Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[8:22am, 10/3/2016] Fatyma Zahra Too Nv: Fertymerh Usman > fertymerh xarah novels
1) MULKI KO SARAUTA?
Na fertymerh xarah
Danqareriyar motace tayi parking harabar gidan,
yanayin parking din motar xai tabbatar ma ranta
a bace yake da sauri ta fito ta nufi cikin gidan
batare da ta kula da mutanen dake xubewa qasa
wurin gaidata ba
a babban falo ta taradda mahaifiyarta tare da
maaikatan gidan , ta shagwabe fuska kamar
xatayi kuka
tace ammi kinga yaya Aliyu ya hanamin sakewa a
party ya hanamin sukuni duk yabi ya takuramin
saboda kawai nasan wadannan kayan shine yace
sai na dawo gida.........sai hawaye sharrrrrrrr
ammi ta dubi shigarta kafin ta maida kallonta ga
aliyu dake shigowa falon
tace Aliyu ko meye damuwarka akan shigar auta
yace ammi da kanki kike wannan mgnr bayan
kinsan wannan shigar bata kamace taba tana
musulma, ammi ta bata rai tana kallon Affiya
tace auta yi haquri kibarsa, jeki cnxa kayan ko ki
dora jallabiya akai, affiya ta tunxure bakinta tayi
kwafa tafice falon tana qunquni
Aliyu ya xauna a luntsumemiyar kujerar dake
falon yana kallonta
yace ammi duk kece ke saganta yarinyar nan wlhy
tace menene riba idan na hana mata yin abinda
takeso a rayuwarta, yayi shiru ganin ta sauya
fuskarta
yace gobe xnje kaduna auren amir idan baffa ya
sauko ki sanar dashi
ta gyada kanta
tace Allah ya kai lfy
ya amsa da amin bayan ya maida idanuwansa ga
t.v
2
TUSHEN LABARI
Alhaji Ahmad merah wanda akafi sani da sarkin
xamfara, yana xaune abuja tare da iyalinsa yana
da mata biyu hjy xainab da hjy hadixa
hjy xainab yayace a gurin hjy amina (mahaifiyar
affiya da aliyu) tana da ya'ya biyu Aiman da
rumaisa
sai hjy hadixa dake da ya'ya uku duka mata
asmau sumayya da firdausi (duk sunyi aure
kasancewar sun girmi su aiman da rumaisa)
gidansu qaton gidane kamr unguwa, gidane da
yawanci mutane kewa laqabi da aljannah duniya
kasancewar dukiyarda aka narka a gidan ga kuma
sarauta
*
[8:54AM, 10/15/2015] Pherty: Alhaji usaman
wanda akafi sani da president mahaifine a gun
affiya da aliyu matarsa dayace hjy amina(qanwar
hjy xainab mahaifiyar aiman da rumaisa) asalinsu
shuwa'arab ne
Alhaji Ahmad da Alhaji usman abokan junane
shiyasa sukayi alqawarin aurad da ya'yansu
batare da sanin juna ba kasancewar aiman na
karatu a pheonix
yarima aiman wnda akafi sani da prince a
pheonix yana gab da kammala karatunsa na likita
yafito amatsayin Dr.Merah wannan shine burinsa
mutum ne miskilin gaske maiji da kansa maiji da
qasaita da sarauta
saboda miskilancinsa abinda bai shafe shi ba
baya shiga kuma yana da kafiya da naci akan duk
abinda yasawa gaba yana da tabbacin sai ya
samesa
mata da yawa na matuqar qaunarsa suna yawan
kawo kansu garesa saboda kyawunsa da ynda
yake tfyr da qasaitarsa
3
Bai taba shaawar ko daya daga cikinsu ba
saboda ba halinsa bane neman mata acewarsa
ma mata basa birgeshi sunfi bashi haushi shiyasa
da yawa yake bata lokacinsa da tunaninsa a
library yana karatu
bai taba so ba, bai taba fadawa akan soba, bai
