har Hajiyar ta idar ta yi addu’a ta shafa.



Ta juyo da murmushi ta ce, “Ya ya Maman Imam? Ina ‘yan rigimar naki sun dawo ne?’



Ta ce, “Sun dawo tun dazu, har anyi wanka an ci abinci an tafi daukar lesson, yanzu aka gama rigimar na sha rabon fada, kin san Imam din nawa ba dai karfi ba. Ai Shahida tana cin duka, wannan bai hanata gobe ma ta sake tsokanarsa kamar ba jikinta ake tika ba”.



Hajiya Mama ta yi dariya ta ce, “A kullum na dubi yaran nan suna tuna min da Kaltume. Da wata hira da muka taba yi da ita. Ta ce Allah Ka bawa Haj. Zainab ‘ya in aurawa Imam”.



Hajiya Zainab ta yi murmushi cikin jin kunya kuma mai ciwo a zuci. Suka ci gaba da hira da _ surukuwarta, duk da shimfidaddiyar damuwar da Hajiyan ta gani a fuskarta a dalilin zancen haihuwa data yi.



Wayar mai girma Gwamna ce ta tada ita daga hirar da suke yi mai ban tausayi a kan marigayi Minista Zubair da mai dakinsa Hajiya Kaltume. Cikin su babu wadda bata zubar da hawaye ba.



Imam na aji uku na sakandire, Shahida na aji shida na firamare. Tenure din Alh. Aliko ta cika, ya sauka daga gwamnatin jihar Kaduna.



Ba yadda jama’a basu yi da shi ba a kan ya sake tsayawa takara amma ya_ ki amincewa, ya ce tunda ya tsira da mutuncinshi da kaunar shi a zukatan al’umma, to Alhamdulillahi. Suka baro Gobt. House suka dawo katafaren gidan da



ya gina a Jabi Road, dake cikin birnin Kaduna.



ASALINSU A salin mahaifin su Alh. Aliko mutumin Kaduna ne, a wani gari, CHIKUN. Cirani ne ya shigo da shi cikin garin Kaduna tare da mai dakinsa Salamatu (Hajiya Maama). Itama ‘yar Chikun ce kamar miinta

Malam Salihu.



Haihuwar Salamatu bakwai duk suna mutuwa (wabi), sai a kan Zubair na takwas Allah Ya bar mata. Ba dadewa ta sake samun wani cikin, ta haifi Alh. Aliko, wanda sunan shi na ainahi, Aliyu. Baban shi ke kiran shi Aliko, kuma sunan ya bishi har girma.



Zubairu da Aliko sun rayu tare da iyayensu har girmansu, kafin Allah Ya dau ran mahaifinsu Malam Salihu. A_ lokacin Zubairu yana da shekaru ashirin, yayin da Aliko ke da sha bakwai.



Duk da iyayensu basu yi karatun boko ba, Mal. Salihu bai bar ‘ya’ yanshi haka ba, sai da ya ga kowannensu a jami’a sannan ya samu kwanciyar hankalinsa. Ya _ tsaya tsayin daka a kan karatun su, wanda shine tsani na duk wani mataki da suka taka yau a rayuwa.



Karatu mai suna karatu, sun yi shi har sun kure biro, idan har ana kurewa, dukkansu akan siyasa. Amincin dake tsakaninsu na shakikan juna, ba kasafai ake samun irin

shi a wannan zamanin ba. Daya baya zartar da komai kan abinda ya shafeshi ko iyalinsa ba tareda yayi shawara da daya ba. daga kan Kakaki (speaker house of representatibe), dan majalisa, kwamishina, sanata, shugaban karamar hukumar Chikun da wasu da dama, har kawo na yau, wato matsayin daya taka na Gwamnan jihar Kaduna.



To haka Zubair ya rike mukamai da dama kafin Allah Ya dau ransa. Har kawo na karshen, wato Ministan FCT. Inda ya gamu da ajalinsa a kan hanyarshi ta zuwa taya dan’uwanshi murnar hayewa kujerar Gwamna.



Mutuwar Zubair ta taba Aliko ba kadan ba, yadda har ta shafi lafiyarshi. Sai dai kullum ya dubi Imam da Shahida dake gabanshi, yana godewa Allah da bai barshi da kewa ba.



Kullum ya daga ido ya dubi Imam (Almustapha) fuskar dan’uwanshi Zubair yake gani a fuskarsa.

Don haka son da yake yiwa yaron ba kadan bane, ta yadda har yake mantawa da cewa ba shi ya haife shi ba. 2K ok ok ok




mam Zubair Dan Kasa, yaro ne mai hazaka tun yana kankaninsa, yana da wasu baiwarwaki da dama da ba duk ‘ya’ya Allah Ya mallakawa ba.



Yaro ne da ya lakanci wani darasi daga cikin darusan da ake koya mishi a makaranta wai shi introductory technology. Ga kyau ga kyan hali, ga nutsuwa da rashin son wasa, ta ko’ina Imam Almustapha, abin alfahari ne ga iyayenshi da ‘yan’uwan shi bakidaya. Rashin iyayenshi da ya yi a_ lokacin kuruciya bai sa shi ya yi maraici ba ko kankani. Baffanshi da matarshi a tsaye suke a kansu, farin cikinsu da walwalarsu. Sannan Hajiya Maama ba ta da abin so irin mijinta Imam, wanda take sawa a gaba tana koyar da shi dabarun zaman duniya, da yadda za a yi a ci ribarta.

