Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

nufa ya zauna tare da fara ƙoƙarin zuba abinci, yana mamakin me ya tsayar da Rumana har ƙarfe biyar saura ba ta dawo a aiki ba.
Bai gama tambayar kansa ba ya ji buɗe ƙofar ɗakinta, da sauri ya juya suka haɗa ido. Tare suka sakarwa juna murmushi, ya mayar kansa kan abin da yake zubawa yana faɗin.
"Kina ciki da ma?"

"Eh, bacci nake motsinka ya farkar dani na ɗauka ma Ramlat ce."
Faɗin Rumana cikin kwababbiyar hausarta, a lokacin ta iso tana zama ta ɗauki spoon ta saka cikin abincin da ya zuba ta fara ci.
Waliy ma spoon ya ɗauka ya fara ci sannan ya ce.
"Ina ta tunanin ina kike."

"Allah My B."
Ta faɗa tana narke murya cikin shaukin son mijintan kuma yayanta.
Murmushi ya mata suka ci gaba da cin abinci cikin nutsuwa, haka suka kammala Waliy ya miƙe ya ɗauki wayarsa ya bar waje.

"Zan leƙa Ammi." Ya faɗa yana fita bai jira me za ta faɗa ba.
Ita ma ba ta damu ba ta kwalawa ƴar aikinta ƙira ta fito ta hau tattare wajen. Ita kuma ta koma cikin falo don jiran dawowarsa.

Waliy a falo ya samu Ammi da Nabeela sai shagwaɓa take zuba mata, gefenta Farah babu Radiyya.
Kujera ya samu ya zauna bayan sun amsa sallamarsa, ya hararo Nabeela yana faɗin.
"Bar nan ko na ɓata miki rai, kin girma ba ki san kin girma ba."

Baki ta tunzura gaba ta miƙe ta shiga ɗakinsu, Farah ta gaishe da shi ya amsa yana tambayarta.
"Ina Radiyya?"

"Tana kitchen."
Farah ta faɗa tana miƙewa ta bar wajen don su gaisa da Ammi da kyau.
Bayan wucewarta Waliy ya kalli Ammi yana tambayarta.
"Ammi ya gida? Fatan babu wani matsala?"

"Babu komai. Ya naka wajen aikin?"
Ammi ta tambaye shi cikin kulawa.
Kansa ya shafa ya ce.
"Allahamdulillahi sai godiya."

Hira suka hau taɓawa har magriba sannan ya mata sallama ya fita, ita ma ta miƙe ta shige ciki don aikatarwa.
Waliy daga nan masallaci ya wuce, bayan an gabatar da sallah ya koma ɓangaren su ya samu Rumana tana jiransa, kusa da ita ya zauna yana binta da kallo. Ita ma kallonsa tayi ta gyara zamanta tana ɗaura kanta saman cinyarsa.
A haka suka gama hiran su wajen ƙarfe goma sannan suka kashe komai suka wuce ɗaki don bacci. Bayan sun yi shiri suka bi lafiyar gado.
Rumana bacci ne ya kwasheta yayin da Waliy tunanin Mariya ya faɗo mishi. Yanayinta ya fara karantowa, farkon haɗuwar su da yanayin yadda take da saurin shiga tsoro, ga kuma ɗazu da abin da ya faru. Tabbas ba shuru shuru kaɗai bane ya sakata zama miskila duk da yanayinta ba mai son surutu ba ce, akwai wani abun a rayuwarta da yake damunta.
Numfashi ya furzar ya sake rumgume Rumana, baccinta take hankali kwance kamar babu wani abu da yake damunta. Yau tsawon sati bai nemeta ba, ko da zasu shekara haka yasan ba za ta nemesa ba wanda ya rasa dalili. A haka bacci ɓarawo ya sace sa.
***

Da safe Abba yasa aka sake zaman cin abinci a tebur, nashi tunanin haka zai sake haɗa kan yaransa. Yaran kamar su yi kuka, har da masu karyar ciwo irinsu Ummi Aisha don ba ta manta marin jiya da ya saka mata ciwon kai ba, sanin bata da lafiya yasa Umma barinta.
Gaba ɗaya suka haɗu a dining ɗin, Abba ya kalli Mariya wacce gaba ɗaya a takure take yasa ta miƙe ta zuba musu abinci shi da Umma da Yaya Haydar.
Kamar ta fasa ihu haka ta miƙe ta zuba musu, sai dai Yaya Haydar ta ka sa zuba masa abinci ta haɗa masa tea ta ajiye kamar yadda jiya ya bata umarni. Tana ƙoƙarin zama ya buga mata tsawa.
"Ɗauke ki shanye tas, uban wa zai sha miki."