san menene so ba bai dauki so da daraja ba ya
daukeshi tamkar damuwa da bacin rai ne shiyasa
baya sa kansa aciki yanajin haushin mutane dake
bata lokacinsu akan soyayya suke bata tunaninsu
da xuciyarsu akan so
[9:04AM, 10/15/2015] Pherty: wani abune da
xuciyarsa da gangar jikinsa sun kasa gasgasta
masa muhimmancin so
bai damu da kallon films ba musamman na india
saboda haushinsu da yakeji yana gani aduniya ba
mutanen dana kaisu xama wawaye kamr ynda
suka maida kansu bayin mata
aduniya yafi bawa kwallo da karatunsa
muhimmanci haka duk tunaninsa da burinsa
nakan kwallo da karatunsa sune ya dauka rayuwa
sune yake gani kamar ginshiqin rayuwa hr yake
ganin idan babusu rayuwarsa ta xama useless ba
wai soyayya da kashi casa'in acikinta duk
yaudara ne
Hankalinsa da tunaninsa nakan laptop dinsa,
xuciyarsa ta soma yimasa xafi saboda yakasa
samun abinda yakeso ya duqufa neman hanyar
da xai sami amsar assignment dinsa
yaja dogon tsaki bayan ya kawar da laptop din
daga gefensa badan ya haqura ba sai dan
nemawa xuciyarsa sassauci daga xafin data
dauka
4
Assalamu Alaikum ta fada cikin siririyar muryarta
mai xaqin gaske, ya amsa sallamar sanin
muhimmancinta batare da ya dubi mai sallamar
ba saboda jin muryar macece
bata damu da rashin nuna kulawarsa ba tasan
sarai kowaye aiman merah taja kujerar dake kusa
dashi ta xauna fuskarta dauke da murmushi
[9:21AM, 10/15/2015] Pherty: tace sannu prince
bai amsa ba bai kuma kalletaba kuma bashida
niyar haka sai ya lumshe idanuwansa yana
tunanin ummansa wanda ya xama dole yaje gida
nigeria dan ganinta
tace aiman kaqi ka kalleni balle nasami damar
sanarda kai abinda k tafe dani
nan ma shiru yayi idanuwansa a lumshe
bata saduda ba taci gaba da fadin
idan kudi kake taqama dasu mahaifina nadasu
idanma kyawune nima inadashi amma meyasa
kake wulaqantani meyasa kake nuna halin ko
inkula agareni duk da dimbin soyayyar da bake
ma
sai alokacin ya ware manyan idanuwansa akanta
sai da xuciyarta na buga saboda tsananin
kyawun da yayi mata baqaramin tsaita hankalinta
tayiba saboda mutuwar jiki da kasala dana
saukar mata
kallonta yake yanason gane wani abu atare da ita
ba abibda ya fahimta illah ita farace kyakkyawa
mai kaurin jiki gajera amma duk bata birgeshiba
ya dauke dubansa gareta ya rasa da wace kalma
xai mata mgn saboda baisaba da doguwar mgn
ba
ya soma kwashe manyan wayoyinsa da system
dinsa ya tashi xai bar wurin itama tayi saurin
tashi
5
tace koda baxaka aureniba ya kamata atleast ka
bani lokaci na nunama irin soyayyar da nake ma
kasoni koda na dan wani lokaci ne pls prince.....
ta fada idanunta taf da hawaye saboda axabtuwa
da take da qaunarsa sai alokacin yasami damar
mgn
yace kinga nayi kama da mutumin bnxane
tayi saurin girgixa kanta
yace kinga ina neman matane
nan ma girgixa kanta tayi
yaja dogon tsaki
yace ke banxa dake kina a hakan kike neman da
soyayya
tace nice banxa aiman
yace eh an fada idan k ba banxa bace meyasa
kike kai kanki ga namiji
tace laifine dan na nuna ma so aiman
[9:51AM, 10/15/2015] Pherty: yace so?
