Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wannan bai hana dukkaninsu samun gurbi a jami’ar Ahmadu Bello ba, a kuma fannin da kowaccensu take so.



Don haka da _ yardar iyayensu. da amincewarsu suka tattara suka koma Zaria (off campus), flat guda Daddy ya kama musu a kusa da makaranta, da karamar mota kirar ‘kia-Picanto’ don zirga-zirgarsu cikin makaranta da wajen ta.



Suka soma karatunsu cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, don Imam din bai kara ta da zancen Safah ba, ya ba ta lokaci har Zuwa sanda yake ganin ta mallaki hankalin kanta.



Ko waya ya yiwa Mami, Daddy da Hajiya Maama, cewa kawai yake a gaishe ta. Sannan shi ma ayyukan gabanshi sunyi mishi yawa. Ko lokacin da zai ‘emailing’ dinta baya da shi, duk da ya sha gwadawa



yana jin sa a rufe.



D addy ya wakilta Zahraddeen Maitama

babban yaronshi dake kula da gidajen man-fetir na ‘Dan Kasa_ Holdings’, matsayin mai kula da al’amuran karatun Safah da Marwah a Zariya, kasancewar shi dan asalin garin Zaria. Duk abinda suke bukata kamar kudi da sauran matsalolin karatun su Zahraddeen za su nema.



Shi kansa wannan mukamin da Daddy ya baiwa Zahraddeen albashi yake bashi mai zaman kansa, sannan a boye kamar wani security ne dake ganowa Daddy halin da ‘ya’yan nasa ke ciki, da irin kawayen da suke mu’amala dasu.



A watanni uku kacal, Zahraddeen, ya fahimci Safah da Marwah ‘yan biyu ne kawai, amma mabanbanta a halayya da dabi’a.



Safah ta fi Marwah mai da hankali a karatu, ta fita nutsuwa da rashin son hayaniya, sannan Marwah ce ma’abociyar hulda da jama’a, duk da bata da samari tana hulda da mazan ajinsu da kawaye da yawa.



Don haka Zahradeen ya sanar da Daddy

obserbations dinsa a kansu. Ko jarrabawar zangon farko da suka yi, Safah ta fi Marwa scoring GPA..



Duk da haka Marwa ba ta fadi ba, ta lashe duka takardunta da maki kadan, wanda ake kira aberage. Ba kamar na Safah ba oberall din ajinsu. Don haka ran Daddy ya baci. Karfe Shidda daidai na yamma suka yi parking motar su a harabar gidansu suka shiga a gajiye. Biola ta karbi jakunkunansu tana yi musu sannu da zuwa.



Gidan ko’ina fes don Biola (yarinyar da Mami ta basu take musu aiki) bata wasa da tsaftarsa, sai kamshin air freshner ke tashi. Ko zama basu yi ba Zahradeen ya yi musu dirar mikiya, Daddy biye da shi. Suka taho da gudu za su rungume Daddy ya daga hannu ya dakatar dasu.Ya ce,



“Babu gaisuwa tsakaninmu Marwah, zuwa na yi in ji dalilin da yasa Safah ta fiki maki Marwah?”



Ta sunkuyar da kanta ba ta yi magana ba. Daddy ya shiga yi mata fada ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba. Har saida ta

soma kuka. Ya ce babu ita babu kawayen da take hulda dasu, in ba haka ba za ta koma gida ya ba da sadakarta tunda aure take so karatun bai dame ta ba.



Tana kuka sosai take ba shi hakuri, ta ce insha Allahu ba za ta kuma ba, kuma zango mai zuwa za ta dage.



Sai kuma ta bashi tausayi, ya sassauta ya shiga yi mata nasiha a kan ta dinga yin koyi da ‘yar’uwarta a kan komai. Ya yi musu addu’a a ranar ya koma Kaduna bai kwana ba.



A karshen satin Zahraddeen ya kawo musu ziyara kamar yadda ya saba. Marwah ba ta gida ta je saloon, sai Safah da Biola a gidan wacce ke kicin tana hada musu abincin rana.