Mariya jiki na rawa ta ɗauka ta fara sha duk zafinsa, Abba ya kalle shi ya ce.
"Kai kuma ai ba haka ake ba, ka faɗa mata tun kafin ta haɗa."

"Abba ai ba ta tambaye ni ba."
Ya faɗa yana kallon Haneefa da yake mata kallon ita kaɗai ce mai ɗan hankalin cikinsu ya ce.
"Ke tashi ki zuba min abinci."

Babu musu ta miƙe ta zuba mishi ta ajiye masa, ta zuba nata kaɗan ta fara ci a hankali, sauran ma suka zuba a dadare don sun san kuskure kaɗan zasu yi Yaya Haydar ya ci kaniyarsu. Haka suka fara ci banda Mariya da aka haɗa da shan shayi mai zafi.
Yaya Haydar ne ya fara miƙewa don kaɗan ya ci ya bari, sai Abba shi ma ya miƙe ya kalli Mariya ya ce.
"Tashi ku tafi."

Cikin hanzari ta ɗago kanta tana kallon Abba jin abin da ya faɗa. Girgiza kanta tayi idanuwanta suka cika da kwalla, ƙasa ƙasa don Yaya Haydar kar yaji ganin yayi gaba ta ce.
"Abba ya je kawai."

"Tashi Sister kar kiyi wani laifin."
Haneefa ta faɗawa Mariya hakan don tuna mata kar tayi wani laifin da zai jawo mata matsala a aikinta.
Mariya kallon Haneefa tayi, ta ga ta ɗaga mata kai alamar ta tashi taje.
Babu musu ta miƙe ta ɗauki handbag ɗinta tabi bayansa don har ya fice a falon tuni, haka Abba ma da ta rasa me zai yi yabi su.
  Yaya Haydar ta samu jikin motarsa, Abba a gefe yana mishi magana. Kallo ɗaya ta mishi ta sunkuyar kanta ƙasa ganin fuskar nan a haɗe  kamar koyaushe, tasan yau mai hanasa mata abin da yaga dama a mota sai Allah.
Ita ta rasa me yasa Abba yake son haɗata da shi, kuma ya san ba shiri suke ba, ya san halin yayan nasu ba ya haɗa hanya da su, ba shi da aiki sai cin zalinsu musamman ita.

'Ko dai daɗi yake ji idan yaga yana cin zalinta?' Ta tambayi kanta.
 
#vote
#comment
[06/06, 7:28 pm] Pharty BB: GOBE DA NISA
Page 9
Na Pharty BB

Mariya da ƙyar taja ƙafafuwanta zuwa gare su, yayinda zuciyarta ta ci gaba da bugawa. Abba da kansa ya buɗe mata gidan gefen Yaya Haydar.
Da murmushi a fuskarsa kamar koyaushe, yana kallon Mariya ya ce. "Shiga ku je Daughter."