ta gyada kanta tana kallonsa
yayi murmushin dana qara fito da kyawunsa karo
na farko kenan a shekarun da ta hadu dashi a
skul din data ga murmushinsa
sai dai taganshi yana waya yana murmushi ko
idan yana tare da abokansa hakan yasa taji
matuqar farinciki a xuciyarta hr batasan lokacin
da tasaki murmushi ba a tunaninta murmushinsa
na nuna amincewa ne akan soyayyarta
ya katse tunaninta ta hanyar fadin baki gayamin
sunanki ba
tace aiman shekara biyu da haduwanmu amma
kace bakasan sunana.ba
ya tabe bakinsa ya juya xai fice alamar ko
ajikinsa tayi saurin shan gabansa
tace tsaya kaji pls sunana Nabila Moh'd, ya
gyada kansa kafin
6
yace nabila kiyi haquri aiman baisan meye so ba
baya son kuma yasani,
nayi matuqar mamakin yanda kika bawa soyayya
muhimmanci har kike xubar da mutuncinki da
darajar ki akan soyayya
what a shameless ya fada yan tsina fuskarsa tare
da kallonta a qasqance
xn gayamiki kifita hanyar aiman kibar xuciyar
aiman karki takuramin ki cnxamin ra'ayi pls
dont mean to hurt you idan kuma xuciyarki ta
tsananta akaina xn tausayamiki for only
friendship shima bawai xamu kasance tare
bane....nooo just xamu dinga gaisawane a hanya
shina ba kullum ba
da fatan my request will be accepted bai jira
amsar tab ya juya ya fice
[10:01AM, 10/15/2015] Pherty: itama xuciyarta
cike da qunci ta fice kamar ta fashe da kuja dan
baqinciki....
cike da isa da qasaita yayi parking din morarsa
ya fito da sauri securities da fadawa suka soma
xubewa qasa suna gaidashi
idan da sabo sun saba sunsan waye aiman .
yarima mutum ne dako gaisuwa wuyar amsawa
take a bakinsa sanin da sukayi masa ko sun
gaidashi ba amsawa yake ba shiyasa basu damu
daya amsa ba ko kar ya amsa
7
ya shiga cikin gidan batare daya kulasuba
ballantana ya amsa gaisuwarsu
toilet ya nufa yayi wanka ya fito yana tsane
kansa da qaramin towel cike da tunanin nabila
yana mamakin yanda xamani ya cnxa aynxu inda
mata ke bibiyar maxa saboda soyayyar bnxa
ya lura matan ynxu basuda aji shi baxai so mace
a rayuwarsa ba saboda rashin muhimmancinsu
agaresa
yaja tsaki cike da takurar haduwa da nabila ya
tsani yarinyar sosai ya soma shirya kayansa cikin
mintuna qalilan ya gama shirinsa ya nufi airport
dan xuwa nigeria
[10:24AM, 10/15/2015] Pherty: Tunda ya shigo
gidan ma'aikata ke xubewa suna gaidashi
sarki yayi mamakin dawowarsa dan bai sanar ba
yace yarima kodai da matsala ne irin wannan
xuwan baxata ba sanarwa
ya girgixa kansa yana yatsina fuskarsa
yace ba komai abba, nagaji 3wks kawai xnyi na
koma, maimartaba ya gyada kansa kawai
umma ma cike da mamaki take kallonsa
tace yarima koda damuwa ne atare dakai
yace nima i just decided to come today, inaso
naxo naga umma na yafada yana murmushi
itama murmushi tayi, rumaisa dake xaune gefe
tana kallonsa ta yatsina fuskarta
tace yaya maina nida ba'aso ba'ayi missing dina
ba sai arufe idanuwa daga kaina
batare da ya kalletaba ya janyo ice cream din
datake sha ya soma sha yana fadin
waya gayamiki hakan, inason ganinki sosai kin