A irin wadannan lokutan, Imam kan dauki dukkan hankalinsa ne kacokan ya likawa Hajiya Maama, yana kwankwadar ilmin manya na yadda za’a gina rayuwa a duk halin da aka samu kai, yana aunawa a ma’auni na hankali da tunaninsa, yana hadawa yana tarawa yana_ rarrabewa, sannan idan ta gama ya jefo mata tambaya wadda ta fi karfin shekarunsa.


Akwai ranar da ya tambaye ta “Me yasa Daddy ya ki ci gaba da takara duk da kaunar da jama’ar Kaduna ke mishi?”



Ta yi murmushi ta ce da shi,



‘Don ya tsira da mutuncinsa ne, ka san an ce tsira da mutunci ya fi tsira da kudi’”. (Wannan Magana ta zauna cikin ran Imam har girman sa)



Akwai kuma ranar da ya tambaye ta, “Ita Mami (Hajiya Zainab) mai yasa ba ta haihuwa?”



Ta ce, “Allah ne bai bata ba Imam, amma ka dinga yi mata addu’a”.



Tun daga wannan ranar Imam bai kara tashi daga inda ya yi sallar farilla ba, ba

tare da ya rokawa Mami dinsa haihuwa ba. 2K ok


ayan barin Alh. Aliko Gwamnati, kasuwanci ya fada ka’in da na’in. Ya hada gwiwa da wani kamfanin kera injinan wutar lantarki dake kasar Birtaniya, suke shigo masa da injina nau’i-nau’i manya da kanana.



Sannan ya bude manya-manyan gidajen man fetur guda uku a ciki da wajen garin Kaduna. Ya kuma zuba hannayen jari a wasu manyan kamfanonin Inshorar Nigeria irinsu. NAICOM_ (National Insurance Commission), African Alliance Insurance, da Consolidated Hallmark Insurance Plc. . Wata ranar asabar Hajiya Zainab ta tashi ba ta jin dadi, kamar da wasa taje ganin

likita, ya dudduba ta ya yi mata tambayoyi, ya kuma umarceta da ta ba shi fitsarinta. Wanda nan take ya mika ‘lab’ aka auna, sakamako ya fito, inda ya tabbatar mata tana da shigar karamin ciki dan watanni biyu.



A nan ofishinsa ta zube ta yi sujjada ga Allah, buwaya gagara misali mai yiwa bawa baiwa da abin da bai isa ya bawa kansa ba.



Sannan ta ja bakinta ta tsuke ba ta gayawa kowa ba. Don ita kunya ma take ji tsofaitsofai da ita da ciki. Ita kadai ta yi ta fama da laulaye-laulayen ta, amma da yake babba-babba ne, Hajiya Maama ta gane.



A lokacin cikin na da watanni hudu Alh. Aliko baya nan yana Bristol, wato ainahin kamfanin dake shigo masa da_ injina samfurin (Binatone). Hajiya Mama ta yi kiranta ta ce, “Zainab kin je asibiti a kan wannan haraswar?”



Ta ce, “Na je”.



Ta ce, “Basu gaya miki kina da juna biyu ba?”

Kanta a kasa ta ce, “Sun gaya mini’. Hajiya ta kama baki cikin al’ajabin fulatancinta, ta ce “To don me baki gaya min ba? Wannan ai abin mu taru mu yi farin ciki ne mu godewa Allah”. Ta tsura mata ido tana ta zuba addu’a na Allah Ya sauke ta lafiya.



Ko da Alh. Aliko ya dawo, dakin mahaifiyarshi ya fara isa kamar yadda ya saba kullum yayi tafiya. Far’ar Hajiya yau ta fi ta kullum. Shi kanshi ya fahimci tsantsar farin cikin da mahaifiyarshi ke ciki.



Ya zauna_~ cikin luntsuma-luntsuman kujerunta ya ce, “Hajiya me muka samu ne? Da alama kina cikin farin ciki”.



Ta ce, “Kwarai, mun samu abin da kudi da mulki basa bayarwa!”’.



Ya ce, “Ni kuwa mene ne shi wannan abun?”



Ta ce, “Da, Zainabu na da ciki har tsayin watanni hudu”.



Suman zaune ya yi, kafin ya tattara hankalinsa da nutsuwarsa ya mika su ga

mahaifiyarshi, ya kuma murza idanunshi ya sosa kunnensa, ya tabbatar ba mafarki yake yi ba.



Ya ce, “Don Allah Hajiya ki kara yi min bayani”’.



Ta ce, “Abin da na fada haka yake Ali, Zainabu za ta haifa maka Da, naka na kanka, hakurinku da tawakkalin ku basu tashi a banza ba!!!””.



Alh. Aliko sai hawaye ya soma sharewa, ya yiwa mahaifiyarshi sallama ya nufo bangarensa. Alwala ya yi ya kawo raka’o’i hudu kwarara domin mika godiyarshi ga Allah bisa wannan falala da ya yi mishi a lokacin da bai zata ba, a kuma lokacin da ya riga ya fidda rai. To ina ruwan Allah. Hajiya Zainab ta shigo ta sha kwalliya, cikin sassalkar shadda_ dinkin ‘yan Senegal, jikinta na fidda wani_irin sihirtaccen kamshi. Tunda ta shigo yake kallon ta har ta karaso gabanshi. Ta mika mishi kofin fadi-ka-mutu cike da tataccen

Please Login or Register in order to submit comment