Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wani al'amarin da ake yi yakan ɗan taɓa talakawa, sannan shi Addininmu ya nuna za'a tambayi duk wani mai mulki haƙƙin yanda ya tafiyar da talakawansa.

*** *** *** ***

Tsarin da Mai Martaba na biyu ya yi, ya burge kowa, ya kuma ƙara masa farin jini a wajen talakawansa. Tsarin kuwa shi ne da kansa ya zagaya garin Jos da kewayenta domin sanin halin da talakawansa ke ciki. Wasu lokutan kuwa ma ba a shigowa a mota sai a ƙafa, wasu kuwa ƙwatami ya yi yawa, wasu ƙauyukan kuma da ƙafa ake zuwansu.

Wannan rangadi ya ɗauke shi tsayin wata biyu har da ƙwanaki goma sha baƙwai,yana yin shi. Wata rana Yarima ya dawo da fara'a, wata rana kuwa da kuka yake iso mini,saboda irin ganin da idonsa ya yi na halin da talakawansa ke ciki.

Ni kuwa ciki ya tsufa, amma har yanzu haihuwa ta ƙi zuwa, wanda zan iya cewa na shanye watan haihuwata, ma'ana na wuce watan haihuwata. Wannan kuwa ya tayar da hankalin Mai Martaba na biyu, Yarima kenan.

Ƙarfe tara na dare shi ne ƙa'idar tashin Yarima daga fada, saboda ya samu lokacin hira da iyalinsa. Yau ma kuwa haka ya shigo gida, ya sameni ƙwance a ƙasan kafet ɗin da kusan launinsu ɗaya da katifa. Suhailat na ƙwance a gabana ta yi bacci. Yanayin yanda fuskarsa ta nuna shine yana tausaya mini. Yana isowa ya sunkuya ya ɗauki Suhailat ya kai ta ɗakinsu, sannan ya dawo ya durƙusa a gabana. Ya sunkuya ya sumbaci kumatuna.

"Sannu." Na ɗan yi fari da idanuwana

"Wallahi Yasmin ina tausaya miki."

*Ni kuma kai nake tausayawa, saboda aikin da ke gabanka na jagorantar mu. Ga ni da ƴaƴanka,iyayenka da nawa,ga jama'ar garin. Ga jama'ar garin nan ba ki ɗaya duk fa a ƙarƙashin ka muke. Yanzu in mutuwa ta kama ka ka ce da Allah me?"

"Wallahi kuwa,ai shi yasa nake son in ga kin haihu lafiya sai mu zauna mu yi shawarar ya zamu yi balle dama duk inda muka je an ɗaukar min shi a kaset, sai mu sa a tsanake mu ƙara gani."

"Honey,tunda haihuwar ta ƙi zuwa me zai hana a fara, tun da idona da bakina za su yi aikin ba cikina ba. Yanzu da ka ce a bari sai na haihu,to in na mutu wajen haihuwar fa..."

"Haba Yasmin ki daina irin wannan mummunar maganar ta ƙananan yara,me ki ke so na koma idan na rasa ki?"

"Baka zama komai."

"Na ji nidai ba na son ki dinga yi mini irin waɗannan maganganun marasa daɗi da ɗaci."

Ya juya har da ɓata rai sosai. Hannu na sa na juyo fuskarsa.

"Sorry, ba zan kuma ba na daina." Na faɗa cikin muryar nadama.

Ya ɗago fuskata ya ƙura mini ido, sai kawai na ga ya kai bakinsa ga nawa. Mun yi minti huɗu ya ɗago.

"Yasmin ni fa har yanzu son ki bai taɓa raguwa a zuciyata ba,kin san Allah duk every day, every time, every minute,every second,sai na ji sonki yana ƙaruwa a zuciyata. Ki daina gaya mini maganar da raina zai ɓaci,ki tayarwa da mijinki hankali,kin ji?" Na ɗaga kai alamar eh.

"To bari na ɗauko kaset ɗaya mu fara da shi."

Na yunƙura zan tashi ya yi saurin kama ni, na miƙe.

"Ina za ki?"

"Da abin hira zan ɗauko maka,in samu kuma in cire maka kayan jikinka."

Ya ja kunnena, har sai da na yi ƴar ƙara.

"Ke ɗin nan ba ki jin magana,sau nawa ina gaya miki cewa idan ina cikin gida kusa da ke na zama ɗan aiken ki.?"

Na narke na yi irin alamar kukan shagwaɓa, tare da maganar shagwaɓa.

"Ni Allah ban yarda ba,ni sai in dinga baka wahala."

"Wallahi na cije bakinki idan ya ƙara yi mini gardama."

"Ni! Ni! Dai...." Ya zare takalman ƙafarsa zai ƙwala mini cikin haushi. Na yi gaba da ɗan guduna, ina kiran.

"Na daina, na daina, Allah....."

Ya kamo ni saboda irin yanayin gudun mai ciki. Ya ɗaga takalman, na runtse idanuwana alamar tsoro, sai na ji ya zagayo ta bayana ya rungume ni yana dariya.

"Ga tsoro ga jan faɗa."

Dama yanda yake rungume ni kenan idan ina da tsohon cikin da zai hana masa sakewa ya rungume ni ta gaba. Ya sumbaci wuyana.

"To mu je in taya ki ɗaukowa."

"To tsaya in cire maka alkyabbar ko?"

Ya juya baya na zare masa alkyabbar jikinsa na ajiye saman kujera, sannan muka isa kicin.

Ba wani abu ba ne mai wahala ba abin hirar tamu. Tuwan abarba ne da inibi,an markaɗe su da ɗan kauri, tare da dabino wanda za'a jiƙa shi ya yi laushi, sai a ajiye ruwan gefe ɗaya, sannan a samu ƙwaƙwa ta ciki a goga ta da abin goga kuɓewa, bayan duk an wanke su kenan, sai a kawo ruwan abarbar da dabino da inibi a zuba a cikin ƙwaƙwar, sai a kawo madarar ruwa a zuba a ciki, ya danganta da yawansa, yawan madarar ga mai son suga ya zuba, ga mai son zaƙi sosai zai ji ya yi daidai. Amma ko ba inibi za'a iya yi, ana iya yi da madarar gari ma.

Cikin ɗan kofunan shan fruit salad ake shan shi, tare da ɗan ƙaramin cokali ana kiranshi da suna Appitizier (Coconut).

Mun kalli kasusuwan da dama a cikin ƙwara tara,babu abin da na lura a ciki wanda yake takurawa talakawa illa abubuwa baƙwai. Abin da muka zauna a yau juma'a muna tattaunawa da Yarima kenan.

"To ke yanzu me kika lura ya damu talakawana?"

"Ai ba talakawanka kaɗai ba, duk ƴan ƙasar Nijeriya."

To yanzu kamar me ye da meye ki ka lura da su?"

"Ruwa, rashin abin ƙonawa, itace ko kalanzir,ko gas,ga masu aiki da shi, ba wai babu ba, tsada ce ta yi masa yawa, suna buƙatar magudanan ruwa,takin noma, magunguna a asibitoci, hanyoyin mota, ballantana a cikin ƙauyuka, wutar lantarki,makarantun boko, Islamiyya tare da ilimintatun malamai,uwa-uba fetirin sawa motoci ko abin hawa ƙanana.

"Gaskiya na yarda. Ke kin ga wani ƙauye da muka je,kin ga ruwan da suke sha kuwa tamkar ruwan ƙwatami? To wai me ki ka ga ya janyo haka?"

"Rashin kulawa da sa ido, da zame hannu da ku sarakuna ku ka yi,ku ka bar wa gwamnati komai, ita zatayi. Ka yi tunani lokacin da sarakuna ke mulkin garuruwansu ka gani,ka san ya sha bamban da yanzu. A da Sarki ke da ikon komai kuma yana samun hanyoyin jin labarin abin da talakawansa ke ciki ta hanyar fadawansa da kuma ƴan garin kansu. Ka tuna a da ko haihuwa aka yi a gari sai Sarki ya sani,ko hakimi,ko Dagaci,ko Mai unguwa, amma yanzu fa? Kai za ka baiwa kanka amsa."

"To yanzu wacce shawara za ki bani?"

"Ni dai shawarata biyar ce. Ta farko itace sarakunan mu su yi haƙuri don girman Allah su dawo da yanayin mulkin su na da, da adalci,su tuna su zasu fi sanin gwamna ko shugaban ƙasa, abin da talakawa ke ciki, saboda sun fi su hulɗa da jama'a,su manta da duk wani abin da aka yi masu,su ji tsoron Allah,su kawar da komai da ke zuciyarsu,su ci gaba da aikata ayyukansu na alheri, kamar yanda ake yi a baya.


######
[3/1, 19:48] Ummi Tandama😇: *ƘASAITA BOOK 3*


*NA*

*MARYAM KABIR MASHI*


Page 11


Su yi tunani da cewa Allah Subhanahu wata'ala ya damƙa ragamar mu a hannunsu, duk da na san yanzu haka in baku sarakuna ba yanda za'ayi gwamnati ta tafiya, duk da na san a kan san rai ne da ɗan nuna maku isa, amma kamata ya yi ku dage da ƙwarjinin da Allah ya ba ku ku nunawa Gwamnati dole sai daku za ta iya tafiya. Lallai wannan babban jihadi ne ga rayuwar duk wani mai faɗa aji a duniyar mu ta musulunci.

Saboda la'akari da abin da malamai suke faɗa cewa, ranar ƙiyama ana fara hisabi ta jini ne, sannan kuma manyan malamai, masu kuɗi, shugabanni, sarakuna, saboda haka wannan ma ya ishe mu ishara ta mu dage mu ga yanda ƴan ƙasa mu suke tafiyar da rayuwarsu, saboda shi Allah ba ruwansa gaba ɗaya zai haɗa mu ya tambaye mu yanda muka tafiyar da mulkinsu, ba ruwanshi da cewa shugaban ƙasa ko gwamna, mulki duk mulki ne.

Ko mace a gidan mijinta ita ma mulki take, haka namiji a tsakiyar iyalinsa duk mulki yake. Za'a kuma yi masa hisabi a ranar gobe ta yaya ya tafiyar da iyalin nan nasa kamar yanda muka sani, ga hadisin Manzon Allah (S.A.W) da wasu daga cikin ayoyin Alkur'ani mai girma.

Lallai waɗannan hadisai ana iya duba su ga litattafan Buhari da sauran sahihan litattafai. Ku sani talakawa na cikin masifa kala-kala, waɗanda suke neman taimakon Allah, tare da shuwagabanninmu. Lallai Allah yana sane da duk wanda ya taimaki wani, ya ƙyautata rayuwarsu ta zamo ingantacciya. Allah ya taimaka maku, shiyasa nake tausaya maka.

A saboda haka fushi da sa ido ga shuwagabanninmu ba na sarakuna ba ne, ba haƙuri da tausayawa talakawansu shi ne nasu, da hanyoyin da za su bi su ga sun gyara, sun dawo mana da jin daɗin da ya wuce, wanda muke tunanin ba zai taɓa dawowa ba,su yi mana bazata su dawo mana da shi. Allah ya taimake ku, ya sada ku da gidan Aljannar fiddausi madauwamiya, Allah ya raya maku zuri'arku, ya ƙara taimaka muku da haƙuri da mu,Amin."

"To yanzu wacce shawara za ki ba ni?"

"Shawarata a nan ita ce,ka fara yin amfani da abin da ke hannunka, ikon mallakar ka."

"Kamar me?"

"Kamar ɓangaren abinci. Ka ga yanzu haka a gidan nan zuwa gidan da muka baro, zuwa gidan Mai Martaba na ɗaya,aƙwai ɗakunan ajiyar abinci sun kai talatin (Stores), kowanne da kala-kalar abin da ke ciki,na yi imani in zamu shekara ɗari ba zamu nemi abinci ba, amma ka sani shi abinci ne ba zai kai shekara ɗari ba, da kuma mu da koyaushe Allah zai iya ɗaukar ran mu, sannan ko da yaushe abincin nan na iya lalacewa.

To me zai hana a taimakawa talakawa da shi, sannan kuma Allah ya hore maka maƙudan kuɗi, ba Mai Martaba na ɗaya ba, ba kai ba,ni kaina da nazo gidanka daga baya, na san na mallaki duniyoyin da zan iya taimakawa da su daidai gwargwado."