manta ke kadaice qanwata dana keda bayan
firdausi
ta tunxure bakinta alamar shagwaba, ya kalleta
yaja hancinta yana fadin sorry sister bayan ya
tashi tsaye
yace umma xnje shan ice-cream rumaisa ta
kwadaitamin da wannan
ta gyada kai tana murmushi
tace adawo lfy ya juya yana murmushi ya fice
8
Tafito sanye da doguwar riga ta shadda tayi
matuqar fito da kyawunta wani siririn gyale ta
yana a kanta kasancewarta yarinya mai son
kwalliya yasa tafito sosai
a makeken falonsu ta taradda mahaifanta xaune
baffa yace kai kai kai auta wannan kwalliyar fa
sai kace xaki gasar sarauniyar kyawawa
murmushi tayi tana kallon Aliyu
tace yaya zan samu kadan kaini nasha ice-cream
ammi tace bayajin dadin jikinsa
ta qarasa inda yake ta riqo hannunsa
tace sorry cwt yaya
batare da yayi magana ba yaciro makullin
motarsa ya bata ta karba tana kallon baffa
baffa xnje shan ice cream
yace tor auta adawo lfy kisanardasu john acika
mota uku da bodyguards su rakaki shan ice
cream
ta gyada kanta tafice
*
[10:55AM, 10/15/2015] Pherty: Tafiya suke
ahankali motocinsu a jere a titi hr suka qaraso
wurin
tan daga cikin motar a xaune suka fito da sauri
suka bude mata motar
ta dade a xaune kafin ta fito da qafafunta masu
dauke da xanen baqin fulawa da surkin ja
ga mamakinsu suna qoqarin shiga aka tsaidasu
wai baxasu shiga ba
menene dalili ta tambaya fuskarta da alamar
tambaya
saboda MAINA DAN SARKI yan ciki
ta gyara tsayuwarta tana kallonsu a wulaqance
tace ni AFFIYA YAR PRESIDENT nace baxan
jirashi yafito ba saboda dai dai nake dashi abinda
yake taqama dashi nima inadashi
ta juya ga mutanenta
tace sujirata batare da tunanin komai ba ta kutsa
kai ta shiga ciki
9
A hankali take taka matattakalar benen shop din
tana tfy kamar bataso hr ta isa qofar tashiga
bata ankaraba sai jinta tayi ta fada ajikin mutum
shi kuma lokacin xai fito
da sauri taja baya shima yaja baya suna kallon
juna
yace ke bakida hankali ne bakisan da mutane
bane kike qoqarin fada masu a jiki, bakisan
kibada haquri bane
kallonsa take a wulaqance
tace dani dakai waxai bawa wani haquri kana
tunanin haqurina na xuwa akan kowane
ya tsuramata ido cike da mamaki dan mace bata
taba tsayawa tagayamasa mgn irin wannan ba
yace ke wacece acikin garinnan mekike taqama
dashi waye mahaifinki a fadin garinnan
murmushin takaici tayi saanan tayi taku daya
biyu uku ta juyo tana kallonsa fuskarta a murtuqe
tace ni mace dayace tamkar da dubu acikin
garinan bana taqama da komai face ilimina
mahaifina ba kowa bane face bawa agun
ubangijinsa
a wulaqance ya jefeta da kayan dake hannunsa
yace shiyasa naga kinxo maula anan kiyi haquri
da wannan ya juya xai fice cike da bacin rai
tasha gabansa ta xare siririn glass din dake
manne a idanuwanta tana kallonsa cike da bacin
rai
tace kayi kuskure a rayuwarka ka kuma manta ko
wacece a gabanka inaso kasani kuma kasa a
ranka affiya tafi qarfinka nesa ba kusa ba ni ba
ajinka bace kuma ba neman kai nake da kayaba ,
me kake taqama dashi MULKI KO SARAUTA?