Tana zaune a falo cikin atamfa mai karshen tsada, kanta babu kallabi, ta matse gashinta a tsakiyar ka, farin gilashin dake idanunta ya kara ma fuskarta ilhama da kwarjini, tana nazarin wani littafin ilmin halin dan adam wanda a fakaice ba komai ne ciki ba sai applied Christianity, amma

Malaman kimiyyar halin dan adam ke amfani dashi a jami’o’I matsayin hanyoyin gyara mu’amalar zamantakewar dan-adam, tana tsintar na tsinta, tana zubar da na zubarwa, sunan littafin “The Power of Positibe Thinking’.



Ya danna kararrawar kofar shigowa, Biola ta bude. Ya bayyana cikin kyakkyawar suit (Japanese) da bakin gilashin Prada a idanun shi.



Falon ya gauraye da kamsassan turaren shi na (Dior Addict), kafafunshi rufe cikin cober baki, da ganin shi ka ga gogaggen dan boko mai ji da bokon da aljihunshi da ya soma nauyi albarkacin aikin sa’a da ‘Dan - Kasa Holdings’.



Kallo daya ta yi mishi ta ji zuciyarta ta buga a yau, kamar yau ta fara ganinsa. Ba wai yau ta fara ganinsa ba. Saidai bata fiya yiwa mutum kyakkyawan kallo ba. Yau ta ganshi ne sosai a gabanta, ba daga nesanesa ba. Shi ma gabansa ne ya fadi, sakamakon ganin Safar yau a ainahinta ba cikin mayafi da rigunan sanyi kamar

kullum ba.



Ta lalubi dankwalinta ta daura, ta zare gilashin idanunta ta yi mishi barka da zuwa, tare da mikewa tsaye (alamar girmamawa irin ta bature ga bakonshi).



A tare suka zauna cikin kujeru masu fuskantar juna. Shiru ta ratsa na ‘yan dakikai, wani chemistry mai ban mamaki na aiki a zuciyoyinsu da kwayoyin idanun su, yana shiga cikin zukatansu. yana kurdawa har cikin kwakwalensu.



Sai da suka ci mintuna biyar suna kallon juna sannan suka kawar da kai a tare, tare da aje wata boyayyar ajiyar zuciya.



Ya ce, “Ina kanwata ne? Ban ji motsinta ba?’



A sanyaye ta ce, “Ta je saloon ne?”



Ya ce, “Na zo ne in ji ko akwai matsala?” Ta zuki iska ta fesar, cikin yangarta ta halitta. Ta ce,



“Dama dazu nake ce da Marwah ta yi maka waya, akwai wasu tedtbooks da suka shafeni da nake bukata matuka ban samu a school bookshop ba; ‘Modern Dental

Assisting’ (Bird Robinson), ‘Esthetics and Biomechanics in Orthodontics’ (Rabindra Nanda), ‘Endodontics’ (Mahmoud Torabinejad) ko za ka samo min a cikin gari?



Sannan motar mu tana bamu matsala kwanan nan, akwai bukatar a sake wata”’. Tunda ta soma magana yake kallon siraran labbanta dake motsi a hankali kamar basu ke furta maganarba, tareda_ sauraron sassanyar muryarta dake fita cikin nutsuwa da taushin kalami. Turancinta a sarke, kai kace a Turai take karatun.



Da kyar ya daure ya ce,



“Gobe zan je Lagos ki rubuta min sunan littafan sai a nemo. Ina zan iya rike wannan compled language naku? Maganar mota zan bar muku tawa ku yi amfani da ita kafin in je Cotono in na dawo Lagos, don Daddy yayo odar wasu motoci daga Cyprus sai a daukar muku daya”.



Ta ce, “Anya mun yi amfani da motar ka? Babba ce sosai, bana son abinda zai ja hankali a kanmu?”

Ya ce, “alright! To ku lallaba takun a hakan kafin a kawo zuwa nedt week, shi kenan?”



Ta ce, “Babu malta a fridge, sannan muna bukatar naman gongoni da juices”.



Ya ce, “Wannan ba matsala, gobe kafin in tafi zan biyo in kawo”’.



Ya mike yana amsa call, sai da ya gama ya juyo ya dube ta da wani irin lallausan murmushi, ya rankwafa ya ce,



“Ko zan iya samun lambar wayar uwargijiya ta?”



Ta dago cikin slow-motion ta zuba mishi kyawawan idanunta farare tas, tana girgiza kai ta ce,



“Bani da waya!”’.



Ya yi mamaki sosai. Sannan ba tare da ya tsawaita mamakin ba ko ya tambayi dalili ba ya zura hannuwanshi cikin aljihun wandonshi ya fiddo kan wayoyi guda hudu ya zube mata guda biyu a kan cinyarta. “Zama haka babu waya a wannan zamanin kanwata ba zai yiwu ba, ko kuma in ce bai dace dake ba. Kuma bashi da dadi.



Ba wai sabida nishadi da bata lokaci kawai da ake yi da wayar ba, ita wayar dai tanada nata amfanin akan-kanta. Ki yi hakuri ki yi amfani da nawa kafin in taho miki da wasu daga Cotono.....ki yi min alfarma kada ki ce min a’ah.......”



Ba ta san me yasa ta kasa yi mishi musu ba. Ya juya ya fita tare da cewa,



‘Na barki lafiya”’.



Ba ta dauke idonta a bayan shi ba har ya fice daga falon, zuciyarta na kai kawon da bata taba ji a rayuwarta ba.



Ta maido idanuwanta bisa cinyarta a hankali, ta zubawa wayoyin da ya zube mata ido.



Wayoyi ne masu tsadar gaske, HTC da BB. Ta debe su ta kaisu ga hancinta, tana shinshina su, ni’imtaccen kamshin ‘Dior — Addict’ ya kama su sosai.



Sai ta samu kanta da lumshe ido, tare da bude su duka a tare, cikin wani sabon



al’amari da ba za ta iya kwatantawa ba. 2K 2K ok

ASALIN SA Z ahraddeen Aminu Maitama, dan talakawa ne tulis! Bazazzagen usuli ne da ya fito daga cikin Mallawan Zazzau na asalin unguwar Tukur-Tukur. Ya yi karatu da tallafin Gwamnati da kulla-kullar mahaifiyarshi da taimakon Allah a jami’ar Ahmadu Bello. Inda ya karanci (Petrochemical Engineering). Ya sha matukar wahala wajen karatun nan, wanda aka yi cikin halin babu, da taimakon Scholarship, abokai da Inna Binta. Bayan kammala hidimar kasa ya sha wahala sosai kafin ya samu aiki. Shekaru hudu kwarara ya kwashe duk da kyan sakamakonsa da nagartar karatunsa bai samu aiki ba. Sai da Gwamnatin NPC ta hau mulki ya samu aiki a matatar man fetur ta NNPC, da taimakon Aliko, wanda ya kasance abokin mahaifin wani abokinsa Idris, aka dauke su su biyu.

A wani juyi da NNPC ta yi, ta zubar dasu a kwandon shara da ta samu wadanda suka fisu yawan kwali. Wannan ya zaburar da Zahraddeen ga komawa makaranta ya yi masters shi da Idris, sannan mahaifin Idris ya hadasu da tsohon Gwamna Aliko DanKasa ya basu aiki da ‘Dan-Kasa Holdings’. Shekarar baya ne Allah ya yiwa Idris rasuwa ya barshi da kewa mai yawa da gurbin da har gobe bai cike ba. Domin bai kara yin aboki ba tun rasuwar Idris. Haka yake cikin rashin karsashi a duk abinda yake yi.



Da lallashi da addu’a Daddy ya samo kanshi, domin malamai na musamman ya sanya suke mishi rubutun dangana ganin yadda gidan mansa ke neman durkushewa saboda rashin maida hankalin Zahraddeen, wanda ke hidimta mishi da dukkan zuciya da amana, ba don kudin da yake biyanshi ba.



Bai taba samun hazikin ma’aikaci irin Zahraddeen ba. Mai innobations cikin kwakwalwarsa (fasahar kawo_ sababbin

abubuwa na cigaba iri-iri). Don haka shi ma bai dauke shi da wasa ba, albashi yake biyanshi mai tsoka, kuma shine (Managing Director) na ‘Dan-Kasa Holdings’ baki dayan ta.



Daddy na yabawa da hazaka da amanarsa, wannan na daga cikin dalilan da ya sanya ya damka mishi amanar kula da walwala da karatun ‘ya’yan shi. Yana kuma gudanar da aikinsa sosai cikin gaskiya da tsayawa bisa matsayin sa. Saidai kuma gashi ga dukkan alamu, a yau Zahraddeen na neman wuce matsayinsa.



Zahraddeen matashi ne dan kimanin shekaru talatin da haihuwa, amma ayyukan da yake gudanarwa ‘Dan Kasa Holdings’ ko dan arba’in sai haka.



Duk inda ake neman kyau ga da namiji, to Zahraddeen ya mallake shi. Kin san dai kyau irin na Mallawan zazzau, farare ne tas masu dogon hanci da yawan suma. Saidai shi Zahraddeen wankan tarwada ne mai kyawawan idanu, farare kal kuma manya masu cike da ilhama.

Shi ne da na farko a gun iyayensa, sai kannin shi Umma, Rabi’a da Nura. Su kenan Inna ta Haifa. Mahaifinshi ya dade da rasuwa tun yana sakandire. Don haka nauyin mahaifiyarshi da kannensa duk a kanshi yake.



Ita Umma anyi mata aure a nan cikin Zaria, Rabi’a na _ karatu) a_ babbar sakandiren ‘yanmata mai tsohon tarihinnan ta Sarauniya Amina dake cikin Kaduna, sai autansu Nura wanda ke JS (karamar sakandire).



Wadannan iyali sun taso cikin kulawa da tarbiyyar nagartacciyar uwa Inna Binta, wadda bata taba gazawa a kan bukatunsu da karatun su ba don sun rasa mahaifinsu. Babu irin sana’ar hannun da ba ta yi don ta tallafi rayuwarsu, ta inganta farin cikinsu. A rugarsu ta ainahin iyaye da kakanni, dake can bayan garin Lere tana kiwon garken shanu da suka gada itada Yayarta daga wurin iyayensu, haka take saida su daya-bayan-daya don hidimar_ karatun Zahraddeen mai tsada, har Allah Ya sa ya

kammala. Shanu kuma babu ko daya. Don haka su ma ‘ya’yan basu da abin so da kauna tamkar ta, da burin faranta mata. Barin Zahraddeen wanda duk abin da ya samo na mahaifiyar shi ne.



Daga fara aikinshi da ‘Dan _ Kasa Holdings’, kodayake kafinnan ma ya tara sosai a aikin da yayi a NNPC, ya bige ginin gidansu ya tsantsarawa Inna Binta ‘bungalow’ gida na zamani mai rufin daukar hankali (modern European bungalow) kalar ruwan kasa mai duhu (deep brown), gidan kuma ciki dawajensa fentt ne ruwan madara, ya ajiye mata karamar motar shiga don bukatunta. Nura ke kaita ko’ina ta ke so. Sannan yayi wa kanshi nashi flat din duk anan cikin gidansu, daidai rayuwar kowanne dan boko mai aji daidai nasa, wato ma’aikaci mai sa’a. Cikin tsari na masu ilmi da sanin ciwon kai, ba na karyar rayuwa ba.



Komai dake cikin gidansu Zahraddeen mai amfani ne, baya bari inna tayi girki da icce saida cooker, bata markade sai a blander,

bata gashi a garwashi sai a oben, bata dumame sai a microwabe zaka rantse da Allah ba gidan tsohuwa bane, duk da dai ma bata tsufan cancan ba, bazata wuce shekaru hamsin da biyu ba, da kwarinta da kuzarinta da koshin lafiya duk albarkacin haihuwa da ilmin data tsayawa Zahraddeen yayi wanda yafi karfin aljihunsu, ga mai aiki ya ajiye mata tana yi musu gyaran gida amma duk rintsi Inna ke girki, don ita kadai Zahraddeen ya yarda da tsaftar ta a duniya kuma ita kadai din ce ke yi mishi abincin da yake gamsar dashi mai cike da hikima irin ta manya da sanin sirrin girki walau na gargajiya ko na zamani, don sau tari Rabi’a tana makarantar kwana.



Ya bawa Umma jari mai tsoka take dinki da kekunan dinki na zamani, har shagon dinki take dashi a kofar gidan ta, ya zuba mata kwararrun teloli tana biyansu kuma tana samu sosai, ya sauyawa Nura da Rabi’a makarantu masu nagarta.



Ba shi da abin da zai ce da Alh. Aliko sai fatan alheri, domin a jikinsa yake samun

duk wannan rufin asirin.



Ko da yake morar juna suke, amma dole ya gode mishi, don abin da yake ba shi ya fi karfin aikin da yake yi mishi.



Ga shi yau ya tsinci kansa cikin wani al’amari mai GIRMA a kan diyar shi, duk da cewa ya san bakin rijiya ba wajen wasan yara bane. Don haka ya soma yaki da zuciyarshi, ta hanyar yakar sabbin kibiyoyin dake huda kowanne sako na cikinta.



Sai dai duk iya kokarinsa a wannan daren ya gaza rintsawa, ko ya runtsan, surar Safah yake gani cikin murmushi. Abin kamar azal.



Don haka da ya yi sallar asubahi ya dade yana rokon Allah sauki cikin al’amarin, amma kamar turi, Safah Dan Kasa, ta kankane ko’ina na _ zuciya’ da kwakwalwarshi, ta kassara gangar jikinsa bata barshi da ko sako daya da zai sanya tunanin kansa ba.



Don haka a washegari shine mutum na farko da ya danna musu kararrawa, Biola
Ko fada su kai a junansu baya wuce kwana daya sun shirya sun manta komai. Don haka ta ga gara ta tunkari Safan kai tsaye ta yi mata bayanin abinda take zargi.



Karfe tara na daren ranar ta yiwa Zahraddeen rakiya ya tafi. Tana dawowa ta cimma Mami a gefen gadonta ta yi tagumi.



Ta zauna a gefenta ta sauke mata tagumin ta ce, “Maminmu, lafiya kika zuba wannan uban tagumi? Har na shigo baki san na shigo ba’.



Ta dube ta sosai da idanunta da ba sauki a cikinsu, ta ce,



‘“Safah”’.



Ba ta amsa ba illa ta dube ta, sabida yadda ta kirayi sunan nata_ cikin kakkausan harshe.



Ta ce, “Me _ ke tsakaninki da Zahraddeen?”



Ta sunkuyar da kanta kasa. Ba ta yi magana ba, sai da Mami ta yi mata tsawa ta ce, “Ba magana nake yi dake ba?”

Cikin sarkewar murya ta ce, “Ki yi hakuri Mami....dama.....dama gobe ne Deen yake son ya sanar da Daddy, ni kuma dama yau zan sanar dake muna son junanmu........mun yanke shawarar yin au....”



Ji kake kauu! Mami ta dauke ta da mari har sai da ta ga wuta, ta nemi ji da ganinta na wucin gadi ta rasa. Mami ta ce, “Abinda za ki yi mana kenan? Tozarcin da zaki yi min kenan? Sabida kin je jami’a idon ki ya bude da maza. Kina nufin ba za ki auri dan’uwanki mai kaunar ki ba? Me Zahraddeen din yake da shi wanda Almustapha ba shi da shi?



Ke ko kunya ba ki ji a ce za ki auri yaron Baban ki? Boyi-boyin Babanki? Dube ki don Allah, kina kallon kanki a madubi kuwa? Amma ki rasa a inda za ki kare da zaman aure sai a cikin garin Zaria?



Me yake da shi? Me zai baki? Duk abin da zai baki daga aljihun ubanki zai fito. Wannan shine abin da kike

ganin kin yiwa rayuwarki daidai?” Tana share hawaye ga mamakin Hajiya Zainab sai ta bude baki muryarta na rawa ta ce, “Mami ni ba ruwana da kudi, matsayi ko mukami, face abin da zuciyata ta aminta da shi. Ni ba kin Ya Imam nake yi ba, kawai dai ba zan iya auren shi ba, don ganin shi nake tamkar dan’uwana da muka fito ciki daya.



Ki yi hakuri Mami ki sanya min albarka, domin Deen nake so, shine zabina.....”.



Mami sai ta saka salati, kafin ta fashe da kuka. Yau tana fada Safah na mayar mata a kan da namiji da baya da tabbas.



Ta ce, “Da gaske Safah ba za ki auri Imam ba?”



Ta ce, “Ku yi hakuri Mami, wallahi bana son sa da aure!”’.



Ta ce, “Ashe kuwa za ki sake wasu iyayen ba mu ba, muddin kika kafe a kan bakan ki. Yaron na dawainiya da son ki tun ranar da aka haife ki, amma

da abin da za ki saka masa kenan?



To wallahi ba da ni ba, wannan cin fuska da cin amanar.....”.



Safah ta ja shessheka ta ce,



‘““Wallahi Mami ban taba yaudarar Ya Imam ba, balle in ci amanar shi. Ko mail da yake mini Marwa ce take amsa mishi bani ba, duk wani hannunka mai sanda da zai nuna bana ra’ayin auren shi na yi mishi tun ma kafin in hadu da Zahraddeen.





Me zai hana ya auri ‘yar’uwata tunda na lura ita tana son shi?”



Haushi ya kashe Mami. Ta ce, “Kin fi shi ido ne, ko kin fi shi sanin da wanzuwar Marwan ya ce ke yake so? Tashi ki bani wuri tun ban yi mugun kalami a kanki ba’’.



Ta mike sum-sum-sum ta fice, a ranta tana cewa, “Ko duniya za ta taru a kanta ba za ta auri wanda zuciyarta ba



ta so ba’. aK ok 2K of



Karfe goma na dare Mami ta cimma

Daddy a dakin barcinsa yana sauraron rediyon BBC. Mami ta samu waje ta zauna ta yi jigum, ranta a jagule, zuciyarta a hargitse.



Kallo daya Daddy ya yi mata ya san yau wani abu ya sukurkuta mishi Zainabu-Abu. Ya rage rediyon ya taso daga mazauninsa ya zauna a gabanta. Ya mika hannunshi ya kama nata ya ce,



“Wa ya tabo min Zaynabu-Abu, uwarbiyu, mai tagwayen suna, mai tagwayen ‘ya’ya?”



Duk da bacin ran data ke ciki, saida ya sata dariya. Ta yi murmushi, wanda iyakacinsa fatar bakinta, ta ce,



‘Daddy kenan, kada ka ce min baka san abin da ke faruwa cikin gidannan ba? Ka taba zama ka yi tunanin dalilin sintirin Zahraddeen a gidannan a ‘yan kwanakin nan?”



Cikin faduwar gaba Ya ce, “Me ya faru? Na ganshi dai yana zuwa, amma ba zan ce ga dalili ba”.



Ta yi kwafa ta yi huci mai zafi ta ce,

“Wai Zahraddeen da Safah son juna suke!”’



Ya ce, “Gyara min kalaman ki Zainabu, ko dai Zahraddeen da Marwah?”



Ta girgiza kai ta ce, “Oh-oh! Yadda na fadi haka al’amarin yake. Baki da baki Safah ta gaya min nan duniya Zahraddeen take so”.



Daddy ya yi shiru, can kuma ya ce, “Wannan ai shirme ne, ki kwantar da hankalinki, zan gansu dukkansu”’.



Ran Mami ya baci ganin bai dauki abin da muhimmanci ba. Ta ce, “Ni dai ka ja mishi kunne, kada in kara ganin kafar shi cikin gidan nan da sunan wai ya zo wurin Safah yana hure mata kunne da_ wannan munafukar muryar tasa kamar ta basarake, Safah da miuinta, kuma ko babu ban ga me za ta ci da Zahraddeen ba.



Bakin rijiya....ba wajen wasan yara bane. Ban da rashin hankali ya dubi Uwargijiyarshi ya ce yana so da aure?

Saboda kankanba da neman wuce gona da iri ko saboda mene? Ai BABBAN GORO SAI MAGOGIN KARFE,...... kuma Tuwon Girma.... Miyarsa nama”



Daddy ya yi murmushi yana kada kai ya ce,



‘“‘Wannan ba hujja ba ce, ku mata ban san irin ku ba wallahi. Ni a wajena Zahraddeen mutum ne har mutum, mai nagarta, daraja da sana’ar da za a bawa aure.



Ba don maganar Imam ba, babu abin da zai hanani wanke Safah in ba shi ba tare da na yi la’akari da hujjojinki ba. Mutum da karatunshi da usuli da lafiya da addini da aikin yinsa, me ake nema a nagartaccen miji da ya wuce wannan?



Jarumi haziki irin Zahraddeen, mai zuciyar neman na_ kansa, mai kwakwalwa, kyakkyawar zuciya da halaye na kwarai, gaskia da amana, wadanda suka yi karanci ga matasan zamanin nan, wallahi ba don Imam ba,

zan baiwa Zahraddeen Safah ba tare da na ji ko da dar ba”.



Mami ta kama baki cikin mamaki. Cikin takaici ta ce,



‘Kenan kana nufin babu matakin da za ka dauka? Idan aka yiwa Imam haka anyi adalci kenan?”



Ya ce, “Ni ban ce miki na amince ba, hujjarki kawai na soka (criticizing). Na ce dake zan gansu, ki bi komai a hankali, ki cire bacin rai, fushin fari ba naki bane, tunda ba ke za ki yi mata zaman auren ba”’.



A wannan daren Mami ba ta yi barci ba, yadda ta ga rana haka ta ga dare. Ita kam duk haushin Daddy ya rufe ta, me Safah take nufi? Da wacce fuska za ta dubi danta Almustapha idan Safah ta watsa musu kasa a ido? A washegari Safah ba ta ga walwalar Mami ba, ta daure mata sosai. Da Marwa take sabgoginta, itama sai ta kama kanta, ta killace kanta a daki tana rubuce-rubucen ta.

Sai dai zuciyarta cike take da tsoron Mamin, idan ta tuna marin da ta sha jiya. Ba ta taba ganin bacin ran Mamin irin jiya ba.



Har kullum ita cikin kauna take nuna musu komai, ba ta taba _ tunanin Mamin na da zafi har haka ba. Ta yarda ta amince akan Imam, Mami zata iya batawa da kowa hada dasu ‘ya’yan cikinta kuwa. Don har fadi musu take



“kafin in sameku shi na samu, a lokacinma dana riga na fidda rai da samun ‘ya’ya. Sai ya zamo wani irin nagartaccen Da, mai debe min kewar ‘ya’yan da bani da su. Don haka zuwanku bai rage komi daga kaunar dana ke yi masa ba. Sabida ya maye min gurbin ‘ya’ya goma, a lokacinda banida ko daya!!!



Balle ke kuma na haife ki ne kawai, amma bansan kashinki ba _ bansan fitsarinki ba, sai shayarwa ta dan lokaci, wadda ciyarwar dashi yayi miki da madara ta fita tsaho”’.

Karfe takwas na dare Zahraddeen ya zo, Mami na falo cikin seater tana sauya tashar MBC zuwa Aljazeera. Tun daga jin sallamar shi ta bi ta daure fuska irin yadda ba ta taba yi masa ba. Ya zube gwiwoyinsa a kasa yana gaishe ta, ta kafa mishi ido ba ta amsa ba. Karshe sai ta mike ta shige kafar benen da za ta sada ta da dakin barcinta, ba tare da ta ce da shi komai ba.



Daga shi har Safah gwiwoyinsu suka yi sanyi, ita Safah ma kunya ce ta kama ta. Aka rasa mai fara yin magana a cikinsu.



Daga baya Zahraddeen yai ta maza, ya yi murmushi cikin basarwa ya ce, “Mun yiwa Mami laifi halan?”



Ta yarfar da hannu, ta lumshe ido “Tun jiya haka take, na kasa gane mata’.



Ya yi shiru cikin tunani,

Please Login or Register in order to submit comment