  Ba ta iya musu ba haka ta shiga ta zauna a dadare, tabbas da tana da dama ko su biyu ne da Abba da tuni ta bijire mishi, amma tasan yin hakan tamkar yin gaggarumin laifi ne a gurin Yaya Haydar.
  A murfin mota ta takure kanta waje ɗaya, motar banda ƙamshin mayen turarensa da sanyin ac babu komai ko karatu balle kiɗa. Tana ji ya yi hon mai gadi ya zo ya buɗe mishi get. Cikin sauri ya fizgi motar suka fita a gida.
  Sun yi nisa a tafiya a tsakiyar hanya taga ya gangara gefen titi, ita dai bata ce komai ba don numfashi ma da ƙyar take ja balle wani motsi, tsoronta ɗaya kar ya mata maganar nema mata sallama a aiki da ya faɗa .
  Yaya Haydar juyawa ya yi ya kalli Mariya, ta haɗe cikin baƙin coat nata da ƙaramin baby hijab fari, jakarta ma fari, dole ta burge mutum kasancewarta ƙarama kuma mace cikin shigar manya.
Gare shi kam ko kusa bata burge shi ba, baki ya taɓe yana ɗauke kansa daga kallonta.
"Fice min a mota don ni ba driver naki bane." Ya faɗa mata cikin muryar nan nasa mai tsoratata.
  Kafin ya gama rufe baki Mariya ta buɗe ƙofar mota ta fice fit. Sam ba ta ji haushi ba, sai ma daɗi da nutsuwa da taji na ganin sun raba hanya.
  Figar motar yayi yabar wajenta, ba ta ko juya ta kalle shi ba ta hau tsayar da napep, bayan ya tsaya ta shiga tana faɗa masa inda zai kaita.
  Suna isa ta biya shi ta wuce ciki, can wajen fakin idanuwanta ya hango mata motar Barrister Waliy da Yaya Haydar. Ɗauke kanta tayi ta ci gaba da tafiya cikin nutsuwarta wanda yake ɗaukar hankalin mutane, wanda kamar da gayya ko yanga take tafiyar.
  Office ta nufa kai tsaye ta shiga musu da sallama, wanda suka ji suka amsa mata. Saman table nata ta nufa ta zauna da bismilla.

"Oga ya aiko ƙiranki." Faɗin ta gefenta mace.
  Mariya cikin mamakin da ya bayyana a fuskarta ta kalleta ta ce.
"Ni ko wa?"

"Ke dai, ko ba ke ce Mariya ba?"
Ta faɗa mata tana mayar kanta kan computer nata.
  Mariya jiki a sanyaye ta miƙe ta fita, ba ta tsaya ko'ina ba sai upstairs da zai sadata da office ɗinsa, haka ta zo ta gifta ta office ɗin Yaya Haydar a tsorace ce tamkar za ta gansa, inda aka yi rashin sa'a wucewarta ta yi daidai da buɗe office ɗinsa ya fito.
  Ba ta lura dashi ba, don ta basa baya a lokacin ta buɗe office ɗin Barrister Waliy ta shiga da sallama.
  Yana zaune kamar kullum yana aiki, ƙyam ta tsaya kanta a ƙasa ta ce. "Ina kwana sir"

  Sai lokacin ya ɗago kansa idonsa ya sauƙa a fuskarta. Karantar yanayin fuskarta ya yi duk da ta dukar idanuwanta ƙasa. Fuskarta kamar koyaushe babu son hayaniya sai alamun tsoro kaɗan.
  Ɗauke kansa ya yi daga kallonta, ya sauƙe numfashi da bai san daga ina ya fito ba. Murya a hankali tamkar ba nashi ba har Mariya sai da ta ɗago, a lokacin ya ce.
"Koma aikinki, anjima zamu fita tare."

  Kanta ta mayar ƙasa ganin ya sake ɗagowa sun haɗa ido, a hankali ta juya ta fita. Office ɗinsu ta koma, computer nata ta kunna don fara duba aikin ciki taji ƙarar wayarta.
Barin abin da take yi tayi ta buɗe jakarta ta ciro, sabon lamba ta gani, kamar ba zata ɗauka ba sai kuma tayi tunanin ko ƙiran yana da mahimmanci, hakan yasa ta ɗauka tare da sallama a hankali.
  Daga can ɓangaren taji muryar Nabeela cikin rawar kannan nata, ta amsa tana tambayarta aiki.
  Murmushin ƙarfin hali Mariya tayi tana faɗin.
"Allahamdulillahi. Ya karatu?"

"Lafiya lau sai wahala. Ga Ammina ku gaisa kullum ina ba ta labarinki."
Nabeela ta faɗa daga ɓangarenta, kafin Mariya tayi wani yunkurin ko magana ta ji ta zare wayar, ta ji muryar Dattijuwar mace tana mata sallama.
  A kunya ce cike da nauyinta Mariya ta amsa tana gaishe da ita. Ammi daga ɓangarenta tuni ta sake yabawa da nutsuwar Mariya, cikin farin ciki ta ce.
"Sai haƙuri da shiriritar Nabeela, kullum tana bani labarinki."