SARAUTA ya bata amsa yana kallonta
[11:10AM, 10/15/2015] Pherty: yace kinga kuwa
tayi wa mahaifinki nisa kuma kinsan ni nafi qarfin
yinki bakida wata daraja da idanuwana xasu
dubeki dashi
ranta yayi matuqar baci xuciyarta ta soma xafi
tace mahaifina yayima nisa kai kanka ballantana
wata sarauta tak ta banxa...... tas kakeji ya
dauke fuskarta da mari ransa a bace
ta dafe kuncinta tana kallonsa dai dai lokacin da
ya xare baqin space din dake idonsa kallo daya
xaka masa kaga bacin rai a tare dashi amma duk
da haka kyawunsa qaruwa yayi ya nuna ta da
dan yatsansa
yace sarauta ba sa'ar yinki bace ki koma inda
kika fito kiyi tmbya akan sarautar merah ciki
kuwa hrda tmbyr ko waye maina aiman
ya maida glass a idonsa ya juya ya fice xuciyarsa
cike da qunci
itama sai ta rasa mexatayi sai ta juya tabar
wurin
10
Suna isa harabar gidan ta fito da sauri kai tsaye
dakinta ta nufa ta soma safa da marwa a
tsakiyat dakin hannayenta goye a bayanta
xuciyarta sai xafi take mata abinda bata taba
karo dashiba wai namiji ya mareta sai takejin
kanta wata iri kamar ba itaba
wlhy sai ta rama sai tayimasa abinda baxai
manta da itaba idanma sarauta ce itama ai tana
da alaqa da ita shi wace sarautar ce yake taqama
da ita
taja dogon tsaki dai dai lokacin hawaye na xubo
mata sai ta rama wlhy baxata barshiba yaci
bulus ya daki banxa
*
[11:17AM, 10/15/2015] Pherty: Anashi bangaren
suna isa gida wanka yayi ya shirya cikin qananan
kaya ya nufi garden wurin shaqatawarsa
ya xauna cike da damuwa xuciyarsa na quna
sakamakon yarinyar daya hadu da ita fitsararriya
ya lumshe idanuwansa a ransa tunani yake ko
wacece wannan yarinyar data kira kanta affiya,
metake taqama dashu waye mahifinta a fadin
abuja da hr xata raina sarautar mera
a iya saninsa da xamansa a skul ba a taba ci
masa mutunci kamr irin na yau ba bai taba
haduwa da macce marar tarbiya ba kamar ta bai
kuma taba sanin akwai macen daxata masa
rashin kunyaba kamar ita
nan da nan idanuwansa suka cnxa launi xuwa ha
saboda bacin rai
dolene ya dauki mataki akanta
dolene ya nuna mata kuskurenta domin sai yayi
mata abinda baxata taba mantashi ba
nan da nan ya soma samun nutsuwa a xuciyarsa
daya tuna marin da yayi mata koba komai taji
haushi yaga bacin rai atare da fuskarta shikuma
yaji dadin hakan
ya qara lumshe idanuwansa yana karanto
fuskarta
fuskarta mai laushi da tsantsi
a qasan xuciyarsa ya furta she x also beauty.
Hausa novel
[8:22am, 10/3/2016] Fatyma Zahra Too Nv: Fertymerh Usman > fertymerh xarah novels
[10:31AM, 1/30/2016] Pherty: 11 Mulki ko
sarauta
Na fertymerh xarah
Dariya yake sosai yana kallonta (wannan kenan
idan kaga murmushinsa ko dariyarsa yana tare da
ummansa ne)
yace umma kidaina wannan mgnr amma kinsan
rumaisa tanaso ta raina ni ne
rumaisa ta qare tunxure bakinta tana kallon
umma
umma kice yadaina bana so kofa agaban
qawayena xai daure fuska ko sun gaidashi hannu
kawai yake daga masu baya amma baya amsawa
sai su riqa cewa yayana bayada faraa basu taba
ganin dariyarsa ba he x not friendly dan Allah
umma kice ya gyara halinsa
yace tor ni sa'ankine da xnje cikin qawayenki ina
dariya
umma tace kai yarima kagayamin idan qanwarka
batayi farinciki dakai ba dawa xatayi
[1:04AM, 10/20/2015] Pherty: Idan bata sami
fuskarka ba tawa xata samu ya dauke dubansa
gareta da alama mgnr ta soma tunxurashi, ta
cigaba da fadin
bakaga ya'yan gwaggwonka ba,Aliyu da affiya ba
haka suke ba,aliyu yana bata lokacinsa saboda
affiya, duk lokacin da kaje gidan xaka samesu
tare inma nan gidan xasu xo tare suke xuwa
yace wai umma affiya na nan kuwa?
tace tor ina xataje bakason xumunci taya xaka
gane tana nan ko bata nan
yace ohhhhh umma kidaina min haka pls kullum
muna tare da aliyu, ko jiya tare mukaje nagaida
ammi amma banga affiya ba, kuma ban tambaya
ba kada yarinyar ta xata na damu da itane
ta tsura mishi ido cike da mamaki al'amarinshi
yafara bata tsoro halinsa daban ne dana kowa a
xuri'arsu
12
yace umma tayi girman rumaisa kuwa?
tace girmansu daya amma rumaisa xatafita jiki,
ya tabe bakinsa
yace chab, tor dan Allah umma kigayawa sarki a
hadata da ita da rumaisa amasu aure tunda sun
girma
tace kayi masu.mijine
cike da mamaki yace umma kamar wadannan ace
basu da samari haba dai umma yanda mutanen
nigeria suka bawa soyayya muhimmanci suke
bata lokacinsu da tunaninsu akan mace sannan
ace ba mai sonsu
tace ita rumaisa aliyu xata aura
affiya fa? ya tambaya
tace ita kuma yarima xata aura
nan da nan ya daure fuskarsa annurinta ya kau
idanunsa nayi ja abin yayi matuqar basu mamaki
dan har tsoro sukaji
[1:15AM, 10/20/2015] Pherty: tace yarima lfyrka
kuwa
batare da yayi mgn ba ya tashi yabar dakin,
rumaisa ta kalleta
umma yaya aiman fa idan ana negative yana
positive, yana abu kamar ba mutum ba dan Allah
umma xai tabbata baiyi aure bane?
ta girgixa kanta tana fadin
ina tsoron kada tunanina ya xama gsky amma
mgnr aure duk tare xaa hadaku
13
yana fita dakin wurin jakadiya ya nufa ya xauna a
kusa da ita yana fadin
baba rakiya kigayamin soyayya dolece
tace a'ah amma ai real ce ga kowa, ya girgixa
kansa
yace bandani baba, ni narasa gane yanda mutane
suka dauki soyayya wata aba alhali maxan da
matan duk suna yaudarar junansu ne, tayi sarin
katsesa
tunaninka kenan uban gidana amma ko wacce
rayuwa ginshiqinta soyayya da aure
ya tabe bakinsa
baxaku fahimceni bane saboda kun taso cikin
soyayya kunyi gini akanta, amma ni naxo ina
neman alfarma gareki jakadiya
jikinta na rawa ta sunkuya
tace ni ranka shi dade, kafadi ko menene xnyima
yace ynxu nakeji magana a bakin umma da gske
affiya xaa aura min?
[1:24AM, 10/20/2015] Pherty: ta gyada kanta
tace eh! ai affiya ba ruwanta yarinyar akwai kirki
yarima
ya tsuke fuskarsa
yace tor da ixinin wa nace ina sontane daxaa
auramin ita inaso kigayawa sarki cewa bana
sonta baxan aureta ba
cikin tashin hankali
ta russuna qasa
tace Allah ya ja da ran dan sarki idan nayi ba dai
dai ba a yafemin nace kodai bakada lfy ne
ya soma taba jikinsa
yana fadin kinga nayi ramane ko wlhy wahalar
karatu ce
tace ba wannan nake magana ba
cike da rashin sanin abinda take nufi
yace wacce rashin lfy ce baba rakiya
tayi jim tanajin nauyin maganar
14
Tace al'amrin ka ke ban tsoro yarima bakason
mace kuma bakason aure shine nace ko bakada
lfy ne
yayi murmushi cikin jin kunya
yace sai marar lfy.ne kawai bayason aure
ta gyada kanta
yace tunaninki kenan amma ni garau nake
tayi ajiyar xuciya
tace taya kake tunanin xan yarda dakai?
ya xuba mata manyan idanuwansa
yace inaji saboda naqi aurene hr kike xargina da
wannan tor shikenan na yarda a daura auren
ta fadada murmushinta
tace ynxu naji.mgn har nake ganinka a mutum
[1:34AM, 10/20/2015] Pherty: yayi dariya sosai
yace ashe ba mutum kike kallona ba kin dauka ni
aljanine
ta russuna tana fadin tuba nake ranka shi dade
ynxu yarima nake kallonka
ya tashi yana kallon agogon hannunsa
yace lojacinki ya wuce kafin tayi magana tuni ya
fice
ta bishi da idanu tana kallonsa
tana son komai nasa duk abinda xaiyi a natse
yake yinsa yana da sauqin kai sai dai akwai nuna
MULKI DA SARAUTA bashida hayaniya miskilin
gaske ne shiyasa duka yaran gidan tafi shaquwa
dashi saboda kirkinsa
15
Yanayi ne na damina garin ya limshe kamar xaayi
ruwa iskace mai dadin gske take.kadawa
ta fito a farfajiyar qaton wani boutique tanufi
motarta tana qoqarin shiga ta tsinkayo motarsa
na shigowa
tayi mamakin ganinsa yau shikadai ba security ko
daya atare dashi hakan yasa ta ja ta tsaya tana
kallonsa dan xata rama wulaqancinta
dai dai inda take tsaye yayi parking din motarsa
ya fito ya nufi inda take tsaye ya xare madubin
idanuwansa yana kallonta sama da qasa a
wulqance
[1:44AM, 10/20/2015] Pherty: yace ashe ke
matsoraciyace fa baxaki iya tafiya ke kadai ba sai
tare da bodyguards saboda ni ko?
tayi murmushin takaici ta kawarda kata gefe
batarr datayi magana ba
bodyguards dinta dake gefenta sukayo kansa da
bindiga tayi saurin dakatar dasu
tace kubarshi, shine fa mutumin da ya mareni
danaje shan ice cream
16
nan john yayi kansa a harxuqe ya saita bindiga a
goshin aiman
yana tsae yana kallonsu fuskarsa a sake babu
wani alaar bacin rai ko raxana atare da shi kuma
ba fargaba a xuciyarshi, illah hakan datayi bata
birgeshi ba ko kadan
cikin tsawa john
yace kaci albarkacin madam datace ta yafema da
sai nayi qasa da kai amma duk da haka kabata
haqur.......yayi shiru sakamakon marin da aiman
ya daukeshi dashi
fuskarsa a yatsine yake kallonsa
yace waya gayama ana min ihu aka karka sake
mamaki ya cika john bakinsa a bude yake
kallonsa yana kallon affiya yana jiran umarninta
kawai ya daukesa da alburushi
aiman ya harde hannuwansa a qirjinsa ya jingina
da motarsa tare da lumshe idanuwansa yana
tunanin yanda kwallonsu xata kasance ayau
[1:50AM, 10/20/2015] Pherty: ta tsura masa ido
sai taga yayi mata wani irin kyau da kwarjini
abinda bata taba gani a sauran maxan ba yafita
daban acikin maxa
tayi saurin kawar da tunaninta
tace sorry john kabarshi nixan dauki mataki da
hannuna sai na nuna masa koni wacece a fadin
garinnan sai na nuna masa qarfin MULKI yafi na
SARAUTA
ta juya tana kallonsa shima ita yake kallo jin ta
ambaci sarauta
tace idan ba tsoroba kashiga wannan motar ta
nuna masa motarta inaso naje dakai inda xn
hukuntaka baxan lamuntama ba sai nama
hukunci dai dai da abinda kamin
fuskarsa dauke da murmushi
yana son sanin hukuncin daxatamasa shiyasa ya
bude gidan baya ya shiga ya kishingida cikin isa
da qasaita yana latsar wayarsa..
Hausa Novel
[10:37AM, 1/30/2016] Pherty: [4:16PM,
10/21/2015] Pherty: MULKI KO SARAUTA
Na fertymerh xarah
Ta juya ga bodyguards dinta
tace kushiga dayar motar kuhe gida xan sameku,
ta shige ta ta motar taja ta fuuuuuuuuu
tafiya sunkayi mai nisa batare da sun tankawa
juna ba kafin ta juyo tana kallonsa fuskarta a
daure
tace kayi shiru ashe kai matsoracine ashe duk
mulkinka isarka taqamarka duk na banxane tunda
kake taqama da sarauta
hmmmm kaga naci nasara a tarkona na biyu
haka nake fatan samun nasara a tarkona na biyu
domin in banbance ma tsakanin aya da tsakuwa
murmushi yayi yana kallonta ta madubin motar
alamar ko ajikinsa sam abinda tayimasa baiji
haushiba illah birgeshi da tayi bai taba haduwa
da mace qarama mai taurin xuciya kamar ta ba
yace akowane lokaci nawa tarkon xai iya riskarki
domin kixama acikin shiri nima xan banbance
maki tsakanin affiya da aiman
murmushi tasakeyi akaro na biyu ta juyo tana
kallonsa kafin ta maida hankalinta kan tuqin da
take
tace kasan shi kudi ba abibda basayi duk da
matsayin mahaifina a qasar nan, ni mace dayace
daya mallaka a rayuwarsa a kaina xai iya rasa
komai nasa dan ganin farincikina
kanagani akwai wani tarko naka da xai sanyani
fargaba gudan ni jinin mulki wacce ke ji da kanta
fagen kyau ilimi kudi da kuma MULKI, kaga kuwa
affiya ta xarce tunaninka
ya kyalkyace da dariyar da bai taba yi ba koda
kuwa agaban ummansa ne aransa yana son sanin
wane irin mulki ne take taqama dashi amma
girman kansa da ajinsa ya hana ya tambaya
domin gani yake idan yayi hakan tamkar
girmansa ya fadi ne agareta
@)
yace kina gani kudi na iya magance ko wace irin
matsala a rayuwa,
kin manta akwai abinda kudi baxasu iya
maganinsaba,kamar yanda kike taqamar k mace
dayace agun mahaifinki
[4:32PM, 10/21/2015] Pherty: haka nima namiji
dayane agun abbana,saboda tsananin son da
yake min dayanada iko ko numfashi baxai barni
nayiba sai dai yamin, kada kibari xuciyarki ta
yaudareki gun jayayya da dan jinin SARAUTA
maiji da qasaita
qasaitaccen murmushi tayi dai dai lokacin datayi
parking harabar wani danqareren gida mai kyau
da tsada wanda mahaifinta ya bata domin ta riqa
hutawa kawai aciki
ta duba taga yanda securitis suke tasan xasu
tambayeta inda tasamo yarima saboda kariyar
lfyta
shikuma yana kishingide hankalinsa a kwance
taxo ta bude masa qofar mota
ya dauki kusan minti talatin bai motsa ba bai
kuma kalletaba harta soma tsarguwa da gajiya da
tsayuwa sai taga ya xiro qafafuwansa waje ya
fito yana gyara alkyabbarsa, ta nuna masu dan
uwantane kafin subarshi ya shiga
tfy suke cikin hadaddun falon masu ktau da tsari
har suka iso wani bedroom ta bashi ixinin ya
xauna saanan ta dubeshi tana murmushi
tace 2 days kawai xakayi anan kafin na maidaka
inda na dauko ka, ba komai xanyimaba kawai
hankali xn koyama yanda xaka riqa respecting din
mutane musamman irina, karkuma ka damu da
motarka nasa a ajiye ma
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment