Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kam ni na zama ƴar gata gaba da baya, balle da cikin nan na jikina ya tsufa. Sarki, Mama, Hajiya, Daddyna, Mamee duk ba sa son abin da zai taɓa ni, wanda kullum sai Sarki ya aiko waziri ko jakadiyar sa tazo ta ga lafiya ta. Mamee kuwa, sai dai waya. Dad kuwa ya zo gidana ya kai sau uku, ba wai don ya ganni ba,idan ya ga Yarima sai ya koma. Shi kansa Yarima ya kasa gane kan Daddyna, saboda ko an ce ya shiga ba ya shiga, sai dai ya ce gaishe mu ya zo yi.

Shalelena kuwa, kullum ana manne da ni,ko fada ma sai na yi da gaske yake sauka, Kaɗan-kadan kuwa ya hayo sama balle in ina ɓangaren gidansa,in kuwa na gidana ne, idanuwana na ga barandar gaba wacce ta koma hanyar zuwa ɗakinsa.

Amma wani abu ƙwaya ɗaya da yake damun zuciyata, shi ne yanda gaba ɗaya suka raja'a da cewa namiji zan haifa, ba sa maganar mace ƙwata-kwata , wannan abu na tayar mini da hankali, ballantana idan na ga Yarima ya ɗaga cikin nawa yana sumbatarsa,yana faɗin ɗan shi ya kusa isowa duniya. A take sai na ji hankalina ya tashi, wannan ne ma yasa wasu lokuta na kan yi shiru tamkar na fita daga hankalina na ƴan mintuna.

Buɗe ƙofa da na ji yanzu ma ita ta dawo mini da hankalina, na gyara kishingiɗar da na yi a saman kujerar falon samana, na juya na kalli Yarima wanda ya fito daga ƙofar ƙuryar ɗakina,su Mansura suka yi saurin russunawa suka yi gaisuwa, sannan suka miƙe domin sauka ƙasa.

Ya iso ya tsugunna gwiwarsa ta hannu a saman cinyoyina, "Honey,na bar ki ko?" Ya ɗan yi tsaki.

"Wallahi Mai Martaba ya ƙi yarda, da yanzu muna can, tare da ke kullum."

Ya sunkuyo sosai, "My boy,how are you today?" Yasa hannu ya buɗe cikin kamar yanda ya saba, ya sumbace shi ya mayar da kansa ya ƙwantar a jikina.

Na sunkuyo na sumbace shi, gashin kaina duk ya rufe mu gaba ɗaya. Na ɗaga kaina sannan na ɗago shi.

"Yarima in tambaye ka mana?"

"Ƙwarai kuwa."

"Me yasa ba ka son a haifar maka mace?"

"Me ki ka gani?"

"Ban taɓa jin ka ambaci mace ba,ko ba ƙwa son a haifar muku mata?" Na yi shiru kaɗan.

"Yanzu in na haifi mace ba zaka zauna da ni ba?"

Sai kawai idanuwana suka ciko da hawaye. Ya miƙe tsaye ya zo ya zauna kusa da ni, wanda hakan yasa na saukar da ƙafafuwan ƙasa. Ya kamo hannuna ɗaya ya riƙe da hannayen shi duk biyun ya fara wasa da ƴan yatsun hannuna,a daidai lokacin da ya fara magana.

"Yasmin kin san dai mutum ba ya haihuwar wata halitta wacce ba mutum ba ko? Sai dai ya haifo nakasasshe ko marar lafiyar jiki,ko wanda halittarsa ba ta cika ba,ko kuwa ma ya mutu a ciki ko?" Na ɗaga kaina.

"To wallahi Yasmin a ce ki haifo wata halitta ta daban,ko ɗaya daga cikin abin da na lissafa, wallahi ni na san ma na so shi na gama,ko da kuwa jama'a za su ƙi ni a kansa, saboda kawai ya fito ta jikinki, ta balle mace mutum. Yasmin ya zan yi naƙi mace, alhalin kin san mu mata rahama ne a gare mu.

Ki tuna ke mace ke kika canja mini rayuwata, ta zame mini abin so da ƙauna, abin sha'awa ga kowa. Ke mace ke kika ƙwantar mini da hankalina lokacin da ya tashi, ke mace ke ce kika rungume ni a jikinki a daidai lokacin da na wuce mahaifiyata ta rungume ni a jikinta.

Ki tuna ke mace, ke ce wacce za ta haifa mini ƴaƴana,ki tuna ke ce tsanin rayuwata gaba ɗaya,in kin ga dama ki ruguza min rayuwata, wanda duk duniya babu mai baiwa ɗa namiji daɗin rayuwa sai Allah da matarsa tagari,in kin so kuma ki gyara mini ita.

Yasmin ki ƙwantar da hankalinki a kaina,ki dinga haifa mini yarana,ko da kuwa duk mata ne, ina so. Wallahi ina so,ni na san dalilin ki,wai sarauta? Ba dole ba ne a ce dama ɗana ya yi sarauta,ko da kuwa duk maza na haifa har guda ɗari,in Allah ya so sai ya ba ƴaƴan ƙannena,ƙila ma wanda ba'a ɗakinmu ɗaya ba da mahaifinsa.

Dakata ma ki ji, wallahi ni yanzun tun da na same ki a matsayin matata, na ji komai na duniya ma ba na son shi sai ke, ke kaɗai nake so. Baki san ma ni cewa nake dama a baiwa Ahmad sarautar nan saboda in zama free man in dinga zama da iyalina a kodayaushe muna hira,muna jin ɗumin junanmu."

Ya ɗago ya kalleni, ya juyo sosai. "No! No!! No!!!." Yasa yatsunsa manya biyu yana goge mini hawayen da suka gangaro.

"Shi yasa na liƙewa Mai Martaba a kan ya bar ni na tafi da ke London, muyi rainon cikinmu a can, ya ƙiya mini,ba don komai ba sai don in zamo kullum ina kusa da ke, da na samu haka da wannan tunanin bai ma zauna a zuciyarki ba."

Ya ɗago fuskata muka haɗa ido, sai na ga ya lumshe ido ya buɗe a hankali, ya kai bakinsa ga nawa.

Mintuna biyu ya ɗauka a haka, na yi dabara na cire bakina daga nasa, sanadiyyar wasu alamomi da jikinsa ya nuna mini. Sai da ya ɗauki tsawon wasu ƴan mintuna yana fitar da numfashi a hankali, sannan ya koma ya zauna. Ganin shirun da ya yi yawa.

"Yarima ka manta da ka baro jama'a?"

Ya ɗago ya kalleni sosai, ya lumshe idanuwansa tare da ɗan mayar da numfashi.

"Yanzu zan tafi, ke ce Yasmin,ke ce."

Ya miƙe tare da ɗan shafar saman kaina, sannan ya tafi. Ni kaina na san ina samun kulawa ɗari bisa ɗari a wajen Yarima, da jama'arsa gaba ɗaya. Ban da iyayenmu da suke zirga-zirga a kan ganina. Ni kam yanzu na riga na san Allah ya gama haɗa mini komai, sai dai in yi godiya gare shi.



########
[2/20, 18:49] Ummi Tandama😇: *ƘASAITA BOOK 3*


*NA*

*MARYAM KABIR MASHI*


Page 5


Tun kafin a kira sallar Asuba idanuwana suka bushe, sakamakon jin cikina ya naɗe ya tattare waje ɗaya, ya hana mini sakewa. Ina zaune lafiya ƙalau, Yarima ya tashi ganina a zaune yasa na ga ya tashi zaune a firgicen shi yana tambayata ko lafiya? Kafin in bashi amsa ma har ya ɗauki wayar hannunsa ya fara daddana ta. Na yi sauri na ƙwace ta.

"Haba Yarima."

"Me ke damun ki?"

"Ba komai."

"Yana gan ki a zaune, kuma sannan ki ce mini ba komai."

"Tun da na ce ba komai ka yarda,cikina ne kawai na ji kamar an ƙulle mini shi waje ɗaya."

"Na yarda, amma kin san dai daga ni har ke ba wanda ya san wata alama ta haihuwa, saboda haka ki yi mini haƙuri in kirayo Hajiya Kilishi."

"Na yarda, amma ka jira na yi sallah tukunna,ka ga yanzu biyar da mintuna ashirin."

Da ƙyar ya amince, sannan muka tashi muka yi alwala tare, wanda ya yi mini sallama ya tafi masallaci.

Shida da ƙwata na asuba Hajiya Kilishi ta iso gidanmu. Yanda Yarima ke bin ta a baya na yi imani shi ya je ya ɗauko ta har gida. Ya iso ya zauna ɗan nesa daga gefen gado,ni kuwa kallona da shi ƴar harara da take nuna alamun ya yi laifi, bai wani kulani ba na ga ya mayar da hankalinsa ga Hajiya da ke ɗan yi mini ƴan tambayoyi.

Dole tasa ni in tashi tsaye, amma tsayuwa ta gagare ni, ni kuwa ba wani ciwon da nake ji,iyakacina dai ƙuguna ya riƙe gam, cikin jikina ya naɗe waje ɗaya. Ganin haka yasa na ji ta ce wa Yarima ya bugawa Doctor Franca waya, wacce ita ce likitan gidan Sarki, sai kuwa Doctor Harisu, mai duba maza,ko wani ciwo amma haihuwa sai Doctor Franca.

Cikin mintunan da ba su wuce ashirin ba sai ga Doctor Franca ta iso. Ina jin Hajiya na tayi mata bayani kamar yanda na yi mata. Cikin ƴar hikima irin ta su ta likitoci ta aiki Yarima akan ya ɗebo mata ruwa a ɗan wani abu, yanda na ga sun kalli juna ita da Hajiya shi ya tabbatar mini suna son ya ɗan ba su waje ne.

Ai cikina kawai ta dafa ta ce haihuwa ce, sai dai kuma miƙewa tsaye ma ba zan iya ba, ballantana in iya tafiya. Ana cikin haka Yarima ya shigo da wata tasa a hannunsa, ya ciko da ruwa, har bakinta. A nan ne take gaya masa haihuwa ce, amma sai an samo kujerar tura ta zuwa asibiti. A zuciyata na ce yanzu a haka za a kai ni asibiti? Ban ƙarasa tunanina ba sai dai kawai na ga Yarima na shirin ɗauka ta.

Kunya kam ta kama ni, amma ganin Hajiya Kilishi ba ta yi masa magana ba, yasa na lumshe idanuwana kawai. Jin an ɗan tsaya da tafiya yasa na buɗe idanuwana. Labulaye kawai na ga an janye, sai da na waiga ma sannan na gane falon sama muke,babu wata alamar ƙofa a wajen da suka buɗe labulan. Hajiya Kilishi kawai na taɓa wani ɗan makunnin kunna fitila, sai kawai na ga ƙofa ta buɗe.

Mamaki biyu ya dirar mini a daidai lokacin da muka shiga ɗakin, ban gama mamakin ƙofar ba sai kuma gani na dasa na ɗakin da muka shiga. Ɗaki ne wanda ba su da maraba da na asibiti. Gado biyu ne a ɗakin irin gadajen asibiti, sai daga can gefe ɗaya an saki wani koran labule. Abin ka ga ƙaton ɗaki, ban ƙarasa gani ba naji an ɗora ni saman gado, wata irin kunya ce ta saukar mini a take sanadiyyar sumbatar goshina da Yarima ya yi a gabansu Hajiya.

Madadin in ga ya fita, sai na ga ya zauna gefen kaina,ya sa hannu yana gyara mini gashin kaina, da ya baje fuskata,ko in ce ya baje ko'ina. Madadin in ji sun ce ya fita, sai dai na ga an sako wani ɗan koren labule, wanda ya sauka saman cikina, ma'ana ya raba tsakaninmu da su. Ni kuwa ta kwance sun raba ni biyu suke nufi kenan, kaina da gangar jikina ta sama ta wajen Yarima, daga cikina zuwa ƙafafuna suke wajensu.

Sam ni ban wani tsorata ba, saboda dama ita ke zuwa yi mini awo duk bayan sati biyu, sannan kusan duk ƙwana uku sai ta zo ganina, ballantana ma da cikina ya tsufa sosai. Shi kuwa ganin an yi haka, sai na ga hankalinsa ya tashi matuƙa, har da wani irin gumi da ke tsiyaya daga saman kansa. Ganin haka yasa na sa hannuna ɗaya na shafo kumatunsa, ya juyo sosai ya kalleni cikin sanyin murya, na ji ya yi mini magana.

"Da ciwo ko?"

Gaskiya ni bana jin wani ciwo ko ɗaya, saboda haka na girgiza masa kai alamar a'a. Hannunsa ɗaya da ke maƙale da nawa ya ɗago ya sumbata,ni kaɗai nake jin abin da ake yi mini,amma ba ni da damar nunawa, ganin yanda hankalin Yarima ya tashi.

Ba afi minti ashirin da kawo ni ɗakin ba na haifi yarona namiji, amma ni kaina na san cikin mintunan na fita daga kamannina, shi kuwa Yarima ya sha cakuma tamkar zan karya shi.

Ni kaina ban san duk jama'a sun san ina ɗakin haihuwa ba, sai da na fito. A nan ne na ga falon sama cike da jama'a. Ina fitowa kuwa bakuna suka dinga haɗuwa wajen yi mini sannu, ban da jakadiya wacce ta rangaɗa guɗa tamkar ta yi hauka don murna. Yarima ne ɗauke da yaron naɗe cikin jakar tawul ɗin jarirai, amma sai da jakadiya ta tsugunna ta karɓe shi daga hannunsa.

Ni kuwa na sha gayuna tamkar ba ni ce na haihu ba. Tun daga ranar kuwa shagali ya tashi, amma kuma Yarima yana liƙe da ni,in ka ga ya fita daga ɗakina,dangin mahaifiyarshi ne ko nawa, shi ma yana yi yana zagayowa.

Ana saura ƙwana biyu suna aka kai wa Mai Martaba jariri har gida, domin yi masa huɗuba, wanda taro suke yi na musamman idan za'a huɗubar nan, duk da dama ba ganin farko ba ne ba ga Mai Martaba, domin jakadiya ta kaiwa Sarki jaririn da Mama tun ranar da aka haife shi. Haka kuma Daddyna shi ma an kai masa shi gida.

Wani abin mamaki kuma shi ne yaron kamar su ɗaya da Mai Martaba Sarki, ba ni da wani bakin magana sai dai kawai na yi wa Allah godiya, na yarda aka nuna mini ƙauna.

Shi kuwa Yarima tamkar yau aka kai ni gidansa, saboda irin yadda yake liƙe mini. Maganar mai taya ni zama kuwa, Yarima sam ya hana mata sakewa, saboda sai ta yi barci, sai kawai na ji shi rungume a jikina,ko da kuwa zan kulle ƙofar barandar bayan ɗakina, sai yasa mukullin ya buɗe.

Tun saura ƙwana biyu suna gida ya ɗauki cika, duk da Mai Martaba yasa a buɗewa jama'a gidan baƙi. Daren suna kuwa, abin har tsoro ya ba ni, irin yawan jama'ar da ke ƙwararowa gidanmu, ban da kaya da aka dinga shigowa da su,wai duk nawa ne ni da jaririna.

Ba zan iya gane ko ƙarfe nawa na dare ba, amma tabbas na san dare ya soma yi sosai. Cikin ɗan sauri na tashi zaune, ina lalubar gabana inda jaririna ke ƙwance, amma ban ji kowa ba,gudun kada in kunna fitila mutanen da ke ƙwance ɗakina duk su farka, yasa na yi amfani da fitilar wayata, amma ban ga jaririna ba. Na haska gaban Aunty Salwa da take ƙwance kusa da ni, sai ƙaton goyon ɗanta a gabanta.

A hankali na miƙe na dinga haska gabanta ina haska gaban baƙin da ke ƙwance a manyan katifu a tsakar ɗakina, duk da ƴaƴan ƙannai da matan yayye da ƴan uwan Mamee, amma duk ba jariri a tare da su.

Na bi a hankali na buɗe ƙofar shiga sama, saboda duba su jakadiya da mata biyun da suke taya ni ƙwana da ƴan hidimomi ni da jariri. Duk na haska gabansu babu alamar ƙaramin yaro a tare da su.

Sam ni ban ruɗe ba saboda na san da wuya a sace yaron nan, sai dai abin da na yi tunani ko dai suna wata al'adar ne wacce sukeyi da tsakiyar dare. Har na koma na ƙwanta sai na ji na kasa bacci ni kaina, ban san ina son jaririna ba sai yanzu. Na miƙe cikin sanɗa a hankali na buɗe durowar da alkyabbobina ke rataye na sanya ɗaya saman rigar barcin jikina.

Ban yi wani motsi da ƙarfi ba har na samu na buɗe barandar ta wacce zata kaini dakin Yarima, domin in sanar masa abin da ke faruwa. Ina buɗe ƙofarshi da makulli ba abin da na ci karo da shi sai ɗan sayon sayon safar jaririna ɗaya. Na sunkuya na ɗauka, sannan na ƙarasa cikin ɗakin.

Fitilar wayata dai na yi amfani da ita ina duddubawa, na yi murmushin da ya ratsa har zuciyata, saboda jin daɗi. Na lallaba na isa inda suke ƙwance. Ƙwance yake a rigingine ya ɗora yaron a ƙirjinsa, fararen kayan sanyi ne ya sakawa yaron,zaman da na yi a gefensu wannan yasa na kunna fitilar gefen gadon da suke ƙwance. Ƙyau Yarima ya ƙara yi mini. Na sunkuya na sumbaci goshinsa, tare da shafa gashin kansa.

Gani na yi ya buɗe idanuwansa a hankali, "Ka firgita ni fa."

Ya yi ƴar miƙar nan ta masu bacci, sannan ya tallabe yaron, ya miƙe zaune tare da sa ɗaya yana murtsikar idanuwansa alamar tashi daga bacci, har da ƴar guntuwar hammarsa. Zolaya ta sa nayi alamar tashi in tafi, sai a lokacin ne ma ya yi magana.

"Ina za ki kuma?"

"Ɗakina."

"Da me ya kawo ki?"

"Neman yarona."

"Shi kaɗai ya dame ki,ni fa? Ko yanzu ba'a yi da ni?"

"Na isa."

"Zo nan."

Ya nuna kusa da shi da hannu ɗaya. Na iso na zauna.

"Dama na ɗauko shi ne saboda ina son yin magana da ke,kin ga da wuya gobe mu samu ganin junanmu da zamu iya tsayawa mu yi magana, saboda jama'a.

Dama game da sunan yaron nan ne. Mai martaba ya mayar masa da sunansa, shi ne na ce bari na tambaye ki in ya yi miki,kin san shawara tana da daɗi."

"Yarima ba ka gajiya,in ba ya ga zolaya irin wacce ka saba yi mini,ya ma zaayi in buɗe baki in ce bana son sunan da Sarki ya sa. Kai dai ka faɗi maganar da ke damun ka, ba dai wannan ba."

"Ita ce mana, sai kuwa maganar zuwa gida wanka, gidan mu fa ake kaiwa, ma'ana wajen Mama za'a kai ki, gidan Sarki, amma za'a tambaye ki ra'ayin ki."

Ya kama hannuna ɗaya, "Don Allah ki ce nan za ki zauna,a kawo miki masu kulawa da ke kawai,kin san Allah ko jakadiya kawai sai ta kula da ke, ballantana daga gobe kin gama wankan ganyen, magunguna zaki cigaba da sha."

Na yi shiru, tunanin ya za'ayi in ce bana zuwa. Na girgiza kaina.

"Ba zan iya ba, kunya nake ji."

"Kunyar me, ba gidan mijinki ba ne ba."

"Saboda me kai kuma ka ke son in Zauna nan gidan."

"Saboda ni."

"Ba ka da lafiya ne?"

"A'a,in dinga ganin ku."

"Ai can ma zaka dinga ganin mu ko?"

"Yasmin, Please understand me."

Na miƙe tsaye, "bari in tafi kada wani cikinsu ya farka bai gan ni ba, kaga kunya zan ji."

Bai ce mini komai ba, ya koma ya ƙwanta. Ni kuwa na juya na nufi ɗakina, amma sai na ji duk jikina ya yi mini nauyi.

Da na ƙwanta kuwa har gari ya waye ban yi bacci ba, saboda tunanin maganar Yarima ina son in ga jakadiya in gaya mata, saboda ko tana da dabarar yi, amma jama'a sun yi yawa.

"Subhanallahi!" Na faɗa a zuciyata, saboda ganin yanda jama'a suka yi yawa, har sun fi duk taron da aka yi. Cikin gidan kuwa jama'a mata da maza,cin abinci akeyi ban da kayan sha,kai abin ya yi mini yawa, har na zamo ba na iya gane komai.

Daɗina ma ɗaya ba yawo ake yi ba, zaune nake a saman kujerar mulkina a falon ƙasa, sai dai kowa ya zo ya kawo tashi gaisuwar,in kuwa na miƙe tsaye, to kaya zan je sakewa. Jariri Jafar Bn Jafar,yana hannun yayar Mamee Ruƙayya a riƙe, sai dai a leƙa a gansa, wanda kuwa yake da buƙatar ganinsa sosai sai dai ya kalli ƙaton hotonsa da ke manne a falona, wanda Mai Martaba ne ya aiko da shi.

Ƙarfe huɗu na yamma kuwa duk jama'ar da ke gidan mu ta dawo waje, ana gama sallah kowa ya nemi wajen zamansa, tamkar dai yanda suke yin kayansu, amma yanzu ya sha bamban da na baya, tunda na baya za ka ga jama'a bayan mu, yanzu kuwa daga ni sai Yarima, sai kuwa dogarawa guda bakwai da ke zagaye da mu.


#####
[2/21, 08:11] Ummi Tandama😇: *ƘASAITA BOOK 3*


*NA*

*MARYAM KABIR MASHI*


Page 6


Yaro Jafar Bin Jafar na hannun jakadiyar Sarki, tsaye wajensu Mama da Mamee da Hajiya Kilishi, ban da ragowar mutanen da ke bayan su. Dad ɗina kuwa ga kujerarsa ga ta Sarki.

Wasan ƙwallon dawaki aka fara yi (Polo), sai kuwa ɗan hawan Daba, sai wani wasa da shanu ke yi (Hawan Ƙaho), ban da wasanni da raye-raye da yare kala-kala suka yi. Saboda Yarima dai shi ne baya magana, amma ta hannu da ta ƙafa yake yi mini magana, shi ne yatsun hannuna ɗaya na riƙe da nashi yana ta wasa da su, ban da idan na gaji na ƙwace ya koma tsokanar ƙafa.

Duk bayan an gama wannan hidimomin ne wanda za mu iya cewa ƙarfe biyar da rabi ta yi, sai na ga wasu irin ƙartin mutane guda biyar sun shigo filin, kowanne ɗaure da bantai a jikinsa, ma'ana ba riga sai wata fata mai ruwan jinin kare ɗaure a ƙugunsu, ga shi iyakacinta cinyarsu.Waziri ne ya miƙe ya fara magana.

"Yau ne ranar da Allah ya kawo muka ga jikan Mai Martaba Sarki, rana ce ta farin cikin kowa. Duk wani wanda yake gidan nan ya san sunan yaron shi ne Jafar Bin Jafar, wanda ya gaji sunan Sarki kenan. Yanzu za mu ƙara tabbatar da cewa yaro namu ne, jinin mai girma Yarima ne, duk kuwa wanda ya tashi a gidan nan ya san ƙa'idarmu ce hakan, saboda haka jakadiya Bismillah."

Ni dai na sa ido in ga ikon Allah, na san kuwa ba ni kaɗai ba, har danginmu gaba ɗaya, shi ne ƴan uwan Mamee da Daddyna.

Jakadiyar Sarki ta sauko daga sama riƙe da jariri a hannunta sanye da kayansa masu ƙyan gaske. Tana shigowa tsakiyar filin nan sai na ga ta miƙawa ɗaya daga cikin ƙartin nan ɗana. Na ɗan yi alamar zan miƙe, Yarima ya riƙe min hannu. Ban ko kalleshi ba, amma na san dai na koma na zauna.

Ina kallo aka tuɓe (cirewa) yarona kayansa gaba ɗaya, ya zamo tamkar yanda aka haife shi. Ganin ƙaton nan ya cilla jaririna sama yasa na yi saurin cakume cinyar Yarima da hannuna ɗaya. Sai a lokacin na ji Yarima ya yi magana, sai da ya jefa shi sama sau uku yana cafewa, sannan na ga ya miƙawa tsohon cikinsu.

Me zan gani? Gani na yi ya saka mini yarona a cikin ruwan nan da ke cike da uban bahon ƙasar nan,ai ban san lokacin da na miƙe tsaye ba na ce "Yarima kalli ka gani, za'a kashe shi." Da sauri na ga Yarima ya fizgo hannuna ya zaunar da ni.

"Yasmin ki ƙwantar da hankalinki, kada ki ba ni kunya. Ni nayi imanin Jafar ɗana ne,ni ne mutumin da ya fara sanin Mamansa,ni na san...."

Ai kuwa wannan tsohon mutumin yasa yarona cikin ruwan nan ya barshi ciki bai ɗauko shi ba. Yarima ya matsa hannuna sosai, "Kalle ni." Na juyo na kalleshi.

"Me ki ka gani?"

"Ba komai." Na juya na kalli inda aka jefa mini yarona.

"Ka gani ko,ka gani ko." Jin ya yi shiru ya ƙyale ni yasa na yi saurin kallonsa.

Fuskarshi ba wata walwala da ya juyo ya kalleni. Ni kuwa har firgita na yi don tsoro, wannan yasa na yi shiru na zauna sosai, sai kuma hawaye da na ci gaba da zubarwa. Ba wani mai ƙwaƙƙwaran motsi a cikin mutanen da ke wajen nan, wajen ya yi shiru kowa yana kallon ikon Allah, tamkar a ce wani shugaban ƙasa ya iso wajen taron,an tashi za'a yi taken ƙasar su.

Abin ka ga uwa, sai na ji na kasa haƙuri, sai da na ƙara kamo hannun Yarima,ko kallona ma bai yi ba, na juya na kalli Dad ɗina,amma ban ga alamar hankalinsa ya tashi ba, kowa na kalla sai in ga hankalinsu ƙwance yake, sai dai alamun su da ya nuna suna jiran ganin abin al'ajabi.

Sai da aka ɗauki tsayin mintuna wajen sha biyar, sannan na ga yasa hannu ya ɗauko shi. Yanda aka yi masa da farko, haka ya yi masa yanzu, shi ne cilla shi sama sau uku. Inda na ga kamar hankalin Yarima ya tashi, shi ne a inda aka cilla shi na farko, sai na ga Yariman ya ɗan yi alamar miƙewa tsaye, na biyu sai na ji yasa kuka irin nasu na jarirai, sai na ga Mai Martaba ya miƙe tsaye.

Gaba ɗaya mutane suka miƙe tsaye aka dinga ihu da tafi,sai a lokacin na ga Yarima yana dariya, ya juyo ya kalleni, kallon da ni da shi kawai muka san fassarar shi. Hankici ya miƙo mini, ma'anar shi na goge hawayen fuskata, tare da cewa.

"Na gode." Cikin sanyin murya.

"Wata al'ada sai mu masu ita."

A nan na ga jakadiyar mu ta gangara tsakiyar filin nan, jakadiyar Sarki na karɓar yaron sai na ga ta baiwa tamu jakadiyar. Murna kuwa da jakadiyar mu ke yi kamar zata kifa don sauri.

Daga nan dai jakadiya ta ɓace mana, sai kuwa Sarki da ya tashi ya yi wa jama'arsa godiya tare da ni kaina da iyayena.

Ana haka aka miƙo mini jariri Jafar,wai zan kai wa Sarki shi. Kamar na yi ihu don kunya. Ganin na kasa tafiya yasa Yarima ya karɓa, ina kallo ya miƙawa Mai Martaba, shi kuwa ya ɗan tsaya yana nunawa jama'a shi, sannan na ga ya miƙawa wazirinsa.

Jafar ya yi lamo cikin baƙaƙen kayan sanyi, waɗanda aka ɗorawa ƙaramar alkyabba a sama. Waziri ya miƙawa Hajiya Kilishi wacce suke rukunin

Please Login or Register in order to submit comment