"Babu komai wallahi. Allah ya ƙara tsawon rai Ammi."
Mariya ta faɗa tamkar yadda ta ji Nabeela ta faɗa mata.
Ammi ta ji daɗin addu'arta sosai, ta amsa da amin ta bawa Nabeela wayar. Anan ta sake haɗata da Farah da Radiyya duk sai da suka gaisa sannan ta kashe, suna yabawa da hankalin Mariya don daga yanayin muryarta babu rawar kai da feleke suka ji.
...
  Mariya kam mamakin Nabeela take ganin yadda ta ɗauketa lokaci ɗaya, hakan yasa ita ma tayi saving number nata kafin ta mayar wayarta jaka ta fara aikinta, so take ta tattara shari'ar Isah Hamza ta damƙawa Barrister Waliy nan da gobe.
Sallar azahar ya ɗagata, ta fita ta yi sallah, ta siya abinci taci sannan ta dawo office. Tana zama ta ji sallama cikin muryarsa, da sauri ta ɗago tana amsawa suka haɗa ido, tayi saurin yin ƙasa da kanta.

"Biyo ni."Ya ce da ita yana juyawa ya fita.
Babu musu Mariya ta miƙe ta ɗauki handbag ɗinta tabi bayansa.
   Wajen parking ta ga ya nufa, ita ma ta ƙarasa zuwa wajen daidai ya buɗe motarsa ya shiga, zagayawa ta yi ta buɗe ta shiga don ta san yace zasu fita tare mai yiwuwa akan aiki ne, hakan yasa tabi sa.
Bayan shigar Mariya ta kulle ƙofa ta gyara zamanta, Barrister Waliy ya yi riverse yaja motarsa suka fita a ma'aikatar.

  Yaya Haydar yana cikin motarsa yana kallon su tin fitowarsu ransa a haɗe, idan ransa yayi dubu ya ɓaci.
Da safe ma ya ganta ta shiga office ɗinsa, yanzu kuma ya gansu sun fita tare. Leɓbensa ya cije kamar zai huda su, a ransa ya kudura niyar zai yi maganinta idan shi ne, sai ta gwammace tabar aikin da hukuncin da zai mata yau idan sun koma gida.
...

  Mariya da Barrister Waliy bayan fitar su wani waje ta rakasa akan wani shari'a da yake dubawa, sun ɗan ɓata lokaci sannan suka kamo hanyar office.
  Shuru cikin motar kamar yadda suka zo, sun kusa isa taji maganarsa ya ratsa dodon kunnuwanta, cikin sabuwar muryarsa da yake ba ta mamakin ashe yana da sanyin murya.

"Ya ku ka yi da Barrister Aliyu?" Ta ji ya tambayeta.
Ita ma a hankali cikin sanyin muryarta da yafi nashi ta ce.
"Bai ce komai ba."

"Ok fine." Ya faɗa yana ci gaba da tuƙi. A haka suka isa court, bayan ya yi fakin kafin Mariya ta fita ya sake tambayarta."Ya maganar case biyun da na ba ki? Ga shi har gobe Friday."

"Gobe zan kawo ɗaya." Mariya ta faɗa mishi, da sauri ta fita a motar ganin mutane suna wucewa suna kallon su.
  Shi ma fita yayi daga nan kowanne ya nufi office ɗinsa.
  Mariya tana shiga sosai ta dukufa akan case ɗin ganin yana nema, ta kammala komai ta ajiye a guri mai kyau, akan gobe za ta ba shi ya duba kafin Monday.
  Ƙarfe biyar da minti goma tabar office lokacin duk kowa ya watse a ciki sai ita, ita ma lokaci ta ƙara gudun ta fita ta haɗu da Yaya Haydar, ko ta koma gida ya ganta ya ce ta yi saurin dawowa.
  Ai kuwa babu motarsa alamar ya tafi, haka ta fice zuwa bakin hanya, napep ta tara ta shiga zuwa gida, bayan ta isa ta biyasa ta sauƙa ta shiga gidan.
  Motarsa kaɗai a filin gidan babu na Abba, addu'arta ɗaya Allah yasa ba ya falo. Da ƙyar ta shiga falon da sallama a bakinta.
  Falon tsit babu wanda ya amsa mata inda ta tabbatar yana nan, zuciyarta ce ta buga wanda ta jima da sabawa da hakan indai akan Yaya Haydar ne, tasan dalilinsa wataran zuciyarta za ta yi bugawar da ba zata sake amfanuwa ba ko yayi ajalinta.
Shi kaɗai ne zaune a falon sai ƙarar TV yana aiki, can dining Umma ce da alama wani abun take yi.
  Mariya durƙushewa tayi har ƙasa, cikin tsoron me zai biyo baya ta ce.
"Sannu da hutawa Yaah Haydar."

"Bar kaina." Ya faɗa mata a tsawa ce.
Babu shiri Mariya ta miƙe tana wucewa ɗakinsu. Ita kam ta rasa me ta tsarewa Yaya Haydar, ba ya ko amsa gaisuwarta daga hantara sai faɗa.
  Numfashi ta sauƙe ta cire baby hijab ɗinta, ta cire coat na sama ta rage daga ita sai rigar sama da dogon wando. Botilar rigarta ta fara cirewa har ta yi rabi daidai na kirjinta ta balla.
Buɗe ƙofar ɗakinsu ta ji anyi, tsammaninta Ummi Aisha ce don ba ta ga alamar Haneefa ta dawo ba, ba ta juyowa ba ta ci gaba da cire botilan, ta ce.
"Akku ina kika shiga?"

  Damƙar gashin kanta da yake parke mai cika da tsayi ta ji anyi ta baya, cikin mutuƙar jin zafi ta bar cire rigarta ta riƙo hannun wanda ya damƙa, da ƙyar ta juya suka haɗa ido da Yaya Haydar fuskarsa a mutuƙar ɗaure.
  Kirjinta kaɗan ya faso ya fito, tuni ta nemi jin zafin da take ji ta rasa, sai neman jin me ta aikata mishi don ba ta hango tausayinta a idanuwansa ba.
  Idanuwanta cike da hawaye tana girgiza kanta da ƙyar don azabar zafi, ta fara faɗin.
"Don Allah Yaah Haydar kar ka dake ni, don Allah ka sakar min gashina zafi yake min."

  Sake damƙa yayi don so yake ta ji zafin da yake ji shi ma a zuciyarsa. Mariya babu shiri ta saka mishi kuka, tana sake riƙe hannunsa ta ma ka sa magana.
  Yin shurunta yasa cikin muryarsa mai firgitata ya fara faɗin.
"Uban me tsakaninki da shi? Da ma maza kika fara bi ba aiki kike zuwa ba?"

  Da sauri Mariya ta dakatar da kukanta ta kalle shi, wani birkitaccen kallo ya watsa mata, ta ɗauke idanuwanta tana runtsewa cikin jin zafin maganganunsa hawayen ciki suka zubo.
  Sauƙar zazzafar mari taji saman fuskarta, babu shiri ta buɗe idanuwanta tana fashewa da kuka mai ban tausayi.

"Ba tambayarki nake ba?" Ya sake faɗa yana riƙe gashinta da ƙarfi.
Cikin kuka Mariya ta buɗe baki da ƙyar ta ce. "Aiki muka fita tare, amma babu komai tsakaninmu na rantse da Allah."