"Ai kuwa na gode, Allah ya yi miki albarka, ya baki ƴaƴa masu ƙaunar ki kamar yanda ki ke ƙaunar ubansu. Da kin haihu kuma zan fara."

"A'a ba ruwanka da haihuwata,ka cigaba kawai."

"Ai saboda matsalar mata sai ke."

"Ga jakadiya nan na amince da ita,ka yi tunanin ƙaunar da take yi mana, iyaka ni zan dinga tsara mata abin da ya kamata ta yi, ba ma sai na fita ba."

"Ni dama ai ba na son ki fita a gane mini ke,kin manta ke One in town ce?"

"Wallah Honey ka bar koɗa ni zanyi maka kuka."

"Na daina,ai ba na son inyi asarar hawayen nan naki masu ɗigon tawwadar ilimantarwa."

"Ka ƙarayi."

"Sorry My Beby na."

Na yi dariyar jin daɗi, tare da juya bayana na ƙwanta a ƙirjinsa, ya rungume ni.

Na godewa Allah da ya wadata ni da miji mai jin shawarata, mai ɗaukar duk kalamain da ya fito daga bakina,ko na iyayena. Wannan dalili ne ma yasa na sadaukar masa da nafila raka'a biyu domin ta zama kariya a gare shi, wacce nake zama musamman in yi masa ita shi ɗaya, da addu'o'in da ke cikinta.

Dalilina kuwa, shi ne duk abin da muka tattauna da Yarima ya aikata shi, duk unguwa idan suka isa, tun daga gidan farko har ƙarshe sai an ajiye masu buhun-hunan abinci da jarin sana'a, wanda na tabbatar zai wadace su. Sannan sai a tambayi matsalar ka ta rashin lafiya ko haihuwa,ko bikin ɗiya,ko gyaran gida, sai a taimaka maka.

Wasu buhun-hunan abincin kuwa, don ajiya har sun lalace da hunhuna, sai waɗanda ƙwari suka cinye suka koma gari. Kai Alhamdulillahi, saboda yanzu ni na san nayi jihadi mai tsananin lada, tun da har Islamiyoyi aka buɗe, ban da makarantu masu ƙyau, ban da ɗaukar nauyin ƴaƴan da iyayensu ba su da halinsa su makaranta.

Sai kuma ni tawa gudunmawar, shi ne taimakawa mata ƴan'uwana da koyar da su ilimin zamani da na addini, yanda za su zauna da mazajensu lafiya da tarbiyyar ƴaƴansu, ga sana'o'i ana koya masu. Abin da ya so ya bamu wahala ni da Mai Martaba na biyu, shi ne Musluntar da arnan da suke zagaye da Jos, waɗanda wasun su ko kaya ba su iya sakawa ba,wasun su ma nama danye suke ci, amma mun samu da ƙyar mun taimaka masu.

Dabarar da muka yi kuwa, shi ne duk garin da suka isa, sai su ɗauko shugabansu su taho da shi cikin gari ya samu wata ɗaya,ko biyu yana ganin yanda jama'a ke rayuwarsu, ana koya masa duk wata al'ada mai ƙyau da Addininmu, to idan ya koma garinsu, shi zai dinga koyar da ƴan'uwansa,idan ya ga suna da sha'awa sai ya dawo gari ya gayawa Yarima, daga nan sai a tayar da mutane kamar ashirin cikin su da malamai da masu taimaka masu da abinci, ruwan sha,wanki. Yanzu haka duk an tura su a matsayin zasu shekara a can.

**** *** ****

Cikin jikina dai har ya shiga wata na sha ɗaya a jikina babu zancen wata haihuwa, sai dai duk inda na zauna sai an taimaka mini nake tashi,don dai ma ni doguwar macece, da gajeriya ce da shi kenan sai an dinga saka ni a kujera ana turawa. Wannan abin yanzu shi ya damu duk wani masoyina.

Kai har da Mai Martaba Sarki ya aiko da cewa mu shirya zai turo likitocin da zasu duba ni. Shi kuwa Mai Martaba Yarima cewa yake gara mu bar ƙasar. Amma Sarki ya hana a je ko'ina ya ce saboda abin da tafiyar mu zata haifar, shi ne a shiga ruɗanin ya ya nake. Ni kuwa har mamaki suke ba ni, saboda ba na jin ciwon komai sai dai nauyin da cikin ya yi mini ya hana mini sakewa.

Likitoci turawa mata,su baƙwai suka iso gidanmu, ba wani ɗan rakiya sai Mai Martaba na ɗaya, yanda suka shigo falon ina tule waje ɗaya, shi ya bani kunya. Cikin matsananciyar kunya na samu na gaida su, daga nan kuwa suka umarce ni da in isa asibitin mu da ke cikin gidanmu.

Yarima kuwa kamar ya saka kuka, da ya ga likitocin nan, sai dai ganinsu tare da Mai Martaba yasa ya kasa yin magana.

Lallai na san an shiga ɗakin asibiti da ni, ɓangaren mu wato Emir's section.

**** *** ****

_Innalillahi wa'inna ilaihir'raji'un!” haka Mai Martaba yake faɗa yayin da yake riƙe da ɗansa Yarima, wanda ke zaune dirshan a ƙasa yana kukan mutuwar matarsa Yasmin. Wanda hakan ya faru ne ta sanadiyyar haihuwa da ta zo mata da gardama.

Babanta Alhaji Sani Sa'id shi ne ke da ƙarfin halin yiwa mijinta nasiha.

"Haba Yarima,ka yi haƙuri mana,ka yi tunani da Allah ne ya baka Yasmin,don ya ɗauke abin shi kuwa,ai ba a ƙi gode masa ba. Mu ma nan fa jiran tamu mutuwar mukeyi, saboda faɗar Allah Subhanahu wata'ala ce da yake cewa KULLI NAFSIN ZA'IKATUL MAUTI (Dukkan mai rai mamaci ne). Saboda haka ƙyau a ce godiya ga Allah ka yi, tare da yi mata addu'a.

Wannan nasiha ita ta ƙarasa rikita Yarima, sai dai aka ganshi zube a ƙasa sumamme,gudun kada hankalin jama'a ya tashi, yasa ba'a yi wata hayaniya da ƙarfi ba, sai dai ɗauke shi aka yi aka kai shi asibiti, wanda likitoci suka bi bayansa.

Maganar da na yi ita ta dawo da hankalin jama'a gareni, wanda ɗakin cike yake da mata ƴan'uwana. Cikin su kuwa har da Mamee, Aunty Salwa,ga Mama,da Hajiya Kilishi, ban da jakadiya da ke rakuɓe a gefe, duk na karanci hakan kafin na kai ga yin magana.

Maganar kuwa ta yi daidai da firgita duk wanda ke zaune, ganin yanda suka nuna.

"Mamee lafiya na ga kuna kuka?"

Tambayar da na yi masu kenan. Gaba ɗayansu sun firgita, wanda dukkansu sun yo kaina, kowa so yake ya rungume ni. Jin jakadiya ta fita da gudu tana kira, "Mai girma Yarima Gimbiya ba ta mutu ba,dogon suma ne."

Maganar ta ta iso a kunnena, ita ta gaya mini da jira ake gari ya waye a kaini kabarina.

Na yiwa Allah godiya da ya taimaka mini na farka kafin gari ya waye. Na yunƙura zan tashi, amma na ji jikina kamar an karya mini ƙafafuna. Sai dai ji na yi Hajiya Kilishi na cewa.

"Jira a taimaka miki. Ke kuwa ai dole jikinki ya yi tsami,a haihu tun safe amma ba wanka." Sai a lokacin na faɗa tunanin abin da ya faru da safiyar yau.

Zuwan likitoci da Mai Martaba Sarki, wanda suka yi mini wasu allurori sun kai biyar. Yarima har faɗa yake masu, shi kuwa yana tallabe da kaina a cinyar shi yana yi mini sannu, balle da na ji wani bala'in ciwo na jijjiga mini tsokar naman jikina. Ban fi mintuna arba'in ba a haka sai na ji kamar an zare numfashin jikina.

Daga nan ne ban ƙara sanin yanda aka yi ba, sai yanzu, amma na ji Yarima na yi masu faɗa. A can cikin tsakiyar kaina ina jin matsanancin ciwon da nake ji, sai na ji suna ce masa wai allurar naƙuda suka yi mini. Haka kurum ruwan da suka sanya mini a hannuna ma na naƙuda ne.

Jin Hajiya Kilishi ta kama ni yasa na dawo hankalina izuwa kallonta, sannu ta dinga ce mini haka ma duk waɗanda ke wajen. Amma Aunty Salwa sai ma sabon kuka da ta saka ana ba ta haƙuri. Mamee kuwa ko motsi ba ta yi ba daga inda take zaune.

Bayan Hajiya Kilishi ta taimaka mini na yi wanka da ruwa mai zafin gaske, wanda ta cika bahon wanka, ta ce in shiga. Bayan na shiga ita kuma ta zuba wani a wata tasa mai faɗin gaske (silba), ta dinga tsoma tawul a ciki tana gasa mini jikina. Ni kuwa kamar kada ta daina saboda daɗin da nake ji.

Ina fitowa aka ba ni kunnun goruba cike da ƙwano aka ce in shanye shi. Ban ƙi sha ba, amma ni na san ba zan iya shanye shi ba. Lallai dole na yi mamakin har yanzu a ce Yarima bai shigo ya gan ni ba. Shin ko dai tsorona yake ji? Ko kuwa ya daina sona yanzu?

Kasa ɗaurewa na yi da na kalli agogon bango na ga har baƙwai da rabi na safe ta wuce, amma Yarima ba wanda bai shigo ya yi mini sannu ba, har da Dad ɗina da yake nuna kawaici a kaina, sun shigo da shi da Mai Martaba Sarki. Ni dai kasa ɗaurewa na yi har na tambayi Hajiya Kilishi.

"Hajiya ina Yarima ne? Ko ya yi tafiya?"

"A'a yana nan, amma na ji Mai Martaba Sarki na cewa jikin nasa da sauƙi, yanzu haka suna wajen shi."

Hankalina na ji ya tashi matuƙa, da a ƙwance nake, amma sai gani na tashi zaune. Ya zan yi ni yanzu? Na tambayi zuciyata. Sai kawai na ji na miƙe tsaye. Hajiya ta yi saurin kama ni.

"Me ye?"

"Hajiya zan iya zuwa wajen Yarima?"

Eh,mu ma yanzu can zamu. Su Mamee ma na can tun ɗazu. Amma ganina da kinyi haƙuri sai Sarki ya tafi da mutanen shi,ki ƙwantar da hankalinki, ba abin da ya same shi, razana ce kawai ya yi."


#####
[3/1, 22:22] Ummi Tandama😇: *ƘASAITA BOOK 3*


*NA*

*MARYAM KABIR MASHI*


Page 12


Ya ya zanyi? Dole na bi maganar manyana. Haka dole na koma na ƙwanta, amma hankalina duk baya jikina. Gudun kada a ce mini Yariman ya mutu, amma kaɗan-kaɗan na tambayi duk wanda na ga ya shigo, cewa, "Ina Yarima?" Sai dai su bani amsa da yana nan lafiya.

Ƙarfe biyu saura minti goma sha ɗaya na ga Yarima ya shigo cikin sauri. Yana shigowa ina ƙwance, ganinsa yasa na yi saurin tashi tsaye. Ya iso ya kama cinyoyin hannuwana duk biyun, ya zame hannayensa suka sauko ga ƴan yatsuna. Ya dawo da hannayensa ya shafi wuyana da su, ya tallabe kumatuna ya kalleni. Sai a lokacin na ga ya yi murmushi, ya mayar da ni ya rungume gam a jikinsa, ya ɗagoni ya zaunar da ni a bakin gado, shi kuwa ya tsugunna a gabana, da gani ya rasa ya zai yi mini. Sai na ga yasa ɗan yatsana a bakinsa.

A tunanina wasa zai yi mini,sai kawai ya cije ni, na sa ƙara irin wacce ke dawo da hankalin Yarima a gareni, sai kawai na ga yasa dariya. Nima ban san lokacin da nasa tawa dariyar ba. Sai na ga ya hayo gadon shi ma yana mai cigaba da dariya, ya mayar da ni ya rungume a jikinsa. Sai kawai na ji lema na tsiyaya cikin rigata ta bayana, na ɗago kansa.

"Yarima me ye kuma na fitar da hawaye bayan ga ni?"

"Yasmin da kin mutu da ya zanyi da ra....."

"Haba Yarima, kamar ba Musulmi ba,za ka dinga kawowa kanka irin wannan tunanin, ba ka san Allah mai rahama mai jin ƙai ne ba. Yanda Allah ya ɗauke maka ni, haka zai musanya maka da wacce ta fi ni."

"Ki yi shiru Yasmin,ke dai kawai ki taimaka mini da murna, da addu'ar godiya ga Allah da ya bar mini ke."

Hawaye ya tsiyayo a kumatunsa. "Ba zan taɓa iya ƙwatanta miki yanda na ji rayuwata ta koma ba a cikin ƙanƙanin lokaci."

"To ba sai..."

Jakadiya ce ta yi sallama, muka saki juna, sannan na ce ta shigo. Ta shigo tana rawar jiki da yaro rungume a hannunta. Har a lokacin ban fahimci me ta shigo yi ba, sai da ta durƙusa gabanmu tare da gaisuwar ta ta miƙo mini yaron hannunta. Sannan na tuna ashe fa haihuwa na yi,ni na ma yi tunanin abin da na haifa ya mutu, shi yasa ban ma neme shi ba.

Yarima ya miƙa hannu ya karɓa, ya ce da jakadiya, "Su Mai Martaba suna nan?"

Ta amsa da, "Suna fada,su Mama ne dai suka tafi."

Ya miƙo mini jaririn hannunsa ya miƙe.

"Tsaya ki kula da ita,in je in dawo"

Jakadiya ta ce, "To." Shi kuma ya sunkuyo ya sumbaci goshina sannan ya tafi.

Sai da na ga fitarsa sannan na dawo da kallona ga abin da ke hannuna, "Mace ce ko namiji?" Na tambayi jakadiya.

Ta amsa da "Namiji ne."

"Ina Suhailat?"

"Mama ta tafi da su ita da Ammar."

"Me yasa ba su zo yi mini sallama ba?"

"Saboda Yarima. Kai Gimbiya ki godewa Allah, Allah Yarima yana son ki,sumansa biyar da aka ce masa kin mutu. Ki duba taurin rai irin na Allah ya ja da rai, amma sai ga shi yana kuka a gaban kowa."

Na yi murmushi irin na wanda ya tashi daga ciwo, sannan na lalubi mama na sawa jariri a baki. Sai da ya kama maman, sannan na samu damar kallonsa sosai, abin ka da jariri sai na kasa gane da wa ya yi kama. Ina cikin ƙoƙarin gano hakan Aunty Salwa ta shigo.

**** **** ****

Rana ta zagayo aka sawa yaro suna Abdul Nasir,amma ba a yi wani taro ba, saboda jikina ya ƙara warwarewa, saboda haka Mai Martaba Sarki ya ce a barshi sai wani satin. Wannan yasa aka ƙara sa masu kulawa da ni su matso kusa da ni domin kulawa da ni sosai.

Su Ammar kuwa sun zama ƴan gidan Mama, saboda sai dai su zo da yawo su koma.

Bayan ƙwana uku da raɗin suna sai aka shigo falo na uku wanda nake zama domin hutawa, aka ce na yi baƙi. Ban tsaya neman ba'asi ba na ce su shigo. Sauran kaɗan in saki Abdul-Nasir ƙasa, saboda mamakin ganin baƙin su huɗu da na yi. Maza biyu, mata biyu,ba zancen koƙwanto na gane su, duk da sun canja kamaninsu. Cikin al'ajabi na kira sunan ɗaya daga cikin su.

"Mansura! Daga ina ku ke haka?"

Madadin su yi magana, sai kawai na ga Mansura tasa kuka, ƴar'uwarta Musulum na taya ta ko kuwa in ce suna taya juna.

"Su waye waɗannan?" Na tambaye su.

"Mazanmu ne, wannan mijin Mansura, wannan kuwa nawa."

"Daga ina ku ke haka? Ya aka yi ku ka san muna nan? Wa ya nuna muku gidan?"

"Mu ma labari muka samu, shi ne muka ce

Please Login or Register in order to submit comment