Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

a zuciyarka,fitowa da shi fili zai iya janyowa mutane su tsane ni."

Ya ɗago ni sosai, "Su tsane ki,su waye mutanen? Wa ya fara canja maki fuska? Gaya mini,kina so in sa duk a kashe su?" Na yi saurin rufe bakinsa cikin tashin hankali, kamar yanda na ga har ya rikiɗe mini ya koma Yariman farko.

Na yi sauri na sulale ƙasan mota tare da riƙe hannuwansa.

"Za ka yarda da duk abin da na faɗa?"

Ya ɗaga kansa.

"Wallahi ba wanda ya taɓa canja mini fuska, kowa na sona kamar yadda ka ke sona. Ina son cewa da kai ka rinƙa ɓoye na ka ne ka bar ni in dinga fito da nawa a fili."

Sai naga yayi ajiyar zuciya, amma kuma ya kasa magana, sai da ya ɗago ni ya rungume gam, tsayin minti biyu, sai na ji yana magana cikin sanyin murya.

"Yasmin ba ki san yanda nake jin ki ba a zuciyata. Kin ɗauka wasa nake ko?"

"A'a na san..."

Ta yi daidai da buɗe motar da aka yi, ya yi sauri ya rufe cikin ƙiftawar ido, jikinsa kuwa tun a lokacin ya kama rawa. Na gyara sannan na ji ya ɗan ƙwanƙwasa gilashin motar, cikin gaggawa aka buɗe mana ta ɗaya ɓangaren, na fito, shi kuwa ta ɓangaren da yake. Sai a lokacin na fahimci gidan Aunty muka zo,gudun kada in ruga in baiwa kaina kunya da uban gidana yasa na tsaya tafiyar wahainiyar da muke ni da Yarima.

Falo kawai muka isa na dinga kwala mata kira. A firgice ta fito daga ɗaki, na ƙarasa da saurin guduna na rungume ta. Ita kuwa sai dariya take yi,tana cewa in sake ta taryi baƙon ta.

Mun samu sama da mintuna ashirin a gidan Aunty Salwa,sannan muka yi sallama da ita, wanda har alƙawari ya yi mini a gabanta zai kawo ni in yini in mun huta. Na dinga murna. Ganin jikin Yarima a sanyaye yasa har na fara shiga damuwa, na matsa na kama hannunsa tare da durƙusawa a ƙasan mota.

"Honey,me ye ya tayar maka da hankali? Wa ye kuma? Nima fa zaka jefa ni cikin damuwa?"

Ya ɗago ni ya zaunar da ni a saman cinyoyinsa, sai da ya sumbaci laɓɓana, sannan ya cire gilashin fuskarsa.

"Ke ce Yasmin, hankalina ya tashi matuƙa a kan ba ki da lafiya, amma ki ka ƙi gaya mini. Yanzu me iyayen ki zasu ce? Bana kulawa da ke?"

"Wallahi ni kaina ban san dalilin yin amaina ba,ni dai na san lafiyata ƙalau. Ni dai zan iya cewa ƙamshin turaren Daddy ne ya saka ni amai, kuma yanzu ni lafiyata ƙalau, zan iya yin komai, zan iya cin komai."

Na koma na ƙwanta a ƙirjinsa, "Kada ka ƙara damun kanka a kaina."

Sai na ga ya ɗago ni ko kasa me zai yi mini ya yi, sai kawai na ga ya dungure mini goshina.

"Kada ki ƙara faɗa mini haka."

A take ma sai na ji ya ba ni dariya. Na sa dariya irin ta nutsuwa, ya rungume ni, shi ma ya yi tasa dariyar irin ta su ta mulki.

A hankali na ga gilashin motar mu na sauka, wannan yasa na yi saurin sauka daga cinyar mijina na gyara zamana sosai. Subhanallah! Jama'a ne tamkar su ɓall gidanmu, tun daga get ɗin gidajen har izuwa harabar gidan mu. Jinjina ake yi, gaisuwa, amma yau Yarima ya burge ni, saboda ɗaga masu hannu da yake yi har da murmushinsa, mutumin da ba ya ko motsi idan ya shiga motar nan, to balle ma an canja wata motar wacce za ta iya ƙara masa girman kai, amma abin mamaki yau har da murmushinsa.

Motar mu na tsayawa na hango wani mutum a tsaye,shi kam tamkar wani saboda yanda na ga an zagaye shi. Sakan ɗaya da tsayawarta aka buɗe mana,kirari irin wanda ake wa Sarakuna, shi aka dinga yi wa Yarima. Gaisuwa da sauran hidimomi irin na sarakuna.

Wani abin da ya fi burgeni, shi ne wannan mutumin da ke tsaye tsakiyar nasa dogarawan, shi na ga an yi saurin kawo aƙwatin kuɗi a gabansa, aka buɗe masa irin na matafiya,brief case. Yana ɗaukar bandir sai dai ya ɓalle ƴar takardar ya watsa su. Amma mutanen mu ko matsawa ba su yi ba, ballantana su san ana zuba kuɗi a gabansu. Sai dai ma dogari ɗaya da yake gabanmu yana share su gefe,gudun kada mu taka. Wannan kuma ina jin dokar Yarima ce,sai ma a lokacin na lura cewa ƴan ɗari bibbiyu ne ake wa wannan watsin da su.

A nan na saki da sha'anin Yarima, wato har dogarawansa ma ya san yanda yake tafiyar da su. Wani abin mamaki Yarima bai tsaya wajen mutumin nan ba, ya yi wucewarsa, sai me? Ai tun daga barandar gidana na ga gidana ya canja. Ƴan matan gidana kuwa, duk sun taru a barandar, suna hango ni sai murna. Ni kaina duk sai na ji na ƙara ƙaunarsu. Mansura kuwa har da gudunta, ta iso ta durƙusa gabana ta kama hannuna. Na yi murmushi na ɗago ta, sai tasa kuka. Na yi murmushi na kama hannunta muka tafi.


#####
[2/19, 22:29] Ummi Tandama😇: *ƘASAITA BOOK 3*


*NA*

*MARYAM KABIR MASHI*


Page 3


Lallai Yarima " Na faɗa a zuciyata,ganin duk ya ƙyale mutanen da ke bin bayansa ya biyo ni gidana. Sai dai na ga ya yi wa wani dogari nuni da hannunsa. A take na ji dogarin na cewa.

"Yarima ya ce a jira shi ya huta. Yarima na gaishe ku. Nan da awa biyu zai fito."

Me zai faru? Ina kunna kai a gidana, na ji wani ƙamshin turaren wuta na tashi. Nan take kaina ya fara juyawa. Cikin ɗan sauri-sauri muka gaisa da jakadiya da jama'arta. Haka shi ma Yarima na ga yana gaisawa da su. Ko lura ya yi,ai muna hawa sama a guje na ƙarasa banɗaki. Yarima na bina shi ma tun kafin in kai ɗan wajen alwala,bath amai ya kubce mini. Alkyabbar jikina kuwa sai dai wata.

Yarima riƙe da ni na dinga ƙwaranya amai kamar dai yanda na yi a gidanmu. Nan take na ji Yarima na waya cikin mutanen shi na ji ya yi wa ɗaya magana. Wai ina likitan da ya ce ya zo gida ya jira shi?

Nan take na ji yana cewa,nan da minti biyar ya hayo sama da sauri yana son ganinsa. Ni kuwa har amai ya kai sai dai ruwa-ruwa, saboda abincin ya ƙare.

Ina gamawa Yarima ya kama ni wanda jikinsa har rawa yake, ya cire mini alkyabbar jikina, ya wanke min fuska. Ban da sannu da yake yi mini, ya ɗago ni idanuwansa sun yi ja, ban da hawayen da suka cika su, ya dinga shafar fuskata. Lallai na amince Yarima son gaskiya ne a jikinsa, saboda ya rasa me zai ce mini. Ya kama ni muka fito ɗakina, ina fitowa wani sabon aman ya taso. Na koma ciki da guduna. Ya biyoni ya yi tsaye a kaina, ina ta faman yunƙurin aman da ba komai a cikina.

"Mama Yasmin zata mutu ta bar ni. Ki zo Mama."

Wannan maganar da ya yi ita ta tabbatar min waya ce ya yi, duk da ban iya ɗaga kaina na kalleshi ba.

"Ka hawo kawai." Wannan ya tabbatar mini da likita yake. Da sauri na ga ya fita, sai na ji yana cewa, "Shigo nan ka ganta. Sau uku kenan tana yin shi a yau,kaga har ya zamanto ba komai a cikinta, kalli yanda take?"

Likita ya sunkuyo, "Sannu Madam." Na ɗaga kaina kawai."

"Me ke saka ki amai?"

Na ɗaga masa hannu alamar ya jira, suna tsaye,Yarima na ta safa da marwa a banɗaki. Har tsayin mintuna goma, sannan na ɗago, wanda a take na ji jikina na rawar zazzaɓi. Ban da jiri da nake gani.

Yarima ya riƙe ni muka fito ɗaki. Muna fitowa na yi saurin komawa banɗaki.

"Yarima bana son warin turaren wutar nan, kaina juyawa yake yi."

Nan da nan ya kuma ruɗewa, "Doctor, ya za'ayi?"

"Yallaɓai ko a tafi da ita sashenka mu gani."

"Haka za'ayi."

Da sauri na ga ya buɗe ƙofar, bayan wacce za'a fita barandar baya, wacce ke kallon ta gidan Yarima, sai da ya buɗe, sannan ya kamo ni. Muna fita madadin in ga fili kamar da, sai na ga an gine ta, ta yi wani zagaye kamar ƙaton fayif na ruwa, ga fulawoyi na gaske nannaɗe da jikinsa.

Ban iya tsayawa na lura da yanda aka yi ta ba sosai, ni dai na ga muna tafiya har mun ɓulla ƙofar barandar Yarima. A take na ga ya buɗe mun shiga, sai na ga ɗakin Yarima. Yana isa ya ƙwantar da ni a gadon shi, ya janyo bargo ya lulluɓa mini,sannan ya koma ga kaina ya zauna, inda likita ya matso ya tsugunna gabana.

"Madam kamar me ki ke ji yana yi miki ciwo.?"

"Zazzaɓi, ciwon kai, sai amai."

"Mara fa,ko ciki?"

"A'a."

"Yanzu za ki iya tuna ko ƙwana nawa rabon ki da al'ada?"

"Likita bana son irin waɗannan tambayoyin fa." In ji Yarima.

"To Yallaɓai an bar su, sai dai ina son fitsarinta, yanzu zan je in dawo. Awa ɗaya za ka bani."

"To ya za'ayi a ɗebi fitsarinta,in ba ya ga rashin hankali irin naka?"

"Allah ya ja da rai,ga ƴar ƙwalbar da za ta yi a ciki ta bani. Yanzu zan tafi da shi, zan yi wani ɗan aiki ne da shi. Wannan kuma jininta za'a ɗiba.

Ya fito da sirinjin ɗaga aƙwatin hannunsa, sannan ya ɗauko wani abu yasa a kunnanshi, sai na ga ya ɗaure mini hannu da wani abu kamar balt (belt).

"Ba hawan jini, Yallaɓai,a taimaka a bayar da jinin da fitsarin." Ya janyo sirinjin zai ɗauki jini. Yana sa allurar na ɗan yi ƴar ƙara.

"Ka bi a hankali fa,in har da ciwo ka barshi kawai."

"Ai an ɗauka ma, sannu." Ya kama ni ya kai ni banɗaki, sai da muka isa ya tsayar da ni, ya tallabe kumatuna, ya dinga shafa su. Da gani ya rasa me zai ce sai kawai na ga ya haɗa bakina da nasa yana tsotsa, ya sake ni.

"Ya zan yi Yasmin?"

"Bana jin ciwon fa."

"Ga jikinki nan da zafi, ga shi har jikinki ya yi laushi." Ya sake ni ya fito kawa.

"Ina fitowa da ƴar ƙwalbar fitsarin a hannuna ya yi sauri ya tarye ni ya karba.

"Tashi likita." Ya kalli agogon hannunsa, ƙarfe huɗu da rabi.

"Nan da biyar da ashirin ina son in ganka cikin gidan nan."

Da rawar jiki likita ya karɓa ya tafi yana cewa, "Insha Allahu Yallaɓai, alheri ne."

Ni ke ƙwance, lulluɓe da bargo, shi kuwa tsugunne a bakin gado, yana ta faman shafa mini fuskata da bayan hannunsa, na mayar da idanuwana na lumshe, sai na ji yana cewa.

"Yasmin." Da sauri na buɗe ido, sai na ga ya yi ajiyar zuciya.

"How do you fell?

"Da sauƙi."

Ana haka Mama ta shigo har da Hajiya Kilishi da wasu su uku. Ya yi saurin taryarsu.

"Mama ga ta nan,zo taɓa jikinta ki ji."

"To mu je." Suka iso gabana.

"Yasmin ya ya jikin?"

"Taɓa jikinta ki ji Mama."

"Na gani ma ba sai an taɓa ba, likita ya zo?"

"Yanzu ya tafi, amma yanzu zai dawo."

"To shi kenan, bari mu jira dawowarsa, sannu Yasmin."

Na ɗaga kai, dukkansu ma suka yi mini sannu, sannan na ji Mama ta ce bari su zauna a nan falo, shi kuwa cewa yake.

"Mama kada ku tafi fa, Mama mutuwa za tayi?.

"A'a."

"Za ta tashi."

"Eh." Ta juya suka tafi. Ko awa ɗaya ba a cika ba, sai ga likita ɗauke da wata ƴar talabijin ɗin ƙwamfuta da shi da wani ɗauke da wasu tarkace a hannunsa. Ya shigo, ya gama jonawa cikin mintunan daba su wuce biyar ba, sannan ya iso wajen Yarima da yake tsaye a kaina." Yallaɓai muna son za mu ɗauko hoton marar ta kawai."

"Bismillah."

"Tsaya ina zuwa." Ya iso ya janye rigata a hankali, tare da rigar ciki ta shimi. Cikin ƴan mintuna ya ce ya gama.

"Me ye."

"Bari mu yi magana da Hajiya, tana falo."

Ya juya ya fita. Cikin mintuna biyar ya leƙo ya ce zai tafi,yana fita su Mama suka shigo.

"Yasmin mu mun tafi, Allah ya bayar da lafiya."

"Mama me ye wai.? Me likita ya ce muku?"

Ko nima sai na ji gabana na faɗuwa da sauri da sauri,cutar me gare ni kuma? Na tambayi kaina. Tambayar da Yarima ya ƙara yi wa Mama ita ta mayar da hankalina gare su.

"Mama don Allah ki gaya mini?"

"Wai me yasa baka tambayar Hajiya ga ta nan sai ni da ka raina? Ku mu je ku ƙyale su." Suka yi gaba abinsu, sai ya bi Hajiya.

"Hajiya me ye?" Sai da ta kusa isa ƙofar fita, sai na ga ta tsaya. Bana jin abin da suke faɗa, amma ni tuni har gefen filona ya jiƙe da hawaye, balle yanda na ji amsar da Mama ta bayar.

Ina kallon su shi da Hajiya, sai na ga ya dafe ƙirji duk hannu biyun,can kuma na ga ya durƙusa ƙasa da gwiwoyinsa duk biyu.

Amma sai na ga yana dariya, ya ɗaga hannu sama, ita ma Hajiya ta yi waje tana dariya. Tana fita, na ga ya rugo a guje ya faɗa saman gadon, cewa yake.

"Allah kana ƙaunata, da za ka ƙara mayar da Yasmin ta zama tawa har abada."

Ya wuntsulo ƙasa ya tsugunna, sai na ga ya janye bargon jikina, ya ɗaga cikina ya shafa fatar shi, ya sunkuya ya sumbace shi. Ya ɗago ga fuskata, ya goge hawayen da yake ta ƙwarara a gare ta.

"Yasmin na rasa da wane baki zan yi miki godiya."

Ya sumbaci goshina, ya dawo ya shafa cikina.

"Yasmin abin farin ciki ya same mu ya ya zan yi miki bayanin shi?"

Ya ɗago ya ƙura mini idanuwan nan nasa masu firgita ƙaramin yaro. Ya ɗago cikina sosai ya rungume shi, tare da ƙwantawa a saman sa.

Ya ɗago, "Baby na ne a nan Yasmin. Na zama Daddy daga yau, kada ki ƙara kira na da Yarima, sai dai Baban Yarima." Ya kanga kunnensa.

"Lah! Yasmin,kin ji wai ƴan biyu ne."

Nan take na gano me yake nufi. Kunya ta yi saurin dirar mini. A take na tambayi kaina, kenan ciki gare ni? To ni ya zan cewa Daddyna,in ya ganni da ciki?.

Ya matso ya ƙwantar da fuskarsa a tawa,na rufe fuskata, ya yi murmushi ya sumbaci kumatuna, tare da faɗar.

"I'm proud of you." Ma'ana "ina alfahari da ke."

Sannan na ji ya miƙe tsaye, ina kallonsa ta tsakankanin ƙofar yatsuna ya fita daga ɗakin. Tsayin mintuna biyu ya yi, sai ga shi ɗauke da ɗan faranti a hannunsa, ya zauna bakin gado tare da ajiye farantin da tree top ya ɗago ni, sai da ya matsa mini na sha, sannan ya ba ni magani ƙwaya ɗaya na sha, na koma na ƙwanta.

Ƙwanciyata ta yi daidai da wata ƙara mai ƙarfin gaske kamar ƙarar bindiga. Ban da ihu da muka ji mutane na yi. Ba Yarima da ke zaune ba,ko ni dake ƙwance ina fama da zazzaɓi, sai da na miƙe cikin sauri. Gaba ɗayanmu sai ga mu tsaye jikin taga, ban da ƙura da ta turnuƙe wajen.

Bayan kamar mintuna uku, sai muka ga ƙura na washewa a hankali. Ganin wani mutum muka yi a tsaye zagaye da shi, ana ta watsa kuɗi, jama'a na ta tsinta. Yarima ya juyo ya kamani.

"Zo ki ƙwanta, bari na sauka ƙasa na dawo."

"Ka turo mini jakadiya." Ya amsa da to. Ya yi waje.

Cikin mintuna sha biyar sai ga jakadiya a nan nake tambayar ta me ke faruwa? Bayan gaisuwar da ta yi mini,a nan take ba ni labari wai wani ɗan Sarki ne ya zo, tun ba mu daɗe da tafiya ba. Ba yaudarar da ba ya yi a gidan nan, shi ne rabon kuɗi, abinci da sauran kayayyaki, duk wanda aka kaiwa ya ƙi karɓa, to zai faɗa ne. Take gaya mini ko ita an bata magani ta zubawa Yarima a abinci da sauran wurare.

"Kin karɓa?"

"Eh, saboda in ka ƙi karɓa sai dai a wayi gari ba kai."

"Ɗan Sarkin wane gari ne?"

"An ce babban Yayan su Yarima ne,wai shi Abdulrahman."

Na yi shiru. A nan take na tunano labarin da Mama ta ba ni, ina cikin wannan tunani sai ga Yarima ya shigo da saurin shi.

"An kashe mutum uku a wajen can."

"Me ye dalilin kashe su?"

"Wai saboda sun ƙi ɗibar kuɗin da yake sa wa ana watsawa."

"Wa ye shi?"

Wai Yayan mu ne."

"Meye dalilinsa na yin haka?"

"Sarauta yake so."

Na yi shiru tare da faɗuwar gaba mai tsanani saboda tunanin kada a kashe mini mijina.

Canja alkyabbar jikinsa ya yi, ya ƙara sa turare a jikinsa.

"Ina za ka?"

"Wa je." Na miƙe da sauri.

"A'a kada ka fita ya harbe ka."

Ya yi murmushi.

"Ai mu ba'a kashe mu ta nan ɓangaren."

Ya nuna jakadiya da ɗan yatsa.

"Kin ga wacce za ki danƙawa amanar mijinki nan. Sai kuwa masu dafa mini abinci, ta sanadiyyar su ake yi mini komai."

Ya iso inda nake tsaye, ya tallafi kumatuna, cikin nutsuwa ya fara magana.

Kada ki tayar da hankalinki,ki yi tunanin cewa kina da yaron ciki, zai iya zuɓewa ta kowanne hali,ki ƙwantar da hankalinki."

Hawaye suka ƙarasa gangarowa.

"Ni dai ban yarda ba."

Ya yi murmushi, "Yasmin kada ki karaya mana. Ki tuna gidan sarauta fa ki ke. Haba Honey."

Na ƙwantar da kaina a ƙirjinsa, sai kuka sosai. Ya ɗago ni ya ƙura mini ido ba tare da ya yi magana ba. Ɗan tsayin minti ɗaya, sai kawai na ga ya mayar da ni ya rungume ni sosai. Ya ɗago ni da saurinsa ya sumbaci goshina, ya dawo ya tsotsi bakina,bai ce komai ba ya ɗauke ni cak ya ɗora a gado. Ya ja bargo ya lulluɓe ni, ya sunkuyo yana gyara gashin kaina, wanda ya zubo a fuskata,ko in ce wanda ya hautsine saboda ƙwanciya.


#######
[2/20, 13:07] Ummi Tandama😇: *ƘASAITA BOOK 3*


*NA*

*MARYAM KABIR MASHI*


Page 4


Ya ƙara sumbatar goshina, kawai ya juya ya tafi. Bin shi na yi da kallo, shi yasa idanuwana suka gane mini ba jakadiya a ɗakin nawa. Yana fita tana shigowa na mayar da kaina na ƙwantar,sai na ji hawaye sun ƙi tsayawa. Jakadiya ta iso ta tsugunna gaban gadona.

Allah ya ja da rai,ai ke ce ya kamata a ce kin ƙara ƙarfafa masa gwiwa tare da shawarwari, ke ce mace,kin fi shi tausayi, ke ya kamata a ce kin tsaya kin lura da tambayar me yakamata a yi wa talakawa,shin hukuncin da bai cancanta ba a yi shi?"

Na tashi zaune. "To yanzu jakadiya,kina jin ya ce an kashe mutum uku, wacce kuma daraja gare shi,ai kin ga bai dace ba ya fita, sai ya tsaya ya ga ya zata kasance."

Ta yi murmushi, "Yana shugaba? Ai shugaba bai ga ta zama ba, ke dai kiyi ƙoƙari ki koyi dabarun taimakawa mijinki da shawarwarin da zai sa jama'arsa ta bi shi, ta kuma ƙara ƙaunarsa."

"Kin san su ne ke? Saboda ni kin ga ba ƴar sarauta ba ce ba,haye min tayi da rana tsakiya. Kin ga kuwa ba zan san komai ba game da ita."

Jakadiya ta yi murmushi, ta ƙara gyara zama. Tun da ta fara magana nake tallaɓe da kumatuna, saboda al'ajabin abubuwan da take faɗa. Wannan ne yasa a take na ɗauki waya na daddana, domin neman Yarima, saboda fara gudanar da dabarar ta farko cikin dabarun da jakadiya ta koyar da ni. Amma ina! Hayaniya ta yi yawa,ko ƙarar ta ma ba ya ji. Wannan yasa na yi haƙuri sai ya dawo gida, na umarci jakadiya da ta je tasa a sa fanka a kori duk warin turaren da suka saka a gidana. Na bata room Freshner gidan Yarima na ce a sa mini ita.

Yariman bai samu shigowa ba sai ƙarfe tara da rabi na dare. Cikin nutsuwa ya zo ya zauna gefen gadon da nake ƙwance, ya sunkuyo ya sumbaci laɓɓana.

"Sannu da dawowa."

"Ke zan yi wa sannu, ke da na barki ba lafiya, na so shigowa in ga jikinki,amma ina, na so in gaishe ki ko da a waya ne, amma duk hakan ba ta samu ba, sai yanzu ma na ga kiran ki a wayata, missed call,ki yi haƙuri ban ji ba."

"Ba komai. Yaya komai dai ya tafi lafiya?"

"Eh, to hakan nake tsammani."

"Wai me ye ya faru?"

"Wani mutum ne ke neman tayar mana da fitina, shi ne na sa aka kama shi har da yaransa, wajen goma, bayan an kama su ne na turawa Mai Martaba Sarki da aiken cewa ga masu son tayar da zaune tsaye an kama. Kafin Mai Martaba ya iso shi ne nasa aka tara jama'a na basu haƙuri da dai bayanan da zai kwantar masu da hankali." Ya koma ya ƙwanta rigingine,saman jikina.

"Kin san ko waye mai son haɗa mana rigimar nan?"

Na ce "A'a." Cikin sanyin murya.

"Wanda na gaya miki ne wai shi Abdulrahman,wai ɗa ne ga Mai Martaba, amma baya son ma a na faɗa, saboda ko a yanzu ma bai bayyana ba,ba kowane ya ji ba. Ni ma waziri ne ke gaya mini."

Ya yi ɗan shiru. "Dama ni Mama ta taɓa ba ni labari cewa akwai su,su biyu ne ma har da Yayarsa. Yanzu dai Mai Martaba ya ja masa kunnansa cewa idan ya ƙara jin labarin ya zo garin nan sai yasa an kashe shi."

Na shafa gashin kansa, "Ka ƙwantar da hankalinka, ba ka tambaye shi cewa me yake so ba.?"

"Sarauta." Na ɗan yi saurin alamun tashi haɗe da tambayar.

"Sarauta ta me?"

"Ta Mai Martaba."

"To kai fa?" Ya yi murmushi, "kina son sarauta ne? Aƙwai wahala fa." Na ɓata fuska sosai.

Ya ƙara yin murmushi, "Yasmin kenan,ki ƙwantar da hankalinki,komai ya wuce, ina nan a matsayina na Yarima mai jiran gado, har da Babyna."

Ya faɗa yana lakatar mini hanci. Kunya ta kama ni. Na yi saurin tura kaina filo, shi kuwa ya kama ƴar dariya irin tasu ta sarakuna. Ya turo kansa cikin filon.

"Yauwa." Na yi saurin fito da kaina daga ƙarƙashin filon na yi alamar tashi da saurina.

Ya yi saurin mayar da ni ya zaunar, tare da riƙe min kunne.

"Kin manta ne ki ke tashi da sauri haka?" Ya ɗaga rigata ya sunkuya ya sumbaci fatar cikina, ya ɗago ya tallabi kumatuna tare da ƙura mini ido.

"Yasmin! Yasmin!!" Ya girgiza kansa.

"Ba zan taɓa iya ƙwatanta yanda nake jin ki ba a raina,son da nake miki yafi ƙarfin duk wani ƙaramin misali."

Na rausayar da idanuwana, waɗanda na ji sun aiko da hawaye. Mayar da su ɗin da na yi na runtse ya yi daidai da gangarowar su saman kumatuna,ni kaina ban san dalilin zubowar su ba, sai dai na ji zuciyata ta yi mini sakayau, ba nauyi. Na san ba abin da take so sai Yarima, mutumin da nake jin ya gauraye jinin jikina gaba ɗaya.

Hawayena kuwa sun tsiyayo ne ta dalilin wani abu da na ji yana yi mini yawo a tsakiyar kaina. Cikin sakan ɗaya na ga ya ruɗe,ruɗewar da take tayar mini da hankali. Gudun kada ya yi saurin fassara hawayena yasa na koma a hankali na ƙwanta a ƙirjinsa, zuciyata na son gaya masa cewa son da na ke masa yanzu ba zai taɓa misaltuwa ba, amma kunyarsa da nauyinsa sun hana ni sai dai na kurɗa kaina a wuyansa, na ce.

"I love You." Cikin sigar raɗa.

Ina jin shi ya ƙara matse ni a jikinsa,sam ban yi zaton ya ji ni ba, sai na ji ya ce "I love You too." Kunya ta sa na mayar da idanuwana na lumshe. Bai fi mintuna biyu ba na yi ƴar dabara na ƙwace jikina, saboda na san halin Yarima, sai mu ƙwana a haka. Na yi ɗan hanzari.

"Jira ina zuwa, na yi mantuwa." Na sauko daga gadona. Har na yi taku uku ya kira sunana, juyowar da zan yi sai na ji ya ce "I Fancy you."

Na yi murmushi na yi gaba. Faranti ne na shigo da shi ɗauke da abinci, har na ajiye farantin ban ga Yarima ya motsa ba, na yi sanɗa na iso inda yake, ya yi kwanciyar nan tasa, tausayin shi ya kama ni. Ganin kafin in je in dawo har ya yi bacci, na sunkuyo na sumbaci goshinsa, ya buɗe idanuwansa a hankali ya yi murmushi.

"Na gaji."

"I know,sannu ga abinci nan na kawo maka."

Na riƙe hannunsa duka biyun.

"Ta so ka ci." Ya miƙe tsaye a inda na yi gaggawar taimaka masa ya cire alkyabbar jikinsa.

**** **** ****

Lallai

Please Login or Register in order to submit comment