  Sakin gashinta ya yi ya turata ta yi baya, da sauri kuma ya fizgota ta faɗo jikinsa ya riƙeta gam ganin za ta buge kanta da gado, kuma za ta ji mummunar ciwo.
  Mariya gaba ɗayanta ta faɗa kirjinsa cikin tsoro tana riƙe shi, hannayenta ya sauƙa a wuyansa ta riƙosa da kyau don ita kanta ta tsorata da faɗuwar da za ta yi.
  Yaya Haydar yana jin yadda take fitar da numfashin tsoro yana sauƙa mishi, ga tudun kirjinta ya tokare shi, hakan yasa ya janyeta jikinsa cikin sauri.
  Babu shiri Mariya ta durƙushe ƙasa tana ci gaba da kuka. Yaya Haydar rankwashi ya sake sakar matar a tsakiyar kanta da ya sake sata sakin wani ƙaramin ƙara don zafi.
  Daga haka ya juya ya fice cike da jin haushinta, yaso ya mata dukan da yafi haka da Umma bata nan, amma yanzu yasan yana farawa kukanta zai jawo hankalin Umma, kuma yanzu ta gama mishi maganar marin da ya yiwa Ummi Aisha ranar.
  Mariya sai da tasha kukanta sosai sannan ta miƙe, ribbon ɗin kanta ta cire ta baza gashinta don yadda kan yake mata zafi sosai. Kayan jikinta ta cire ta wuce bathroom, shower ta sakarwa kanta ruwa ya fara jikata sosai musamman kanta da har ya fara ciwo.
  Tsawon mintuna kafin ta yi wanka ta ɗaura alwala ta fita, ta saka riga marar nauyi ta gabatar da magriba jin ana ta ƙira.
  Bayan ta idar ta cire hijab ɗinta don kanta a jike yake, ta baza gashin yasha iska. Kanta ta jinginar da gado ta lumshe idanuwanta da suka ɗan kumbura don kuka.
  Yanzun ma zuciyarta tayi rauni, kuka take son yi. Komai ya fita a kanta a rayuwarta, lokaci yayi da za ta cika burinta da mafarkinta ko zata samu salama da kwanciyar hankali a rayuwarta.
'Sai dai ta ya? Ta tambayi kanta.
"Dole sai da taimako wani ko wata don ita ɗin har yanzu ba ta zama cikakkiyar lauyar da zata tsayawa kanta ba."
  Ta faɗawa kanta tare da tsunduma tunani har lokacin idanuwanta rufe. Da sauri ta buɗe idanuwanta jin wanda zuciyarta ta ambo mata takai kokon bararta wajensa.
  Haka har dare ya shiga tana tunani a ɗaki ta ƙi fita, duk yunwar da yake cinta ta kasa fita gudun gamuwa da Yaya Haydar, sai dai ta sha ruwan tap na bathroom ta fito.
  Ƙarfe tara ta gabatar da sallar isha'i ta haye gado ta kwanta, tana mamakin ina Ummi Aisha ta shiga, ba ta ji ko surutunta ba balle motsinta, ta san da Haneefa tana nan sai ta kawo mata abinci har ɗaki, amma ita ma ba ta nan.
  Nan ta ji tsoro ya kamata ganin ita ɗaya a ɗakin za ta kwana, abin da tun da ta yi wayo ba ta taɓa bari Ummi Aisha ko Haneefa su barta ita ɗaya ta kwana ba.
  Ji take kamar ta fita ta nemo Ummi Aisha ko ta tafi ɗakin Umma ta kwana ko nasu Maryam, amma ta ka sa hakan don ba ta saba kwana a ɗakin Umma ba, hasalima basa kwana ko da wasa dukkansu yaran, gwara ma Ummi Aisha tana kwanciya wani lokaci.
  Tun tana zuba ido don jiran zuwan Ummi Aisha har bacci ya ɗauketa. Ga yunwa ga tsoro, amma da yake a gajiya take ga kukan da tasha tuni wani bacci mai nauyi ya kwasheta.

  A hankali ta ji ana shafa mata kirjinta cikin wani irin salo, motsi ta yi ta juya tana gyara kwanciyarta sai dai ji tayi tamkar ba a saman gado take ba. Hakan yasa ta sake juyi za ta yi magana ta ji bakinta a rufe gum.
  A tunaninta cikin mafarkinta ne da ta saba, hakan yasa ta fara shure-shure don ta farka amma sai ji ta yi an rirriketa da ƙarfi ana ci gaba da shafarta musamman kirjinta, hakan ya tabbatar mata da a gaske ne a zahiri yau komai yake faruwa.
  Cikin mugun tsoro da ya ziyarci zuciyarta da ilahirin jikinta ta ci gaba da turjewa, tana shure-shure da neman kwatar kanta, ta ka sa ihu don bakinta a rufe sai nishi take. Hakan da take tamkar ƙara ingizawa take, ba zato take ta ji an ɗaga doguwar rigarta sama.
Cinyoyinta ne suka bayyana duk da a duhu ne, Allah ya taimaka mata da pant a jikinta, hakan yasa aka sakar mata jiki aka fara ƙoƙarin jan panta nata ƙasa.
  Wannan damar yasa ta kai hannunta ta zare abin da aka toshe bakinta da shi, ba ta yi ƙoƙarin hana janye pant ɗinta ba ta daddage ta fasa gigitacciyar ƙara da ya saka mai cire mata pant dakatawa.
  Hasken wuta da aka fara kunnawa a gidan tare da tahowar takun mutane wajen yasa aka ɗagata tare da barin gurin da sauri. Mariya kuka ta sanya da ƙarfi ta janye pant ɗinta ta mayar.
   Yaya Haydar da Abba kusan tare suka iso wajen jin inda ihun ya fito, bayan su Umma sai Maryam da Khadeeja da sauran maza da suka ji suka fito su ma cikin tsoro.
  Mariya ganinsu yasa ta sakin wani ƙara ta sume a kwancen da take. Abba da Yaya Haydar har rige rige suke na isa wajenta cikin tsantsar mamakin me ya kawota nan, ga ta kuma birkice ga ta sume.
  Abba yana shirin ɗagata cikin tsorata Yaya Haydar ya hanasa ya ɗagata cikin jarumtar da ya sakawa kansa, cak ya ɗauketa ya nufi falon Umma da ita, a saman kujera ya ajiyeta ya ɗaura kanta saman cinyarsa. Hannunsa saman fuskarta yana ɗan bugawa alama ta farka.
  Umma da sauri ta ƙarasa dining ta ɗauki goran ruwa ta dawo, Abba ya karɓa ya buɗe ya yayyafa mata. Ko motsawa ba ta yi ba, hakan yasa Yaya Haydar karɓar goran ya tultula mata ruwan a fuskarta.
  Mariya numfashi ta ja a gigice tana neman miƙewa, Yaya Haydar ya riƙota jikinsa yana faɗin.
"Ke ki nutsu."

  Jin muryarsa yasa ta ɗan nutsu tare da kankameshi iya ƙarfinta. Bai hanata ba don yasan tana cikin tsoro ne amma da tuni ya janyeta. Luf ta yi tana sauƙe numfashi cike da tsoro.
  Ya kalleta yaga rigar jikinta duk ya manne a jikinta ya fito mata da jiki, kuma babu hijab gashin kanta duk ya hargitse. Idanuwansa ya ɗauke da sauri ya kalli ƙannensa ya ce.
"Ku je ku kwanta."

  Don tsoronsa yasa suka bar wajen. Yaya Haydar ya kalla Abba da Umma ya ce. "Abba kuma ku kwanta dare ya yi sosai."

  "Amma Aliyu me yake faruwa da ita? Dubeta ka ga? Me ya fito da ita cikin wannan dare? Ganta gaba ɗaya a hargitse take."
  Abba ya faɗa yana kallon Mariya cike da tausayinta. Shi kam ya so ayi maganar yanzu don jin me ya sameta a wannan dare.
  Umma ita ma ta ƙara da faɗin. "Gaskiya kam? Mariya me ya sameki?" Ta tambayeta cikin tashin hankali, ta rasa wani irin tunani za ta yi akan fitowar Mariya zuwa bayan ɗakunan su cikin wannan dare, abu kamar aljanu.
'Ko dai su ne.' Ta tambayi kanta tana ƙara kallonta.

  Mariya shuru ta yi ta ka sa magana, hakan yasa Yaya Haydar ɗagota yana kallon fuskarta yaga idanuwanta a runtse. Kallon su Abba ya yi ya ce. "Zuwa safe ku yi maganar."
     Daga haka ya miƙe yana miƙar da ita suka bar wajen, ita kam da ƙyar take tafiya don jikinta ciwo kamar wacce ta yi mugun dambe.
  Gefe ɗaya kuma mamakin Yaya Haydar ne ya cika ranta ganin ya ƙi maganar gaba ɗaya, uwa uba yadda ya yi wani bake-bake ya hana kowa ko tambayarta, sai ma kulawar da ya nuna mata.

#vote
#comment
[06/06, 7:28 pm] Pharty BB: GOBE DA NISA
Page 10
Na Pharty BB

Mariya gani ta yi Yaya Haydar ya nufi ɗakinsu da ita, da sauri ta tsaya turus cike da tsoro, ba za ta iya kwana a ɗakin nan ita ɗaya ba, gani take za a sake zuwa mata.
 
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment